Category: WikiHausa

Yadda ake amfani da WikiHausa

  • Yadda ake Gudanar da Wasan Ƙunshi

    Yadda ake Gudanar da Wasan Ƙunshi

    Da zarar watan azumin ya kama, watan (Ramadan), ‘yan mata su ne masu ko suke gudanar da wannan wasa a ƙarƙashin tallafin ‘yan uwa da abokan arziƙi na danginsu da ma na dangin surukai, har ma da abokan ‘ya’yansu, da samarinsu da abokan samarin, da duk waɗanda suka sani suna da alaƙa da su.

    Wannan alaƙa ta ‘yan uwantaka ko kuma ta zaman tare, a ɓangaren cinikayya ko kuma a zaman unguwa ɗaya, mutun ya kan bayar da tallafinsa na gudanar da wannan wasa da zarar watan ya kama na azumi daga dangi na kusa da na nesa.

    Yadda ake karɓar wannan tallafi shi ne yarinya za ta yi wanka ta ɗaura atamfa kyakkyawa kamar ranar Sallah, a wannan lokaci tana bin gidajen danginta, tana zuwa gaishe su, inda za ta faɗa musu ta zo karɓar hatsin ƙunshi. Nan take idan wurin da za a yi wasa da dariya ne, sannan a ɗebo abin da ya samu a ba ta.

    Waɗansu sukan bayar da gero, ko dawa ko maiwa ko shinkafa ko kaza ko zakara ko ɗan shila. Waɗansu na bayar da zabi waɗansu ƙwai waɗansu kuma sukan bayar da kuɗi da dai sauran abubuwan da mutum yake da halin da zai iya bayarwa. Idan ta haɗa waɗannan kayayyaki ta kammala karɓar tuwon ƙunshi na wannan shekara ke nan.

    Abu na gaba, za ta tafi ta ɗauki ‘yar ƙunshi. Ita ‘yar ƙunshi yarinya ce ‘yar ƙarama za ta samu ko ‘yar yayarta ko ‘yar ƙanwarta ko kuma ‘yar uwar ɗakinta, ko kuma ‘yar abokiyar wasanta, ko kuma wata daga cikin dangi. Wannan yarinya ita ce ‘yar ƙunshinta, sai ta sanar da mahaifan yarinya, yarinyar wacce ba ta wuce shekara shida zuwa shekara tara ba (6-9).

    Daga wannan lokaci su ma iyayen yarinya ta same su, domin kuwa su ma za su haɗa kayan abinci su ba uwar ɗakin ‘yarsu, daga wannan lokaci wannan yarinya da aka ɗauko wato (‘yar ƙunshi), shi ke nan duk wata ɗawainiyarta, ta koma kan uwar ɗakinta, (wato wannan budurwa).

    Wankanta da shanta da cinta, waɗansu ma idan suna da hali har ma tufafinta duk sun koma kan uwar ɗakinta. Wannan nauyi ya ɗoru har lokacin da za a yi auren wannan budurwa. Wannan yarinya ita ce za ta zama ‘yar zaman ɗaki kafin kwana arba’in (40).

    Za a saka tabarma ta kaba (turarriya) a yi mata ado mai kyau. Wannan tabarma za a ba wa ‘yar ƙunshi a ce mata ga tabarmarmu ta cin tuwon ƙunshi, saboda haka, wannan yarinya ita ce mai alhakin kula da ita, bayan an kammala waɗannan shirye-shirye. Ga waɗanda suke da hali suna yin sababbin ɗinkuna, waɗanda kuma ba su sami halin hakan ba, sukan sanya tufafinsu kyawawa.

    Ita wannan yarinyar za a yi mata ƙunshi tare da uwar ɗakinta kafin lokaci ya rage kwana ɗaya ko biyu. A ranar da ake azumi na ashirin da shida (26), a wannan rana kowace budurwa komai girmanta, ba za ta yi azumi ba, saboda rana ce ta wannan wasa na ƙunshi.

    Dangane da waɗancan kayayyakin abinci da kuɗaɗe waɗanda aka samu daga dangi da abokan arzuƙa. A ranar ashirin da shida (26) har zuwa ashirin da takwas ana girke-girke, na alfarma a duk gidan da budurwa take, idan an gama dafa abinci, su yara ƙanana-ƙanana suna shiga gida-gida suna cewa a ba su tuwon ƙunshi, kowanne da kwanonsa, za a karɓa a zuba musu.

    Da rana ta yi, za a tafi wani gida da aka ware ko dai gidan wata Amarya a unguwar ko kuma gidan wata mata wadda ta yi fice a wannan unguwa, inda ‘yanmatan suke wasanninsu tare hirarsu a gidan, sai su ce bana a gidan wance za a ci tuwon ƙunshi.

    Idan an kammala dafa abinci kowacce ‘yar ƙunshi da aka ɗauko za a ɗora mata wannan tabarma a saka ta a tafi wancan gida da aka ambata a can za a ci tuwon ƙunshi. Kowacce budurwa a nan gidan za ta ɗauko abincinta ta ci. Kuma kowacce zata zo da sabuwar tabarma da aka saƙa ta musamman.

    A wancan lokaci yara maza suna zagawa wurin waɗanda suka sani, suna cewa a ba su tuwon ƙunshi, kowanne da kwanonsa. A ɓangaren yarinyar ‘yar ƙunshi a ranar babu abin da za ta yi sai zama da kuma cin abinci wadda take so. Sannan a hannu guda kuma, ita wannan matar gida, ‘yanmata za su zuba abinci a kwano a kai mata.

    Haka abubuwan za su ta tafiya tare da kai wa-da-komowa wasu zau tafi dandali wasu kuma bayan gari ya danganta inda suka ga dama har bayan sallar la’asar ana guje-guje da tsalle-tsalle da wasannin gargajiya iri-iri da gata da waƙoƙi da sauran wasanni har zuwa almuru ko kuma faɗuwar rana, sai kuma a dawo wannan gida, kowacce ta rage kuma ta ajiye abincinta haɗi da tabarma ta za a ɗauko sauran abincin a ƙarashe shi, daga nan an gama cin tuwon ƙunshi na ranar farko.

    A rana ta biyu (2) wato ranar ashirin da bakwai (27) da kuma ranar ashirin da takwas (28), duk waɗannan wasannin iri ɗaya ne, sai kawai hidimar wata rana tana fin ta wata rana, a nan ake samun bambanci. To idan an yi wannan abinci na ranar ashirin da takwas ga wata (28), wato ranaku uku (3) ke nan ana gudanar da wannan wasa, to shi ke nan an kammala cin tuwon wasan ƙunshi.

    Ita kuma ‘yar ƙunshi za a yi mata saye-saye daga gidan su uwar ɗakinta (wadda ta ɗauko ta), sannan ta ɗauke ta mayar da ita wurin iyayenta, shi ke nan wannan ‘yar ƙunshi ta yi uwar ɗaki, shi ke nan duk shekara ta zama ita ce ‘yar ƙunshinta ba wacce za ta ɗauki wannan yarinya sai ita.

    Yayin da wannan budurwa ta kawo munzalin ayi mata aure, ita mahaifiyar ‘yar ƙunshi sai ta taka rawar gani a al’amarin auren, idan an yi auren ‘yar ƙunshin da ita za a tafi gidan mijin, sannan a canza mata suna ta koma ‘yar burganci”, ma’ana mai yi wa amarya aikace-aikacen gida, da ayyukan da amaryar nan za ta yi. Wannan ‘yar burganci ita ce mai yi mata hidima kamar share-share da wanke-wanke da duk wani aiki da amarya za ta yi. A nan gidan take kwana take tashi, har kwana arba’in.

    Game da azumin da ba a yi ba wato suka sha ya tafi shi ke nan, sannan kuma sauran azumi guda biyu (2) ko ɗaya (1) ba kowace budurwa rama shi ba ko kuma take ƙara yinsa ba, da yawa ba sa ramawa, wasu kuma sukan ƙara har zuwa ashirin da tara ko talatin (30) ya danganta da yadda aka yi a wannan shekarar, ashirin da tara (29) ko talatin (30).

    Wanan bayanin an ciro shi ne daga maƙala mai taken Nazarin Wasan Ƙunshi Jiya Da Yau A Ƙasar Gaya wadda Magaji Ahmad Gaya Ph.D Sashen koyar da Hausa Jami’ar Northwest, Kano ya wallafa.

    Emai: magaya@nwu.edu.ng

    0806600903

    Danna nan don karanta Bukukuwa Da Wasanni Da Nishadi Na Bahaushe

    Edita@rumasau-kallamu

  • Menene Wasan Ƙunshi?

    Menene Wasan Ƙunshi?

    Wasan ƙunshi, yana daga cikin nau’o’in wasannin gargajiya wanda samari da ‘yan mata suke aiwatarwa shekara-shekara. Sannan yana ɗaya daga cikin wasanni na al’ada da ake aiwatar a watan cika ciki.

    Mafi tsufa daga cikin mutanen da aka gana da su sun bayyana cewa wannan wasan haka suka tashi suka ga ana gudanar da shi ba za su iya tabatar da lokacin da aka fara shi ba. Sun bayyana mana sunayen iyaye da kakanninsu da suka yi wannan wasa irin su: Uba maiwake da Hamza Kashi da Tokare da sauransu. (Hira da Shehu Maroɗo).

    Wasan ƙunshi wasa ne na Hausawa na gargajiya a ƙasar Gaya ya nuna al’ada ce daɗaɗɗiya “wasa ne da ake gudanar da shi domin nuna farin ciki musamman a cikin watan azumi.”(Hira da Ɗahiru Roka). “Wasa ne na gargajiya wanda ake haɗuwa samari da ‘yan mata da yara wajen nuna farin ciki da sanya nishaɗi.” (Hira da Rabi’u).

    Don haka,a taƙaice wasan ƙunshi wasa ne wadda ake gudanar da shi a tsakanin ‘yan mata da samari domin sanya nishaɗi tare da motsa jiki bisa tsarin gargajiya.

    Ranar Wasan Ƙunshi

    Babu wata rana da ake sanyawa domin a tsayar da lokaci ko wuri wajen aiwatar da wasan. Wannan ya samo tun asali tun farko farko samar da wasan, saboda haka kowa ya san watan da kuma ranar aiwatar da shi.

    Amma a wannan lokaci ko kuma a yanzu saboda tasirin zamani ana yin la’akari da ranakun da ba a yin aikin gwamnati, misalin Asabar ko Lahadi, domin ranaku ne da ba a zuwa makarantun boko, suna yin haka, saboda wasu daga cikin ‘yan matan da ake shirya wasan tare da su, suna a makarantun kwana.

    Hanyoyin Sanarwa da Sadarwa

    Kafin samun kafofin sadarwa na zamani da kuma hanyoyin isar da saƙo na karta kwana, babu wata hanya da ake amfani da ita wajen sanar da wasan sai ta hanyar gargajiya, ita ce wannan ya faɗawa wannan da dai sauran hanyoyin isar da saƙo na gargajiya.

    Amma a sakamakon juyawar zamani ana amfani da waɗancan kafafen yaɗa labarai da kuma wayoyin tafi da gidanka wajen faɗakar da al’umma, musamman samari da ‘yan mata.

    Masu Aiwatar da Wasan Ƙunshi

    Bisa al’ada yawancin wasannin gargajiya a ƙasar Hausawa, ya fi ta’alaƙa ga samari da ‘yan mata musamman wajen aiwatar da shi, domin su ne matasa manyan gobe. Haka abin yake a wasan ƙunshi, masu aiwatar da wannan wasa su ne samari da ‘yan mata sai kuma ƙananan yara waɗanda suke taimakawa wajen gudanar da shi, duk da kasancewar iyaye mata ba abar su a baya ba, domin suna bayar da gagarumar gudummawa tare da ruwa da tsaki wajen aiwatar da wasan.

