Category: Littattafan Tarbiya

Mun samar da wannan ɓangaren ne domin samar da Littattafan tarbiya a cikin harshen Hausa a sauƙaƙe. Za ku iya kai wa gare su ta hanyar amfani da kwamfutoci ko wayoyin hanu.

wikiHausa ta kowa ce. Kowa zai iya taimakawa da ilimi ko gyara. Bugu da ƙari, kowa na iya amfani da wannan kafa wajan ɗora Littafi ko saukewa.

  • Amfanin Sanin Kai

    Amfanin Sanin Kai

    Kafin na yi nisa cikin wannan littafin, yana da kyau na fara kawo kaɗan daga cikin amfanin sanin kai ga kowanne mutum da yake da mafarkin rayuwa mai kyau.

    ❖ Sai Ka San Kanka Za Ka Ci Gaba

    Babu wanda ya zo duniya da sani, kowa a gidan duniya ya san duk abin da ya sani. Haka nan babu wani da yake samun ci gaba sai ya ci gaba da neman sani, duk wanda ya tsaya da neman sani daga nan rayuwarsa take ƙarewa.

    Za ka yi mamaki idan na ce da kai ‘ƴan gargajiyar da muke gani a yanzu masu ilimi ne a zamaninsu, sun ƙi yarda su karɓi ilimin sabon zamanin da suke ciki ne ya sa ake musu kallon ‘ƴan gargajiya. Haka duk wanda ya ƙi ci gaba da neman ilimi zai zama a zamanin gaba.

    Mene ne alaƙar ci gaba da sanin kai? Sai ka san kai wane ne da matakan da ka taka na ilimi kafin ka san inda za ka ɗaura. Wanda ya san bai iya turanci ba misali, ba zai yi karambanin karanta littafin turanci mai wahala ba, in kuwa zai karanta da wuya ya tsinci wani abu. Inda iliminka ya tsaya daga nan za ka ɗaura in ka san kanka, in ba ka san kanka ba kuwa za ka iya kamawa daga ko ina sai abu ya yi nisa ka ga ashe akwai wani giɓi a baya da ka baro.

    Sanin kai wane ne zai haska maka wuraren da kake da rauni, da wuraren da
    Allah ya maka baiwa, hakan zai taimake ka ka mayar da hankali wajen inganta baiwarka sama da ƙorafi a kan gazawarka. Wanda ya mayar da hankali kan inda baiwarsa take shi ne rayuwarsa take ci gaba ba wanda yake ta faɗi-tashi da rauninsa ba.

    Hakan kuwa ba lallai ya zo da mamaki ba saboda ƙa’idar ita ce: duk abin da aka mayar da hankali kansa shi ne yake ƙara girma da haɓaka.

    ❖ Za Ka Dena Haɗa Kanka Da Wasu

    Muna rayuwa a wani zamani da bayanai suka yawaita, abubuwan da muke karantawa, kallo da saurare ba ƙaramin tasiri suke mana ba a rayuwa, don haka muke shafe shekaru ma su tsawo a rayuwarmu muna kamanta kanmu da wasu, muna ganin cewa mu ma ya kamata mu yi rayuwa irin yadda suke yi, har ma mukan shiga damuwa a dalilin hakan.

    Wanda ya san kansa ba zai tsaya damuwa da kwatanta rayuwarsa da ta kowa ba, ya san me yake so, ya san ina zai je, ya san kuma hanyar da zai kama domin isa wurin, to yaushe zai tsaya tunanin wane ba haka yake rayuwa ba? Sanin kaina ya taimaka min sosai wurin rayuwa irin wacce ta dace da ni, zan ga mutane suna yin abubuwa, amma saboda abubuwan ba su shalle ni ba, ba na fatan na zama su, ina so ni dai kawai na fi yadda na ke a jiya.

    ❖ Za Ka So Kanka

    Son kai yana daga cikin abubuwa mafiya wahala a wannan zamanin, mutum ya ji yana ƙaunar kansa a yadda yake ba tare da jin haushin gazawarsa ba. Yana daga cikin dalilin da ya sa malaman tarbiyya suke ba wa iyaye shawarar su dinga nuna wa yaransu ƙauna, yaba musu in sun yi abin kirki, yaba musu a cikin mutane in sun yi bajinta, ba su ƙwarin gwiwa, rashin gwale su ko disga su, neman shawararsu da ba su dama su yi wasu
    abubuwan da kansu (Dr. Aisha Hamdan: Nurturing Eeman in children).

