Category: WikiHausa

Yadda ake amfani da WikiHausa

  • Wasu Kayan Aikin Rini

    Wasu Kayan Aikin Rini

    1. Tukumar baba

    2. Zarta

    3. Babah

    4. Shuni

    5. Mucciya

    6. Toka

     

    7. Katsi

    8. Marina

    9. Mabugi

    10. Ƙaro

    11. Itace

    12.Makuba

    13. Ƙaiƙayi

    FASIHIN KAITA

    Danna nan don karanta Wasu Kayan Aikin Ƙira

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Uku

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Uku

    Sai bayan la’asar suka dawo tare kamar yanda suka fita, a lokacin yara suna islamiyya. Don haka cikin walwala ya ƙarasa ciki don ya san Khadeeja ta kular masa da yaran. Sai da ya leƙa parlor ɗinta ya gaya mata ya dawo sannan ya wuce ɗakinsa. Yara suna dawowa daga islamiyya suka wuce parlor ɗin Naja inda suka jiyo su ita da Abbansu.

    Kafin wani ya yi magana Shukra ta faɗa jikin Naja tace ‘Yauwa Anti kin dafa mana abinci ko? Wallahi yau gari muka sha mu da Anti, tace idan kin dawo za ki dafa mana abinci. Ta kalli Mustapha sanna ta sake kallon Shukran, kafin tace wani abu Mustaphan ya janyo Shukra jikinsa yace ‘Gari kuka ci Shukra?’

    Ta ɗaga masa kai. Nan take ragowar yara suka tabbatar masa da haka aka yi. Ya kalli Afaf wadda shigowarta kenan tana ƙoƙarin zama yace ‘Ke ba sai ki dafa muku ko indomie ba ce? Ta zumɓura baki ta kawar da kai ba tare da tace komai ba. Ya yi gajeren tsaki sannan ya dubi Nasreen yace ‘Ina Hafsa? Ita ba sai ta dafa muku ba?’

    ‘Ita ma garin ta ci ai, Anti ba ta ce ta dafa komai ba haka tace mu jira Anti Naja ta dawo ita ce da girki. Ya kalli Najan wadda take ta faman cika tana batsewa, ya miƙe a fusace ya fice daga parlor ɗin. Tana zaune a parlor ɗinta tana shan kunun alkama ya same ta.

    Kafin ta gama amsa sallamarsa ya fara magana a fusace ‘Khadeeja wane irin raini da wulaƙanci ne zai saka ki ba wa yara gari, ke ba za ki girka musu abinci ba kuma ba za ki saka yarinyarki ta girka musu ba. Ta ajiye kofin kununta ta kalle shi tana jijjiga kai sannan cikin halin ko in kula tace ‘To ai mai girkin ba ta bar musu abinci ba kuma ba ta barwa yarinyar tawa wani abu tace ta dafa musu ba, shi yasa da aka ji yunwa na haɗa mana gari duka muka sha. Ina laifi?’

    Ya fesar da iska mai zafi saboda yanda takaici ya kama shi, ba ya son yanda idan Khadeeja za ta yi masa fitina take zama da nutsuwarta shi kuma tana saka shi yana yin spark. ‘Khadeeja, don Allah me kike so ne kike min wannan wulaƙancin? ‘Ba wulaƙanci nake maka ba. Abu ɗaya kawai nake so shi ne ka yi adalci.

    Yanda nake buƙatar hutu daga kwana saboda jego haka nake buƙatar hutu daga hidimar gida da ta yara, don dama wallahi dagewa nake yi. Idan kuka gama arba’in ɗin muka fara rabon kwana sai na dinga haɗawa ina karɓa. Ya ja dogon tsaki ya yarfar da hannu, har ya buɗe baki zai yi magana kuma sai ya fasa. Ya juya ya fice daga parlor ɗin.……..

    Duk yanda yake tunanin Khadeeja za ta saurara masa hakan bai samu ba. Yana so ya mayar mata da kwananta da ya karɓa ya ba wa Naja amma kuma yana son ƙarin lokaci don ya ƙara sabawa da Najan. Haka dole ya haƙura ya zuba musu ido; sai dai duk wani jin daɗi da yake sa ran zai samu daga wajen Najan ba ya samuwa saboda yanda take wuni a gajiye saboda hidima.

    Suna kwanciya bacci yake kwashe ta; ga shi kullum cikin yi masa mita take a kan ita ya mayar da hidimar yara wajen Khadeeja. Duk da kusan Khadeejan ta sallama musu Hafsa tana taya ta. Ita kuwa Khadeeja gaba ɗaya haushinta yake ji don gaba ɗaya ya daina kula ta, a yanda yake ji yanzu ma ba ya jin zai kula ta koda ta yi arba’in ɗin idan dai ba itace ta kawo kanta ta ba shi haƙuri ba.

    Duk yanda Naja ta za ta kula da yaran nan zai yi mata sauƙi abun ba haka ba ne, domin da ƙyar take kai wa yamma saboda gajiya. Ga shi Khadeeja ta sallama musu Hafsa kullum cikin taimaka mata take; abu ɗaya da Khadeeja ta hana Hafsa yi mata shi ne girki. Ta so ƙwarai a ce ta dinga bar wa Hafsa tana yi musu girki idan ta fita, amma Khadeeja ta ƙi bari.

    Don haka kullum kafin ta fita aiki sai ta dafa musu abincin rana kuma idan ta dawo sai ta yi na dare. Ga shi duk da suna shiri da Afaf ta gane Afaf ta fita son jiki, don duk yanda take jin za su taya ta aiki hakan ma bai samu ba.

    Yau satinta biyu da tarewa; yana zaune a parlor ɗinta shi da yaransa kamar yanda suka saba suna kallon TV bayan sallar isha’i. Ita kaɗai ce a tsaye tana ƙoƙarin jera abincin dare a dining. Tana jerawa tana mita a ranta yanda yaran ba sa taya ta aiki, ko da za ta ce su taya ta to fa idan dai yana nan ba za su taya ta ba; sai dai ta yi aikinta ita kaɗai.

    Gashi kuma ba ya son Hafsa ta dinga yi masa girki. Bayan ta gama jera abincin suka taso gaba ɗayansu suka zauna har da ita suna cin abinci. Jollof sphagetti ce da kifi; ana cikin cin abincin Shukra ta ɗaga kifin da yake kwanonta tace ‘Abba a cire min ƙaya. Har ta buɗe baki za ta ce Afaf ta cire mata ya yi sauri yace ‘Ki miƙowa Antinki ta cire miki.’

    Haka Afaf wadda take zaune a tsakanin Najan da Shukran ta ɗauki plate ɗin da yake gaban Shukran ta miƙawa Naja. Ba tare da ta ce komai ba ta sa hannu ta ɓara kifin gida biyu ta cire ƙayar sannan ta miƙawa Afaf wadda ta sake miƙawa Shukra. Haka har suka gama cin abincinsu babu wanda Naja ta sake yi wa magana.

    Tana zaune a gefen gado tana shirin kwantawa bacci ya tura ƙofar ya shigo da sallama, da ƙyar ta amsa sallamarsa saboda yanda take jin haushinsa. Gani take kamar da gayya ya bari matarsa ta sallama mata yaran sannan kuma sun kai su kula da kansu amma komai sai yace sai ta yi musu.

    Ya ƙarasa ya hau gadon ta bayanta ya kwanta, tana kwanciya ya janyo ta jikinsa. Ta ɗan ture shi tana cewa ‘Bacci fa nake ji Habibi, wallahi na gaji. Kuma ka ga gobe yara za su makaranta kuma zan je aiki. Ya ƙara ƙanƙame ta yana laluba jikinta yana cewa ‘Sannu, bari na yi miki massage yanzu gajiya za ta sauka.’Ta dage ta janye jikinta ta zauna a kan gadon, hakan ya sa shi ma ya tashi ya zauna a kusa da ita yana kallon fuskarta kamar mai neman amsa a fuskar tata.

    Kafin ya yi magana ta langaɓe kai tace ‘Habibi ni dai don Allah ka mayarwa da maman Hammad kwananta, in ya so mu cigaba da yi kwana bibbiyu yanda tsarin yake. Da mamaki ya kalle ta suka haɗa ido sannan yace ‘Kin gaji da ni kenan Baby. Ta miƙa hannu ta shafi gefen fuskarsa tana murmushin yaƙe sannan tace ‘Ya za a yi na gaji da kai, ni kam ai ban ƙi ba a ce ni kaɗai ce matarka kullum muna tare.

    Amma ka ga aiki yana yi min yawa sosai, yi wa yara abinci kaɗai ya ishe ni da shirya su makaranta. Kullum a gajiye nake kai kanka ba ka samun yanda kake so a wajena. Amma ka ga idan zan dinga samun kwana biyu a tsakani na huta ai ina ga hakan zai fi mana sauƙi ko?

    Tunda nace a ɗaukar min mai aiki ka ce Hafsa ta ishe mu; ita kuma wannan yarinyar wallahi ƙarin aiki ce saboda ta fi su wasa da son jiki. Ni ban ma san yanda aka yi Khadeejan take zama da ita ba. Kawai dai kace ta karɓi kwananta. Har ta gama maganar yana bin ta da kallo ba tare da yace komai ba, sai da ta gama ta numfasa sannan yace ‘Um haka ne, amma dai ai kin ga kula da yaran yanzu fa ba wani aiki ba ne tunda gaba ɗayansu kowa ya iya kula da kansa.

    Kusan za a iya cewa abinci ne kawai sai an dafa musu. Ta kalle shi suka haɗa ido. Har ta buɗe baki za ta yi magana kuma sai ta fasa; ta kula ba so yake ya karɓi uzurinta ba. Yaran da hatta kula da kan nasu ma da yake cewa sun iya idan dai ba ta tsaya a kansu ba babu wanda zai yi, idan kuma aka bar su haka yace zai yi wa mutane fada.

    Ta ja numfashi sannan tace ‘To ka dai mayar mata da kwananta don Allah, a fara rabon haka tunda ka ga yanzu saura kusan sati uku ta cika arba’in ɗin. Ya numfasa ya zame sannan ya janyo ta jikinsa ta gyara mata kwanciya yana shafa bayanta sanna yace ‘Kada ki damu, in sha Allahu da safe zan yi mata magana. Ai na san kina ƙoƙari wajen kula da yaran nan kuma suma za ki ga suna jin daɗin zama a wajenki, nagode sosai da kike kula min da su.’

