Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya daga Masallaci mai Alfarma 7th March 2025

0
31

Aminu Bashir

  1. Mai Huɗuba: Sheikh Dr Abdullahi Bin Awwad Aljuhani

Mai Fassara: Dr Usman Muhammad Ahmad

Shugaban Shashi: Dr Abdurrahman Muhammad Sani Yakubu

Huɗuba Ta Farko

Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Mai yawan baiwa, Mai yalwar falala da kyautatawa, Ya wajabta azumin watan Ramadana ga bayinSa Muminai. Ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, Majiɓincin masu taƙawa da bayinSa nagartattu, Ya karrama al’ummar Annabi Muhammadu tsira da amincin Allah masu yawa su tabbata a gare shi da watan Ramadana.

Kuma ina shaidawa lallai Shugabanmu kuma Annabinmu Muhammadu BawanSa ne kuma ManzonSa, Mafi alherin wanda ya yi Salla da azumi, kuma ya yi ɗawafi a ɗakin Allah, daɗin tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da Sahabbansa, taurarin shiriya kuma fitulu a cikin duhun ɓata.

Bayan haka:

Ina muku wasici da kiyaye dokokin Allah Maɗaukakin Sarki, da Masa biyayya a kowane waje da lokaci, kuma ku sani cewa ɗan ƙanƙanin aiki da yawa yake a wajen Allah idan ya haɗu da tsoron Allah Maɗaukakin Sarki, mai yawansa kuma ɗan kaɗan ne idan bai haɗu da tsoron Allah ba, kuma ku yi riƙo da rukunen Addini da rassan Imani, saboda ba za ku tsira ko ku rabauta a cikin rayuwarku da mutuwarku ba sai da jin tsoron Allah Maɗaukakin Sarki da Imani da Shi.

Kuma ku yi Amfani da damar da kuke da ita a cikin wannan rayuwa kafin ta kuɓuce muku, sannan ku yi rigegeniya izuwa ga ayyukan ɗa’a, saboda ku fa kuna cikin mafi ɗaukakan lokutansu ne. Shi mutum a wannan rayuwa ta duniya ba za a ba shi rayuwa da ba ta ƙarewa ba, kuma ba zai wanzu ba, bari dai, shi samamme ne daga babu, kuma mutuwa ita ce ƙarshensa, kuma lallai lokuta da suke gittawa ga mutum a wannan rayuwar duniya kamar ƙiftawar ido suke, ƙiftawa bayan ƙiftawa, haka mutum zai ta rayuwa har zuwa lokacin da zai isa zuwa ƙarshen rayuwarsa, kuma wannan lamari ne da kowane ɗaya daga cikinmu yake ji a jikinsa.

Kuma a kodayaushe mu riƙa tuna ‘yan uwanmu da suka kasance tare da mu a shekarar bara, suna jiran watan Ramadana watan alheri da albarka, amma sai dai ajalinsu ya cimmu su, kuma ayyukansu sun yanke, sai suka samu kansu a cikin wasu ramuka na ƙasa da babu komi tare da su a cikinsa face ayyukansu, kuma ba su bar wa kawunansu komi a bayansu ba face wata sadaka mai gudana, ko wani ilimi da ake amfanuwa da shi, ko wani ɗa nagari da yake musu addu’a, kuma mu masu tafiya ne izuwa ga wajen da suka tafi.

Kamar haka ne kuma zamani ya juyo, kuma watan Ramadana ya dawo a wannan shekara, ya dawo bayan mun yi mantuwa mai yawa, bayan mun kutsa muna masu ninƙaya a cikin al’amuran duniyarmu ninƙaya mai zurfi, to, watan Ramadana ya dawo, kuma muma an ƙaddara mana dawowa tare da shi don mu shaida kwanakinsa masu haske kuma mu raya dararensa masu ƙyalli.

Ya ku Musulmi!

Lallai yana daga cikin mafiya girman ni’imomin Allah Maɗaukakin Sarki a kan bayinSa Muminai, ni’ima da Ya yi musu a cikin waɗannan kwanaki na riskar wani lokaci cikin lokutan alhairai, wanda shi ne watan Ramadan, ma’abocin rahama da albarkatu, watan da masu azumi suke farin ciki a cikinsa, kuma masu aiki suke samun riba a wajen Allah, watan da ake ruɓanya ladan farillai a cikinsa sama da ladan farillai a waninsa, watan da nafilolinsa kamar farillai suke a wani wata da ba shi ba, watan kyauta da sadaka, watan da ake yafe kurakurai a cikinsa, kuma ake kankare zunubai, Allah ya wajabta mana azumtar sa, shi kuma Manzon Allah tsira da amincin Alah su tabbata a gare shi ya sunnanta mana tsayuwa a dararensa.

