An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) Haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “kada ku mayar da gidajenku kamar maƙabarta; Haƙiƙa Shaiɗan yana gudu daga gidan da ake karanta Suratul Baƙara a cikinsa”. (Muslim 708).
An karɓo daga Abu Umamah (Radiyallahu Anhu) haƙiƙa ya ji Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) yana cewa; “ku riƙa karanta suratul Baƙara saboda riƙo da ita albarka ne, barinta nadama ne; kuma matsafa ba sa iyawa da ita”. (Muslim 804).
Wato karanta suratul baraƙa yana maganin sihiri da tsafi da kuma sharrin shaiɗanu.
Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Falalar Karanta Ayatul Kursiyyi Ya Ke danna nan.
Domin karanta cikakken bayani akan Wajibcin Karatun Fatiha A Cikin Sallah danna nan.
Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.