Gudunmawar Tsangayun Alƙur’ani Wajen Cigaban Al’umma

0
370

Za mu iya cewa tsangayun Alƙur’ani da cibiyoyin ilmin Addinin Musulunci su ne tushen wayewa a wannan nahiya ta Afrika; wadda al’ummar duniya ke kallo a matsayin koma baya (har ana yi mata laƙabi da “Dark Continent” – Turawa, irin su Captain Hugh Clapperton da Major Dixam Denham da Dr. Waller Oudney; da Richard Lander ganau ne su, ba jiyau ba.

Domin kuwa a lokacin da suka fara shigowa Wannan nahiya (Niger-area) a 1820 sun ga bambanci a bayyane tsakanin al’ummar Musulmi, idan aka kwatanta mu da mutanen Kudanci masu tafiya cikin tsiraici da rayuwa mai kama da rayuwar dabbobi. Domin kuwa sun tarar da cibiyoyin ilmi a tsangayu sama da dubu ashirin (20,000) a Arewacin Najeriya, ga Cikakken tsarin shugabanci da zamantakewa, ga mu da kotuna da wasiƙun hulɗar jakadanci da Larabci da Ajami da Limamai da masana daban-daban. Babban abin alfaharin Arewacin Najeriya a yau shi ne, zai yi wuya a haifi yaro ya girma ya balaga ba tare da ya dangana da makarantar allo ba.

Tsangayun Alƙur’ani ba su gushe suna bayar da gudunmawa wajen cigaban al’ummar Najeriya ba; har sai da ta kai ta kawo cewa, idan ta fuskar noma da kasuwanci ne, to ana cin arziki da ƙwazo da himmar ma’abota tsangaya. Alal misali, tun kafin a samu man fetur a Najeriya; tattalin arzikinmu ya ta’allaƙa ne kan noman auduga da gyaɗa da sauransu. Kuma mun san irin yadda makarantan tsangayu suka yi fice wajen noma da gogayya da masu sayan gyaɗa da auduga tun a wancan lokaci.

Ta fuskar kasuwanci kuwa, tsangayun Alƙur’ani sun shahara wajen yaye gardawa da matasa masu kishin kai da neman na kansu. Babban misali a nan shi ne irin hulunan Zanna Bukar da aikin Kwaɗo-da-linzami da Asake da ‘yan tsangaya ke yi. Waɗanda sun sami matuƙar karɓuwa, har ana safarar su zuwa wasu ƙasashe da ke Afrika ta Yamma.

Cinikayya kuwa ba ta yiwuwa sai da kyakkyawar tarbiyyar ruhi da amana.

Wannan ya sa irin almajiran da tsangayun Alƙur’ani suka yaye su suka mamaye kasuwanninmu na Kwari da Dawanau da Sabon Gari da sauransu. Rashin irin wannan tarbiya ta sanya ‘yan makarantun boko manya kamar jami’o’i ba sa iya gogayya a fagen kasuwanci. Dalili a nan kuwa shi ne, su sun fi so su ci da biro cikin ofisoshi.

An ce kusan cikin kowaɗanne ‘yan kasuwa goma da ke Kasuwar Kwari; za ka iske fiye da biyar (5) asalinsu almajiran tsangaya ne. Cikin waɗanda suka yi fice akwai Alaramma Alhaji Malam Ibrahim Tal’udu; da Alhaji Rabi’u Mai Shadda da Alhaji Ahmadu Kofa da Malam Sa’idu. Idan kuwa muna zancen odar kaya daga ƙasashen waje ne ko mallakar kamfanoni ne; to ‘yan tsangaya irin su Alhaji Is’haƙa Rabi’u ba sa buƙatar sharhi.

A taƙaice dai, tsangaya na tarbiyyantar ‘ya’yanta kan dogaro da kai komai ƙanƙantarsa. Shi ya sa ba za ka taɓa jin labarin ɗanta ɗaya ya gudu da kayan ‘yan’uwa cikin tsangaya ba; ko kuma a ce alarammomi sun yi yajin aiki don ba albashi.

Amma ina iyakar adadin ‘ya’yan da boko ta yaye da suka wawashe kuɗaɗen ma’aikatunsu; ko na jihohinsu ko ma na ƙasar baki ɗaya?

Daga ƙarshe, kada mu manta rawar da makaranta AIƙur’ani ke takawa wajen suturta kowannenmu in ya riga mu gidan gaskiya; da ɗaurin aure da raɗin suna da sulhu tsakanin Al’umma, ga uwa-uba; jagorancin Salloli da kuma yin addu’o’in zaman lafiya da koyar da Alƙur’ani ga ƙananan yara da manya dare da rana.

Domin karanta cikakken bayani a kan Zuwan Tajwidi Da Musabaƙa Da Tasirinsa Cikin Tsarin Tsangaya danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Sahabban Da Suka Fi Kowa Rawaito Hadisai danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

labarin da ya wuceKayan Karatu A Tsangaya
Labarin na GabaZuwan Tajwidi Da Musabaƙa Da Tasirinsa Cikin Tsarin Tsangaya