    Wanda ba ya son kansa ba zai taɓa tsinana komai ba, zai cika kansa da tunanin gazawarsa da rauninsa dan haka sai wannan ya zama masa matsala. Wanda ya san kansa ya san wuraren da Allah ya fifita shi a kan sauran mutane dan haka zai gode masa kuma zai cigaba da aiki tuƙuru a wannan fannin. Haka nan kuma zai san wuraren da yake da rauni, don haka zai dinga taka-tsantsan a wannan ɓangaren.

    ❖ Za Ka San Abokanka

    Zaɓar aboki wani ɓangare ne mai wahala a rayuwa musamman ga mutane shiru-shiru irina, ba mu da saurin ƙulla abota. Amma duk da haka duk lokacin da muka san kanmu muna samun sauƙi wurin zaɓen aboki. Aboki wani jigo ne na rayuwa, ana tasirantuwa da shi matuƙa, dan haka ake so mutum ya yi taka-tsantsan wurin zaɓar abokai.

    Misali, a sanin da na yi wa kaina tunani ya fi aikina yawa, zan daɗe ina tunanin abu har sai na gano ba zai yiwu ba sai na watsar tun kafin na fara, da na ƙulla abota da Mallam
    Bahaushe wanda shi kuma yana aikin yana tunanin a lokaci guda, sai ya zama na tasirantu da shi na koyi haɗa dukka biyun ni ma daga gare shi.

    Wataƙila da ba mu ƙulla abota ba da wannan littafin ma yana nan zaune cikin tunanina har yanzu. Sanin kanka da sanin manufarka zai sauƙaƙa maka wannan ɓangaren na
    rayuwarka, za ka yi abota da wacce ta ku ta zo ɗaya, za ka yi haɗaka da wanda za ku ƙarfafi raunin juna, za kuma ka ci gaba da mutunci da sauran mutane, domin ƙa’idar dama ita ce “ba a ce sai kowa ya zama abokinka ba, amma za ka iya yin mutunci da kowa”.

    ❖ Za Ka Koyi Yi Wa Mutane Uzuri

    Wanda ya san kansa yana saurin sanin cewa mutane kowa da yanayin halittarsa, yadda yake ba haka kowa yake ba, kuma yana lura ya gane ya mutane suke, hakan yana taimakonsa wajen yi musu uzuri.

    Kafin na samu haske kan ni wanene wannan yana daga cikin ɓangaren da ya fi wahalar da ni, sai in kasa gane me yasa mutane suke abu iri kaza, ko meyasa suke son su ga ina yin abu iri kaza, ko meyasa su ba sa lura da kaza da kaza.

    Wannan Ilimin yana daga cikin abubuwan da suka ɗaga darajar Ma’aiki mai tsira da aminci kan sauran shuwagabannin duniya. In kana bibiyar tarihinsa za ka ga yana bambance sahabbansa ko wurin sanya su aiki yana mai la’akari da yadda suke. In ana buƙatar zafi ba ya neman sayyadina Abubakar, sayyadina Umar yake nema, haka nan in ana buƙatar wata maslaha ko wani abu na sauƙin kai, ba ya neman sayyadina Umar sai dai ya nemi sayyadina Abubakar. A rubuce-rubucena na “Iya ruwa…” na kawo
    makamancin wannan misalin.

    ❖ Za Ka Ɗauki Alhakin Rayuwarka

    Sanin kai yana ragewa mutum yawan ƙorafi da ɗaurawa wasu lefin matsalarsa. Wanda ya san kansa zai gwammaci ya mayar da hankali kan abin da zai amfani rayuwarsa sama da ba wa kansa hanzari ba gaira ba dalili. Kai ne ya kamata ka zama a kujerar mai tuƙi a motar rayuwarka ba a kujerar mai zaman banza ba (Sean Covey: 7 habits of highly effective teens).

    ❖ Rayuwarka Za Ta Yi Sauƙi

    In ka san kanka komai zai zo maka da sauƙi. Misalin wanda ya san kansa kamar misalin me yin bulaguro ne, ya san inda za shi, ya san a ina zai samu mota, ya san wacce hanya za a bi. Idan ka san kanka komai za ka san irin na ka, tun daga kan abinci, tufafi, abun hawa, wasa, kai hatta kallo da zuwa wuraren nishaɗi, za ka je ko aikata abin da bai ci karo da kai waye ba ne, balle ka samu ƙunci.

    Za ka rage damuwa da kallon da mutane za su maka don kai ka san abin da ba su sani
    ba game da kanka (kamar yadda na yi tsokaci a baya, akwai lokacin da dole sai ka saje da su don maslaha).