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana albishir wa Sahabbansa yana cewa: (Watan Ramadana ya zo muku, watan albarka, Allah Yana saukar da rahama a cikinsa, kuma Yana yafe laifuka, Yana amsa addu’a, kuma Allah Yana alfahari da ku ga Mala’ikunSa, don haka ku bayyana wa Allah alheri daga gare ku; saboda taɓaɓɓe shi ne wanda aka haramta masa rahamar Allah a wannan wata). Haisami ya dangana shi ga Ɗabarani a littafin Maj’ma’uzzawa’id.

Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Idan watan Ramadana ya shigo ana buɗe ƙofofin Aljanna, kuma ana rufe ƙofofin wuta, sannan kuma ana ɗaure shaiɗanu). Bukhari da Muslim ne suka rawaito.

Haƙiƙa yana daga cikin shiriyar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi wanda shi ne mafi cikar shiriya, Yawaita mabanbantan ibadu, haƙiƙa ya kasance ya fi kowa yawaita kyauta a cikin mutane, kuma yafi yawaita kyauta a watan Ramadana, yana yawan sadaka a cikinsa, da kyautatawa, da karatun Alƙur’ani, da zikiri, da i’itikafi, kuma ya kwaɗaitar a kan yin Umara a watan Ramadana.

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce wa wata mata cikin Mutanen Madina: (Me ya hana ki yin aikin Hajji tare da mu?), sai ta ce: “Mun kasance muna da wani raƙumi mai bayin ruwa, sai baban wane da ɗansa- wato mijinta da ɗanta- sai ya bar wani raƙumin muna bayi da shi”, sai ya ce: (To, yin Umara a watan Ramadana kamar aikin Hajji ne tare da ni). Bukhari da Muslim ne suka rawaito.

Kuma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana keɓance watan Ramadana da wasu ibadu da ba ya keɓance sauran watanni da su, don haka ku gode wa Allah a bisa ni’imar riskarsa, kuma ku gode Masa ta hanyar ƙara himma da ƙoƙari da raya lokutansa da ayyukan ɗa’a mabanbanta, kuma ku fuskance shi ta hanyar kiyaye shi daga kurakurai da laifuka, Allah Ya muku rahama.

Waɗannan lokuta ne masu falala, ina masu amfana da su? Waɗannan lokuta ne na kasuwanci mai ba da riba, to, ina masu nema?

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce: (Dukkan ayyukan ɗan Adam nasa ne, Sai dai azumi, domin shi Nawa ne, kuma Ni ne zan ba da sakamakonsa, Azumi garkuwa ne, idan ya zama ɗayanku na azumi a wani yini, to, kada ya yi yasasshen zance, kuma kada ya yi hayaniya, idan wani ya zage shi ko ya nemi yin faɗa da shi, to, ya ce: Ni ina azumi. Ina rantsuwa da Wanda ran Muhammadu ke hannunSa, warin bakin mai azumi ya fi ƙamshi a wajen Allah fiye da ƙamshin almiski. Mai azumi yana da farin ciki guda biyu da zai yi, idan ya sha ruwa zai yi farin ciki, haka kuma idan ya haɗu da Ubangijinsa zai yi farin ciki da azuminsa).

Allah Ya taimake ni tare da ku a kan azumtar sa da tsayuwa a dararensa muna masu Imani da fatan samun lada, kuma Ya gafarta mana kurakurai gaba ɗaya, Ya suturce mana dukkan laifuka, kuma Ya mana yafiya a ranar tambaya da hisabi.

A’uzu billahi minash-shaiɗanir-rajim. Bismillahir-Rahmanir- Rahim: (Ya ku waɗanda kuka yi Imani an wajabta muku azumi kamar yadda aka wajabta wa waɗanda suka shuɗe gabaninku don ku samu taƙawa).

(Waɗansu kwanaki ne ƙididdigaggu. To duk wanda ya kasance marar lafiya a cikinku ko yake halin tafiya, to, (idan ya sha azumi) sai ya rama a waɗansu kwanakin na daban. Kuma waɗanda za su yi azumi da wahala su ba da fansa ta ciyar da miskini; to, duk wanda ya ƙara (a kan abincin miskini), to hakan alheri ne gare shi, amma ku yi azumin shi ne ya fi muku alheri, in har kun kasance kun sani).