    Lokacin Gudanar da Wasan Ƙunshi

    Wasan ƙunshi, wasa ne da ake gudanarwa shekara-shekara, ana gudanar da shi a cikin watan azumi (Ramadan). Watau ana fara wa daga ranar ashirin da shida (26) ga watan, zuwa ashirin da takwas (28) ga wannan wata, wato kwanaki uku (3) ake yi ana gudanar da shi

    Tanade-Tanaden Wasan

    Iyaye mata sukan tanadi wasu abubuwa waɗanda za su taimakawa ‘ya’yansu wajen alkinta kafin lokacin aiwatar da wasan, a wasu lokutan akan tanadi kayayyakin amfanin gona da aka samu daga roro ko kale ko ja-gindi ko tsinka da sauransu, wacce yarinyar ta samo domin adanawa sai lokacin ya zo, wadda da irin wannan ne ake sayarwa domin a yi mata sabon ɗinki da takalmi da a warwaro da sauran kayan ƙawa.

    Haka nan, Budurwa takan kai ziyar gidajen ‘yan uwa da abokan arzuƙa, da sauran dangi, bayan sun gaisa akan ba ta wasu abubuwa da suka haɗa da; sabulai da turare da kayayyakin abinci kamar hatsi da wake da gyaɗa da sauran nau’o’in kayan amfanin gona. Wasu kuma sukan bayar da kuɗi, dukkaninsu suna daga cikin tanade-tanaden gudanar da wasan ƙunshi.

    Sannan samari da ‘yammata sukan tanadi kuɗaɗe, idan ranar wasan ta kusanto sukan je kasuwa su sayo kayayyakin da suke da buƙata. ‘Yammata ne suke ɗaukar nauyin saye-sayen kayayyakin da ake da buƙata, domin samarinsu da iyayensu na samar masu da kuɗaɗen, domin su sami damar sayen kayayyakin da suke buƙata.

    Amma a yau abubuwa wasu sun sauya saboda sauyin zamani inda samarin da ‘yanmatan su ne suke tanadar waɗannan abubuwa da kansu da suka haɗa da; kayayyakin ciye-ciye wadda suka haɗar da; biredi da cincin da biskin da doya da kwai da arnaki da biri-biri. Sai kuma kayayyakin shaye-shaye, waɗanda suka haɗa da; kyayyakin tsotse-tsotse, misalin; alawar madara, da sauran alawoyi, iri daban-daban.

    Ana amfani da kayayyakin shaye-shaye na zamani, irin su lemukan roba da bobo da yagot da lemon kwalaba kamar fanta da kokakola da diyu da kuma lemukan gwangwani kamar maltina da fefsi da lakasera da mirinda da sifirayit, da lemukan kwali, misalin fayif alayif da kuma ruwa iri daban-daban.

    Daga cikin samari da ‘yan mata masu aiwatar da wannan wasa akan samu wasu daga cikinsu sukan ɗinka sababbin tufafi domin yin amfani da su, a lokacin wasan. Amma yin ɗunkuna ba wajibi ba ne. Saboda haka, ana samun wasu daga cikin samari da ‘yan mata waɗanda ba su yi sabon ɗinki ba a lokacin wasan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga maƙala mai taken Nazarin Wasan Ƙunshi Jiya Da Yau A Ƙasar Gaya wadda Magaji Ahmad Gaya Ph.D Sashen koyar da Hausa Jami’ar Northwest, Kano ya wallafa.

    Emai: magaya@nwu.edu.ng 08066009039

    Karanta Waiwaye A Kan Al’adun Gargajiya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Bakwai

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Bakwai

    Kamar yanda Khadeeja ta faɗa ba ta sake kula hidimar yaran a ranar da ba ita ce da kwana ba, sai dai ranar kwanata tana fitowa ta sallami kowa sanna ta cigaba da harkarta. Idan kuma dare ya yi ta shiga ɗakinta ta yi kwanciyarta don ta tabbatarwa Mustapha cewa ta ba shi kwanan.

    Ranar Asabar ce don haka yara babu makaranta duk suna gida, kamar yanda suka saba tunda Khadeeja ta ƙi hidimar yaran to duk ranar girkin Naja Anti Wiyya ce take abinci har yaran. Ita kuma Najan ita ce za ta tsaya a kansu su yi wanka su shirya, sai dai ranar da ba ta tashi ba dole haka Mustaphan yake tashi ya yi ta faman yi musu faɗa har ya samu su gama shiryawa a hankali.

    Afaf ce ita kaɗai a parlor ɗin Naja tana kallo saboda TV ɗin parlor ɗinsu Startimes ce ita kuma ta fi son DSTV wadda take parlor ɗin Naja; yayin da Anti Wiyya take ta kai wa da kawowa tana ƙoƙarin dora a bincin rana. Ta wuce Afaf a parlor ta shige ɗakin Naja inda ta same ta a kwance a gefen gado; bayan ta amsa sallamarta ta ƙarasa ta zauna a gefen kafarta kamar a fusace.

    Tace ‘Sannu Anti, kina ta hidima. Lallaɓa ta nake yi idan ta ƙoshi goya ta zan yi na fito na taya ki. Salaman ma ina jin yau ba za ta zo ba; ko wa take so ya yi mana wanke-wanke da sharar oho ga girki. Ta yi tsaki ta kawar da kai tace ‘Kin ganni a cike nake da haushinta, ga shi kamar ta shirya wulaƙanci tunda yau wanke-wanken ya fi na kullum yawa sannan ta ƙi zuwa.’

    ‘Hmm! Ai sai haƙuri masu aikin zuwa da dawowa ba su da kirki, ni ma da na gama jegon nan me kwanan zan ɗauka. Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan Anti Wiyya tace ‘Ita kuma wannan ‘yar taki wallahi ita ma ba ta da mutunci; yaushe za a ce budurwa kamarta ba za ta yi aiki ba komai ƙanƙantarsa?

    Sai dai ta dinga bin mutane da kallo suna mata aiki sai kace ubanta sayenmu ya yi. Gaskiya ku sake zama a gidan nan, haba! Idan banda ma rashin mutunci ya za a ce mace tana jego kuma a barta da kula da gida da yara bayan tana da kishiya? Ai kamata ya yi ta karɓar miki aikin. Ko da yake wannan ‘yar mulkin kishiyar taki na kula daga ke har maigidan tsoronta kuke yi.’

    Ta tashi zaune ta kwantar da Rukayya wadda ta riga ta yi bacci, ta kama haɓa ta dubi Antin tata tace ‘A a shi dai yake tsoron matarsa, duk abinda ta ga dama tace ba za ta yi ba haka zai yi ta kame-kame saboda ita ba a iya yi mata dole. Ta kalle ta sheƙeƙe tana cewa ‘Kece karkatacciyar kukarsa mai daɗin hawa ko? Shi yasa kina jego amma aka lafta miki aiki?

    Ita ko kunya ba ta ji? Sai ta sauko ta ishi mutane da gaishe-gaishe kamar wata musulmar ƙwarai. Cikin damuwa tace ‘Haka take fa, da an haɗu ta yi ta haba-haba da mutum amma mugun halinta yana nan fal cikinta sai mu da muke zaune da ita muka san halinta. Anti Wiyya ta ɗan yi ƙasa da muryarta tace ‘To gaskiya dai dole a yi aiki a kan wannan matar, yanda ta kama maigidan nan tana juya shi ai ba fin mu iyawa ta yi ba.

    Kema idan kika zo yawon arba’in da kaina zan kai ki inda za a taimaka miki a ƙwato miki daraja. Wannan kwarjinin da take da shi take yi wa kowa har maigidan ke ma a samo miki shi. Taimako ne da ayar Allah ina da malamina a hannu kuɗi kawai za ki bayar. Har yaran ma don ubansu ko su bi ki su zauna lafiya ko kuma su koma ‘yan kallo.’

    Tana ta jijjiga kai saboda gamsuwa tana cewa ‘Babu komai Anti, in sha Allahu za mu je. Don ni ma wallahi zaman haka ya ishe ni. Kuma dama Yaya ma tace za mu je ban san me ya ɗauki hankalinta ba. Nan suka zauna suka gama ƙulla yanda za a yi sannan suka fito suka kama hidimar gidan.

    Haka suka cigaba da yi har Naja ta yi arba’in; duk wata kalma da Mustapha zai yi amfani da ita ya sa Khadeeja ta karɓi hidimar nan ba ta yi amfani ba har ya gaji ya sakawa sarautar Allah ido. Sai da Naja ta yi arba’in sanna suka cigaba da rabon kwana. Idan Khadeeja ce da kwana sai Mustaphan ya je ɗakinta yayin da ita kuma Naja take zuwa ɗkinsa.

    Kwanci tashi har ya zama ta mayar da saman nasa kamar nata, ya zama kullum tana ciki ko parlor ɗinsa ko ɗakinsa. Ba ta daɗe da yin arba’in ɗin ba kuma Khadeeja ta gama bautar ƙasa; sai dai duk yanda ita da Baffanta suke ƙoƙarin samar mata aiki bai samu ba. Inda ta yi bautar ƙasar ma ta so su riƙe ta amma suka nuna mata ba sa buƙatar ma’aikata.

    Ba ta son zaman gidanta, domin ta san in dai ya zama Naja za ta tafi aiki ta barta a gidan da yara to dole Mustapha zai yi duk yanda zai yi ya tursasa ta ta dinga kula da yara. Ya zama shi da matarsa suna yawon neman kuɗi ita tana musu hidimar gida da ta yara. Don haka ta sanar da manager za ta dinga zuwa Litinin zuwa Juma’a tana yi musu aiki kyauta.

    Da ya ji haka sai ya sa aka ɗora ta a kan tsarin internship da suke da shi; inda duk wata za a dinga ba ta naira dubu goma sha biyar har zuwa lokacin da za a sami wani gurbi a gidan rediyon kawai sai a ɗauke ta. Sosai hakan ya yi mata daɗi, kuma ba tare da wata fargaba ba ta sanarwa Mustapha sun riƙe ta aiki, ta cigaba da zuwa.

    Kusan wata takwas kenan da haihuwar da Naja ta yi; kuma kamar yanda suka tsara an kai ta wajen malami. Bayan malamin ya ji bayaninsu ya ba ta wani abu mai kama da gishiri yace ta yi sati tana zuba musu a abnci duk gidan kowa ya ci har Khadeeja. Haka ta dage ta yi amfani da abun nan sai dai ba ta da tabbcin Khadeeja ta ci abun marmarin da take girkawa tana aika mata, shi ma Habib ba ta da tabbacin cinsa domin ya fi cin abinci a wajen Khadeeja.

    A hankali ta fara ganin sauyi, kamar dai duk yaran da Mustaphan suna saurararta; tunda wasu lokutan idan ta sa Afaf aiki haka za ta tashi ta yi ko ba ta so kuma Mustaphan ya daina hanata.

    Sun gama magana da ita a kan zai siya mata mota, amma ga shi lokaci yana ta ƙurewa yanzu ya ma ce mata shi ba alkawari ya yi mata ba; shi kawai ce mata ya yi zai yi tunani. Cikin damuwa suke waya ta sanar da Anti Wiyya halin da ake ciki; tace ‘Wallahi Anti nema yake ya canza maganar.

    Kuma dama na gaya miki aikin malamin nan ba kullum yake ci ba, tunda ko Mustaphan ya fara saurarar maganata da an kwana biyu sai ya sake komawa kamar da. Gani ma nake kamar duk lokacin da matarsa ta karɓi kwana sai ta warware min aiki, shi yasa nake ta fama da shi. Daga ɗaya ɓangaren Anti Wiyya tace ‘Au haka ne? To bar ni da su, ai ba mu za a yi wa bariki ba.

    Akwai wani malamin aikinsa yana da zafi sosai, in kin sami lokaci kiyi min waya sai mu je wajensa. Ke kanki sai kin yi mamakin aikinsa. Suka ƙarasa hirarrakinsu suka yi sallama. Ta jefa wayarta a kan gadonta cike da ƙwarin gwiwa; ta san Mustapha yana ƙoƙari wajen kyautata mata amma ita gani take kamar tsoron khadeeja yake yi. Kuma ma ita so take ya zama gaba ɗaya gidan sai abinda ta faɗa za a yi.