    Kana buƙatar wani cikin waɗannan abubuwan a rayuwarka? In amsarka e ce to mu je zuwa, in kuwa ta zamto a a, ina mai ba ka haƙuri wannan littafin ba na ka ba ne.

    Wanan bayanin an ciro shi ne daga littafi mai taken Ka San Kanka wanda AHMAD SANI ya wallafa.

    Danna nan don karanta Ka Ɗauka Ka Sani

    Edita@rumasau-kallamu

  • Ka Ɗauka Ka Sani

    Ka Ɗauka Ka Sani

    Gabatarwa

    Da sunan Allah mai Rahama mai Jin ƙai.
    Abin da za ka karanta mai yiwuwa ya iya canja maka rayuwa, yana da kyau ka samu wurin da babu kowa ka nutsu, ka kashe tv, ka kashe data, domin karanta wannan ɗan littafin a cikin cikakkiyar nutsuwa.

    Ba haka kawai na faɗa ba, ni ganau ne ba jiyau ba, na sha fama da abubuwa da dama a rayuwa, ga shi dai babu abin da na nema na rasa a gida, amma kullum ina ganin rayuwata tana shan bamban da ta sauran jama’a.

    Na daɗe ina yi wa kai na tambayoyi game da rayuwa, wasu daga cikin irin tambayoyin sun haɗa da:

    • Me yasa wasu mutanen surutu da shiga mutane ba ya musu wahala wasu kuwa yake musu?
    • Me yasa wasu sun gwammance su zama kullum suna su kaɗai wasu kuma ko da kuɗi ba za su iya ba?
    • Me yasa wasu duk abin da in dai a aji za a koyar ba abin da zai hana su ganewa wasu kuma sai an nuna musu shi ɓaro-ɓaro sun gani ko ma sun taɓa?
    • Me yasa wasu suke da saurin sabo da ƙulla abota wasu kuma sai an ja daga?
    • Me yasa wasu sun fahimci rayuwa da wuri wasu kuma har sun fara gangarawa amma ba su san inda suka dosa ba?
    • Me yasa wasu suke da naci, duk abin da suka sa a gaba sai sunga abin da ya turewa buzu naɗi, wasu kuma daga sun fara kamar ana mintsininsu suke bari?
    • Me yake sa mutum ya ji ga shi dai yana rayuwa kuma yana cimma abubuwa amma ba ya ganin ma’anar rayuwar ta sa, wani da bai kai shi ba kuma yana masa ganin ya kai wani mataki har yana sha’awarsa?

    Ba iya tambayoyin ba kenan, wannan kaɗan daga cikinsu ne, in kai iri na ne mai yawan zama yana ƙoƙarin gano wani abu ba mamaki ka taɓa yi wa kanka wasu daga cikin tambayoyin nan. Ko ka samu amsa ko ba ka samu ba, ni dai abin da nake fahimta shi ne, akwai lokacin da mutum yake matuƙar buƙatar ya san kansa, sanin kansa ne zai ba shi damar iya amsawa kansa mafi yawancin tambayoyinsa.

    Wasu tambayoyin ko da ka tambayi makusantanka, ko wasu da kake ganin sun fi ka, za ka ga ba za su ba ka amsa a yadda kai kake kallon abun ba, domin yawancin jama’a suna magana ne suna masu la’akari da yadda su suke.

    Wannan dalilin kaɗai zai iya hana abin da za su faɗa ya iya gamsar da kai. Amma idan kai ma ka san kanka fa? Za ka san a yadda za ka musu tambayar, kuma za ka fahimci a yadda suka kalli abun sannan ka alaƙanta amsarsu kai ma da yanayinka.

    Ni ba masanin kimiyya ko halayyar ɗan Adam ba ne, ni mai sha’awar rubuce-rubuce ne kawai, a wannan ɗan littafin na yi ƙoƙarin tattara abubuwan da na ci karo da su a halin binciken da na yi ta yi game da sanin kai na.

    Tambayoyi da dama na samu amsarsu, waɗanda ban samu ba kuma ina ci gaba da nemansu. Jin daɗin da nake yi a yanzu da na fahimci kaina ya wuce misali, haka kawai don mutane suna yin abu ba zai sa ni na yi ba, in ba ni da buƙatarsa (wannan ba ya kore siyasa ta rayuwa, in ka tsinci kanka a wurin da kowa yake da jela kai ma ka samu tsumma ka ɗaura, in ba haka ba za a dinga kallonka a matsayin barazana har a iya maka illa ta inda ba ka yi tsammani ba).