    A haka dai ya samu ya lallaɓata suka kwanta. Ya san wulaƙancin Khadeeja, tabbas idan ya je yace mata za a fara rabon kwana yanzu ba lallai ta saurare shi ba. Baya jin ma zai iya tunkararta da wannan maganar idan dai ba so yake ta yi masa dariya ba. Haka ya cigaba da lallaɓar Naja don ba ya ma son ya tayar da maganar mayarwa da Khadeeja kwananta da ya ƙwace.

    Tunda ta kwana ashirin da bakwai da haihuwa ta yada wankan jego, kuma da yake ita ɗin mace ce wadda ta damu ta fatarta sai ta mayar da hankali wajen gyaran fata da gashin kanta waɗanda ruwan zafi ya ɓata. A zaman da suke yi da Mustapha ta san yana jin haushinta saboda ta ƙi ta cigaba da kula da yara shi da amarya su yi amarci, ta san ba lallai ya ba ta wasu kuɗi ba.

    Don haka ‘yan kuɗaɗenta da ta samu a barkan Hammad su ta fito da su ta nemi Baffanta ya ƙara mata dubu goma sannan ta haɗo kayan gyaran fata. Nan da nan cikin sati guda haske da santsin fatarta ya fara dawowa. Kamar yanda ya saba kullum da safe zai leƙa su gaisa kafin ya fita. Yau ɗin ma haka ya shigo parlor ɗin da sallama.

    Suna zaune a parlor ɗin ita da Habib suna cin abinci; ita tana zaune ta miƙe ƙafa da Hammad a kan cinyarta yayin da shi kuma Habib yake zaune daga gefenta yana cin nasa abincin. Funkaso ne ta soya da zafinsa tare da parpesun kaza suke karyawa da shi; don kanta ta dafa farfesunta amma ta riga ta saba shi Habib idan dai tana nan ba ya cin abinci a wajen Naja.

    Don haka idan dai ya shigo ba ta hana shi, domin wani lokacin ma ajiyewa take yi don ta san zai zo nema. Ya ƙarasa ya zana a kan kujera daga kusa da Khadeejan, bayan ya amsa gaisuwarsu yace ‘Nan kuka ƙule kuna cin daɗi ashe shi yasa na ji shiru. Ta yi dariya kawai ba tare da tace komai ba, Habib ne yace ‘To ai Abba Anti Naja tuwo ta dafa jiya na san ɗumame za a ci shi yasa na gudo.’

    Suka yi dariya gaba ɗaya. Ta san so yake yace zai ci domin yana son funkaso, ita kuma ba ta so yace zai ci saboda dafawa ta yi har abincin rana tunda so take ta fita idan ta dawo kawai sai ta ci abunta. Ya dube ta tana cinye funkason ƙarshen yace ‘Idan akwai funkason ki zuba min na ɗan ci, duk da dai na yi breakfast amma ya ba ni sha’awa.’

    Ji ta yi kamar tace masa babu, amma Allah ya sa ba ta iya rowar abinci ba, musamman ga mutumin da shi ya kawo cefanen. Don haka bayan ta cinye nata ta miƙe ta kwashi kwanukan ta shige kitchen bayan ta miƙawa Mustaphan Hammad; Habib shi ma ya kwashi nashi kwanukan ya bi bayanta.

    Jimawa kaɗan suka fito tare, ta kawo tray ɗin da ta riƙo ta ajiye a gaban Mustaphan sanna ta sa hannu ta karɓi Hammad; shi kuma Habib ya fice daga parlor ɗin.Ya sauka ƙasa ya fara cin abincin sannan ya dube ta yace ‘Shi ne kin yi funkaso ko ki kirawo ni. Ta yi ‘yar dariya tace ‘Ai na san ka riga ka ci better ka cika cikinka shi yasa na sa yarona a gaba muna ci mu kaɗai.

    Ya yi dariya ya mayar da hankali wajen cin abincinsa. Jimawa kaɗan ta tashi ta shige ɗaki, ba ta daɗe ba ta fito tana riƙe da takarda a hannunta. Sai da ta zauna sannan ta miƙa hannu ta ajiye takardar a gafensa tana cewa ‘Ga posting letter ɗina, jiya na karɓo. An yi posting ɗina gidan talabijin na ARTV.’

    Nan da nan ya ɓata rai, bai ce mata komai ba sai da ya ƙarasa cinye abincin sanna ya dube ta yace ‘Kin san dai ba na son aikin jaridar nan ko, sai da nace ki saka a yi posting ɗinki makaranta amma shi ne kika je kika saka aka kai ki gidan talabijin don ki dinga fitowa a TV.’

    Ta kawar da kai tana mamakin Mustapha. Tana karatunta na aikin jarida ya ganta ya auro ta amma tunda ya ga ta kusa gamawa yake ta faman gaya mata aiki ɗaya zai bari ta yi shi ne koyarwa. Wataƙila ma da a ce bai ƙara aure ba da ta haƙura ta yi koyarwar amma yanzu kam babu yanda za a yi ya auro amaryarsa tana aikin office duk da dai ba na TV ba ne; sannan ita yace koyarwa za ta yi.

    Tace ‘Ni ba ni nace su kai ni can ba, sun duba abinda na karanta ne kawai. Kuma idan nace a kaini makaranta na je na koyar da su me? Ni da na karanci aikin jarida.’Cikin halin ko in kula yace ‘Ko Hausa ba sai ki koyar ba ko English, amma kin san babu yanda za a yi na barki kina fitowa a gidan TV duk duniya suna kallonki kina iyayi ko?’

    ‘To yanzu ya kake so a yi? Ki je kawai su canza miki, idan kuma ba haka ba ni zan je a canza amma ba za ki yi aikin TV ba matuƙar da aurena a kanki ba na so. Ta ɗan gyara zama tace ‘To ai ko na je gidan ARTV ɗin ma ba lallai na dinga fitowa a TV ba tunda aiyukan suna da yawa kuma ba duk ma’aikatan ne suke fitowa a TV ba.’

    Ni dai ba na son ki je wajen kwata-kwata tunda idan dai kana wajen wata rana za a saka ki a wani shirin kuma babu yanda za ka yi. Kawai ki je su mayar da ke makaranta ko kuma ki ba ni takardun ni na je.’ Ya faɗa yana miƙewa tsaye. Ba ta ce komai ba yace ‘Ni na tafi gidan Hajia.’

    ‘A dawo lafiya, ka gaishe min da su.’ Ta faɗa ba tare da ta kalle shi ba, kuma da yake shi ma ba kallon nata yake yi ba bai ma san yanayin da take ciki ba. Ta bi bayansa da kallo bayan da ya fice daga parlor ɗin; ta ma rasa me za ta ce masa. Koyon aikin jarida ya ganta tana yi ya auro ta, kuma sau da dama ta sha gaya masa cewa babu abinda take so take buri kamar a ce yau ga ta a gidan talabijin tana karanta labarai ko kuma gabatar da wani shiri.

    Sai da ta kusan gama karatun sannan yake sanar da ita shi ba ya son matarsa ta dinga fitowa a TV, kuma duk lokacin da ya gaya mata ana gaya masa cewa ita kuma burinta ɗaya kenan a duniya. Daga baya ne ma ta fahimci cewa da ba don ya auro Naja a ma’aikaciya ba to da tabbas ba zai bar ta ta yi aiki ba ma gaba ɗaya.

    Yanzu kam ma sai ta ga kamar yana dai so ya takura ta ne saboda ba ta yi masa yanda yake so ba, amma za ta san yanda za ta ɓullo wa lamarin. Sai da ta bari dare ya yi lokacin ta san Baffa yana zaune a gida sannan ta kirawo shi, bayan sun gaisa ta sanar da shi abinda Mustapha ɗin yace game da inda aka kai ta bautar ƙasa.

    Bayan a saurari bayaninta yace ‘To ke ki je makarantar mana, ai ba shi ne aikinki ba tunda bautar ƙasa shekara ɗaya ne kawai. Tace ‘To ai Baffa idan na je ina fatan ne su riƙe ni su ba ni permanent aiki, kuma ka ga Baffa gaskiya ba zan iya aikin koyarwa ba don za a dinga samun matsala da ni.’

    ‘Um haka ne, to bari mu gani. To ko gidan rediyo za ki je a mayar da ke? In ya so sai na yi wa Mustaphan bayani. Baffa ni dai da ka yi masa magana ya bar ni na je gidan TV ɗin. Yace ‘A a, ki yi haƙuri ki yi a gidan rediyo tunda dai yace ba ya son a dinga nuna matarsa a TV kin ga kuma hakan ya nuna yana kishinki. Ki je ki yi a gidan rediyo ta yanda ko da an saka ki a wani shiri to muryarki kawai za a ji ba za a ganki ba.’

    Ta so ƙwarai a ce Baffa ya goya mata baya ta tafi gidan TV domin shi ya san tun tana yarinya burinta kenan, amma ta san tunda yace haka ba zai goya mata baya ba; sai dai idan ta matsa ranta ya ɓaci. Don haka sai kawai ta haƙura. Suka yi sallama da Baffa suka ajiye wayar.

    Sati yana zagayowa ta fara bautar ƙasa a gidan radio na Freedom Radio bayan da Baffa ya kirawo Mustaphan ya yi masa bayani sannan ya ba shi haƙuri a kan ya bar ta ta yi a nan ɗin. Haka ya bari ba don ya so ba.

    Tunda ta fara zuwa aiki kuma sai aikin gida da na yara suka ƙara taruwa suka yi wa Naja yawa. Domin sai ya zama kullum idan Khadeeja za ta fita da Hafsa take fita saboda riƙe mata Hammad a wajen aiki. Ganin haka ya sa Naja ta saka Mustapha a gaba sai da ya bari ta ɗauki mai aiki wadda take zuwa kullum tana tafiya da yamma; tunda ya ce ba za ta raba wa su Afaf wanke-wanke da gyaran gidan su dinga yi idan sun dawo daga makaranta ba.

    Babu yanda ba ta yi da shi ya mayar wa da Khadeeja kwananta ba amma ya ƙi; saboda ƙi-faɗi. Duk da shi ɗin ma yanzu zai so a ce sun fara kwana bibbiyun tunda yanzu yana son shiga harkar Khadeejan; amma dai ya san Khadeeja ba za ta karɓi kwanakin nan da ta bayar ba tare da son ranta ba sai ta saka masa ciwon kai. Ita kuma ta so ta yi wa Khadeejan magana amma ba za ta yi ba.