    Tana ganin yanda maza suke yi wa matansu kyauta ta burgewa, ita ma haka take so ya dinga yi mata, duk abinda ta nema ya ba ta kawai tunda ta san yana da kuɗin. Idan ma ta sami yanda take so to ko ganin Mustapha yaran ba su isa su yi ba sai da izininta, domin ta kula da yanda yake saurararsu yana bin ra’ayinsu kamar su suka haife shi.

    Sai an yi magana yace su marayu ne. Tabbas dole gidan nan gaba ɗaya ya dawo tafin ƙafarta don ta gaji da wannan mulkin da ake mata ana kasa mata hankalin miji tsakanin uwargidansa da yaransa.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Shida

    Edita@rumasau-kallamu

  • Samuwar Rubutun Ajami

    Samuwar Rubutun Ajami

    Bincike ya nuna cewa an fi samun rubuce-rubucen Ajami na zube a cikin hanyar rubutu Magaribi, wato ba a faye samun rubutun Ajami da yawa a cikin rubutu na sharƙiyya ba. Haka kuma bincike ya nuna cewa, an fi shekaru ɗari biyu (200) ana amfani da Ajami a ƙasar Hausa kafin shigowar rubutun boko wanda sai kuma ya faru ne a dalilin zuwan Turawa ƙasar Hausa.

    Dalilin cewa rubutun Ajami ya shekara 200 kafin na boko shi ne idan mutum ya yi la’akari da irin rubuce-rubucen da aka samu tun wajen ƙarni na 17 irin rubuce-rubucen Malam Abdullahi suka Kano da Wali Ɗanmasani a cikin Birnin Katsina da Malam Muhammadu na Birnin Gwari da dai sauransu.

    Amma dangane da ilimin Arabiya da samuwar Musulunci wannan tun wajen ƙarni na 9 ne, domin akwai alaƙa tsakanin ƙasashen Hausa da na Larabawa tun a wannan ƙarni inda a Jami’ar Al-azhar akwai wani sashen da ake kira Ruwaq- Al-Barno, inda mutanen Borno suke zama a cikin Jami’ar. Yahaya (1988)

    Har kwanan gobe Malaman zaure na ƙasar Hausa idan za su yi rubutu na zube a cikin rubutun Ajami suke ƙaddamar da shi. Haka kuma akwai jaridu da akan buga a cikin ajami kamar su Albishir da Alfijir. Haka kuma ba wai kawai a Hausa ba hatta a ƙasashen Afirka ta Gabas kamar su Tanzaniya da Uganda da Afirka ta kudu suna rubuta harshen Ki-swahili da Ajami.

    Amma a ƙasar Hausa Ajami bai sami cikakken gata ba sai a 1985 a Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo da ke Sakkwato ƙarƙashin shugabancin Shugaban Jami’ar na wannan lokaci, wato Farfesa Mahdi Adamu Ngaski inda ya sa aka kira taro na ƙasa domin kyautata rubutun Ajami inda aka kira manyan malamai daga ko ina a ƙasar Hausa, taro ya fara zama ranar 28 ga watan Janairu na 1985 inda aka yi kwana uku sai kuma a cikin 19 ga watan Agusta inda aka sake kiran taron aka yi kwana uku aka tattauna akan abubuwa kamar haka:

    a)A samar wa Ajami tsayayyiyar ƙa’idar rubutu
    b)A kyautata rubutun Ajami domin a sauƙaƙa wa mai karatu yadda zai ji daɗin karanta shi.

    Ka san an ce “Ajami gagara mai shi”, da aka kirawo taro, daga ƙarshe an samar da nagartacciyar hanyar rubuta Ajami, karɓaɓɓiya wadda wata hukuma ce ta gwamnati ta yi wannan hoɓɓasa . Kafin wannan lokaci masana sun kasafta hanyar rubuta Ajami zuwa gida uku:-

    1700-1950

    1950-1985

    1985/88 zuwa yau

    Daga 1700 inda aka sami rubuce-rubuce irin na su Wali Ɗanmasani babu wata ƙa’idar rubuta Ajami kowa yana rubutawa yadda yake so, sai a 1950 inda Alhaji Halliru Binji da Alhaji Na’ibi Sulaiman Wali suka rubuta wani littafi mai suna Mu Koyi Ajami Da Larabci (1950). Shi kuwa wannan yunƙuri ba na gwamnati ba ne, illa dai mutane kawai wanda ya karanta shi ke nan.

    To sai a 1985 inda Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo aka kira masana suka gabatar da shawarwari a kan ƙa’idar rubutun Ajami to amma rahoton binciken da masanan suka yi bai fito ba sai a 1988, wato bayan shekara uku, mai suna “Report On Hausa Ajami Writing” (1988). Shi wannan littafi a kan Ajami ya ƙunshi babi (13) amma babu 2-10 su ne suka ƙunshi zallar yadda ƙa’idar rubuta Ajami take.

    Idan aka ce rubutun zube ana nufin rubutun da ba waƙa ba, ba kuma wasan kwaikwayo ba. Zube ana nufin tsagwaron rubutu kai tsaye wanda aka yi shi cikin shafi ko shafuka da sakin layi daban-daban, a rubuce ko a maganance, wato ta hanyar magana.

    Rubutun zube na Hausa ya samo asali ne ta hanyoyi guda biyu. Hanya ta farko ita ce ta hanyar addini wato rubutun zube ta hanyar Ajami wato hanyar rubuta Hausa cikin haruffa na Larabci. Wannan hanya Hausawa ne suka ƙirƙiro abarsu tun asali ta hanyar rubuta sunaye na gargajiya a jikin fahami kamar misali; Malam Ɗantsoho, Malam Ɗantsamiya, da kuma ire-iren sunayen da akan haɗa laƙunƙuna da su kamar gaɓar kara, ɓawon yawa, da dai sauransu to ta irin wannan hanya kuma manya-manyan malamai da manyan sarakuna sukan rubuta wasiƙu a tsakaninsu. Mukhtar (2004)

    Samuwar Rubutun Boko

    Kafin a fara rubutu da Hausar boko a ƙasar Hausa, sai da aka daɗe ana amfani da ita a ƙasashen Turai. Amma mutumin da ake jin ya fara amfani da ita shi ne wani Baturen ƙasar Jamus mai suna James Frederick Schon wanda ya zo ƙasar Saliyo aikin Mishan a 1840. Schon shi ya yi tunani ya kuma ƙirƙiro cewa ya kamata ya yi amfani da haruffan Latiniyya ya rubuta lafazin Hausa:-

    “na riya waɗannan ƙa’idojin rubutu a raina ne, bayan na yi shakaru inda lura da abubuwa. Saboda haka na yi amanna da dacewarsu.” (Schon, 1862:X).

    Bayan da Schon ya yi niyyar amfani da haruffan Latiniyya ya rubuta Hausa, sai wani Bature mai suna Lepsius, ya ba shi shawarwari a kan yadda zai kyautata rubutun. Sauran Turawa waɗanda suka biyo irin wannan hanyar rubutu ta J.F. Schon sun haɗa har da Prietzer (1904), sai Mischlich a (1906) sannan Westermann a shekara ta (1911) da sauran waɗanda suka biyo baya.

    Wata hanyar rubutun zube cikin boko da aka fito da ita, ita ce wadda Robinson (1896) ya fito da ita, ko da yake Robinson shi ma Latinanci ya yi amfani da shi, sai dai shi ya ɗauki tsarin Ajami ne wajen sarrafu baƙaƙen da babu su a wasu harsuna. Misali v da q da x da sauransu a hanyar rubutu ta Robinson waɗannan haruffan ɗigo ake musu a ƙasa irin na Ajami maimakon lanƙwasa. Wato sai a rubuta su kamar haka:- b k d ba tare da lanƙwasa ba.

    A lokaci na farko da hukuma ta tsoma baki a kan rubutun zube shi ne lokacin mulkin mallaka a nan Nijeriya inda Hanns Vischer wanda ake kira Ɗan Hausa ya tsara ƙa’idojin yadda za a yi amfani da Hausar boko a (1910) sai dai shi ma ya yi amfani ne da Hanyar Robinson inda yake sa ɗigo a ƙarƙashin harafi mai alhamza.

    Wata hanyar rubutun zube kuma ita ce wadda Bargery (1934) ya yi amfani da ita; shi kuma waƙafi ya dinga sa wa hamzatattun haruffa maimakon ɗigo. Kamar haka:-

    ‘b k’ ‘d da kuma dai sauransu.

    Hukumar Fassara ta Jihar Arewa ita ce ta fara ba da shawara a (1938) cewa ya kamata duk hamzatattun baƙaƙe a dinga lanƙwasa su maimakon ɗigo ko waƙafi.

    Litattafan Ƙagaggun labarai da marubuta ke rubutawa sun kasu gida hudu:

    1.) Akwai masu gajeren zango wato (fiction) wadanda ba sa wuce shafuka arba’in (40) zuwa shafi 200 da kuma,

    2.) Masu dogon zango, wato (novels) masu shafuka 200 zuwa sama.

    3.) Akwai Litattafan Kagaggun labarai da aka yi su, domin Hausawa a cikin akwai garuruwan Hausawa da tattalin arziki irin na Hausawa tunani irin na Hausawa. Sai kuma

    4.) Litattafan Kagaggun labarai da aka rubuta su da Hausa, kawai domin a gabatar da saƙon da Hausa a matsayin harshen sadarwa amma labaran ba domin Hausawa aka gina su ba.

    Irin waɗannnan ba na gyaran hali ba ne, shi ya sa akan samu batsa a ciki, sannan Hausar ba ta inganta ba. Don haka waɗanda aka gina labaran don Hausawa akwai ilmantarwa, nishaɗantarwa da gyaran halin al’umma. Saboda haka Wannan tana da muhimmanci domin tunatar da malamai, iyaye da marubuta wajen fahimtar yadda ƙagaggun labarai ke tasiri wajen gina tarbiyyar matasa. Haka kuma za ta ƙarfafa wa matasa gwiwa domin su karanta littattafai masu ɗauke da darussa da koyarwar tarbiyya a cikinsu.

    Masana da dama sun tattauna a kan irin rawar da adabi yake takawa wajen gyaran halin Bil adama. Misali, Abubakar Imam cikin littafinsa Magana Jari Ce ya yi amfani da ƙananan labarai wajen koyar da gaskiya, haƙuri da adalci. Haka kuma Hafsat Abdulwaheed cikin So Aljannar Duniya ta nuna illolin soyayya marar tushe da muhimmancin kyawawan halaye a tsakanin matasa.

    Waɗannan misalan sun nuna cewa ƙagaggun labarai ba wai nishaɗi kawai suke sa wa ba, har ma suna zama kayan gyaran hali da watsar da munanan ɗabi’u da ba nagari ba a cikin al’umma. Saboda haka dai a wannan takarda an yi amfani da hanyar binciken ɗakin karatu (Library Research Method), inda aka tattara bayanai daga littattafan Hausa, mujallu da wallafe-wallafen ca suka shafi adabin Hausa da yake magana a kan tarbiyya.

    Wanann bayanin an ciro shi ne daga muƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

    Danna nan don karanta Amfanin Ilimin Kwamfuta

    Edita@rumasau-kallamu

  • Waiwaye A Kan Al’adun Gargajiya

    Waiwaye A Kan Al’adun Gargajiya

    Masana irin su Ibrahim (1982) da Bunza (2006) sun gabatar da bayanai dangane da asali da ma’anar kalmar al’ada. Don haka a taƙaice kalmar al’ada tana nufin dukkanin rayuwar ɗan Adam tun daga haihuwarsa har zuwa kabarinsa.

    Dangane da wannan fasali da ake magana a kai, al’adun gargajiya na nufin tsarin rayuwar Hausawa wadda ta shafi abinci da sutura da muhalli da zamantakewa da shugabanci da bukukuwa da wasanni da makamantansu.