    Abubuwan da na ke sa ran za ku ƙaru da su a wannan ɗan littafin ga su kamar haka:

    • Meyasa ba ka san kanka ba
    • Muhimmancin sanin kai
    • Dabarun sanin kai
    • Amsa wasu tambayoyi da za su bayyana maka kanka
    • Muhimmancin samar da manufar rayuwa
    • In ba za ka iya sanin kanka ba to ka yi…

    Abin da na ke buƙata daga kai mai karatu shi ne wannan littafin na rubuta shi ne a matsayin wata ƴar ƙaramar tunatarwa ga kaina da sauran mutane da nufin ya yaɗu a tsakankaninmu mu ma su jin yaren Hausa. Don haka in ka samu kuma ka karanta kada ka bar shi a zaune haka nan, ka turawa abokananka ko da guda 3 ne domin su ma su amfana.

    Idan ka karanta wannan littafin ba ka ƙaru da komai ba, na bar “link” na whatsapp ɗina a kowanne shafi na littafin, za ka iya min magana don bayyana min kura-kuren da ke cikin littafin, da kuma bubuwan da suka sa littafin ya gaza wurin amfanar da kai.

    Idan ka ƙaru sosai kuma kana sha’awar cigaba da samun rubuce-rubuce na, ka ziyarci shafinmu na fesbuk da yake saman kowanne shafi domin mu ci gaba da ƙaruwa da juna.
    Allah nake roƙo ya amfanar da duk wanda wannan littafin zai isa gare shi, sannan ya ba mu ikon yin aiki da abubuwan da suke ciki ni da ku gaba ɗaya.

    Ka Ɗauka Ka Sani

    Sau da dama in na fito daga gida zan ga mutane a zazzaune suna hirar duniya ko a ƙarƙashin bishiya ko a kan wani dakali ko benci. Cikin irin hirarrakin nan da suke zai yi wuya ka ji babu labarin wani a ciki.

    Misali idan hirar ƙwallo suke za ka ga sun san komai game da gwaninsu, sun san haihuwarsa, garinsu, iyayensa, yaushe ya fara buga tamola, ƙungiyoyin wasannin da ya bugawa wasa, kofi nawa ya taɓa ɗauka, yanzu a wacce ƙungiya yake, nawa ne albashinsa da sauransu.

    Haka nan in hirar siyasa suke yi, komai na wannan ɗan siyasar sun sani, in hirar malamai ce ma haka, kowanne hali suke ciki suna sane. Haka nan idan ‘ƴan wasan kwaikwayo ne ko ma su sarauta. Abun ba ya tsaya a iya shahararrun mutane ba ne kaɗai, har waɗanda ake unguwa ɗaya da su, waɗanda suka kai, da waɗanda ba su kai ba za ka ga duk an san komai nasu.

    Wani abun ban mamaki shi ne da za ka kalli wannan mutumin shi a karan kansa, ta hanyar nazarin halayyarsa za ka fahimci ya san kowa ban da mutumin da ya fi cancanta ya sani, wato kansa.

    Ba haka kawai mutane suke nuna halin ko in kula da sanin kansu ba, saboda daɗewar da suka yi da kansu ne ya sa suka ɗauka sun san kansu, don haka suka mayar da hankalinsu kan sanin sauran mutanen duniya.

    Wannan kuwa ba abun mamaki ba ne, domin bincike kan bincike na masana ya tabbatar da cewa mutum halitta ce da dole sai ta yi imani da wani abu, in ba ta samu abun da za ta yi imani da shi ba sai ta ƙirƙiro abubuwa, ko ta dinga zato da tsammani kan wani abu, sannan ta mayar da zaton nan gaskiya a zuciyarta (Andrew Newberg: why we believe what we believe).

    Wataƙila wannan dalilin ya sa mutane da yawa suke ganin sun fahimci kansu, idan kana/kina cikin mutanen da suke ta ƙoƙarin ganin sun fahimci kansu amma sun rasa mafita saboda ƙarancin bayanai ko taimakon da zai haskaka musu su waye, to wannan littafin na ka/ki ne.

    Idan kana cikin mutanen da sun riga da sun ɗauka sun san kansu, amma hakan bai taimake ka wajen tsinana wani abu a rayuwa ba, yana da kyau ka ɗan duba wasu shafuka kaɗan cikin littafin nan. Idan ka fahimci kanka, kuma ka gamsu haka kake amma kuma ka kasa yin komai da rayuwarka duk da haka, akwai shawarwarin da zan kawo a gaba da za su taimaka maka. Sai a biyo ni domin shan karatu.

    Wanan bayanin an ciro shi ne daga littafi mai taken Ka San Kanka wanda AHMAD SANI ya wallafa.