Domin Karanta Shakku a Cikin Sallah danna nan

(Watan Ramadana shi ne wanda aka saukar da Alƙur’ani a cikinsa, shiriya ne ga mutane kuma ayoyi ne bayyanannu na shiriya, kuma mai rarrabewa. Don haka, duk wanda ya riski wannan wata daga cikinku, to, ya azumce shi, kuma wanda ya kasance marar lafiya ko yake halin wata tafiya, to, (idan ya sha azumi) sai ya rama a wasu kwanakin na daban. Allah yana nufin sauƙi a gare ku, Kuma baya nufin tsanani a gare ku, don ku cika adadin (Kwanakin Ramadana), kuma domin ku girmama Allah bisa ga shiryar da ku da Ya yi, don ku yi godiya).

Allah Ya albarkace mu da Alkur’ani, kuma Ya amfanar da mu da abin da yake cikinsa na bayani. Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina neman gafarar Allah Mai girma gare ni tare da ku da dukkan Musulmi daga dukkan zunubi, don haka, ku nemi gafararSa, lallai Shi ne Mai yawan gafara, Mai jinƙai.

Huɗuba Ta Biyu:

Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Wanda Ya lulluɓe zukatan bayinSa da ni’imominSa, kuma Ya raya zukatansu da hasken Addini da hukunce-hukuncensa, kuma Ya musu wasici da riƙo da abin da Ya shar’anta musu daga hikimarSa da hukunce-hukuncenSa.

Ina shaidawa lallai babu abin bautawa bisa cancanta sai Allah Shi kaɗai, ba Shi da abokin tarayya a zatinSa da siffofinSa da aikinSa. Kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa, Ya aiko shi ga dukkan mutane don Ya rinjayar da shi a kan dukkan addinai. Tsira da aminci su tabbata a gare shi da Alayensa da Sahabbansa masu riƙo da igiyarsa.

Bayan haka:

Ina yi mana wasiyya da jin tsoron Allah, da yin gaggawa wajen neman gafarar Allah da kuma neman Aljanna wadda faɗinta yake daidai da sammai da ƙasa, wadda aka tanade ta ga masu taƙawa.

Kuma ku sani cewa watanmu mai albarka, watan falala da alheri, kuma lokacin ayyukan ibada da kyawawan ayyuka, wasu ranaku sun shuɗe daga cikinsa, kuma kwanakinsa suna ci gaba da tafiya, kuma nan ba da daɗewa ba za su ƙare. Marabauci a cikinsa shi ne wanda ya yi tunani cikin lamarinsa, ya yi takatsan-tsan, kuma ya yi amfani da wannan damar kafin ta wuce, kuma ya ribaci falalar Ubangijinsa Ma’abocin kyauta da karamci da kyautatawa.

Saboda haka, ku yawaita karatun Alƙur’ani, da ciyar da abinci, da sadaka ga talakawa da marayu, kuma ku kiyaye gaɓɓanku daga aikata laifuka da zunubai a cikinsa. Kuma ku yawaita salati da sallama ga Shugaban halittu kuma cikakken haske. ((Lallai Allah da Mala’ikunSa suna yi wa Annabi salati. Ya ku waɗanda kuka yi Imani! Ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)).

Ya Allah Ka yi salati da salama ga Shugaban dukkan halittu, Shugabanmu kuma Annabinmu Muhammadu, da Alayensa nagartattu tsarkaka, da Sahabbansa masu haske da albarka, amintattu a kan da’awarsa, kuma komondojin rundunarsa, waɗanda duk wanda ya roƙa musu rahama, kuma ya yi musu addu’a, sannan babu ƙiyayyarsu a cikin zuciyarsa, to lallai shi ne wanda Allah Maɗaukaki ya nufa da faɗinSa:

(Waɗanda suka zo bayansu suna cewa: “Ya Ubangijinmu Ka gafarta mana mu da ‘yan’uwanmu waɗanda suka riga mu yin Imani, kuma kada ka sanya wata ƙullata a zukatanmu game da waɗanda suka yi Imani. Ya Ubangijinmu! Lallai Kai Mai tausayawa ne, Mai jinƙai).

Da kuma waɗanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar Alƙiyama. Ka yarda da mu tare da su, ya Ubangijin talikai.