    Ma’anar Wasa

    Sa’id, B. (2006) sun bayyana ma’anar wasa da cewa, “abu ne da akan yi don raha ko nishaɗi, ko motsa jiki.” A wata ma’anar kuwa Ɗangambo (2008) ya bayyana kalmar wasa da cewa, “shi ne motsa jiki don samun walwala.” Duba ga waɗannan bayanai da ma’anoni da suka gabata, za a iya cewa wasa shi ne sanya walwala da nishaɗi tare da nuna farin ciki, wanda a wasu lokutan har da motsa jiki.

    Wasannin Gargajiya A Ƙasar Gaya

    Al’umma kan tafiyar da rayuwarsu, da al’adunsu cikin gwagwarmaya don cimma wasu buƙatu na rayuwa. Wannan yakan jawo wa al’ummar ingantaccen tarihi mai cikakken asali da abubuwan alfahari. Haka kuma al’adun kan samar da annashuwa ba ya ga ilimantarwa.

    A ƙasar Gaya akwai wasannin gargajiya waɗanda al’ummar suke gudanar da su, wasu daga cikin wasannin sun haɗa da: wasan Mage da wasan Ƙunshi da wasan Jemau da wasan Taushen fage da wasan Dagajirau (saran-kai) da sauran wasanni waɗanda sun sha bamban da al’ummar ƙasar Hausa.

    Wanann bayanin an ciro shi ne daga maƙala mai taken Nazarin Wasan Ƙunshi Jiya Da Yau A Ƙasar Gaya wadda Magaji Ahmad Gaya Ph.D Sashen koyar da Hausa Jami’ar Northwest, Kano ya wallafa.

    Emai: magaya@nwu.edu.ng

    08066009039

    Danna nan don karanta Nason Al’adun Baƙi Maƙwabta Na Kusa A Wanzancin Hausawa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Wasu Kayan Da Hausawa Ke amfani Da Su Ga Doki Suke

    Yadda Wasu Kayan Da Hausawa Ke amfani Da Su Ga Doki Suke

    1. Bante
    2. Bawaji (majanyi)
    3. Bulala (kurhu)
    4. Dabaibayi.
    5. Ɗangaba

    6. Ɗangamba
    7. Ɗangoshi
    8. Ɗan wuya
    9. Ɗan kai
    10. Caraskiya

    11. Gindi/Tarnaƙi
    12. Ilgami
    13. Ja-kuturi.
    14. Jikka
    15. Jalala

    16. Kwacciyar sirdi
    17. Kwarno
    18. Kubuttai
    19. Ƙaimi
    20. Kalmazuru

    21. Likkafa (karama)
    22. Likkafa (Wangami)
    23. Linzami
    24. Mashinfiɗi
    25. Maɗauri (sarka/igiya)

    26. Ragama
    27. Talala
    28. Turke
    29. Turmi/Baho/Diram.
    30. Tumbas

    31. Kitso
    32. Zabba
    33. Zabukka
    34. Sirdi (Hausa/Turawa/Azbin)
    Da sauran su.

    FASIHIN KAITA

    Danna nan don karanta Wasu Kayan Aikin Rini

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Shida

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Shida

    Tun wajen 12pm ta nemi izini a wajen aikin nata ta fice, kai tsaye gidansu ta nufa. Ta ci sa’a ta sami Mommy da Yaya Mama suna zaune a parlor suna hirarrakinsu. Bayan sun gaisa Khadeeja ta dubi Yaya Mama tace ‘A nan kika kwana Yaya. Ta yi dariya tace ‘Ga jakata a kusa da ni kina kallo amma kike min wannan tambayar, to ni yanzu ma zan tashi saboda 2pm zan ɗauko yara a makaranta sannan mu wuce gidan.’

    Ita ma ta yi dariyar, ta umurci Hafsa da ta shiga ɗakin Nabila ko ta je kitchen wajen masu aikin gidan ta zauna. Tun kafin tace wani abu Mommy ta dube ta tace ‘Lafiya dai na ganki kamar a fusace, sarkin rigima. Ta zumɓura baki ta sunkyar da kai tana kallon hannunta kamar me ƙunƙuni, sai da ta gama zumɓura bakin sannan cike da takaici tana ƙoƙarin danne hawayen da ya taso mata tace ‘Mommy ni Mustapha zai mayar ‘yar aiki, kuma Baffa ya goya masa baya.’

    Mommy ta gyara zama ta fuskance ta sosai tana kallon fuskarta da mamaki sannan tace ‘Ban gane ba, kuma me kawo Baffanki a cikin mayar da ke ‘yar aiki? Shi Mustaphan me ya yi miki? Tana buɗe baki za ta yi magana hawaye ya ƙwace mata, ta sa bayan hannunta ta goge sannan ta labartawa Mommy abinda ya faru.

    Zuwa lokacin hawayenta ya gama ƙwacewa yana zuba kamar ana zubar da ruwan famfo, Mommy ce ma take ƙoƙarin goge mata. Tace ‘Mommy yanzu shikenan haka zan yi wata tara ina mata hidimar gida tana kwana da miji, bayan ni haka na yi nawa laulayin ko tausayina ba ya ji. Ko haihuwar Hammad fa ana gama suna dole na miƙe na koma hidimar gidan saboda ban ma ga fuskar cewa ba zan iya ba.

    Amma yanzu saboda ya auro ‘yar gwal shi ne zan karɓar mata aiki ita kuma ta yi laulayi. Yaya Mama tace ‘Ni fa gaba ɗaya ban gane ba. To ke me yasa ba kya zuwa ɗakin kike barinta ta je, ai da sai ki je ki yi kwanciyarki a can ki ga ta inda marasa kunya za su kwana tare.’

    Kafin ta yi magana Mommy tace ‘Gaskiya ni ma dai ban gane dabarar yin hakan ba, ai ɗakin ya kamata ki gyara ki tare har sai kin gama kwananki. Ta sa bayan hannunta ta goge hawayenta sannan tace ‘Mommy ba zan iya ba, ya kwana da wata matar a kan gadon sannan ni ma ya kwana da ni a kan wannan gadon.

    Wataƙila ma da ya yi aurensa ba tare da ya ci min mutunci ba abubuwa da dama za su zo min da sauƙi, amma gaskiya ba zan iya ba. Tunda ko bayan ta tare ranar da zan karɓi girki bayan da ta gama kwana takwas ɗinta na shirya tsaf zan shiga ɗakin, amma har magriba ba ta fito daga ciki ba. Lokacin shi kuma ya riga ya fita.

    Don haka na ƙyale ta na shirya masa abincin dare tunda na gama kintsawa. Amma yana dawowa ko kallon abincin bai yi ba ya same ni wai tunda ina jego na ba shi kwanakin ya kai wa amaryarsa in ya so idan na yi arba’in sai a fara rabon kwanan. Kin ga kenan ita ta riga ta san ba zai ba ni kwanan ba shi yasa ta ƙi fita ma daga ɗakinsa.

    Daga wannan lokacin ɗakin da me ɗakin suka ƙarasa fice min daga rai gaskiya. Idan yana buƙata ta ya same ni a ɗakina, kuma yana zuwa ɗin. ’Mommy wadda take binta da kallo tana jijjiga kai tace ‘Lallai Mustapha, ni na rasa ma me zan ce. Ni fa mamakin da nake Baffanki ko gaya min bai yi zai je ba balle da ya dawo ya gaya min, wataƙila jiya bayan ya fita da magriba Mustaphan ya yi sa’a ya same shi a gate suka gama magana.’

    Yaya Mama tace ‘Hmm! Ai komai daɗinki da miji idan dai wata macen ta gifta to sai abinda kika gani. Watan haƙurinki ne ya kama har ya gama yayinta. Mommy tace ‘To yanzu ya za a yi? Kin ga Baffanki ya riga ya sa baki a maganar ba tare da kin gaya masa ainahin abinda yake faruwa ba.

    ‘To Mommy ya za ayi na yi masa duk wannan bayanin ya gane, ai ban ga alamar zai ma gane ba tunda ko a lokacin ma yace amfanin mata biyu kenan ɗaya ta taimakawa ɗaya. Kuma ya za a yi na zauna ina gaya masa Mustapha yana satar min kwana saboda na ƙi zuwa ɗakinsa? Umm, haka ne kuma. To Allah ya kyauta.

    Yanzu kam sai dai ki yi haƙuri a ga abinda hali zai yi tunda dai babu wanda zai je ya kwance maganar Baffanki. Ina ga kula da yaran wanda kika yi a baya bai kashe ki ba ba na jin na wata tara nan gaba zai dame ki. Haka suka zauna suka yi ta ba ta hakuri; sai daga ƙarshe Yaya Mama tace ‘Kuma ke ma idan kin gaji kawai ki yi pretending ki kwanta masa, wallahi da kaina zan zo na taho da ke na kawowa Mommy ta yi jinyarki idan kin huta kya koma.’

    Mommy ta kai mata duka tana cewa ‘Allah ya shirye ki yayar kwabo. Suna nan zaune wajen 1:30pm Baffa ya shigo gidan da sallama, bayan ya amsa gaisuwarsu da sannu da zuwa ya dubi Mommy tana zaune a tsakiyar su Khadeeja yace ‘Gulmar wa kuke yi suka saka ki a tsakiya haka. Ita ma dariyar ta yi tace ‘Ba dai gulmarka muke yi ba.’

    Yaya Mama ta yi musu sallama ta fice yayin da Khadeeja ta miƙe ta nufi ɗakin Mommy ba tare da tace komai ba. Baffa ya bi bayanta da kallo sannan ya yi dariya ya dubi Mommy yace ‘Wannan iya rigimar ƙarata ta kawo ko? Ta harare shi tace ‘Ashe ka san ka yi mata laifi? Ya yi dariya yace ‘Rabu da ita da-Allah, ya za a yi a ce mutum yana da mata biyu a ce ɗaya ba za ta karɓi ɗaya aiki ba idan ba ta da lafiya? Ai ita ma ba ta so a zauna lafiya ba.’

    Nan ta ƙara yi masa bayanin yanda zaman nasu yake, sai dai ta kasa gaya masa cewa Mustaphan yana ba wa Naja kwanan Khadeeja saboda Khadeejan ba ta yarda ta je ɗakinsa. Yanda ta san shi ta san tabbas ba zai ɗauki wanna ba, tunda shi ma tashi uwar har ta koma ga Allah turaka take zuwa ranar kwananta.

    Haka dole Khadeeja ta haƙura ta cigaba da hidimar gida da ta yara. Shi ma Mustapha da ya gama zagaye-zagayen haka ya same ta a ɗakinta yana nuna mata jin daɗinsa ganin yanda take kula da yaran sai dai baya jin daɗin yanda idan ta jera abinci take komawa ɗaki ta bar su shi da ‘yayansa.

    Duk yanda ya so ta ba shi haɗin kai su tattauna maganar ta ƙi, da ya dame ta da zance ma sai tace ‘Don Allah ka bari! Kai dai ba so kake na cigaba da hidimar gidanka da yaranka ba amaryarka tana hutawa? To ai ina yi ko? Ina ga duk a inda na zauna na ci abinci ma wannan bai kamata ya zama damuwa ba tunda dai ku kun ci naku.’

    Kafin ya ba ta amsa ta fice ta bar masa ɗakin. Dole ya haƙura ya zuba mata ido tunda dai tana yin abinda yake so kuma duk ranar da ya kai mata kwananta ba ta hana shi buƙatarsa.

    Da fari lokacin da Mustapha ya ƙara aure Khadeeja ta ga ‘yan uwansa ba sa wani damunta ta yi zaton tunda an mata kishiya sun fita harkarta. Sai dai tunda suka ji labarin Naja tana da ciki sai suka kama zarya gidan; babu yanda za a yi Yaya Jidda ta yi sati ba ta zo gidan ba. Haka za ta taho da girki a flask wai Hajia ce tace a kawo wa Naja saboda kwaɗayin mai ciki.

