Haƙƙoƙin Shugabanni A Kan Mabiyansu

0
565

Haƙƙoƙin Shugabanni – Kamar yadda iyaye suke da haƙƙoƙi a kan ‘ya’yansu; haka su ma Shugabanni suke da haƙƙi a kan mabiyansu; kai haƙƙoƙin shugabanni sun ma fi na iyaye nauyi da cancantar a kula da su, saboda su iyaye ‘ya’yansu kaɗai suke kula da su; amma su shugabanni gaba ɗayan al’umma suke kula da su.

Illolin saɓa wa iyaye ba sa yin naso mai yawa ta yadda zai shafi kowa; amma musibar da take biyo bayan saɓa wa shugabanni da yi musu tawaye; babu wanda ba ta shafa ba.

Haƙƙoƙin shugabanni a kan mabiya a taƙaice;

1. Yi wa shugabanni biyayya a fili da ɓoye, sai dai in sun yi umarni da a saɓa wa Allah; ko kuma sun hana a bi Allah, to a nan ba za a bi su ba.

2. Yi musu nasiha da ba su shawarwari na gari; a fili da ɓoye tare da girmamawa da tausasawa da kuma mutuntawa. Ba tare da aibatawa ko suka ko zagi ko gallazawa ba.

3. Taimaka musu da ƙarfafar su da goya musu baya; saboda ƙarfinsu ƙarfin Musulunci ne; rauninsu rauni ne ga Musulunci da musulmai. Kada a soma mara wa ‘yan adawa baya don a cutar da shugaba. Ko a hana ko a lalata wani aikin alhairi da yake yi ko kuma yake yunƙurin aikatawa.

4. Girmama shi da mutunta shi, da ba shi matsayinsa a fili da ɓoye

5. Faɗakar da shi da sanar da shi duk abinda zai kawo gyara da maslahar al’umma; ka da a yi ƙwauron magana; amma a iya a cikin ladabi da girmamawa. Haka zalika da nusar da shi kurakuransa, domin ya gyara duk wannan a yi a cikin girmamawa da tausayawa.

6. Ba shi kariya gwargwadon ikon daga sharrin maƙiyansa; da masu yi masa hassada da sanar da shi ƙulle-ƙulle da makirce-makircen da suke shiryawa.

7. Taimaka masa da goya masa baya domin ya sauke nauyin da yake kansa.

8. Wayar da kan ‘yan adawa da maƙiyansa da fanɗararru domin su fahimce shi; su daina adawar da kangarar da suke yi masa.

9. Taimakon sa da dukiyarka da harshenka da matsayin ka da jikinka; da duk abin da za ka iya a fili da ɓoye.

Domin karanta cikakken bayani a kan Taƙaitaccen Tarihin Ƙasar Hausa danna nan

Domin karanta cikakken bayani a kan Abubuwan Da Za su Taimaka wa Mutum Wajen Tsara Lokacinsa danna nan

labarin da ya wuceFalalar Ƙulhuwallahu Ahad
Labarin na GabaAddu’a Idan Mutum Ya Yi Fushi