Falalar Sadaƙar Mai Ƙaramin Ƙarfi

0
12

An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu anhu) ya ce: “Haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam) yace: “Sadaƙar dirhami ɗaya ta rigayi sadaƙar dirhami dubu ɗari” Sai wani mutum ya ce; Kamar yaya Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam)?

Sai ya ce: “Mutum ne yana da dukiya mai yawan gaske, sai ya tsakuro dubu ɗari ya bayar sadaƙa; kuma wani dirhami biyu ne kaɗai da shi. Sannan ya yi sadaƙa da dirhami ɗaya” (Nasa’I Ibn Khuzaimah), (Sahihul Targib 875).

Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Ciyarwa Da Shayarwa Da Tufatarwa danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Ratiban Nafiloli danna nan.

Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceTarihin Gwani Saleh Ɗanzargu
Labarin na GabaYadda Falalar Karatun Al-Ƙur’ani Ya Ke