Koyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Ado Ahmad Gidan Dabino

0
85

Gabatarwa

Ado Ahmad Gidan Dabino yana daga cikin fitattun marubutan Hausa na zamani, waɗanda suka ba da gudunmawa wajen ilmantarwa da tarbiyyar al’umma ta hanyar rubuce-rubuce. Ayyukansa suna ɗauke da saƙonni masu cike da darussa na rayuwa, da koyar da kyawawan ɗabi’u musamman ga matasa da mata.

Ado Ahmad Gidan Dabino a Taƙaice

An haifi Ado Ahmad Gidan Dabino a Kano, kuma ya shahara wajen rubuta littattafan soyayya, zamantakewa da addini. Yana ɗaya daga cikin masu kafa “Soyayya Books” a cikin shekarun 1980s zuwa 1990s. Sannan kuma ya shugabanci ANA. Wato ƙungiyar Marubuta Nijeriya. Daga cikin sanannun littattafansa akwai:

  • In Da So Da Ƙauna
  • In Da Ruwan Zuma
  • Malam Zalimu

Koyar da Tarbiyya a cikin Rubuce-rubucensa

Tarbiyyar Addini

A cikin littattafan Gidan Dabino, ana samun koyar da imanin Musulunci, ibada, da gujewa haramci.

Misali:

  • A cikin Malam Zalimu, ya nuna muhimmancin amincin kasuwanci.
  • A wasu daga cikin rubuce rubucucensa, ya nuna sakamakon zinar aure da rashin kunya.

Tarbiyyar lyali da Aure

Ayyukansa suna koyar da yadda aure ya kamata ya kasance bisa so, fahimta, da mutunta juna.

Littafin In Da So Da Kauna ya bayyana cewa so ba ya wuce gona da iri, dole ne a daidaita tsakanin soyayya da tarbiyya.

Tarbiyyar Matasa

Marubucin ya yi nuni da yadda matasa ke fuskantar ƙalubale na zamani, kamar shaye- shaye, bin duniya, da son hawa-hawa. Ya gargaɗi matasa cewa su mai da hankali kan ilimi da gaskiya.

Tarbiyyar Zamantakewa

Ado Gidan Dabino yana amfani da labaransa wajen koyar da al’umma muhimmancin:

  • Hakuri da juriya a rayuwa
  • Girmama manya
  • Girmama mata da iyaye
  • Guje wa zalunci da ƙeta da kuma amfanin haɗin kai

Salon Koyarwarsa

  • Yana amfani da labarai masu jan hankali, amma a ƙarshe yana gargaɗi ne da nasiha.
  • Yana ɗora saƙon tarbiyya cikin maganganun jarumai a cikin labaransa.
  • Yana haɗa adabi da addini domin isar da saƙo cikin natsuwa.

Wanann bayanin an ciro shi ne daga maƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

Danna nan don karanta Koyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Bilkisu Ahmad Funtuwa

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceKoyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Bilkisu Ahmad Funtuwa
Labarin na GabaRubuce-Rubucen Talatu Wada Ahmed A Kan Tarbiyya
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.