Category: WikiHausa

Yadda ake amfani da WikiHausa

  • Yadda Ake Ittikafi

    Yadda Ake Ittikafi

    Ittikafi: shi ne dauwama a masallaci, domin yin ibadah, Salloli da tasbihi haɗi da tahlili, takbiri da salatin annabi da karatu alƙur’ani mai girma da sauransu a cikin masallacin Juma’a.

    حدثنى يحي عن مالك عن إبن شهاب عن عروة بن الزبير عن عَمْرَةَ بِنْتُ عَبْدُالرَّحْمَنْ عَنْ عَائِشَةُ زَوْجِ النَّبِيُ صَلَى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ أَنَّهَا قَالَتْ :كَانَ رَسول الله صلى الله عليه وسلم إِذَا عْتَكَفَ يُدْنِى إِلَى رَأْسَهُ فَأُرَجِّلُهُ ,وَكَانَ لاَ يَدْكُلُ الْبَيْتَ إِ لاَّ لِحَاجَةِ الإِ نْسَانِ.

    An rawaito daga Yahaya daga Malik daga Ibin Shihab daga Urwata bin Azzubairu daga Amrata binti Abdulrahman daga Aisha matar annabi (Sallallahu alaihi wasalla) ita ce tace “Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) ya kasance, idan yana ittikafi, yana kusanto kan sa kusa da ni (ma’ana sai annabi ya miƙa kansa ta taga , saboda gidansa yana kusa da masallaci ne) sai ta tsatstsefe (tatacewa) masa kansa, sannan (annabi) ya kasance ba ya shiga gida, don buƙatar wani mutum”. Idan yana ittikafi.

    Saboda haka mai ittikafi ba zai shiga gida ba, don buƙatar wani mutum daban, Haka ma mai Ittakafi ba zai fita cikin masallaci ba, sai don buƙatar kansa kamar su, rashin lafiya, abinci, idan babu mai kawo masa abinci da sauransu.

    Buku da ƙari kuma, mai Ittakafi ba zai tafi ziyarar maƙabarta ba, ba zai tafi zance ba ko gurin ɗaurin aure, ba zai kwana agidansa ba, sai dai idan a cikin masallaci ne, ba zai yawaita yawan surutu ba, sannan kuma dole ne a kan mai Ittikafi ya nisanci dukkanin abin da ya kamata ya nisanta. Misali kamar su kasuwanci, labaran duniya, kallon tsaraici, maganganun batsa ko kwarkwasa da sauransu.

    Haka kuma mai Ittikafi ba zai tafi gida ba, idan an ga wata (shan ruwa), har sai ya dawo daga masllacin idi kamar yadda ya zo a cikin wannan hadisin na annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasalla), sai dai idan akwai wani dalili mai ƙarfi.

    حدثنى يحي عن زياد عن مالك : أنه رأى بعض أهل العلم إذا عتكفوا العشر الأواخرين من رمضان ,لا يرد إلى أهاليهم حتى يشهدوا الفطر مع الناس .

    An ruwaito daga Yahaya daga ziyadi daga Malik (yace), haƙiƙa shi yaga sashin ma’abota Ilimi, idan suka yi Ittikafi na kwanaki goman ƙarshen watan Ramadan, ba sa dawowa gidan su (wajan iyalansu), har sai sun halarci masallacin Idi tare da musulmai.

    Sannan kuma babu laifi a kan mace ta yi Ittikafi kamar namiji, idan mace tana Ittikafi, sannan sai halarta ta same ta a cikin wannan hali (Ittikafi) me za ta yi?, Amsa idan mace hailarta ta same ta a wannan hali za ta koma gida ne, idan ta yi tsarki, sai ta dawo masallaci ta gina ko ta ɗora a kan abin da ya wuce na Ittikafinta, kamar macen da akwai ramuwar azumi wata biyu (60) a kanta, kuma waɗanda ake jera su, sai ta fara ramuwar azumi da ake binta, sai kuma halarta ta zo mata, sai ta tsaya da yin azumin, idan ta ɗauke mata, sai ta ɗora a kan abin da ta yi na aziminta.

    Hakan kuma babu laifi a kan mai Ittikafi yin aure ko Aure, matuƙar ba zai fita cikin masallaccin ba, sannan kuma ba zai sadu da matar ba, har sai bayan ya fito daga masallaci. Bugu da ƙari kuma, an hana saduwa da Iyali ga mai Ittilafi da safiya ne ko daddare ne, har sai bayan ya kammala Ittikafinsa.