    Ga shi idan ta zo a wajen Najan za ta sauka, sai dai idan Khadeejan tana nan ta shiga su gaisa sai ta koma wajen Najan. Sai kuma ta yi ta aiko yara; a ba ta abinci. Idan ta cinye kuma tace a ba ta wani ɗan abun taɓawa. Ranar da ba ta zo ba kuma sai a turo yaranta da abincin; haka za su zo ta wuni surutu da hidima da su ba ta taɓa jin wani yace Hajia tana gaisheta ba.

    Kuma shi ma Mustaphan yana kallo ana yi amma bai taɓa cewa komai ba; sai dai yawan godiya da za ta ji shi yana yi wa mutan gidan nasu. Haka ta kawar da kai ta cigaba da duk wannan hidimar tana ganin rawar kai kala-kala. Haka ta cigaba da dagewa har Allah ya sauki Naja lafiya, aka sami yarinya mace wadda tun ranar da aka haihu Mustapha ya yi mata huɗuba da suna Rukayya.

    Ba su tsara za ta tafi gida ba don haka sai aka kawo ƙanwar mahaifiyarta Alawiyya wadda suke kira da Anti Wiyya ta zo yi mata zaman daɓaro. Tun Khadeeja tana saka ran za ta ji Mustapha yace zai haɗe mata kwanan saboda Naja tana jego har dai ta fitar da rai. Ranar da aka kwana takwas da haihuwa ranar ta kama kwanan khadeeja ne sai dai a daren ranar za ta fita daga girki.

    Da yake a ɗakinta suka kwana a nan yake shirin fita office; musamman tunda banɗakin ɗakinsa ya kwana biyu rabon da a wanke saboda Naja ba za ta iya wanke wa ba kuma Khadeeja ta ƙi ma shiga ɗakin; ga shi kuma yana ƙyashin ya saka Afaf ta wanke tunda ba ya son damuwarta. Yana zaune a gaban mudubinta yana shafa mai ta fito daga wanka, ta ɗauki kayan shafawarta ta koma gefen gado, suna yi suna taɓa hira.

    Jimawa kaɗan tace ‘Yauwa, tazarce za mu yi ko? Sai na haɗe kwanakin tunda Naja tana jego har zuwa ta yi arba’in ko? Ya ɗan yi dum, alamar maganar ta shammace shi; tun ranar da Naja ta haihu ta gaya masa ba za ta bayar da kwananta ba saboda ko ba za ta iya biya masa buƙatarsa ba tana so ya kwana da su ita da Baby, in ya so kwana biyu sai su haƙura.

    Ya riga ya amsa mata hakan domin shi ma hakan ya yi masa; duk da dai shi ba mutum ne mai son jarirai ba domin ko ɗaukan yaro ba ya son yi har sai yaro ya iya zama sosai. To amma dai tunda ta nuna tana so shi ma sai ya ji hakan ya yi masa ko hira ce sa yi, musamman da yake bai taɓa tsammanin Khadeeja za ta nemi wani ƙarin kwana ba duk da ita ta ba da nata kwanan an ba wa Najan.

    ‘Um, no ina ga ba haka za a yi ba. Na riga na yi magana da ita amma ba ta ba da kwanan nata ba, tunda kin ga ke ma tambayarki na yi kika bayar ba tare da na yi miki dole ba. To ita ba ta bayar ba, don haka sai a cigaba da kwana bibbiyun kawai.’ Ya faɗa cikin in-ina yana satar kallon Khadeejan ta cikin mudubi.

    Sai da ta yi da gaske sannan ta haɗiya malolon da ya tokare mata maƙogoro; duk da dama hakan ta sa rai zai faɗa amma sai da abun ya yi mata ciwo. Ita ba ta ma yarda Naja ce ba za ta ba da kwananta ba, ta fi yarda shi ne dai ba zai iya ba ta kwana arba’in ba ba tare da ya ji ɗumin rabin ransa ba.

    Ta daure ta yi murmushin yaƙe sannan tace ‘Allah sarki haka ne kam, to babu damuwa Allah ya raya mana Rukayya ita kuma mai jego Allah ya ƙara mata lafiya. Shikenan ai tunda ta haihu lafiya idan ta karɓi kwana yau to ta haɗa da sauran hidimar gida da yara da nake yi ni ma na samu na huta.

    Ya yi shiru da bakinsa a buɗe yana kallon Khadeejan ta cikin mudubi; to a gaban Antin tata zai sakar mata aikin gida da na yara bayan ga ɗanyen jego sannan kuma ga Khadeejan tana kallo? Kuma a ce ita ce za ta tashi ta shirya masa yara, duk da dai kusan sun iya shirya kansu amma dai idan ba a tsaya a kansu ba haka za su yi ta shiririta har su makara.

    Ga shi Afaf ta shiga SS 3 yanzu tun 7:15 am ake tare su makara. Ya san idan dai ba a tsaya a kansu ba to kullum sai dai ya dawo da Afaf. Ya rasa ma me zai ce mata, domin ya san kusan ko me yace tana da amsar ba shi kuma ya tabbatar fitinar da ba ta yi ba ce a lokacin da Baffanta yace ta dinga taya Naja aiki take shirin biyan bashinta yanzu. Ta miƙe ta kwashi mayukanta da ta gama shafawa ta ƙarasa gaban mudubin ta ajiye.

    Ta ɗan tsaya daga gefensa tana kallonshi fuskarta cike da walwala kamar ba yanzu ta haɗiye ɓacin rai ba, tace ‘Kuma ni na yafe nawa kwanan ka haɗa mata, idan kuka yi arba’in sai mu cigaba da rabon. Ka ga ita da Baby suna buƙatar lokacinka da kulawarka sosai a waɗannan kwanakin. Ta wuce ta nufi gaban wardrobe domin saka kaya.

    Yana nan zaune a gaban mudubin ta shirya ta fice ta bar shi a ɗakin; nan da nan ta haɗa masa breakfast ta jera a kan table sannan ta dawo ɗakin ta same shi ya riga ya gama saka kaya. Tana tsaye daga bakin ƙofa tace ‘Na yi serving breakfast. ‘Ok.’ Ya amsa. Ta juya ta fice ya biyo bayanta. Suka zauna tare suna cin abincin. Har suka ci kusan rabin abincin babu wanda yace wani abu; kowa da abinda yake ransa.

    Ya ajiye kofin shayinsa bayan da ya kurɓa sannan ya ɗauki fork ɗinsa ya tsikari dankalin baturen da yake gabansa, ya ɗan ajiye fork ɗin ya kirawo sunanta a hankali kamar ma ba ya so ta ji kiran. Ta ɗaga kanta daga kallon kwanon abincinta ta amsa tana kallonsa. Ya yi gyaran murya sannan yace ‘Um, da-Allah ki yi haƙuri ki cigaba da girki a ƙalla har zuwa lokacin da Antin Naja zata gama yi mata wanka ta tafi.

    Tunda kin ga ga Hafsa nan tana taimaka miki kuma na san Afaf ɗin ma yanzu duk abinda kika gwada mata za ta iya taya ki da shi. Saura kaɗan dariya ta ƙwace mata; wato yanzu Afaf ta kai ta taimaka wajen girki kenan tunda ya auro matar so? Ashe ma ya san kunya tunda ga shi ba ya so ya ji kunyar iyayen Naja.

    Ta ajiye cokalinta ta kurɓi shayinta sannan tace ‘Don Allah Abban Afaf mu bar wannan maganar, hidimar gidannan ta wata takwas na karɓar mata. Ai na yi ko? Yanzu sai ta cigaba daga inda ta tsaya. Kwanan kuma da nace na ba ta da gaske nake, ku je ku yi jegonku na masoya kwana arba’in; wataƙila dai a kwankin da suka kama nawa ne na yi aikin gidan idan ina nan in ya so ita sai ta kwana da angonta.’

    Cike da jin zafin abinda ta faɗa yace ‘Khadeeja ni kike gayawa wannan maganar? A cikin abinda ta faɗa ba ta san menene ya ɓata masa rai haka ba tunda ita dai a iya saninta ba rashin kunya ta yi masa ba, amma ta ga ya fusata yana faman yi mata muzurai. Ita da ya kamata a ce ita ce ranta ya ɓaci haka saboda nauye-nauyen da yake nema ya ɗora mata waɗanda ƙarara suke nuna rashin adalci.

    Ta kalle shi ta kawar da kai tace ‘Allah ya ba ka haƙuri. Ta kurɓe ragowar shayinta ta miƙe da kofin da kwanonta ta wuce kitchen. Tana ajiye kwanukan ta fito ta wuce ɗakinta, tana turo ƙofar ɗakin hawayen da take riƙewa suka ƙwace mata, ta ƙarasa ta zauna a kan kujerar gaban mudubi. Ta zubawa mudubin ido tana kallon yanda hawaye suke fita daga idanuwanta suna gangarewa ta kan kumatunta.

    Wai me Mustapha ya ɗauke ta ne? Mai aikin Naja? To da me yasa ya aure ta ne? ko dama haka ake soyayya? Ba ta sami amsar tambayoyinta ba ƙarar fitar motarsa daga gidan ta katse mata tunani, ta tuna ita ma aiki za ta tafi. Don haka ta miƙe ta wanke fuskarta ta ƙarasa shiryawa ta fice daga gidan zuciyarta cike da damuwa.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Biyar

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Biyar

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Biyar

    Haka rayuwarsu ta cigaba; duk yanda ya so Khadeeja ta dinga bin shi ɗakinsa gaba ɗaya ta ƙi. Don haka ba shi da zaɓi duk daren da yake buƙatarta sai dai ya bi ta ɗakinta su kwana, idan bai je ba sai dai kawai ta leƙa ɗakin nasa tace masa sai da safe. Sau da dama ya sha ƙyale ta ya ga ko za ta biyo shi amma da zarar ta shiga ɗakin tace masa sai da safe sai ta yi ficewarta.

    Da farko duk ranar kwananta idan bai ya buƙatarta ya yi kwanciyarsa a ɗakinsa haka yake kwana shi kaɗai, amma tunda Naja ta gane sai ta dinga bibiya; idan ta same shi shi kaɗai sai ta yi kwanciyarta a nan da uzirin laulayi. A zatonsu Khadeeja ba ta sani ba; sai dai ita ɗin ta zaɓi ta yi shiru ne tunda ta san yana yin hakan ne don ta hakura ta koma kwana ɗakinsa.

    Ita kuma har ga Allah gani take yi babu yanda za a yi kowa take aure ta kwana gadon da yake kwana da wata matar; musamman Naja wadda ba ta taɓa tsanar wata mace kamar ita ba. Tunda Khadeeja ta dawo daga gida kuma sai laulayi ya saka Naja a gaba. Haka za ta wuni jikinta babu ƙwari, abinci kuwa to idan dai ita ce ta dafa ba za ta iya ci ba dole sai dai ya siyo mata wanda zata ci.

    Yau Khadeeja take fita daga girki don haka a wajenta shi da yara suka ci abincin rana. Ragowar abincin ranan shi ta ɗiba ta zuba a flask ta ajiye musu ita da Hafsa saboda ta huta shiga kitchen da daddare. Tana zaune a parlor tana ba wa Hammad nono ya shigo parlor ɗin, bayan ta amsa sallamarsa ya zauna kusa da ita.

    Sai da ya gama kame-kamensa yace ‘Da-Allah ki yi abincin dare gaba ɗaya saboda Naja ba ta da lafiya, kin san na gaya miki ciki ne da ita kuma yana ba ta wahala. Ko da dai ba ta zata abinda ya zo faɗa kenan ba amma tana jiran wannan ɗin ma domin tun tuni yara suka gaya mata Najan ba ta da lafiya kuma ta fahimci menene ciwon.