    Saboda kusan tunda ta zo gidan ba wata magana da take haɗasu da Khadeejan bayan gaisuwa; da yake ma Khadeejan ba mai son fitowa ba ce sai ya zama idan dai ba aiki za ta je ba to za su iya kwana biyu ma ba su haɗu ba. Haka suka cigaba da rayuwarsu.

    Ranar Juma’a ce ta kama ranar da Khadeeja ta cika arba’in. Duk wani shiri ta gama yinsa, ta gama gyaran jikinta kamar yanda duk wata maijego take yi. Sai dai ba ta sa rai zai ba ta kwanan ba kuma ta ci alwashin ba za ta taɓa kai masa kanta ba sai dai shi ya kawo kansa. Bayan ta idar da sallar asuba sai ta sake bin gado ta kwanta tunda ta san Hammad ba zai taɓa wuce ƙarfe takwas yana bacci ba zai tashe ta.

    Ba ta san iya tsawon lokacin da ta ɗauka tana bacci ba bugun ƙofar da ake mata ne ya tashe ta, a tare suka farka da Hammad wanda ya sa kuka. Ta lalubo wayarta ta duba lokaci inda ta ga 8:30am; nan da nan ta mutssike ido don ya kamata a ce kafin ƙarfe tara ta fita ta tafi gidan rediyo. Sai da ta ɗauki Hammad sannan ta miƙe ta buɗe ƙofar. Hafsa ta gani a tsaye; bayan ta gaishe ta tace ‘Anti na gama aikin gaba ɗaya na ga ba ki fito ba kuma jiya kin ce min na shirya da wuri za mu fita.’

    ‘Hmm! Bacci ne ya kwashe ni. Zauna ki jira ni na shirya Hammad na miƙo miki shi ni ma na shirya mu tafi. Nan da nan ta shirya Hammad ta miƙa shi wajen Hafsa suka zauna a parlor sannan ta koma ɗakin ta shiga wanka. A gurguje ta yi wankan ta fito ɗaure da ƙaramin farin tawul ɗinta, tana riƙe da wani tawul ɗin tana goge jiki. Mustapha ta hango yana zaune a gefen gadonta ya miƙe kafa yana kallo a waya.

    Ba ƙaramin mamaki ta yi ba domin gaba ɗaya ta kasa tuna me yake jira. Ba wai ba ya shiga ɗakin ba ne amma dai tunda Naja ta tare bai zauna a ɗakin ba sai dai ya shiga ya gaya mata abinda zai gaya mata yana daga tsaye ya fice. Ta ɗan tsaya kaɗan ta kalle shi sannan tace ‘Ina kwana. Ya ajiye wayar ya amsa gaisuwar tata da fara’a. Ta ƙarasa gaban mudubi tana goge jiki yayin da shi kuma Mustaphan ya miƙe tsaye ya nufo ta.

    Ya ƙarasa ya tsaya a bayanta ya rungumo ta ta baya, ta kalle shi ta cikin mudubin suka haɗa ido tace ‘Fita fa zan yi ka ga ma na makara. Ya yi murmushi ya saka bakinsa a kan kunnenta yace ‘Ni ma fita zan yi, amma dai kin san yau kin yi arba’in ko? Ta ɗan motsa saboda yanda yake ƙara shigewa jikinta tace ‘Um. ‘Ok, ki karɓi kwananki yau sai ki ajiye min dinner.’

    Murya ƙasa-ƙasa tace ‘Toh. Ya sumbaci gefen wuyanta sannan ya sake ta ya juya. Har ya kusa zuwa bakin ƙofa kuma sai ya juya ya dawo, kafin ya ƙarasa inda take ita ma ta juyo don haka ya tsaya a gabanta. Cike da damuwa ya kirawo sunanta, bayan ta amsa yace ‘Bana jin daɗin yanda kuke zama da Naja kamar kuna gaba, please ki dinga ɗan zama a parlor ɗin kasa saboda ku saba.

    Ta dan yi murmushi tace ‘Ba wata gaba da muke yi tunda muna gaisawa, kuma duk abinda ya kama na magana ai muna yi. Ya kalleta suka haɗa ido sannan ya riƙe ƙwayar idonta yana cewa ‘Duk da haka dai ki dinga dan zama a can kuna hira. Kin ga idan kina nan ba za ta shigo ba ita ma sai ta yi ta zama a parlor ɗinta inda ke ba kya shiga.’

    Ba ta son ta ja zancen saboda ba ta son ta makara, don haka tace ‘To shikenan. Ya sake tsattsare ta da ido sannan yace ‘Please! Ta yi gajeren murmushi ta ɗaga kai. Ya fice bayan tayi masa a dawo lafiya. Ta ja tsaki bayan da ya fice; ba ta jin za ta iya raɓar Naja, ta tsaneta.

    Wataƙila hakan yana da alaƙa da yanda Mustaphan ya ɓata mata rai a kan Najan tun kafin aurensu da kuma maganganun da ta gani a wayar Afaf da suna chatting da Naja. Gaskiya ba za ta iya hira da wata Naja ba, gashi kuma ba ta iya munafurci ba balle ta je ta yi na ƙarya. Shi dai da ya ga Naja yana so ya auro ta suje can su ƙarata. Cikin sauri ta karasa shiryawa suka fice ita da yaranta.

    Tun kafin Magriba ta gama abincin dare, don haka Habib yana shigowa daga masallaci sallar magriba ta tura shi ya kirawo ƙannensa a wajen Naja. Nan suka zauna a parlor ɗinta suka ci abinci inda ta dafa macaroni da miyar hanta da salad. Suna gama cin abinci Afaf wadda dama bayan sallama ba ta ce mata komai ba ta tashi ta fice daga parlor ɗin. Sauran yaran kuma suka zauna a nan aka cigaba da hira ana kallon TV.

    Wajen 8:30pm duk suka fara jin bacci don haka da kanta ta tashi ta raka su ɗakinsu, ta shirya shukra sannan ta tsaya Nasreen ma ta shirya suka yi brush suka kwanta sanna ta koma nata ɗakin. Shi ma Habib ya yi mata sai da safe sannan ya wuce nashi ɗakin. Har zuwa lokacin Mustapha bai dawo ba, sai dai ya yi mata waya ya sanar da ita sun fita da Alhaji don haka sai ta gan shi.

    Don haka bayan ta yi wanka ta yi shirinta na bacci sai ta koma ta jera masa abincinsa a table ɗin parlor ɗinta sannan ta wuce ɗakinta ta kwanta. Sai wajen 9:30pm sannan ya shiga gidan. Kai tsaye bayan ya kulle gidan parlor ɗin Naja ya shige tunda ita ce a ƙasa. Tana zaune a kan kujera tana shan cornflakes ranta a ɓace. Ya ƙarasa bayan ta amsa sallamarsa ya sumbaci kumatunta sanna ya zauna a kusa da ita yana cewa ‘Cornflakes kike sha a daren nan?’

    ‘Um. To me gidan ce da girki kuma ba ta ba ni nawa abincin ba shi ne na haɗa cornfakes nake sha tunda ban saba zama da yunwa ba.’ Ta faɗa tana ƙara shan kunu. Ya ɗan shiga duhu, yace ‘Umm, Khadeeja ba ta yi abinci ba ne? Ta yi, amma nan ta turo aka kirawo yara suka je samanta suka ci abinci. Da suka gama cin abincin ma a can suka yi zamansu Afaf ce kawai ta sauko ta taya ni hira.’

    ‘Um! To ai na zata kowaccenku dama girkinta za ta dinga yi ko? Ta harare shi sannan tace ‘A ina ake haka? Tunda wadda take da girki ita ce za ta dinga kula da yara ai girkin ma gaba ɗaya za ta dinga yi. Shi yasa ni ma idan na yi abinci nake fito wa da shi nan parlor ɗin inda kowa zai iya ɗiba, ita ce ba ta fitowa ta ɗiba saboda ba ta son ganina.’

    ‘Wa ya gaya miki? Ba haka ba ne. Bari zan yi mata magana in ya so sai ta dinga yi da ke, ke ma ranar naki girkin sai ki dinga yi da ita kun ma ragewa kanku aiki. Ta zumɓura baki ‘Ah to don ni dai haka na san duk masu mace sama da ɗaya suna yi. Ya yi mata sallama ya wuce sama. Bata taɓa sanin idan Khadeeja ta karɓi kwana abun zai sosa mata rai ba sai a wannan lokacin.

    Gaba ɗaya zucuyarta ta yi ƙunci, haka ta bi bayansa da kallo har ya fice daga parlor ɗin ya rufe mata ƙofa. Nan take hawaye ya wanke mata fuska; ta ajiye kofin da yake hannunta a kan tebur ta haɗa kai da gwiwa ta sa kukan da ta kasa gane me ya kawo shi. Haushin Khadeeja ta karɓi kwana ko kuwa haushin an barta da yunwa?

    Yana ƙarasa shiga parlor ɗinsa ya kalli dining table, bai ga alamar abinci ba. Kamar ma ko taɓa wajen ba a yi ba tunda ya fita da safe. To me Khadeeja take nufi? Duk wannan ɗokin da yake na zuwa wajenta ita ashe ba ta gama fushin ba kuma ba ta gaya masa ba? Cikin sanyin jiki ya ƙarasa ya shiga ɗakinsa. Ga mamakinsa ɗakin ma ba a gyara ba.

    Yanda Naja ta fita ta bar shi da safe yana nan a haka, babu ma alamar da take nuna mutum ya shiga ɗakin bayan fitarsa. Khadeejan ma da yake sa ran zai gani a ɗakin ba ta ciki. To ina take? Me take nufi bayan ya sanar da ita yau ita ce da kwana?

    Gaba ɗaya  ranshi ya gama baci; ba ya son fitinar Khadeeja don ita rigima da ita ba ta ƙarewa, musamman a yanzu da yake da buƙatarta. Har ya juya zai fita kuma ya fasa, ya tsaya ya canza kaya ya shirya sannan ya ɗauki wayarsa ya fito ya nufi ɗakin Khadeejan.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Wasu Kayan Aikin Ƙira

    Wasu Kayan Aikin Ƙira

    1.Masaɓa
    2.Uwar maƙera
    3.Awartaki
    4.Zuga-zugai
    5.Guduma
    6.Gawayi
    7.Zarto

    FASIHIN KAITA

    Danna nan don karanta Wasu Kayan Sana’ar Saƙa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Biyu

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Biyu

    Ta yi zaton ranar da kwana zai dawo kanta za ta ji tana cikin yanayin murna, sai dai ba hakan ya kasance ba. Yau ne za ta karɓi kwana amma sai ta ji kamar ma ba za ta iya bari ya kusance ta ba saboda kamar dai har yanzu ƙoƙari take ta saba da cewa su biyu ne matansa.