Ya Allah, ya Mai kawar da damuwa, Mai yaye baƙin ciki, Mai karɓar addu’ar waɗanda ke cikin matsanancin hali, Mai Rahama Mai jinƙai a duniya da lahira, Kana bayar da su ga wanda Ka so, kuma Kana hanawa ga wanda Ka so, Ka yi mana rahama wacce za ta wadatar da mu daga neman rahamar waninKa, ya Ubangijin talikai.

Ya Allah muna neman tsarinKa daga talauci da rashi da ƙasƙanci, kuma muna neman tsarinKa kada a zalunce mu ko mu yi zalunci. Ya Allah! Ka wadatar da mu da halal daga barin haram, kuma Ka wadatar da mu da falalarKa daga falalar waninKa, ya Ubangijin talikai.

Ya Allah, Ya Wanda zunubin masu zunubi ba ya cutar da Shi, kuma biyayyar masu biyayya ba ta amfanar da Shi, Ka yi mana rahama, Ka yi falala ga waɗanda suka miƙa hannayensu gare Ka suna masu ƙanƙan da kai, suna neman Ka ‘yanta su daga wuta ma’abociya tsanani da muni.

Ya Allah muna roƙon Ka Ka sanya mu daga cikin waɗanda za Ka ‘yanta daga wuta a cikin wannan wata mai albarka, kuma daga cikin masu tsira daga gidan halaka gidan wuta, daga cikin waɗanda za su dawwama a gidan tabbata Aljanna. Lallai Kai Mai rahama ne, Mai yawan gafara, ya Ubangijin talikai.

Ya Allah lallai Muna roƙon Ka a cikin wannan wata mai albarka, muna kamun ƙafa da fuskarKa mai girma, da LittafinKa mai hikima, kada Ka bar mana wani zunubi a wannan lokaci face Ka gafarta mana, kuma kada Ka bar mana wani aibi face Ka suturce shi, ko wata damuwa face Ka kawar da ita, ko wata cuta face Ka warkar da ita, ko wata matsala face Ka yaye ta, ko wani Imani face Ka tabbatar da shi, ko wata zuciya face Ka yalwata ta, ko wani ɓatacce face Ka shiryar da shi, ko wani marar lafiya face Ka warkar da shi, ko wani mamaci face Ka yi masa rahama, ko wani da ake tambaya cikin ƙabari face Ka datar da shi, ko wani da ke tsoron azabarKa face Ka amintar da shi.

Ya Allah, Ka gafarta mana abin da muka riga muka aikata da abin da zamu aikata, da abin da Ka ƙididdige na zunubammu mu kuma muka manta, da abin da Ka sani amma muka jahilta.

Ya Allah, kada Ka bar mana buri face Ka cika mana shi, ko wata buƙata face Ka sauƙaƙa mana ita, ko wani alheri face Ka ba mu shi, ko wani sharri face Ka nisantar da mu daga gare shi, ya Mafi alherin Wanda bawa ya dogara da Shi kuma ya yi fatan samun alheri daga gare Shi, Ya Ubangijin talikai.

Ya Allah, Ka amintar da mu a ƙasashenmu, Ka shiryar da shugabanninmu da masu jagorancinmu, Ka ƙarfafi Hadimin Masallatai biyu masu alfarma Sarki Salman bin Abdulaziz da Magajinsa amintacce Muhammad bin Salman da ɗaukaka da nasara bayyananniya.

Ya Allah, Ka kiyaye su cikin cikakken lafiya da kariya, Ka saka musu da mafificin alheri game da hidimar Masallatai biyu masu alfarma da wurare masu daraja ga Musulunci da Musulmi.

Ya Allah, Ka datar da dukkan shugabannin Musulmi kuma ka shiryar da su zuwa ga abin da yake alheri ne ga Addini da ƙasashensu. Ya Allah, Ka kare sojojinmu, Ka kare iyakokinmu da sansanoninmu, Ka kare jami’an tsaronmu, ya Ubangijin talikai.

Ya Allah, muna neman gafara daga gare Ka, lallai Kai ne Mai gafara, Ka saukar mana da ruwan sama mai albarka. Ya Allah, Ka saukar mana da ruwa ya Allah, Ka saukar mana da ruwa ya Allah, Ka saukar mana da ruwa. Ya Allah, mu halittu ne daga cikin halittunKa, kada Ka hana mu falalarKa saboda zunubanmu.

(Tsarki ya tabbata ga Ubangijininka Ubangijin buwaya daga abin da suke siffantawa. Aminci ya tabbata ga Manzanni, kuma godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin talikai).

Danna nan don karanta Falalar Salati Ga Annabi SAW

Edita:@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceFaten Doya Da Wake