    Ta cire Hammad daga nono ta saka shi a kafaɗa tana cewa ‘Ai kuwa ka ga yau ba girki zan yi ba ga ragowar abincin rana can shi na ajiye za mu ci da daddare. Allah ya ba ta lafiya. Ya sake ɓata rai ‘Khadeeja, da-Allah ki bari. Yarinyar nan ba ta da lafiya ko abincin ma ita ba ta iya ci, kuma ba ita nace ki yi wa girki ba. Ni da yara za ki girkawa, idan ta sami lafiya za ta karɓi girkinta.’

    Ta kwantar da Hammad a gefenta sannan ta fuskance shi gaba ɗaya don ba ta cikin yanayi na son zance, tace ‘To ai cikin ba wani abu ba ne, ko ka manta ne? Haka na dinga haɗawa da cikin da komai duka da ƙarancin shekaruna ga rashin mataimaki. Ita kuwa yanzu ka ga tana ma da mai aiki; ai babu wani abu da zai gagare ta. Idan dai kwana ya zagayo kaina insha Allahu zan yi kamar yanda muka saba.’

    A fusace ya kalle ta na ɗan lokaci sannan yace ‘Yanzu kenan ke babu halin a ce ki yi wani abu sai ki tuno abinda ya faru shekarun da suka wuce? Kuna zaune tare a gidan kina kallon ba ta da lafiya nace ki yi girkinta amma kina nema ki ce ba za ki yi ba? Wai ke me kike son zama ne? Babu wanda ya isa ya tanƙwara ki kenan saboda zaman kanki kike yi ko me?

    Ta sunkuyar da kai murya ƙasa-ƙasa tace ‘Ba haka ba ne, kawai dai ni ma mutum ce, yanda aka yi min na zata haka ake yi wa mutanen da ake so shi yasa nake so ko yaya ne a yi adalci. Ba ta saurari abinda zai faɗa ba ta miƙe ta ɗauki Hammad a hankali saboda ba ta son ta tashe shi ya fara bacci, ta wuce ɗakinta ta bar shi a nan.

    Yanda ta yi wannan tafiyar ya tabbatar ko me zai yi ba zata saurare shi ba; wanda hakan yake nufin shi da yaransa za su shiga halin rashin samun kulawa na tsawon wata takwas har Naja ta haihu, sai dai su sami kulawa kwana biyu kwana biyu kuma a bar su a gantale. Babu yanda za a yi a ce ya ɗauki wannan kuma a halin yana da mata biyu.

    A yanda cikin nan yake wahalar da Naja kuma dole Khadeeja ce za ta ɗauki wannan hidimar har zuwa lokacin da za ta haihu. Sai da ya gama lissafinsa sannan ya miƙe ya fice, kai tsaye ɗakinsa ya wuce ya ɗauki mukullan motarsa. Bai zame ko ina ba sai gidansu Khadeeja; ba ya son kai ƙara don ya kula ita ko ya kai ƙararta ma goya mata baya za su yi, sai dai yanzu ba shi da wani zaɓi da ya wuce hakan.

    Ya ci sa a yana shiga gidan Baffa yana shirin fita, a nan bakin gate ya tsaya ya yi masa bayanin halin da ake ciki. Cike da kulawa Baffa ya jijjiga kai yace ‘Subhanallahi, to Allah ya ba ta lafiya. Yanzu ka ga fita zan yi amma in sha Allahu idan na gama abinda nake zan zo har gidan na sami Khadeejan. Kada ma kace mata zan zo, ka ƙyale ni da ita zan zo na same ta ka ji.

    Ai ɗaya daga cikin amfanin ƙarin auren kenan ɗaya ta taimakawa ɗaya a irin wannan yanayin. Suka yi sallama kowa ya nufi inda zai je. Ba shi da tabbacin abinda Baffa zai yi a kan wannan matsalar amma dai yana saka ran Baffan zai fahimce shi ya saka Khadeeja ta dinga taimakawa Naja, a ƙalla a lokutan da ba ta da lafiya; idan ba haka ba menene ribar mata biyun ga namiji.

    Ba ta samu ta yi sallar isha’i a kan lokaci ba don haka har wajen 8:30pm tana zaune a kan dadduma, Hammad yana wajen Habib wanda yake zaune a parlor ɗinta yana kallon TV. Ta so ta jiyo muryar Baffanta suna gaisawa da Mustapha a tsakar gida, amma da yake bata sa rai da zuwan Baffan ba sai kawai ta zata kunnenta ne ya jiye mata ba daidai ba.

    Tana nan zaune Mustapha ya turo ƙofar ɗakin ya shigo da sallama, bayan ta amsa sallamarsa yace ‘Baffan Mommy ne yazo, ga shi nan a parlor na. Da mamaki ta kalli Mustaphan da alamomin tambaya a fuskarta, tace ‘Baffana? Ya yi ‘yar dariya saboda yanda ta tambaya sannan yace ‘Baffan Nabeela dai. Ita ma sai ta ɗan yi dariya tare da miƙewa tsaye; kwata-kwata ba ta yi zaton ƙararta Mustapha ya kai wajen Baffa ba.

    Ta yi zaton zuwa ya yi ya ga sabon gidansu kamar yanda take ta faman roƙonsa tunda suka tare ya zo ya ga gidan. Nan da nan ta tashi ta fice don zuwa ta taryi Baffan nata. Sai da ta shiga kitchen ta jera ruwa da lemo a faranti sanna ta fito, ta dubi Habib wanda yake zaune a parlor ɗin yana riƙe da Hammad tace ‘Yaya ku taso ku gaida Baffa ga shi nan a parlor ɗin Abbanku.’

    Tana shiga parlor ɗin ta same shi da Shukra da Nasreen yayin da Abban nasu yake zaune daga gefe a kan kafet; yanayin zaman da Mustaphan ya yi kawai ta kalla ta sha jinin jikinta. Ko da bai kai ƙararta gida ba to tabbas ta san a wannan ɗan zaman da Baffan ya yi ya gaya masa laifinta. Ta ƙarasa ta ajiye ruwan a gaban Baffa a daidai lokacin da Naja wadda ita ma ta shigo ta gaishe shi take ficewa daga parlor ɗin.

    Ta zauna daga gefen ƙafarsa sannan ta gaishe shi ya amsa cike da girmamawa. Sai da ya gama raha da yaran sannan ya zaro sababbin kuɗi a aljihunsa ya ba wa kowa naira dubu sannan ya sallame su suka wuce suka bar su daga shi sai Khadeejan da Mustapha. Ya dubi Khadeeja ya yi gyaran murya sannan yace ‘Deeje, garin yaya kika ce ba za ki taimaka ki karɓarwa abokiyar zamanki hidimar gida ba bayan ba ta da lafiya?

    Haba Khadeeja, hakan ai shi ne zaman tare tunda dai Allah ya haɗa ku. Ta yi shiru ta sunkuyar da kai tana tunanin ta inda za ta fara, ina ma da Baffa ya zo da Mommy. To ta ina za ta fara gaya wa Baffa yanda Mustapha ya yi mata lokacin tana nata laulayin? Kuma ya za a yi ta gaya wa Baffa cewa ita ba ta bin Mustapha ɗakinsa kuma duk ranar da ba ta bi shi ɗakinsa ba Naje yake kira ta taya shi kwana?

    To ai Baffa ma sai dai ya sake yi mata faɗan ƙin zuwa ɗakin miji domin tabbas abu ne da haka aka saba; kuma ta sani mata biyu ne da kakanta mahaifin baffa. Wanda da wayonta kafin dukansu su rasu ta san matan ne suke zuwa ɗakinsa. Wannan kam ai sai dai ta ƙara kai ƙarar kanta.

    Muryar Baffa ce ta katse ta yana cewa ‘Deeje me yasa ba za ki taimakawa abokiyar zamanki ba? Ta ɗan yi firgigit kamar wadda aka tasa daga bacci sannan tace ‘Uhm Baffa wallahi ni ma daurewa nake ina yin hidimar ranar girkina, tunda ga jego ina yi sannan kuma ina zuwa aiki. ‘Eh, ai wannan ba zai gagare ki ba tunda kin ga da a ce ke kaɗai ce a gidan ai duka za ki haɗa ko?’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci sannan daga baya tace ‘Baffa ni ma fa haka nake haɗa nawa laulayin da aikin gidan babu wwanda yake taya ni. Kuma ka ga Baffa akwai mai aiki fa wadda za ta iya yi mata duk abinda take so idan ta yi mata bayani. Baffa ya ɗan yi murmushi sannan yace ‘Na fahimce ki Khadeeja, amma dai ki yi haƙuri ki karɓar mata aikin.

    Tunda kin ga yanzu ke ma idan kika kuma samun wani cikin ai za ta karɓar miki ko? Ki yi haƙuri Deeje, ba na son taurin kai da yawa. Allah zai ba ki lada har kashi biyu, ladan biyayya wa miji da kuma ladan taimakon ‘yar uwarki musulma wadda take neman taimakon naki. Ki yi haƙuri kin ji, tunda ga yarinyarki nan tana taimaka miki ki zauna lafiya tunda dama yara duka naki ne tun kafin ma a auro ta.’

    Haka Baffa ya ɗauki lokaci yana ba ta haƙuri, daga ƙarshe kuma ya ba ta umarnin lallai ta taimaka wa Naja ta karɓi hidimar gidan. Bayan ya miƙe duka suka miƙe gaba ɗaya, a nan ya yi sallama da Khadeeja yace ta koma ciki. Suka fice shi da Mustapha wanda ya yi masa rakiya har wajen motarsa sannan ya yi masa sallama ya tafi.

    Ya san ko da ya koma wajenta a yanzu ba za ta saurare shi ba sai dai ma ta gaya masa maganganun da ba ya son ji, don haka ya wuce wajen Naja tunda dama kwananta ne. Har turiri take ji yana taso mata a ƙirjinta saboda tsabar yanda zuciyarta take tafasa; sai da ta yi da gaske sannan ta kai kanta ɗakinta ba tare da ta rushe da kuka ba. Ya za a yi a ce ta karɓarwa Naja girki saboda kawai tana da ciki?

    Bayan ita a lokacin da tana da nata cikin haka ya dinga barinta da duk wata hidima yana hana yaranshi su taya ta. Sannan kuma idan ta yi magana ya dinga nuna mata cewa laulayi ba komai ba ne kamar ma dai ita ce take son nuna raki. Yanzu kenan haka za ta kwashe wata takwas ko tara tana kula da yara yayin da Naja take kwana da miji tunda laulayin bai hana idan ta same shi shi kaɗai a ɗakin ta kai masa kanta ba?

    Tana shiga ta murza mukulli ta rufe ƙofar, sai da ta ƙarasa kan daddumar da ta tashi sannan ta zube da gwiwoyinta ta rushe da kuka. Shikenan ita ta zama baiwar Mustapha ne? Ya iya nunawa kowa ƙauna da tausayi a duniya amma banda ita? Anya za ta iya wannan rayuwar a gidan Mustapha kuwa? Amma ta san dole ne ta bi umarnin Baffanta, musamman da yake a gaban Mustapha ya ba ta umarnin. Ta kifa goshinta a ƙasa ta sake rushewa da kuka.

    Ya so ƙwarai kamar yanda ya saba leƙawa da daddare ya yi wa wadda ba ta da kwana sai da safe ya leƙa wajen Khadeeja, amma da yake bai shirya rigimarta ba sai kawai ya ƙyale ta suka shige ɗaki shi da Naja suka yi kwanciyarsu. Ba ƙaramin daɗi ya ji ba da ya dawo daga masallaci sallar asuba ya jiyo motsinta a kitchen, tabbas ya san ta ji maganar Baffanta.

    Ba tare da ɓata lokaci ba ta shirya su sannan ya fito ya kai su makarantar. Kafin ya dawo daga kai su makaranta ta gama nata shirin, a zaune ya same ta a parlor ɗinta tana karyawa. Babu yabo babu fallasa suka gaisa, sai dai daga gaisuwar ba ta sake ko da kallon inda yake ba. Jimawa kaɗan ya miƙe zai fice, tace ‘Idan na tsahi daga aiki zan je gidan Mommy.’