    Haka dai ta tashi ta gama duk wata hidima da take yi. Ya riga ya sanar da su cewa da daddare za a dinga karɓar kwanan don haka tun yamma ta shirya abincin dare; duk da ba ta cikin walwala amma haka ta girka abincin da ta tabbatar yana so; tuwo miyar kuɓewa danya. Ta haɗa komai ta jera a table ɗin sama.

    Sai dai ga mamakinta har wannan lokaci Naja tana ɗakinsa na sama, don haka ma ba ta ko je kusa da ɗakin ba tana jiran ya dawo ta ji ko shi ne zai biyo ta ɗakinta tunda dai kwananta ne. Da yake bayan ya ci abincin rana ya sake fita sai wajen 8pm ya shigo gidan.

    A ɗakinta ya same ta tana miƙe a kan gado da Hammad a kwance a kan cikinta yana wutsil-wutsil ɗinsa. Bayan ya amsa sannu da zuwanta ya ƙarasa ya zauna gefen gadon ya sa hannu ya ɗauki Hammad yana masa wasa. Suka ɗan taɓa hira sanna tace ‘Um ga abinci can a dinin fa, idan ka shirya sai mu je mu ci.

    Yara dai sun ci nasu don yau tun magriba Nas ta fara jin yunwa. ‘Oh,Ok.’ Ya amsa kamar mara gaskiya. Tace ‘Kuma na ga amarya har yanzu tana ɗakin naka fa, ko a nan za mu kwana ne? Kamar wanda aka tayar daga bacci yace ‘Umm. No, umm kin gane? Dama ina so na yi miki magana don da na san za ki dafa abincin daren zan ce ki dakata.’

    Ta kalle shi da mamaki tana jira ta ji ƙarashen bayanin, suka haɗa ido ya yi sauri ya kawar da idonsa. Suka ɗan yi jim sannan ya cigaba ‘Ina ga ya kamata tunda ke kina jego ki bar mata kwanakin naki zuwa lokacin da za ki cika arba’in ko? Ta tashi zaune tana ƙarewa Mustapha kallo ko zai sauya maganarsa, kamar bai fahimci saƙon ba don sai ya ƙara haɗe rai yana wasu muzurai.

    Ta yi murmushin yaƙe tace ‘Oh, yanzu kenan kwanan gaba ɗaya na amarya ne har sai na cika arba’in da haihuwar Hammad? ‘Eh, to ai kinga kina jego. Menene amfanin kwanan? Ta sunkuyar da kai, ta ɗago ta kalle shi sanna ta yi gajeran murmushi tace ‘Haka ne, Allah ya kai mu arba’in ɗin.’

    Kamar wanda aka tsikara ya miƙe yana yage baki yana cewa ‘Yauwa, to bari na je sai da safe ko. Cikin sauri ya miƙa mata Hammad fice daga ɗakin kamar wanda yake tsoron kada ta riƙe shi tace ta fasa. Ta bi ƙofar da kallo bayan ya fice; wasu hawaye masu zafi suka gangaro kan fuskarta a daidai lokacin da wani malolo ya taso ya tokare mata maƙogoro take neman kasa numfashi.

    Sautin rufe ƙofar ya dawo da tunaninta cikin ɗakin bayan da ta kifta idonta; ta yi murmushi mai ciwo tare da sunkuyar da kai. Wato dai yanzu Mustapha ya yi sabuwar amarya har ya fara gudunta, tunda ai lokacin da ta yi ɓari sai da ya nuna ɓacin ransa a kan tafiyar da ta yi gida. To me yake nufi da ita?

    Wato idan wahala ce ta je ita kaɗai ta yi ta sha kenan, lokacin da zai iya morarta shi ne lokacin da zai ba ta kwana. Lallai akwai aiki amma dai ba za ta fasa addu’a duk da zuwa yanzu duk dan wani karsashin kyautatawa Mustapha da take so ta yi ya zirare. Sai da Hammad ya fara kuka sannan ta yi ajiyar zuciya ta sa bayan hannunta ta share hawayenta sannan ta miƙa hannu ta ɗauko shi daga inda yake kwance ta saka masa nono.

    Har ya gama shan nonon ya saki tana ajiyar zuciya, ta shirya shi ta goya shi sannan ta fice daga ɗakin. Da yake dare ya yi tana jiyo muryarsu ƙasa-ƙasa sun hira tunda ɗakin nasa yana jikin nata ɗakin. Haka ta wuce da yake a parlor ɗinta ta jera musu abincin daren can ta wuce ta je ta kwashe ta mayar kitchen tana ƙwafa. Ta dawo suka kwanta ita da Hammad.

    Duk yanda take jin bacci a wannan daren kasawa ta yi, sai dai da yake bacci ɓarawo ne sai da ya faki idonta ya sace ta; sai ji kawai ta yi ana assalatu. Duk da ba sallah za ta yi ba sai da ta tashi ta wanke fuska sanna ta zauna ta yi azkar ɗinta sannan ta koma ta kwanta.

    Tun kafin a ɗaura aurensa da Naja ya riga ya gaya mata amarci za su yi na kusan kwana talatin domin lokacin da za ta tare zai yi daidai da kwanan Khadeeja goma sha biyu da haihuwa. Don haka ya sanar da ita gaba ɗaya kwanan nata ne har sai Khadeeja ta gama jego kwana arba’in. Ita Khadeejan ce bai gayawa ba shi yasa ma ta zata za a yi yanda aka saba ne ta karɓi kwananta bayan kwana bakwai.

    Ba ƙaramin daɗi ya ji ba da Khadeeja ta amsa masa ko da yake dama bai sa ran za ta ba shi matsala ba tunda dai ta san ba za ta biya masa buƙatarsa ba wadda a wannan lokacin ko Allah ma bai haramta masa ya kai wa ɗaya matar tasa buƙatar ba. Cikin walwala suka kwana shi da amaryarsa, ko da ya fito da asuba zai tafi masallaci ya hango fitila ta kasan kofar ɗakin Khadeeja don haka ma ya san ta riga ta tashi.

    Da sallama ya shigo parlor ɗin bayan ya dawo daga masallaci, kai tsaye ya nufi kitchen ɗin don ya jiyo motsinta a can. Tana tsaye da goyon Hammad tana zuba ruwan zafi a flask. Bayan ta amsa sallamarsa ta gaishe shi; yana ta wani kau da kai yana muzurai kamar yanda ya saba idan yana so ya gwada mata son kai haka ya amsa gaisuwar tata.

    Ta mayar da kettle ɗin inda take sanna ta buɗe fridge don ta ɗauko ragowar peppersoup ɗinta. Yace ‘Ina yaran? Ba su taso ba. ‘Eh.’ Ta amsa a gajarce ba tare da ta bar abinda take yi ba. Ya kula da yanayinta idan ya takura ta za ta iya birkice masa a safiyar don haka yace ‘Ok, idan sun shirya ki ce su buga min ƙofa please.’

    ‘Ok.’ Ta sake ba shi amsa a gajarce. Ya juya ya fice daga kitchen ɗin. Ta ƙarasa ɗumama soup ɗinta ta juye a flask, ta ɗauki ruwan zafinta ta haɗa ta kai ɗaki sannan ta dawo ta ɗauki kayan shayi duka ta shigar ɗaki. Ta zauna ta ci burodi da soup ta sha shayinta mai kauri sannan ta koma ta kwantar da Hammad ita ma ta kwanta.

    Ba ta daɗe da kwanciya ba kuwa bacci ya ɗauke ta saboda dama na jiya ba isar ta ya yi ba. Kamar a mafarki ta ji ana buga mata ƙofa, ta yi firgigit ta buɗe ido. Ko ba a gaya mata ba ta san wannan bugun Habib ne don haka ta tashi zaune ta janyo wayarta ta duba lokaci; 8:25am. Ta janyo zanin goyon Hammad da ke kusa ta rufe jikinta sanna tace ‘Shigo Habib.’

    Ya turo ƙofar ya shigo da sallama, tun kafin ta gama amsa sallamar tasa yace ‘Anti yau makara kika yi ne? Yanzu har past 8 fa kin ga ba mu tafi makaranta ba. To me yasa ba ku tafi ba? Ni ai na zata kun tafi tuni. Ya ƙarasa ya zauna a bakin gadon da mamaki a fuskarsa yana cewa ‘Anti ba ki tashe mu ba fa; ni ma bayan mun dawo daga masallaci da Abba har na yi wanka fa na ɗan kwanta don na san za ki tashe ni shi ne bacci ya kwashe ni.

    Su Afaf ma ga su can ko sallah ma ba su yi ba sai yanzu na taso su har Hafsan. Ta kama haɓa tana cewa ‘Ikon Allah. To ai ba ni ce da girki ba Habib, Antin ku ce. Ita ce za ta tashi kowa ta shirya shi yasa ma ka ga ban fito ba. Ya taɓe baki yana zare ido ‘Tab, to ai kuwa daga ita har Abban babu wanda ya fito.’

    ‘To Allah ya sa dai lafiya, ka je ka buga musu ƙofa. Ka murɗa kofar parlor ɗin a buɗe take sai ka ƙwanƙwasa ɗakin ka ji. Ya miƙe ya fice daga ɗakin yayin da ita kuma ta zame ta gyara kwanciyarta da niyyar komawa bacci.

    A tsakiyar parlor ɗin Habib ya ci karo da Abban nashi yana fitowa da gaggawa, suka haɗu a tsakiya suka yi cirko-cirko. Abban nasu yace ‘Kai Habib meye haka? Na cewa Anti ku taso ni idan kun shirya me yasa ba ku taso ni ba? Kai ko uniform ma ba ka saka ba. Yace ‘Abba ai makara muka yi, Anti Najan ba ta tashe mu mun shirya ba.”

    Kafin ya ba shi amsa sauran yaran suka shigo kowa da kayan bacci, ya kalle su sannan ya mayar da hankalinsa kan Habib din yana cewa ‘Wace Anti Naja kuma, ko dai Anti Khadeeja? ‘To ai ita ma Antin bacci take yi yanzu na je tashinta tace min ba ita ce da girki ba Anti Naja ce za ta shirya mu.’

    Mamaki ya kama shi; ya za a yi Khadeeja ta gayawa yaro wannan maganar? Wane irin wulaƙanci ne bayan ita ce ta saba shirya yaran kawai kuma yanzu sai tace Naja ce za ta shirya su? Ba tare da yace komai ba ya wuce yaran ya nufi ɗakin Khadeejan. Habib ya dubi ‘yanuwansa yace ‘Yau dai mun yi mising school, ni yunwa nake ji ma ku zo mu je ƙasa bread yana can ko shayi sai mu haɗa.’