    Danna nan don karanta Sababbin Karin Maganar Hausa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Rubuce-Rubucen Talatu Wada Ahmed A Kan Tarbiyya

    Rubuce-Rubucen Talatu Wada Ahmed A Kan Tarbiyya

    Gabatarwa

    A fagen adabin Hausa, musamman na zamani, marubutan mata sun taka muhimmiyar rawa wajen isar da saƙonnin da suka shafi rayuwa, tarbiyya, da matsayin mata a cikin al’umma. Ɗaya daga cikin fitattun marubutan nan ita ce Talatu Wada Ahmed, wadda rubuce-rubucenta suka yi tasiri matuƙa wajen gina tunanin matasa da wayar da kan al’umma game da darajar tarbiyya, ‘yanci, da ilimi.

    Wannan takarda na nazari ne kan yadda rubuce-rubucen Talatu Wada Ahmed suka ba da gudunmawa wajen inganta tarbiyya ta fuskar ilimi da halaye a tsakanin matasa, musamman mata.

    Tarihin Talatu Wada Ahmed

    Talatu Wada Ahmed an haife ta ne a shekara ta 1966 a ƙauyen Gaurawa da ke Jihar Katsina. Ta yi karatun farko da na sakandare a garuruwan Katsina kafin ta wuce zuwa Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), inda ta kammala digiri a fannin ilimi.

    Talatu Wada Ahmed tana daga cikin marubutan farko mata a arewacin Najeriya da suka fara rubuta littattafan soyayya da suka ɗauki jigogi masu ƙarfi na tarbiyya, ilimi da ‘yancin mata. Rubuce-rubucenta sun taimaka wajen kafa tubalin da marubutan mata suka bi, musamman a tsakanin shekarun 1980 zuwa 1990.

    Jigogin Rubuce-Rubucenta

    Rubuce-rubucen Talatu Wada Ahmed sun fi mayar da hankali ne kan batutuwan da suka shafi tarbiyya, soyayya, da matsalolin zamantakewa. Littafinta mafi shahara, ‘Rabin Raina’, ya nuna yadda mace ke da ikon yin zaɓi a cikin rayuwarta ta aure da soyayya.

    Wannan jigo yana nuni da tarbiyya ta zamantakewa da kuma buƙatar inganta fahimtar mace a cikin al’umma. Bugu da ƙari, rubuce-rubucenta suna da manufar ilmantarwa da inganta tunani, domin suna amfani da labarai wajen koyar da halaye nagari, gaskiya, da mutuntawa.

    Gudunmawar Rubuce-Rubucenta ga Tarbiyya

    Rubuce-rubucen Talatu Wada Ahmed sun taka muhimmiyar rawa wajen gina tarbiyyar matasa ta hanyoyi da dama.

    • Na farko, ta yi amfani da labarinta wajen nuna muhimmancin ilimi ga mace, ta yadda mace za ta fahimci darajar kanta da kuma rawar da take takawa a ci gaban al’umma.
    • Na biyu, ta ƙarfafa girmama iyaye da bin dokokin addini a cikin labaran nata.
    • Na uku, ta yi kira ga zaman lafiya, juriya, da fahimtar juna tsakanin ma’aurata da al’umma baki ɗaya.

    Waɗannan saƙonni suna nuni da cewa rubuce-rubucenta suna koyar da halaye na gaskiya, amana, da mutunci waɗanda su ne ginshiƙan tarbiyya.

    Littafin Ina Son Sa Haka ya nuna cewa tattaunawa kan soyayya, aure da rayuwar matasa ba kawai don nishaɗi ba ne, har ma don gina tarbiyya. Ta hanyar labaranta, Balaraba Ramat Yakubu ta zama malamar tarbiyya ta hanyar adabi – tana koyar da gaskiya, ilimi, da gyaran halaye cikin salo mai sauƙi da jan hankali a taƙaitaccen darasi.

    Wanann bayanin an ciro shi ne daga maƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

    Danna nan don karanta Koyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Ado Ahmad Gidan Dabino

    Edita@rumasau-kallamu

  • Koyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Ado Ahmad Gidan Dabino

    Koyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Ado Ahmad Gidan Dabino

    Gabatarwa

    Ado Ahmad Gidan Dabino yana daga cikin fitattun marubutan Hausa na zamani, waɗanda suka ba da gudunmawa wajen ilmantarwa da tarbiyyar al’umma ta hanyar rubuce-rubuce. Ayyukansa suna ɗauke da saƙonni masu cike da darussa na rayuwa, da koyar da kyawawan ɗabi’u musamman ga matasa da mata.