    Ya ɗan tsaya yana kallonta yana ƙoƙarin su haɗa ido ko zai karanto wani abu a fuskarta, sai dai ba ta ba shi damar ba. Daga tsayen yace ‘Ki gaishe min da mutanen gidan. Ya fice ita kuma ta cigaba da cin abincinta ba tare da ko da ta kalli inda ya wuce ba; gaba ɗaya ma a halin yanzu ko kallonsa ba ta son yi.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Huɗu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Huɗu

    Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Huɗu

    Yana shiga parlor ɗinta ya kai hankalinsa kan dining table, yanda ya ga wajen a jere da kwanuka ya tabbatar abincin ne ta dafa ta ajiye masa. To me yasa ta yi hakan? Ya ƙarasa kan tanle ɗin ya buɗe kwanukan ya ga abinda ta dafa, sannan ya taɓa flask ɗin ruwan zafi ya ji shi a cike; tabbas ya san shayi ta dafa masa.

    Ya gyaɗa kai ya juya ya nufi ɗakinta. Duk da ita ba mace ce mai son mu’amala ta turaren wuta da humra ba amma dai tana son ƙamshi, tana da haɗaɗɗun turarkanta na jiki da na kaya waɗanda idan dai ta zauna a waje sai ka ji ƙamshinsu. Yana tura ƙofar ɗakin nata ƙamshin turarenta ya yi wa hancinsa maraba.

    Fitilar ɗakin a kashe take sai dai dim-light wadda take ajiye a kan durowar gefen gado ita ce a kunne; ga alama bacci ne ya kwashe ta ba tare da ta kashe fitilar ba. Ya ƙarasa kan gadon inda take kwance, ya leƙa fuskarta; bacci take yi hankalinta a kwance ga shi yanayin baccin ya yi wa fuskarta kyau. Kamar ya ƙyale ta sai kuma ya canza tunani, ya zauna a hankali a gefen gadon daidai inda ƙafafunta suke, ya ɗaga abinda ta rufa da shi ya sosa mata tafin ƙafa a hankali.

    Ta janye ƙafarta da sauri sannan ta buɗe ido a hankali hankalinta gaba ɗaya yana kan Hammad wanda yake kwance a cikin gadonsa na baby a gefen gadon nata. Ya yi dariya a daidai lokacin da ta gan shi, ya lakace mata hanci yana cewa ‘Yanzu mutum ɗaya ne a rayuwarki wato Hammad ko? Ke na taɓa amma ba abinda ya taɓa ki kike nema ba yaronki kike nema kada a taɓa miki shi.’

    Ta yi murmushi ta mutssike idonta tana gyara zama sannan tace ‘To ina laifi, ni ce gatansa ka ga kuwa dole na kula da amanar Allah. ‘Haka ne. To a taso a ba ni abincina yunwa nake ji sosai. Ta zubo ƙafafunta daga kan gadon ta miƙe tana cewa ‘Bari na wanko baki. Ta wuce ta gaban shi ta nufi banɗaki.

    Ya bi bayanta da kallo yana yaba yanda jego ya karɓe ta. Ya daɗe bai ganta a haka sanye da rigar bacci kamar wannan ta jikinta ba sai yau kuma ta yi matuƙar burge shi. Yana nan zaune yana lissafi ta fito daga banɗakin suka fito parlor ɗin. Sai da ya zauna a table ɗin sannan ta zuba masa abincin ta ajiye a gabansa, ta koma ta haɗa masa shayi kamar yanda yake so shi ma ta ajiye masa ta koma ta zauna a kujerar kusa da shi.

    Tun kafin ta zauna ya fara cin abincin saboda da gaske yunwar yake ji; bayan ya cinye lomar bakinsa ya dube ta yace ‘Ke kin ci abincin ne? Tace ‘Um, mun ci ni da yara mun ƙoshi tun ɗazu. Suka yi shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan yana cin abincinsa yace ‘Wai me yasa ba ki saka abincin a parlor na ba kika kawo shi nan?’

    Ba tare da wata damuwa ba tace ‘Ba komai, kawai dai nan ɗin ya fi min kusa da kitchen saboda sauƙin aiki ko? Um haka ne. Ki dinga sakawa a parlor ɗin kawai kin ji can ɗin zai fi yanda duk wanda yake son ya ci zai iya ɗiba. ‘Ok, next time in sha Allah. Suka sake yin shiru na ɗan lokaci, jimawa kaɗan ya ajiye cokalinsa ya fara shan shayin.

    Bayan ya kurɓa ya ajiye kofin sannan yace ‘Kuma na ga ba ki gyara mana ɗakin ba, yanzu za ki gyara kenan ko a haka kike so mu kwana? Ta kalle shi da mamaki tana ɗan zare ido ‘Duk gyaran da na yi kuwa? Ko dai ba ka kalli ɗakin ba? Koda yake ba ka kunna fitila shi yasa ba za ka ga ɗakin sosai ba amma na gyara sosai fa.’

    Ya kula da tana maganar hankalinta yana kan ƙofar ɗakinta kamar dai ta za ta ɗakinta yake nufi ba ta gyara ba, yace ‘Ba fa ɗakinki nake nufi ba, ɗakina nake nufi tunda ai a nan za mu kwana. ‘Oh,..’ sai kuma ta ɗan sunkuyar da kai kamar dai ta kasa faɗin abinda take son faɗa ne. Ya kurɓi shayi ya bi ta da kallo yana jira ta ƙarasa faɗin abinda ta fara faɗa.

    ‘Gaskiya mu kwana a dakina, in ya so duk ranar kwana kai sai ka dinga zuwa ɗakina muna kwana. Da mamaki yake kallonta yana dariyar yaƙe ‘Khadeeja a ina kika taɓa jin miji ya bi matarsa ɗakinta kawai saboda su biyu ne? shikenan yanzu duk wacce take da kwana ni ne zan je ɗakinta kenan? Ta ɗan ɓata rai ‘Ni fa ba haka nace ba, ita idan tana so ta dinga zuwa ɗakinka ba ni da matsala da hakan amma ni dai sai ka dinga zuwa ɗakina.’

    Dariya ma maganarta ta ta so ta ba shi; tunda yake bai taɓa jin inda maigida yake bin ɗakin matansa ba sai dai a inda ba shi da ɗakin saboda ƙanƙantar gidan ko kuma a gidan haya. Amma ya za a yi yana da gida kamar wannan ga ɗakinsa da parlor ɗinsa amma a ce shi ne zai dinga bin mace ɗakinta? Allah ma dai yasa Khadeeja wasa kawai take yi.

    ‘Tunda kike don Allah kin taɓa jin inda aka ce maigida kamar wannan yana bin matansa ɗaki saboda kwana madadin su su je ɗakinsa?’ Ya tambaye ta yana nuna gidan, sannan ya cigaba ‘Kuma ma a wanne karatun aka biya miki haka bayan ga yanda kika taso kika ga ana yi? Ta kalle shi ta marairaice da fuska tana cewa ‘Don Allah ka bari mana, na ga ɗakin nawa ma duk gidanka ne ai meye don ka kwana a ciki.

    Ita ma Najan idan tana buƙatar hakan ba sai ka je ɗakinta ka kwana ba? ‘Oh, ni ne ma zan dinga bin ku ina kai muku kwanan kenan? ‘To meye a ciki, abu ne fa wanda ya zo a tarihi ma. Ya ɗan zaro ido yana kallonta ‘Wanne tarihin Khadeeja? In ce ko dai tarihin tsumburbura ne? Ta kula dai so yake ya raina mata hankali, kuma idan ba ta yi da gaske ba so yake ta dinga zuwa ɗakinsa kwana.

    Ita kuma gaskiya ba ta jin za ta iya kwanciya gadon da ya kwanta da wata matar ko da kuwa ba Naja ɗin ba ce. Gara kawai ya dinga zuwa ɗakinta. Ta ƙara ɓata fuska tace ‘To a islamiyya dai tunda ake biya mana sirah sai dai a ce Annabi SAW ya je ɗakin Aisha, ko ya je ɗakin Hafsa da sauransu, duk bayanan da aka yi mana sun nuna shi yake zuwa ɗakin kowacce.

    Kuma tunda dai auren nan shi ake kwaikwayo SAW ai ba zai zama matsala ba idan an kwaikwayi wannan ɗin ma. Buɗe baki ya yi kawai yana kallonta; ya rasa yanda aka yi Khadeeja take lale shi haka har take samun damar gaya masa duk maganar da ta ga dama. Ya jijjiga kai yace ‘To idan nace ba zan zo ba fa sai dai ke ki zo ɗakin nawa?’

    Ta yi murmushinta wanda yake ƙara ba shi mamaki; kana cikin magana da ita fuska murtuke sai kuma ta koma murmushi har ka ga kamar da zuciyarta take murmushin, haka ma kuma idan tana walwala lokaci guda za ta sha kunu ka zata kamar ba ta taɓa murmushi ba.

    Muryarta ce ta katse masa tunanin tana cewa ‘Na san ma ba za ka ce hakan ba, kai da gidanka. Abinda ko a parlor ka kwana babu wanda zai nuna maka yatsa balle don ka kwana a ɗakin matarka? Bin ta kawai yake da kallo yana jijjiga kai, yace ‘Toh tsara ni Khadeeja. Ta yi dariya tana miƙewa tsaye tana cewa ‘To ina laifi, yaushe rabon da a tsara ka.

    Kasa magana ya yi kawai ya dinga bin ta da kallo har ta gama kwashe kwanukan. Buƙatar ta yake yi saboda shi kansa ya san ya yi kewarta, don haka ma ba ya son ya ja rigima a wannan daren da yake son ya huce gajiyarsa. Gashi sai kai wa da kawo wa take yi tana kwashe kwanuka tana juya jikinta kamar da gayya, ya ma rasa me zai ce mata.

    Bayan ta gama kwashe kwanukan ta dafa kafaɗarsa tace ‘Sai ka shigo. Ba ta ko saurari amsar shi ba ta wuce ɗakinta ta bar shi a nan. Sai yau ya tabbatar Khadeeja ta raina shi; tunda yake bai taɓa ganin matar da idan ta yi niyyar abu sai ta yi shi ba ko da tsiya ko da tsiya-tsiya sai Khadeeja.

    Anya kuwa ba wani abu Khadeeja ta yi masa ba; idan ta ga dama ta gwada masa taurin kai da fitina idan kuma ta ga dama ta mayar da shi kamar wani sakarai ta yi masa wayo? Amma dai gaskiya ba zai juri bin ta ɗakinta ba dole ta haƙura ta yi yanda aka saba wato duk mai kwana ta bi miji ɗakinsa.

    Babu yanda ya iya da yake shi ne yake da buƙatarta dole ya tashi ya bi ta ɗakinta; kafin ya je ma bacci ya riga ya kwashe ta. Don haka sai da ya tashe ta ta sake lallaɓa ta sannan ya sami biyan buƙatarsa.

    Washegari ya kama ranar Asabar ce don haka yara ba su da makaranta; ko da ya dawo daga masallaci a kan dadduma ya sami Khadeeja a ɗakinta tana azkar, bayan ta idar ta gaishe shi sannan tace ‘Mantawa fa na yi jiya ban gaya maka yau ne bikin su Fatin Baba Sani wanda na nuna maka invitation ɗin last week ba. ’Ya gyara pillow ya kashingiɗe a kan gadon yana cewa ‘Ok, Allah ya sanya alkhairi.

    Ai insha Allahu ni ma za ni ɗaurin aure don Baffa da kansa ya turo min kati. ‘Ok. Ni sai wajen azahar zan tafi don ka ga ban je yawon arba’in ba sai na haɗa gaba ɗaya, idan na kwana biyu a gidan Mommy ranar Litinin sai na dawo. Ya ɗan ɓata fuska ‘Kuma shi ne har kwana biyu? Ai na zata a gidan bikin za ki ga duk wani wanda ya kamata ki je masa yawon.’