    Ya wuce suka bi shi suka sauka ƙasa. Kusan a fusace ya tura ƙofar, hango ta da ya yi a kwance tana bacci ya ƙara harzuƙa shi. Sautin buɗe ƙofar ne ya farkar da Hammad daga bacci. Ta tashi zaune tana mittsike ido sanna ta miƙa hannu ta ɗauke shi. Ta dubi Mustapha cikin halin ko in kula tace ‘Ohhh! Abba ka tayar min da yaro yanzu babu sauran bacci.

    Ta ɗaga shi ya yi miƙa sannan ta saka masa nono yayin da Mustaphan yake cewa ‘Me ya faru na ga ba ki tashi kin shirya yara ba bayan yau akwai makaranta, kuma fa ko da asuba sai da na ce miki idan sun shirya ki ce su yi min magana? Tace ‘Oh! Ai ba su zo sun ce min sun shirya ba na zata ma sun gaya maka kun wuce sai da Habib ya gaya min yanzu sannan na sani.’

    ‘Ban gane ba, wai wace magana kike yi ne? To me yasa ba ki tashi kin shirya su ba? ‘Oh to ai wadda take da kwana ita ce da gida musamman ma da yake ni ina jego. Na zata da ka kai mata kwanan ka gaya mata abinda aka saba yi na running gidan. Mamakin da yake fuskarsa ya ƙaru ya haɗe da takaicin Khadeeja, yace ‘Ban gane wadda take da kwana ita ce take da gida ba Khadeeja.

    Ke kika saba shirya yaran nan kullum kuma kin san haka, shi ne yau saboda ganin ido za ki ce ita za ta shirya su? Idan kina jin haushina ai sai ki gaya min tunda ba dole na yi miki kika bar mata kwanan ba ko? Za ki fara wulaƙancin naki ko Khadeeja? Ta yi dariyar yaƙe tace ‘Wallahi ni duk ban gane ba.

    Ai ni a yanda na sani duk matar da take da kwana da girki ita ce take duk wata harka ta kula da gida, ni ma idan na karɓi girki sai na haɗa gaba ɗaya na yi. ‘Khadeeja, ba na son wulaƙanci. Yaran nan a hannunki suke kuma da ke suka saba, ya za a yi tana zuwa ki ɗora mata kula da su ita da yau za ta koma aiki ma.’

    ‘Amma dai ba da su na zo ba a nan na same su ko? Kuma idan ban manta ba ni ma daga zuwana aka haɗa ni da su, kamar ma ita an ɗaga mata ƙafa. Hidimarsu ta makaranta ma wadda ta riga ta saba yi tun ma kafin ta auri ubansu balle yanzu da ta aure ka, ai ina ga wannan ma ƙaramin abu ne.’

    Ya gama ƙulewa har wani huci yake, ya cije leɓe sannan yace ‘Khadeeja ba na son wulaƙancinki fa, yanzu me kike nufi da yaran nan? ‘Alkhairi nake nufi da kowa, kawai dai duk wadda take da kwana ta haɗa duk har gidan da yaran ta kula da su. Shikenan. Har ya juya zai fita ya juyo ya nuna ta da yatsa yana cewa ‘Yanzu shikenan kin tura mata yara har tsawon sati huɗu?

    Ta ɗago ta kalle shi cikin halin ko in kula tana cewa ‘Na tura mata mijin ma? ‘Mtsewww!’ ya ja dogon tsaki ya fice ya maka mata ƙofar. Ta yi ‘yar dariya ta cigaba da wasa da Hammad. Har ya koma ɗakin tana kwance tana baccinta domin office ɗin da za ta ta riga tace sai wajen sha ɗaya za ta tafi saboda an canza mata branch sakamakon aurensu da Mustapha; ta san tunda yau za ta fara reporting tana da damar makara.

    A hankali ya buɗe ƙofar ya shiga saboda kada ya tashe ta daga bacci, ya ƙarasa ya zauna a gefen gadon. Ya zuba fuskarsa a tafukan hannunsa yana shafa fuskar, gaba ɗaya kansa ya kulle. Ya yi zaton yaran nan tunda suna wajen Khadeeja shikenan a wajenta za su cigaba da zamansu ko da ya ƙara aure.

    Gaba ɗaya ma shi bai taɓa zama sun yi maganar yara da Naja ba, kawai dai yana saka ta hidimarsu idan ta kama kuma yana nuna mata cewa yana so su sami kulawar da yake jin sun rasa daga wajenta. Baya jin za ta ba shi matsala saboda yanda ya ga tana kulawa da su tun ma kafin ta aure shi balle yanzu da za ta yi da hujja. Ya juya ya ɗan taɓa ta. Ta buɗe ido ta kalle shi ta yi murmushi sannan ta yi miƙa.

    Tace ‘Honey har ka dawo? Ya ɗan kawar da kai sanna yace ‘Daga ina? ‘Umm! Na zata ‘yan makaranta ka kai. ‘No, ban kai su ba sun riga sun makara sosai sai gobe. ‘Ok, Allah ya kai mu. Ta zuro ƙafafunta ƙasan gadon ta kwanta a kafaɗarsa tana cewa ‘Bari na je na yi wanka sai na fito na haɗa mana breakfast. Ina jin ma kawai sai na shirya ka ba ni lift.’

    Yace ‘Ai kuwa sai ki yi sauri don ga yara can ma ke suke jira ki zo ki ba mu abincin gaba ɗaya. Ta ɗaga kafaɗarsa ta ɗan kalli fuskarsa da mamaki ‘Antin ba ta nan ne? Ya kawar da kai daga kallon da ta kafe shi da shi, yace ‘Tana nan. To ai kin ga kece da kwana don haka ke ce za ki dinga yin abincin duka gida kina kula da yara, in ya so idan ta karɓi kwana sai ta cigaba.

    Duk wadda take da kwana ita ce da gida. Ta sake leƙa fuskarsa da mamaki a kan fuskarta tace ‘Ban gane ba, ai ni ban karɓi girki ba, kwana ne kace ka tambaye ta ta ba mu har ta yi arba’in. kuma yara ai na zata tunda a wajenta suke sai su yi zamansu duk abinda ya kama ai zan saka hannu.’

    ‘A a, wadda take da kwana ita ce za ta dinga haɗawa ta yi komai kawai. Ki yi sauri ki yi wankan ki zo ki ba mu abinci. Shiru ta yi kawai tana bin shi da kallo. Jimawa kaɗan ya kalle ta suka haɗa ido, ya gyara zama ya kama hannuwanta duka biyun ya riƙe sannan yace ‘Kin ga wannan fa ba wani abun damuwa ba ne, ai dama kin san duk inda ake da mace sama da ɗaya ai dama duk wata hidima rabawa ake yi.

    Idan yanzu kika ki yin wani abu ai sai ki janyo kwanan amarcin ya ƙare tunda kin ga dole ne na koma kan tsarin kwana bibbiyu don tabbatarwa an yi adalci ko? Ta sunkuyar da kai tana kallon ƙasa don gaskiya ita ba ta zata haka ba; ba wai ba za ta kular masa da yara ba amma dai ta sa rai za su yi zamansu a wajen uwarsu ita ce za ta dinga hidimarsu ta kullum in ya so ita duk wanda ya zo inda take a cikinsu za ta yi masa duk wani abu da ya kama.

    Ta ɗago ta kalle shi tace ‘To yanzu kenan duk wadda take da kwana ita ce za ta dinga tashi tana yi wa yara komai? Ya ɗaga mata kai alamar e. ‘To idan za ni aiki fa. Ya kama haɓarta ya ɗago fuskarta, suka haɗa ido ya yi mata murmushi sannan yace ‘Ki bari wannan a hankali za mu ga yanda za a yi.’

    Ta ɗan ja baya za ta tashi, ya riƙe fukarta ya sake tsare ta da ido har sai da ta yi murmushi, ya sumbaci leɓenta sannan ya miƙe yana cewa ‘Muna ƙasa muna jiranki ni da yara. ‘Ok.’ Ta amsa sannan ta shige banɗaki. Ya tashi yafito daga ɗakin. A parlor ya tarar da yaran suna zaune suna shan shayi da burodi wanda Hafsa ta dafa musu ruwan zafin. Ya nemi waje ya zauna ya ɗauki remote ya canza channel.

    Ya fi minti talatin da zama shi da yaran suna ta hira sannan ta sauko, ta sha kwalliya sai ƙamshi take yi. Bayan ta amsa gaisuwar yaran kai tsaye ta wuce part ɗinta, nan da nan ya tashi ya bi bayanta yayin da Nasreen da Shukra suka rufa masa baya. Nan da nan ta soya ƙwai ta haɗa musu da shayi suka zauna shi da ita a dining table suka karya.

    Suna gama karyawa shi ma Mustaphan ya shirya suka fito tare. Har za su sauka daga bene sai kuma ya ba ta mukullin motar yace ta fito ta jira shi zai yi sallama da Khadeeja. A parlor ɗinta ya same ta tana kwance a kan doguwar kujera da remote a hannunta yayin da Hammad yake cikin baby rocker ɗinsa yana ta wutsil-wutsil.

    Tana daga kwance ta amsa sallamarsa, ya ƙarasa kusa da kanta yace ‘Za mu fita ni da Naja, ita ma yau za ta koma aiki. Tace ‘Ok, a dawo lafiya. Har ya juya zai fita tace ‘Ta dai bar wa yara abincinsu ko? Ga shi za su je islamiyya ko da yake na san sun yi wanka in lokacin ya yi ko Hafsa sai ta taya su shiryawa su wuce.’

    Ya juyo ya tsaya ya zuba mata ido na ɗan lokaci; ya ma rasa ta ina zai fara. Ya kan rasa yaren da zai yi wa Khadeeja magana da shi idan ta fara wannan taurin kan nata, lokuta da dama ya kan ɗauka cewa tana jin tsoronsa amma fitinar da yake gani a ƙwayar idonta idan tana wannan taurin kan tana ba shi tsoro. Ya cije leɓensa sanna yace ‘Fita fa nace miki za mu yi, ya kike so ta yi da abincin ranansu?’