    Ado Ahmad Gidan Dabino a Taƙaice

    An haifi Ado Ahmad Gidan Dabino a Kano, kuma ya shahara wajen rubuta littattafan soyayya, zamantakewa da addini. Yana ɗaya daga cikin masu kafa “Soyayya Books” a cikin shekarun 1980s zuwa 1990s. Sannan kuma ya shugabanci ANA. Wato ƙungiyar Marubuta Nijeriya. Daga cikin sanannun littattafansa akwai:

    • In Da So Da Ƙauna
    • In Da Ruwan Zuma
    • Malam Zalimu

    Koyar da Tarbiyya a cikin Rubuce-rubucensa

    Tarbiyyar Addini

    A cikin littattafan Gidan Dabino, ana samun koyar da imanin Musulunci, ibada, da gujewa haramci.

    Misali:

    • A cikin Malam Zalimu, ya nuna muhimmancin amincin kasuwanci.
    • A wasu daga cikin rubuce rubucucensa, ya nuna sakamakon zinar aure da rashin kunya.

    Tarbiyyar lyali da Aure

    Ayyukansa suna koyar da yadda aure ya kamata ya kasance bisa so, fahimta, da mutunta juna.

    Littafin In Da So Da Kauna ya bayyana cewa so ba ya wuce gona da iri, dole ne a daidaita tsakanin soyayya da tarbiyya.

    Tarbiyyar Matasa

    Marubucin ya yi nuni da yadda matasa ke fuskantar ƙalubale na zamani, kamar shaye- shaye, bin duniya, da son hawa-hawa. Ya gargaɗi matasa cewa su mai da hankali kan ilimi da gaskiya.

    Tarbiyyar Zamantakewa

    Ado Gidan Dabino yana amfani da labaransa wajen koyar da al’umma muhimmancin:

    • Hakuri da juriya a rayuwa
    • Girmama manya
    • Girmama mata da iyaye
    • Guje wa zalunci da ƙeta da kuma amfanin haɗin kai

    Salon Koyarwarsa

    • Yana amfani da labarai masu jan hankali, amma a ƙarshe yana gargaɗi ne da nasiha.
    • Yana ɗora saƙon tarbiyya cikin maganganun jarumai a cikin labaransa.
    • Yana haɗa adabi da addini domin isar da saƙo cikin natsuwa.

    Wanann bayanin an ciro shi ne daga maƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

    Danna nan don karanta Koyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Bilkisu Ahmad Funtuwa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Koyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Bilkisu Ahmad Funtuwa

    Koyar Da Tarbiyya A Cikin Rubuce-rubucen Bilkisu Ahmad Funtuwa

    Tarbiyyar Addini

    Funtuwa tana jaddada muhimmancin bin koyarwar addinin Musulunci, musamman ga mata. Misalai:

    Wa Ya San Gobe, ta nuna sakamakon barin ibada da zaluntar mata.

    Wannan yana koyar da darasin tsoron Allah, gaskiya, da bin halal.

    Tarbiyyar Aure da Iyali

    Wannan batu yana da muhimmanci a yawancin littattafanta.

    • A Rabon Juna, ta bayyana yadda haƙuri, juriya da fahimta ke kawo zaman lafiya a cikin aure.
    • A Wa Ya San Jiki, ta nuna illolin rashin biyayya ga miji ko rashin adalci daga ɓangarorin biyu. Ta koyar da cewa aure ya kamata ya kasance bisa soyayya, tausayi, da girmama juna.

     Tarbiyyar Mata

    Ayyukan Bilkisu Funtuwa suna mai da hankali sosai ga wayar da kai Ta koyar da cewa:

    • Mace ta zama mai mutunci da kunya.
    • Ta guji fitina, gulma, da zubar da mutunci.
    • Ta nemi ilimi da sana’a domin taimakon kanta da iyalinta.

    Tarbiyyar Matasa

    Hajiya Bilkisu Funtuwa tana amfani da jarumai matasa domin isar da saƙon tarbiyya.

    • Ta gargaɗi matasa su guji soyayya marar iyaka.
    • Ta jaddada muhimmancin karatu, ladabi, da bin iyaye.
    • Ta nuna illar bin abokai marasa tarbiyya.

    Tarbiyyar Zamantakewa

    Bilkisu Funtuwa tana amfani da labarai wajen:

    • Koyar da tausayawa da taimakon juna.
    • Nuna cewa zalunci da mugunta suna da sakamako mai muni.
    • Ingiza al’umma su kare martabar addini da al’adun Hausa.