    Ta yi ‘yar dariya sanna tace ‘Kada fa ka manta bikin na dangin Baffa ne, ‘yan uwan Mommy su kuma ai sai dai na je musu gida yawon arba’n ɗin ko? Hajiya Nana dama ban kai mata baby ba ga su Anti Halima da Baba Usman. Ka ga yau a gidan biki zan wuni, gobe kuma tun safe za mu fara da Nabila; dama za mu kai musu katin bikinta tunda ka ga an fara rabo duk da dai bikin saura sati uku.’

    ‘Uhm, sai kun dawo. ‘Mun dawo kuma? Ni kaɗai fa zan tafi, Hafsa kawai zan ɗauka saboda Hammad. Ya tashi zaune yana fuskantarta ‘Na zata ke da yara za ki tafi kamar yanda kuka saba. Ta jijjiga kai tana dariya ‘Haba dai, yawon arba’in ɗin na kwashi yara har huɗu? Dama saboda babu mai kula da su ne yanzu kuma ka ga Antinsu tana nan. Ni kaɗai zan tafi.’

    Duk yanda ya so ta tafi da yaran nan haka ya haƙura ya ƙyale ta domin ta ci alwashin ba za ta sake tafiya da su danginta ba tunda yanzu suna da uwar ɗakin da za su dinga kawowa gulma. A kan lokaci ta gama abincin safe, sai dai da yake yana nan babu yanda ta iya haka ta jera a dining table ɗin parlor ɗinsa. Dankalin bature ta soya da ragowar sauce ɗin jiya da aka ci abincin dare sannan kuma da soyayyen ƙwai.

    Kowa a plate ɗinsa ta zuba masa har shi Mustaphan ta saka sauce a gefe da kuma soyayyen ƙwai. Nashi ta fara ajiye masa tare da na Shukra sannan ta juya ta koma kitchen ɗin. Tana shigewa kitchen ɗin ya dubi Afaf yace ‘Je ki ƙasa ki kirawo Antinki ta zo mu yi breakfast.’

    Nan da na ta miƙe ta fice, ya dubi Habib ya miƙe yana shirin ya bi Khadeeja kitchen ya karɓo nashi abincin yace ‘Shiga parlor ɗin Anti ka ɗauko kujerar dining guda ɗaya a ƙara. Don haka ya bi bayan Khadeejan. A hanya ta haɗu da shi ta riƙo plate biyu, tana ƙoƙarin miƙa masa yace ‘Abba ne yace na ɗaukowa Anti Naja kujera tare za a yi breakfast ɗin da ita.

    Kafin ta gama fahimtar abinda ya faɗa ya wuce ta ya nufi dining; tana ƙarasowa ta ajiye farantan hannunta ɗaya a gaban Nasreen ta zagayo da ɗayan za ta ajiye a kujerar da take kusa da Mustaphan a daidai lokacin da Afaf ta shigo tare da Naja suna tafe suna hira. Kafin ta yi magana ta zauna a kujerar da take kusa da Mustapha daga damansa a daidai lokacin da Khadeejan take shirin ajiye nata abincin a wajen.

    Ta yi cak ta ɗauke farantin da take niyyar ajiyewa ta dubi Habib tace ‘Yaya ka je kitchen ka ɗauko naka abincin ke kuma Afaf ungo wannan ni sai na ɗauko wani. Cike da fara’a Naja tace ‘Ina kwana Umman Hammad. Ita ma nan da nan ta saki fara’a ‘Lafiya ƙalau amarya ba kya laifi, ya gajiya? ‘Alhamdulillah. Sannu da aiki. ‘Yauwa.’

    Har cikin ransa ya ji daɗin yanda suka gaisa, haka yake son iyalansa ko da dai idan ba ya nan ba za su haɗu su yi hira ba to idan yana nan a zauna duka kamar haka a ci abinci tare; ya dubi Khadeeja yace ‘Yauwa ita ma ki taho mata da abincin ko? ‘Ok.’ Ta amsa a gajarce sanna ta juya ta nufi kitchen ɗinta. Kafin ta ƙarasa kitchen ɗin zuciyarta ta gama tunzura; Mustapha so yake ya yi mata dole kenan?

    Ta gaya masa ba za ta yi abinci da matarsa ba amma shi ne zai saka a kirawo ta har da zama a kujerarta. Lokacin da ita Najan take girki ai bai taɓa kiran Khadeejan yace ta zo su ci abinci ba shi ne sai yanzu don ya tabbatar mata Naja ita ce matar da yake ƙauna shi ne zai ce ta ba ta abinci. Nan take ta juye ragowar dankalin wanda dama ba yawa ne da shi ba ta ajiye ne saboda Shukra, ta haɗa da wanda da ta zuba wa Afaf ta zuba sauce da ƙwai.

    Ta haɗa shayinta mai kauri ta ɗauka ta wuce ɗakinta ta bar Hafsa a kitchen tana cin nata abincin. Shiru Khadeeja ba ta fito ba, kowa yana ta cin abinci yayin da Naja take shan shayinta wanda ta haɗa. Shirun ya yi yawa ya dubi Habib yace ‘Je ka dubo ko Antinka dankalin ta tsaya soyawa? Bai daɗe da shiga ba ya dawo yace ‘Abba ba ta kitchen ɗin, tana ɗakinta kuma ta kulle ƙofar.

    Ya zauna ya cigaba da cin abincinsa ba tare da wata damuwa ba. Ajiye fork ɗin da ke hannunsa ya yi, ya yi shiru saboda takaici; mantawa ma ya yi ya ba wa Khadeeja mukullin ɗakinta saboda a da ya yi alƙawarin ba zai sake ba ta mukullin ɗakinta ba saboda yanda take kulle kanta a ciki ta yi burus da kowa. Ya ture kwanonsa ya miƙe, ita ma Naja ta miƙe a lokacin.

    Ya kalli plate ɗinsa; ya riga ya ci da yawa sannan kuma sauran duk ya dame da sauce. Cike da damuwa ya cewa Naja ‘Ko wannan za ki ci naje na dubo. ‘No, kada ka damu. Ku ci abincinku akwai bread a ƙasa zan je na ci.’ Ta juya ta fice daga parlor ɗin ba tare da ta surare shi ba. A fusace ya nufi ɗakin Khadija, tun kafin ya fara buga ƙofar ya kirawo sunanta.

    Ba tare da ɓata lokacin ba ta amsa sannan ta taso ta buɗe masa ƙofar, ko a fuska ba ta nuna masa ta san ta yi laifi ba. Ya shige cikin ɗaki ya kalli abincin da take ci a gefen dadduma yace ‘Ya za ki taho nan ki kama cin abinci ki bar mutane? Kuma kina ji nace ki ba ta abincin ita ma. Duk yanda ta so ta bi maganar a hankali bai samu ba, domin yanda ya yi mata wannan tambayar da isa da gadara take ta ji duk wata kara da za ta iya yi masa ta bushe.

    Ta kalle shi ta kawar da kai sanna ta wuce shi ta koma ta zauna a gaban abincinta inda ta taso sannan tace ‘Gani na yi kun cike table ɗin, abincin kuma babu tunda ni ban soya dankali da ita ba. Me kake so na ba ta? ‘Ai tun jiya nace ki dinga saka abincin a can don kowa ya ci kuma kika amsa ko? Me yasa ne kike so ki dinga raina ni a gaban mutane? Saboda me nace ki ba ta abinci ba za ki ba ta ba zaki shigo nan ki bar mutane?’

    Ta kula dai duk wani zille-zille ba zai yi mata ba, ta kalle shi suka haɗa ido ta yi murmushin yaƙe mai ɗauke da takaici sannan tace ‘Kwana kusan talatin ta yi a gidan nan tana girki ba ta taɓa ba ni ba, kuma tare kuke cin abinci kai da ita da yara ba ka taɓa cewa a kirawo ni na ci abinci ba; ko da yake ko ka kirawo ni ma ba ci zan yi ba tunda ni ma na iya girkawa.

    Ka yi haƙuri ba zan haɗa girki da matarka ba ita ma kar ta haɗa da ni, duk wanda ya girka yaci shi da maigida da yara kawai. Ta miƙa hannunta ta ɗauki fork a kan plate ɗin da yake gabanta ta fara wasa da shi tana ƙoƙarin tokare takaicin da yake taso mata yana neman ya saka ta kuka.

    ‘Wai ke me yasa ban isa na gaya miki magana ki ji ba ne Khadija? Ko.. ‘Ita da ka gaya mata ai ta ji har ta ba ni abincin, ko da yake ita ka ɗauka mutum shi yasa kake nema mata abinda za ta ci. Ni da babu wanda ya damu da rayuwata ina nan kake fita ka siyo muku abinci ka saka ta a gaba ita da yaranka ku cinye ba tare da ko rabona an ba ni ba. Ban yi magana ba, shi ne kuma yanzu za a ce ni zan ba ta abinci; to ta cigaba da jira na ta ga idan za ta ci abinci.

    Ta gyara zama ta jingina da bango ta kawar da kai. Ya rasa abinda zai gaya mata saboda tabbas ya san duk abinda ta faɗa gaskiya ne, sai dai a wancan lokacin ai laifi ta yi masa na ƙin amincewa ta kula da yara don haka bai ga dalilin da zai sa ya ba ta abincin da ya siyo ba bayan ta ƙi ta girka. Ba tare ya ce mata komai ba ya fice daga ɗakin don a yanda ya san Khadija da taurin kai sai dai ya datse igiyar auren nan amma ba za ta yi abinda yake so ba.

    Sai dai tabbas idan ta cigaba da gwada masa taurin kai irin wannan zai datse igiyar auren ya huta, ta je can gidansu ta cigaba da taurin kan. Haka ya ƙarasa shiryawa zuciyarsa babu daɗi, don ko ɗakin Najan ma bai shiga ba suka fice tare da Habib suka tafi ɗaurin aure. Yana ficewa ita ma ta gama shiryawa, ta kulle ɗakinta da parlor ɗinta gaba ɗaya.

    Ta haɗa mukullanta da wanda ta cire daga jikin nashi keys ɗin duka ta jefa a jaka don ba ta so ko shi ya buɗe mata waje idan ba ta nan. Ta goya Hammad ta tasa Hafsa a gaba, suna saukowa ƙasa ta shiga parlor ɗin Naja inda ta jiyo hayaniyar yaran, ta dube ta da fara’a tace ‘To Anti ni na fita, zan je gidanmu ne in sha Allahu zan kwana biyu. Sai ranar Litnin zan dawo.’

    Ta juyo ta yi mata wani kallo na raini sanna tace ‘A dawo lafiya. Shukra ta tashi da gudu ta kama hannunta tace ‘Anti gidan Mommy za ki je? Ta shafa kanta ‘Can zan je Shukra, sai ranar Monday zan dawo. Ta langaɓe kai tana cewa ‘Kai Anti ina son zuwa fa, kwana biyu ban je wajen Anti Nabila ba fa.’

    ‘Ai kin ga Monday akwai school ko? Shi yasa ba zan tafi da ke ba. Amma idan zan koma ranar da babu makaranta zan tafi da ke kin ji. Haka ta tsaya ta lallaɓa ta sannan ta wuce.

    Danna nan don karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ashirin Da Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Makaman Da Hausawa Ke Amfani Da Su Wajen Faɗa Ko Yaƙi

    Makaman Da Hausawa Ke Amfani Da Su Wajen Faɗa Ko Yaƙi

    1. Adda
    2. Adaka (bindiga)
    3. Barandami
    4. Baushi
    5. Garkuwa

    6. Gariyo
    7. Ƙaho
    8. Kibiya
    9. Ƙota
    10. Kokara

    11. Kansakali
    12. Kwari da baka
    13. Bakan danƙo
    14. Lifidi
    15. Mashi

    16. Sulke
    17. Takobi
    18. Tsitaka
    19. Gorah

    FASIHIN KAITA

    Danna nan don karanta Wasu Kayan Aikin Rini

    Edita@rumasau-kallamu