    Ta tashi zaune ta gyara zamanta sannan tace ‘Yanda nake yi idan zan tafi makaranta ko? Ya jijjiga kai sanna yace ‘Khadeeja please kada ki saka min ciwon kai da safen nan, ga yara nan ki ba su abinci in ya so idan mun dawo ta ba su na dare. Idan kuma kin ga dama ki bar su da yunwa. Ta kalle shi suka haɗa ido ta yi masa gajeran murmushin yaƙe ta zame ta kwanta ba tare da ta ce masa komai.

    Haka shi ma ya juya ya fice zuciyarsa cike da wasi-wasi saboda ya san wannan murmushin nata ba wai yana nufin za ta kula da su ba ne, amma dai ya tafi yana addu’ar Allah ya sa ta kula masa da su.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Ɗaya

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Ɗaya

    Cike da ɗoki ya shiga ɗakin amaryarsa riƙe da ledarsa ta kayan ciye-ciye; tana zaune a can a ƙuryar gado. Ko da a ce ta amsa sallamarsa to shi dai bai ji ba, amma ya riga ya san yanda amare suke. Har inda take ya ƙarasa ya same ta bayan ya ajiye ledar hannunsa a kan mudubi.

    Ga mamakinsa bayan ya ɗaga fuskarta kuka take yi sosai da hawaye kamar wadda aka yi wa auren dole, don haka nan take ya shiga aikin lallashi. Sai da suka kusan minti talatin sanna ya samu ta goge hawayen ta saurare shi. ‘Wai me ya faru ne kike ta faman kuka haka sai kace wadda aka yi wa auren dole?’

    Ta ɓalla masa harara ta ɗauke kai sannan tace ‘Ni da ka kawo na zaɓi ɗakin da nake so a sama kusa da naka ɗakin shi ne za a kawo ni a ajiye ni a nan, ka sa ina nema na yi musu da masu kawo ni. Ya yi murmushin yaƙe ya sake kamo hannunta wanda ta riga ta fizge yana cewa ‘Haba ke kuwa? Ai na zata da suka zo kafi sun gaya miki.’

    Ta zumɓura baki ‘Ni babu wanda ya gaya min, sai da aka kawo ni kawai na ga an ajiye ni a ƙofar gida kamar wata wadda ba a so zuwanta ba. Nan ya shiga faman ba ta haƙuri da bayani tana faman fizgewa har dai ya samu ta sauko. Ta kalle shi tace ‘Amma gaskiya ni fa ba zan zauna a nan ba, matarka da yaranka da kai kuna sama.

    Kenan fa duk ranar da ba kwana na ba ni kaɗai ce a ƙasa bakin ƙofa. Gaskiya wannan tsarin bai yi min ba, ko dai a ba ni sama ko kuma gaskiya ka nema min wani gidan. Wannan ai duk wanda ma ya zo ya san matsayina. Ya ƙara matsawa ya janyo ta jikinsa ‘Kin ga, kada wannan ya dame ki. Ko da ban kama wani gidan ba za ki iya komawa saman in ya so ko ni sai na dawo ƙasan ku kuma gaba ɗaya ku yi zamanku a saman.’

    ‘Ni dai ba haka nace ba, amma gaskiya ka cika min alƙawari don ba zan yarda wata tana sama ni ina ƙasa ba. Haka ya yi ta lallaɓa ta har ya samu ta amince masa. Ya tattara musu kayansu suka wuce sama ɗakinsa wanda da farko ta so ta ƙi zuwa, sai kuma ta tuna gara ita ma ta hau saman ta ga yanda Khadeejan za ta yi.

    Da yake dama Hammad bai saba barinta baccin safe ba yau ɗin ma tun wajen 6am ya tashe su, ba ta buɗe ɗakin ba sai da ta yi wanka shi ma ta shirya shi. Ta riga ta ji motsinsu tun dare don haka ta san a ɗakin Mustaphan suka kwana. Tana fitowa ta taso Hafsa suka shiga kitchen.

    Ya siyo burodi kamar yanda ya saba duk dare, don haka nan da nan ta soyawa kowa ƙwai ta haɗa kayan shayi tsaf ta ba wa hafsa ta sauko da shi ƙasa. Kafin ƙarfe takwas ta jera komai da suke buƙata ita da yara na breakfast a parlor ɗin ƙasa. Tana shirin hawowa bene Hafsa ta biyo ta da wayarta ta miƙa mata tana ringing. Tana dubawa ta ga Baffa ne.

    Bayan sun gaisa ya ƙara yi mata nasiha sanna yace mata nan da awa ɗaya Nabeela ta shirya Ahmad zai zo ya ɗauke ta.Ba ta ji wata damuwa ba saboda dama ta san halin Baffa, ba tare da ɓata lokaci ba ta taso Nabila ta sanar da ita. Nan da nan ta haɗa kayanta don ko wanka cewa ta yi idan ta je gida ta yi abunta, haka ma breakfast cewa ta yi idan ta je gida ta ci kosai don tabbatar yau Lahadi ƙosai Mommy ta yi.

    Wajen 9am suna zaune a dining table ita da yara in banda Afaf wadda ba ta tashi ba ko kuma ba ta fito daga ɗakinsu ba. Breakfast suke yi suna ta hirarrakinsu Shukra sai labari take ba su suna dariya gaba ɗaya. Da sallama ya sauko daga benen ya ƙarasa gaban table ɗin yana cewa ‘Ina can ina nemanki a ɗakinki ashe kina nan ke da yara kuna ta jin daɗinku.’

    Ta yi murmushi ta kawar da kai. Ita da yaran duka suka gaishe shi, bayan ya amsa ya dube ta yace ‘Idan kun gama cin abincin ki zo ki ba ni nawa breakfast ɗin ni da ƙanwarki. Ta yi murmushin yaƙe tace ‘Da yake mu ma bread da shayi muka sha ba wani abu ba,  amma dama na ga bread ɗin da yawa ka siyo ga shi can mun bar muku guda ɗaya ka ɗauka ka haye muku da shi.

    Ko a nan za ku yi breakfast ɗin? Ya kalle ta da ɗan mamaki ya cije leɓe don ba ya son ya ja zancen a gaban yara yace ‘Um, idan kin gama dai kya hawo da shi.’ ‘Ok.’ Ta amsa cigaba da cin abincinta. Sai da suka gama cin abincinsu tsaf sannan ta ɗauki bread ɗin ta haye sama, tana shiga babu kowa a parlor ɗin don haka ta ƙarasa kan dining table ta ajiye bread ɗin ta shige ɗakinta.

    Kamar tare suka shiga ɗakin don ko zama ba ta yi ba ya shigo ya tura ƙofar, yana daga tsaye a jikin kofar yace ‘Wai ya na ganki a nan ina breakfast ɗin namu ni da ƙanwarki? Ta ƙarasa ta zauna a kan gadon ta jingine ta miƙe ƙafarta tana cewa ‘Oh, ga bread ɗin can na ajiye muku ai ko akwai wani abun ne?’

    Da mamaki yace ‘Ai na zata za ki ɗan dafa wani abu ko don saboda ganin ga baƙuwa kin kwana da ita a gidan. Ba ta san lokacin da dariya ta ƙwace mata ba, haka kawai maganar tashi sai ta ba ta dariya musamman da ta kalle shi kuma yana cewa wai “kin kwana da baƙuwa”

    Ta ɗan gintse tana ƙoƙarin saita fuskarta sanna tace ‘Na kawana da baƙuwa ko ka kwana da ita? Tea and bread muka ci fa kuma ga shi can na ajiye mata ita baƙuwar tawa, ina ga kamar ai dafa ruwan zafi bai kamata ya zama matsala ba ga wanda aka ba wa burodi ko? Ya ɓata rai saboda kwata-kwata bai zata haka ba; a iya saninsa sai sun kwana bakwai da amarya Khadeeja tana yi musu girki sannan sai a raba kwana amma ga shi tana nema ta kawo masa raini.

    ‘Ba fa na son raini Khadeeja, duk wanda ya ƙara aure matarsa ta gidan ita ce take yi wa amarya girki har sai ta kwana bakwai amma zan zo ina miki magana kina min wani zancen banza. Ai ko bazawara na aura kin san ya kamata ki yi mata abinci na kwana uku balle budurwa. Ta kalle shi ta kawar da kai; babu yanda za a yi ta yi wa Naja girki sai dai duk abinda zai yi ya yi; ta tsani Naja ta tsani jin sunanta.

    Wataƙila da a ce ya biyo ta hanyar da ta dace wajen sanar da ita zai ƙara aure da wadda zai aura da haushin da take ji bai kai haka ba, amma gaskiya babu abinda zai sa ta yi wa wata Naja girki. Ya auro matarsa ya gama more kwanan amarci sanna ita kuma bayan bacci da ba ta yi cikin nutsuwa ba kuma ita yake so ta tashi da sassafe ta haɗa musu breakfast na warware gajiya, bata taɓa ganin rainin hankali irin wannan ba.

    Ta ɓata rai sannan tace ‘Ba a biya mana wannan hadisin ba a islamiyya. Mamaki ya kama shi ya buɗe baki amma ya rasa abinda zai gaya mata. Yana kallo ta zame ta gyara kwanciyarta ta juya masa baya. Bai shirya da wannan mahaukacin taurin kan nata ba wanda idan ta fara shi sai duk garin kowa ya ji.

    Ya ɗan tausa muryarsa yace Bana son wasa Khadeeja, don Allah ki tashi ki samarwa yarinyar nan abinci. Next week ai za ku raba girkin kowa ta dinga yin nata, amma for now ki tashi ki ba mu breakfast. Ta sake gyara kwanciya ba tare da tace masa komai ba. Ya kalli kasa yana jijjiga kai don ya san ta gama magana; takaici ya kama shi.

    To yanzu ya za a yi tana amarya ya ba ta bread ruwan zafin ma a ce sai ta dafa. Haka ya fice daga ɗakin yana wasi-wasi. Yana ficewa ta juyo ta harari ƙofar kamar yana wajen ta ja dogon tsaki tace ‘Ɗan rainin hankali!’

    Yana shiga ya tarar da ita ta fito daga wanka tana shiryawa. Tun kafin ya gama shiga ɗakin tace ‘Allah ya sa dai an gama abinci don wallahi yunwa nake ji kamar an min sata a ciki. ‘Akwai dai bread, sai dai idan kin fito ki dafa ruwan zafi da ƙwai haka sai mu karya.’