    Wanann bayanin an ciro shi ne daga maƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

    Karanta Koyar Da Tarbiyya A Cikin Littattafan Yusuf M. Adamu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Koyar Da Tarbiyya A Cikin Littattafan Yusuf M. Adamu

    Koyar Da Tarbiyya A Cikin Littattafan Yusuf M. Adamu

    Gabatarwa

    Yusuf M. Adamu yana daga cikin manyan marubutan Hausa na zamani da suka yi fice wajen rubuce-rubucen adabin ilimi, tunani da tarbiyya. Rubuce-rubucensa suna ɗauke da saƙonni masu zurfi da suka shafi rayuwa, ilimi, addini, da halin ɗan Adam. Ya yi amfani da adabi a matsayin hanya ta gyaran halaye da tunani musamman ta fuskar tarbiyya.

    Taƙaitaccen Tarihin Yusuf M. Adamu

    An haifi Yusuf M. Adamu a Kano a shekarar 1968. Malami ne, marubuci, kuma masanin kimiyyar ɗan Adam da muhalli (Geography). Ya rubuta labarai, gajerun labarai, da waƙoƙi masu  dauke da darussa. Daga cikin sanannun littattafansa akwai:

    • Idan So Cuta ne
    • Ummul-Khairi

    Tarbiyyar Addini

    Ayyukan Yusuf Adamu sun nuna muhimmancin bin dokokin Allah da guje wa haramci. Misalai:

    • A cikin littafin Ummul-Khairi, ya bayyana irin goyon bayan da iyaye ke ba wa ‘ya’yansu a bin hanyar Allah.
    • A Idan So Cuta ne, ya nuna illolin son zuciya da rashin haƙuri, yana koyar da cewa komai nufi ne na Allah. Wato dogaro da Allah Jari, wato a taƙaice dai haƙuri.

    Tarbiyyar Zamantakewa

    Yusuf Adamu yana nuna muhimmancin girmama mutane, gaskiya, da adalci. Yana nuna cewa mutunci da amana su ne ginshiƙin zaman lafiya.

    Ya koyar da mu’amala mai kyau tsakanin maza da mata, manya da ƙanana.

    Tarbiyyar Iyali

    Yana ba da muhimmanci sosai ga dangantakar aure da tarbiyyar gida.

    • A Idan So Cuta ne, ya nuna cewa aure ba wasa ba ne, kuma ya kamata ya kasance bisa gaskiya da jituwa.
    • Ya gargadi matasa kan auren dole ko auren soyayya ba tare da an yi hankali ba,

    Tarbiyyar Ilimi Da Aiki

    Ayyukan Yusuf Adamu suna ƙarfafa:

    • Neman ilimi a matsayin hanya ta ceto al’umma daga jahilci.
    • Aiki tuƙuru da gaskiya, a maimakon neman riba ta hanyar yaudara.
    • Ya nuna cewa ilimi da tarbiyya su ne ginshiƙin ci gaban al’umma.

    Tarbiyyar Matasa

    A cikin labaransa, Yusuf Adamu yana jaddada cewa matasa su guji bin son rai, su zama masu hangen nesa, su kuma zama abin koyi ga al’umma.

    Yana sukar:

    • Shaye-shaye
    • Rashin biyayya
    • Rashin mutunci

    Sannan kuma yaba wa:

    • Neman ilimi
    • Girmama iyaye
    • Taimakon al’umma

    Wanann bayanin an ciro shi ne daga maƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

    Danna nan don karanta Yanayin Littattafan Ƙagaggun Labarai Da Suke Koyar Da Tarbiyya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Abubuwan Da Za su Taimaka wa Mutum Wajen Tsara Lokacinsa

    Abubuwan Da Za su Taimaka wa Mutum Wajen Tsara Lokacinsa

    Abubuwan da za su taimakawa mutum wajen tsara lokacinsa suna da yawa waɗanda za ka iya ribata da yin su cikin minti ɗaya rak:

    • Cewa subhanallah ko salatin Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) da sauran zikiri
    • Sallama ga abokinka koda ta yin saƙon “text” cikin wayar tafi-da-gidanka (G.S.M).
    • Sake jaddada alwala.
    • Amsawa mai tambaya.
    • Sakin fuska ga mutane.
    • Kawar da abu mai cutarwa daga kan hanya.
    • Tsallakar da makaho ko wani rarrauna titi.
    • Tura wa mutum motarsa da ta mutu.
    • Miƙawa wanda yake a kan dabba abinsa da ya faɗo.
    • Maimaita wata aya daga ayoyin Alqur’ani.
    • Yiwa yara tsawa kan wata ɗabi’a mara kyau. Da sauransu.
    Yin Jadawalin Ayyukan Rana Da Yini A Rubuce

    Yin jadawali (Time-table) ga masulmi ya sha bamban da yadda ‘yan duniya ke tsara jadawalinsu. Musulmi zai yi jadawalinsa ne, yana mai rinjayar da abubuwan da za su jawo masa ribar lahira da yardar Ubangiji. ‘Yan duniya kan tsara lokutansu, ta yadda za su sami damar yin wasanni, kamar shaƙatawa a bakin ruwa, ko don yin guje-guje da tsalle-tsalle, ba tare da ba wa mahaliccinsu wani kaso ba.