    Da mamaki ta kalle shi tana cewa ‘Ruwan zafin ma sai na dafa? Yau ne fa kwanana na farko a gidan, haba! Kitchen ɗin ma ban san inda yake ba. Cikin damuwa yace ‘To ko order za a yiwo? ‘Ni ban gane ba, wai ita matar gidan ba ta girki ne? Ya ƙarasa kusa da ita yana ƙoƙarin kama dogon gashinta da take tajewa yana cewa ‘Ki bar wannan maganar, ki zo mu je na nuna miki kitchen ɗinki sai ki samar mana ruwan zafi mu karya.

    Idan kuma akwai inda za ki iya yiwo mana order a kawo nan da awa ɗaya haka to sai na tura kuɗin. Ta jijjiga kai ‘Gaskiya babu, sai dai ko na rana don wallahi kwana bakwai ɗin nan sai na yi su ba tare da na ɗora tukunya ba. Don ni abinda na sani matar gida ko ‘yar gwal ce idan aka yi amarya ita take girki kafin a zauna a raba.

    Haka ya yi ta ba ta haƙuri yana lallaɓa ta, daga ƙarshe ta shirya suka sauko parlor ɗinta ta dafa musu ruwan zafi sanna ya ɗebo ƙwai ta soya musu. Wajen 12pm ya haɗa su a parlor ɗinsa ya yi musu introduction; ita Naja amarya sai muzurai take yi tana wata yanga, ita kuwa khadeeja cike da walwala ta yi mata maraba suka gaisa babu laifi.

    Ya sanar da su idan an kwana bakwai za su raba kwana kowacce kwana biyu. Ba ƙaramin mamakin Khadeeja ta yi ba, ko da yake wannan ba baƙon abu ba ne a wajensa. Ta yi masa rashin kunya mintuna kaɗan kuma ta koma kamar ba ita ba. Shi yasa a lokuta da dama yake kasa fassara ta.

    Ganin walwalarta ya saka ya sa rai cewa za ta yi abincin rana da su, amma gudun kada a kuma ya sa ya bi ta don ya tabbatar. Sai dai ta tabbatar masa da cewa ta riga ta dafa abincin rana tun da safe kuma nasu ne ita da yara, sauce ne kawai a fridge za ta ɗumama ta haɗa musu salad su ci. Ko amsa bai ba ta ba ya fice ya bar ta a ɗakin, ta bi bayansa da harara tana dariya.

    Don haka da rana ta yi sai kawai ya yiwo order ɗin abinci aka kawo musu har gida, haka ya kirawo yaransa gaba ɗaya suka haɗu da Naja suka ci suka ƙoshi. Ita kuma Khadeeja ko damunta abun bai yi ba, ta ci abincinta ta zuba wa Hafsu sannan ta bayar da ragowar. A haka aka ƙarasa wannan amarcin. Kullum Khadeeja za ta dafa abincinta shi kuma zai yiwo order su ci su ƙoshi tare da amarya da yaransa. Babu wanda ya taɓa yiwa Khadeeja tayi ita kuma ba ta taɓa tambayarsa nata kason ba.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin

    Edita@rumasau-kallamu

  • Wasu Kayan Sana’ar Saƙa

    Wasu Kayan Sana’ar Saƙa

    1.Uwar Masaƙa
    2.Allera
    3.Ɗan Iffa
    4.Cakarkari
    5.Hanjin ƙoshiya
    6.Ƙoshiya

    7.Kunkuru
    8.Jakki
    9.Mataki
    10.Matuƙi
    11.Matsefa
    12.Takala
    13.Wuƙa ko aska

    FASIHIN KAITA,

    Danna nan don karanta Wasu Kayan Aikin Fawa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Wasu Kayan Aikin Fawa

    Wasu Kayan Aikin Fawa

    1.Baho
    2.Barho
    3.Daro
    4.Jantadi
    5.Faranti
    6.Kurada

    7.Waya
    8.Tire
    9.Tsinka
    10.Tugufa
    11.Marari
    12.Wuƙa
    13.Kurada

    FASIHIN KAITA

    Karanta Wasu Kayan Aikin Sassaƙa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Wasu Kayan Aikin Sassaƙa

    Wasu Kayan Aikin Sassaƙa

    1. Gizago
    2. Ƙurfi
    3. Kibiya
    4. Matani
    5. Matankwari
    6. Tunga
    7. Kalaba

    FASIHIN KAITA

    Karanta Wasu Kayan Busar Hausawa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Matsayar Ɗanbala

    Matsayar Ɗanbala

    Lokacin da muke da manya,
    Lau muke ba a kashe wa.

    Zamanin da muke da manya,
    Babu bandits kaf Arewa.

    Sa’ilin da muke da manya,
    Babu kinafas Arewa.

    Lokacin da akwai su Baba,
    Duk da tarbiyya Arewa.

    Zamanin Ulama’u na nan,
    Babu mai kafurta babba.

    Lokacin da muke da manya,
    Ba mu yin rigima Arewa.

    Lokacin da su Inna na nan,
    Kanmu ɗai yake ba rabe wa.

    Lokacin Malamai su na nan,
    Ƙanƙana na bin na gabba.

    Lokacin su Waziri na nan,
    Malamai ba su fanɗare ba.

    Lokacin da muke da manya,
    Ba mu san Boko Haram ba.

    Zamanin da akwai mazaje,
    Ilimi namu bai zube ba.

    Lokacin da su Kawu na nan,
    Tsintsiya muke ba kawai ba.

    Yanzu da yake babu manya,
    Ba mu san asalin gabas ba.

    Yanzu da yake mun rasa su,
    Sai kashe mu ake Arewa.

    Yanzu da yake babu babba,
    Ƙanƙana ke zage babba.

    Tun da mun yi rashin su Inna,
    Dole mui ta ganin mu baibai.

    Kuma da yake ba magaji,
    Shi ya sa mu muke ta ɓarba.

    Babu babba a yau Arewa,
    In akwai sunansa kama.

    Na faɗa maka babu babba,
    In akwai ka kira shi yanzu.

    Da a ce ko muna da manya,
    Da ba mui ta ganin hakan ba.

    Da a ce da akwai su Baba,
    Ƙanƙana ba su zagi babba.

    Da da wanda muke jin tsoro,
    Da ba mu raba al’umma ba.

    Shehu Khalidu babu babba,
    Yanzu kaf a cikin Arewa.

    Wanga ita ce fahimta ta,
    Ko a gobe ina faɗa ma.

    Da da babba a yau Arewa,
    Da ba zan yi musun hakan ba.

    Ɗanbala daga Borno ne ni,
    Mai yabon a wurin Masoyi.

    Ɗan Amina abin nufina,
    Na riƙe shi ba zan shika ba.

    Ahlihi nasa na riƙe su,
    Ba riƙon igiya na yo ba.

    Da Sahabu ina biyan su,
    Ban da masu kiran gumaka.

    ©
    Mohammed Bala Garba
    6:39pm
    30 November, 2025.

    Karanta Ta’aziyyar Hauwa Ƙamshi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin

    Ranar ɗaurin aure tun da sassafe baƙi suka fara zuwa gidan, zuwan nasu ma sai ya fi mata sauƙi tunda ya ba ta dama ta baro Mustapha a sama ta taho wajen baƙin. Ba za ta iya tsayawa a inda yake ba yana ta faman walwala yana kai wa da kawowa yana kwalliya, sai ta ga kamar yana yi ne don ya ba ta haushi.

    Don haka ta ji daɗi sosai da aka ce mata Yaya Jidda ta zo da mutane. Nan ta sauko suka gaisa, ta buɗe musu ɗakin baki tunda dama a ɗaya parlor din suka sauka wanda ba na amarya ba. Sosai Yaya Jiddan ta so su hau sama amma sam Khadeeja ta ƙi ba da fuska, don haka suka haƙura suka baje zugarsu a nan ƙasan.

    Duk wani abu da suke buƙata na cefanensu sun taho da shi da manyan tukwanensu, shi kansa Mustaphan bai san a nan za su yi girkin ba da ya biya an girka musu don ba ya son a ɓata gidan nan. Amma haka yana ji yana gani kafin ma ya sauko an sauke kayan aiki an hau ƙoƙarin hura wuta; a cewar Yaya Jidda sun bayar a yi musu tuwon shinkafa da masa da shinkafa amma masu yi miyarsu ba ta daɗi don haka su za su girka tasu miyar.

    Nan da nan ya ja motarsa ya fice daga gidan suka tafi ɗaurin aure. Tunda Mustapha ya fita ta ɗauki Hammad ta haye sama, suka zauna da Nabila wadda dama ba ta sauko ba ma balle ta ga kalarsu. Hafsa mai aikinta dai ita dole ta zauna ana komai da ita, sannan ga su Afaf waɗanda tuni suka shiga cikin dangi ana ta rawar kai.

    Can kusan la’asar su Yaya Mama suka zo ita da cousins ɗinsu mutum biyu da kuma ƙannen Mommy su biyu. Bayan sun gaisa da Yaya Jidda a parlor ɗin ƙasa kai tsaye suka haye sama. Ba su daɗe da hayewa ba kuma Hajia mahaifiyar Mustaphan ta iso da tata zugar, nan da nan gida ya cika ana ta kai wa da kawowa.

    Bayan an gaggaisa Hajia ta dubi Yaya Jidda tace ‘Ina Khadeejan ne? Ban ganta ba. Inna Ramla ta yi sauri ta amsa kafin Yaya Jidan tace wani abu ‘A a suna saman benen nan fa ita da ‘yanuwanta, benen da ‘yan gidan ma ban ga suna hawansa ba tunda duk ga su nan tare da mu.’

    Ta sake duban Yaya Jidda tace ‘Ban gane tana sama ba. Ta taɓe baki ‘Toh haka muka gani, tana saman ita da ‘yan uwanta. Kafin tace wani abu Khadeejan ta sauko parlor ɗin da sallama; Shukra ce ta hau ta gaya mata zuwan Hajia shi ne ta yi sauri ta sauko saboda kada ta yi laifi.

    Ta ratsa mutanen har gaban Hajia ta tsuguna ta gaishe ta cikin girmamawa sannan ta yi mata Allah ya sanya alkhairi. Ta dubi mutanen duk suka gaggaisa tana kama sunan waɗanda ta sani. Har ta miƙe Hajia tace ‘Ina Mommyn naki, ba ta zo ba? Tace ‘Eh, ba ta zo ba, su Yaya Mama ne kawai suka zo.’

    ‘To madalla.’Ta miƙe ta fice tsakar gidan suka gaggaisa da mutanen da ke zazzaune, ta kalli wajen da su Yaya Jidda suka yi aikinsu yanda ya yi kace-kace ta ɗauke kai. Har ta juya za ta koma ciki Habib ya turo gate ya shiga, daga inda yake ya kirawo sunanta ‘Anti.’ Ta tsaya ta juyo ‘Yaya Habib, ina ka shiga ne tun ɗazu Shukra take nemanka.’

    ‘Ina nan Anti, wajen abokina na je. Yanzu ma wallahi yunwa nake ji, abinci za ki ba mu. Tace ‘To ai Anti Jidda za ka yi wa magana ga abinci nan an dafa. Ya shafa kai yana cewa ‘Anti ai na gaya mata, tuwo ne fa da masa Anti don Allah ni dai ki ba ni abinci. Ta yi dariya don ta san tabbas Habib ba ya cin tuwo da masa da ma abincin gargajiya da yawa, tace ‘Kaje sama wajen Anti Nabeela ta zuba maka.’

    Har ya wuce yace ‘Ni da abokaina Anti? ‘Eh, ka gaya mata ko ku nawa ne. Bai jima da hayewa ba ita ma ta bi bayansa, kafin ta je ya ɗauko flask Nabeela ta zuba masa shinkafa da kaza ga coleslaw da sauce ɗin dankalin bature wanda duk a nan saman suka dafa shi tunda ba su da yawa. Ya ɗauko kwanukan ya sauko ya fice.

    Haka aka yi ta hada-hada ana kai wa da kawowa. Sai dai zuwan Hajia ya sa babu yanda Khadeeja za ta yi dole ta zauna a ƙasa a yi da ita, don haka Yaya Mama da kuma Anti Innani suka sauko suka gaida Hajia suma suka zauna don taya ta zama. Bin mutane kawai take yi da kallo zuciyarta tana ƙuna; ji take a ranta kamar da za a buɗe zuciyarta to da za a tarar tana turiri saboda zafin da take ji.

    Fuskokinsu take kallo ɗaya bayan ɗaya, musamman Hajia wadda ake ta yi mata Allah ya sanya alkhairi ana barka da arziƙi tana amsawa kamar wadda aka yi wa bushara da kujerar Makka. Haka tacigaba da zama a cikinsu tana jin kamar ta ruga da gudu; sai dai lokaci zuwa lokaci ta kan tashi kamar mai duba wani abu ta haye sama, idan ta ja numfashi ta share ƙwalla sai ta dawo.

    Haka suka yi ta yi har gefin magriba; abokan ango suka zo da motaci suka ɗebi yan ɗauko amarya sannan suka tafi ɗauko amarya. Har ta yi sallar magriba zuciyarta tana dukan uku-uku; ta rasa ma abinda yake ɓata mata ran. Tabbas tana kishi to amma ta fi tsoron rashin adalcin da take ji a jikinta Mustapha zai shimfiɗa; amma tana addu’a kuma ba za ta fasa ba don ta san tabbas Allah ne gatanta.

    Wajen 8:30pm aka shigo da amarya, nan da nan gida ya ɗau guda mata na ta shewa. A lokaci guda kuma bugun zuciyar Khadeeja ya ƙara gudu. Tana zaune a kan kafet kusa da Hajia; duk su Yaya Jidda suka miƙe suna tarbar amaya, aka buɗawa waɗanda suka riƙo amarya suka ƙarasa gaban Hajia wadda take hakimce a kan 3-seater. Aka zaunar da amarya a gaban Hajia, mata suka cigaba da zabga guɗa.

    Sai da hayaniya ta lafa sannan aka gaisa da masu kawo amarya, suka miƙa ta hannun Hajia. Hajia tace ‘Masha Allah, Allah ya sa wannan aure har aljannah. Wannan ai ‘yar uwarta za a ba wa ita ba ni ba, ina Khadeejan ne da fa tana nan zaune kusa da ni. Wadda take zaune kusa da Khadeejan tace ‘Gata nan fa.’

    Mutane ne suka zauna a gabanta suka kare ta da aka shigo da amaryar; nan da nan aka buɗa. Hajiya ta miƙa hannu yayin da Khadeejan ta matso tana cewa ‘Zo Khadeeja ga ƙanwarki an kawo miki. Ta sunkuyar da kanta tana duban cinyarta domin tana tsoron kada idanuwanta su ba da ita ta hanyar tunkuɗa hawaye a daidai wannan lokacin.

    Hajia ta kama hannunta sanna ta kamo hannun Naja ta ɗora ta haɗa ta riƙe tana kallon Khadeejan tana cewa ‘Ga amanar ƙanwarki nan, ki riƙe ta amana ku zauna lafiya ku samarwa da mijinku nutsuwa. Allah ya haɗa kayuwanku. Mata suka kaure da amshi ‘Amin. Amin.’

    Wata cikin iyayen amaryar ta karɓe ta cigaba ‘Eh gata nan amana, a yi haƙuri uwargida sarautar mata ku zauna cikin amincin Allah domin kayan Allah na annabi ne. Aka sake kaurewa da guda. So take ta zare hannunta amma Hajia ba ta ba su dama ba; bugun zucuyarta ƙara sauri yake yayin da take jin hanunta kamar ta riƙe wuta.

    ƘoƘari take ta dafe bakinta saboda kada abinda yake zuciyarta ya fito; Amana! Ita za a ba wa amanar matar Mustapha? Ina ruwanta da ita? Ko sun yi mantuwa ne? Shi da ya ga zai iya da amanar ai ya yi gammo ya ɗauko. Don me za su ce ita aka ba wa amana? Tabbas wanna amana ce da ba ta karɓa ba kuma ba za ta taɓa iya karɓa ba.

    Sai da aka gama addu’oi sannan Hajia ta saki hannuwansu, cikin dabara Khadeeja ta faki ido ta goge ƙwallar da ta taru a kwarmin idonta. Ba daɗewa kuma aka fara miƙewa aka kama hannun amarya aka nufi ɗakinta, a haka ne Khadeeja ta samu ta sulale ta haye sama, yayin da su kuma matan suka bi bayan amarya.

    Haka ta koma cikin su Yaya Mama ta cigaba da dagewa, su kuma suna ta ba ta baki da nasiha. Wajen 9pm gayya ta fara watsewa, aka kirawo ta ta yi sallama da Hajia, ba daɗewa kuma su Yaya Mama suma suka yi mata sallama suka bar ta ita da Nabeela. Tana zaune a gefen gadonta tana jiyo yara wajen 11pm suka hawo saman, gaba ɗayansu sai da suka leƙa ɗakinta suka yi mata sai da safe amma banda Afaf, suka wuce ɗakinsu inda suke kwana tare da Hafsa.

    Ba su daɗe ba kuma Nabila ta fito daga ɗakin baƙin da yake saman ta turo ƙofar ɗakin a hankali ta shiga, ta wuce Khadeejan a gefen gadon ta zagaya ta kwantar da Hammad a gafe ta lullube shi. Ta zagayo ta zauna a kusa da Khadeejan, ba ta motsa ba kamar ma ba ta san an zauna a kusa da ita ba. Ta mika hannu ta dafa nata hannun da yake kan cinyarta tana kallon fuskarta tana cewa ‘Yaya Khadeeja ga Hammad fa na kwantar miki da shi.’

    Ta kalle ta suka haɗa ido, ba tare da tace komai ba ta sake kawar da idonta saboda ta tokare hawayen da suke neman ƙwace mata. Nabila ta ɗan matsa hannunta tana cewa ‘Ya Khadeeja. Kafin tace wani abu hawayen ya fara bin idonta, gaba ɗaya ta sake su saboda yanda take faman riƙe su tana jin kamar an ɗora mata dakon wani kaya mai nauyi.

    Gaba ɗaya ta faɗa jikin Nabeela wadda ta rungume ta gaba ɗaya suka sa kuka. Ita Nabeela auren ma gaba ɗaya ya ƙara ba ta tsoro, kuma ta tabbatar ko da wanne lokaci za a iya ɗaura nata auren; tunda da ba don Ahmad ya tafi UK ƙaro karatu ba da tuni ta shekara a ɗaki. Ita kuma Khadeeja gaba ɗaya komai ma ya tsaya mata; tana dai fatan Allah ya sa Mustapha ya zama mai adalci.

    A hankali suka fara lafawa, Khadeeja ta zare jikinta ta kalli Nabeela. Suna haɗa ido suka tuntsire da dariya duk da hawayen da suke fuskokinsu. Suka riƙe hannun juna suna murmushi. Khadeeja ta dube ta tace ‘Sorry. Itama murmushin tayi mata tana cewa ‘Its’s ok, you will be fine in sha allah. Komai zai wuce kamar ba ayi ba.’

    Murmushi ta sake mayar mata sanna tace ‘Ki je ki kwanta, na san yanzu Abbansu zai shigo. Ta sake rungume ta sannan ta yi mata sallama ta fice ta rufe mata ƙofa. Ba tare da ɓata lokaci ba ta miƙe ta shiga banɗaki inda ta yiwo wanka sannan ta fito da alwala, ta shirya ta sa kayan baccinta sannan ta kabbara sallar isha’i.

    A nan ya shigo ya same ta tana zaune a kan dadduma tana gyangyaɗi; kallo ɗaya ta yi masa ta ji zuciyarta ta sake komawa cikin damuwa wadda ta fi ta da. Sai wani faman yage baki yake yana muzurai a lokaci guda; a sanin da ta yi masa ta san murna ce da ɗoki yake yi na amarya kuma yana ƙoƙarin tabbatarwa ita ɗin ba ta kawo masa cikas ba.

    Nan da nan ta danne duk wata damuwa da take ranta ta ƙaƙalo murmushi ta yi masa sannu da zuwa. A tsaye ya amsa ya yi mata bangajiyar biki sannan yace ‘Um ni bari na je, na ga ke ma bacci kike ji. In ya so da safe na shigo da ƙanwar taki ku gaisa. ‘To Allah ya kai mu. Ya juya ya fice ya rufo mata ƙofa.

    Ta ji daɗi sosai da ya sanar da ita ba zai shigo da matarsa a wannan daren ba, domin gaba ɗaya a gajiye take. Ba jikinta ba har ruhinta ma ji take ya gaji, fatanta kawai waɗannan kwanakin su wuce ko kuma ma ta farka ta ga mafarki take yi.

    Ta ga rayuwarsu ta dawo kamar yanda take a farkon aurensu; ko da yake a farkon auren ma babu wani abun kirki da za ta ɗorar; kamar dai gara ma tace rayuwarsu ta dawo yanda ake kafin aure. Sai da bacci ya fara ɗibanta sannan ta tashi ta kwanta a kan ganto ta kashe fitila.

    Edita@rumasau-kallamu

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Goma Sha Tara