    Shi kuwa musulmi, zai tsara mafi yawan lokacinsa ga Ubangiji Maɗaukaki ta yadda barcinsa da shaƙatawarsa duk za su zamo ibada. Manzon Allah (Sallallahu alaihi wassallam) ya nuna mana cewa hatta mutum in ya biya buƙatarsa da iyalinsa ma lada ne, matuƙar ya bi koyarwar Manzon Allah (Sallallahu alaihi wassallam).

    Da mutum zai tsara ranarsa da ayyukansa ta yadda zai  ware sa’a guda a kowacce ranar aiki daga Litinin zuwa Juma’a, da zai samu kimanin awoyi 260 a shekara. Wanda wannan ya yi daidai da kwana talatin, ma’ana wata guda cur.

    A lokacin kuwa, na tabbata mutum zai iya abubuwa masu amfani ga rayuwarsa misali, zai iya:

    • Haddace wasu sassa na Alqur’ani.
    • Sauke wani littafi na fikhu ko hadisi.
    • Koyon wata kwarewa (kamar kwamfuta).
    • Koyon wani harshe kamar Larabci ko Ingilishi ko kuma Faransanci.
    • Rubuta babin littafi mai amfani ga musulmi.
    • Yin kos din diploma a tsarin karatu daga gida(Distance learning).
    Yi wa Kai Hisabi A Kowace Rana (SELF ASSESSMENT)

    Wannan wata hanya ce dake taimaka wa mutum mai himma, wajen tabbatar da mutum ya ribaci lokutan rayuwarsa, kuma ya yi zikirin safiya da yammaci da sauransu. Don haka sai mutum ya zana wani jadawali na yi wa kai hisabi. Ya bibiyi wuraren daidai, ya kuma sanya alama (√) sannan wuraren kuskure kuma, ya sanya alamar (×).

    Ta haka mutum zai san sau nawa ya rasa sallar jam’i ko kuma shin yayi sadaƙa a wannan ranar? Shin ranaku nawa ne suka wuce shi bai yi karatun Alƙur’ani ba? Idan ya ga adadin alamar (√) daidai bai kai na kuskure ba (×). To ya ƙara himma.

    Akwai iyaye maza da ke da himma har sukan yiwa matansu da ‘ya’yansu irin wannan jadawali don taimakawa rayuwarsu.

    Taswirar Jadawalin Yi Wa Kai Hisabi

    Rana¬¬¬¬………………. Kwanan wata……………….

    Sallah    Zikiri   Karatun Alkur’ani   sadaqa   zumunci    Umarni da kyakkyawa

    Safe            Yamma X X
    A B X X
    A Z
    L S
    M G
    I S

    Hanyoyin Da Ke Taimakawa Wajen Kaucewa Asarar Lokaci Sun Haɗa Da:
    1. Tsara duk abinda kake son yi a safiyar kowace rana a rubuce.
    2. Da ka samu rarar lokaci sai ka shigar da shi wajen haddar alkur’ani da karatun Littafi mai amfani da zikiri da dai sauransu.
    3. In ku ka yi alƙawari ka tabbata an tsaida tsayayyen lokaci.
    4. Ka/ki tabbata ka/kin tanadi kayan aiki, kafin fara aiki, girki, tsara lacca, gini da sauransu.
    5. Kar ka fara tafiya zuwa wurin da wasiƙa ko waya za ta iya biyan buƙatar.
    6. Ka tabbata kana da mai motarka ko babur ɗinka a kowane lokaci.
    7. Kar ka yi tafiya, ba tare da safayar taya ba.
    8. Da ka ga za ka makara wurin alƙawarin da ka yi, yi saƙo da “text message.”

    Domin karanta cikakken bayani akan Ƙa’idoji Goma Sha Ɗaya Na Samun Nasara A Rayuwa danna koren rubutun nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Lokaci A Rayuwar Musulmi Tsakanin Riba Da Asara wanda Sunusi Iguda Ƙofar Nasarawa ya wallafa shi domin karanta cikakken littafin danna koren rubutun nan.