    Sannan kuma babu laifi ga mai azumi, idan yana da mataye ko ‘yan uwa, sai su kawo masa ziyara cikin masallacin, amma kuma ba za su yi maganar wasa ba ko kwarkwasa. Har ila yau, mafi alherin Ittikafi kwana goma, ƙarancinsa kwana ɗaya da yini, haka kuma ba’a yin Ittikafi sai da azumi, kamar yadda Allah (S.W.A) ya faɗa a cikin Baƙara ayata (187)

    Sannan kuma mai Ittikafi ya shagaltul da karatun Alƙur’an ko nafilfili ko Istigifari ko ambaton Allah (S.W.A) dare da rana. Haka ma ya dage da neman kusanci ga Allah da mazonsa haɗi da neman addu’ar ci gaban addinin musulunci da musulmai da kuma kare su daga sharrin maƙiya da mahassada, domin alfarmar annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasalla). Bugu da ƙari kuma, babu laifi a kansa idan yana da wasu buƙatu ya roƙi Allah (S.W.A).

    Saboda haka Ittikafi yana ɗaya daga cikin manya-manyan Ibada masu girman gaske, sannan kuma shi Ittikafi riba biyu ce ko ma uku, na farko Ibadah ce mai girma , na biyu ga samun ƙarin girma a wajen Allah da manzonsa, matuƙar ya cika sharaɗan Ittikafi, na uku ga samun lada mai yawa haɗi da biyan buƙata da kuma samun farin jini a wajen al’umma da sauransu.

    Haka nema yasa ba kowa ba ne yake iya samun yin Ittikafi, saboda falalar da ke cikinsa, saboda duk wanda zai aikata abin da zai nisanta shi daga shiga wuta, sai shaiɗan ya ɗora masa kasala da gajiya, wajen ya ga ya hana shi aikata haka.

    Bugu da ƙari ma yana hana su yin aikin alheri kamar su kyauta, sadaka, ciyarwa, nafilfili da sauran su. Saboda haka sai ka ga mutane sun ƙi shiga Ittikafi, har sai ka ga masu shiga Ittikafin sun kammala, sun dawo suna zama tare da su, ka ga su, sun aikata Ibadah mai girma, sannan kuma sun dawo suna zama tare da su.

    Daga ƙarshe kuma, ina kira ga waɗanda ba su samu ikon shiga Ittikafi ba, to su samu abinci ko abin sha ko kayan marmari, su ba masu yin Ittikafi da sauransu, domin samun falalar da suke cikin, saboda duk wanda ya ciyar da mai azumi, Allah (S.W.A) zai ba shi lada kwatan-kwancin wanda ya yi azumi, ballantana ma a ce ka ba mai yin azumi kuma wanda yake cikin Ittakafi.

    Saboda haka ina ba da shawara ga waɗanda suke zuwa Umarah duk shekara, ga wata falala mai ɗimbin yawa, wanda ya kamata su dunga aikatawa, saboda kuɗin da suke kashewa a ƙalla zai iya ciyar da mutane abinci haɗi da nama na mutane guda dubu ɗaya, saboda haka yaya kake tunanin a cikin kowane gari a samu mutane guda goma su aikata haka, mutane dubu nawa ne za a taimakawa, a maimakon su dunga zuwa umrah duk shekara.

    Sannan kuma duk abin da mutum ya ciyar da wani mutum, to Allah (S.W.A) zai riɓanya masa sau ɗari bakwai (700) ko ma fiye da haka, sannan kuma ga samun zaman lafiya a tsakanin mawada da talakawa haɗi da yabo na karamci da addu’o`i agare su da sauransu.

    Muna roƙon Allah (Subhanahu Wa Ta’ala) ya ba mu ikon aikata wannan Ibadah ya kuma sa mu dace, Ameen, domin alfarma annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasalla), sannan kuma mutum ya guji yin ƙarya a lokacin da yake yin ittikafi, saboda dukkanin wanda ya yi ƙarya ko kasuwanci ko saduwa da mace ko catin da waya (WhatsApp ko Facebook) ko yawan surutu, to ittakafin sa ya ba ce, sai ya sake wani, matuƙar ya shagaltu da aikata haka. Wasu malamai suka ce kuma ‘a a, ittikafinsa yana nan, sai dai ya rage ma kan sa lada”.

    Danna nan don karanta Lailatul Ƙadri

    Edita@rumasau-kallamu

  • Lailatul Ƙadri

    Lailatul Ƙadri

    Wasu kwanaki ne masu ɗimbin falala, waɗanda suka fi watanni dubu, sannan kuma ba a samunsu, sai a cikin watan Ramadan, a kwanaki goman ƙarshensa.

    حدثنى زياد عن مالك عن يزيد بن عبدالله بن الهاد عن محمد بن إبراهيم إبن الحارث التيمى عن أبى سلمة  بن عبدالرحمن عن أبى سعيد الخدرى أنه قال :كان رسول الله صلى الله عليه وسلم يعتكف العشرالوسط من رمضان فاعتكف عاما , حتى إذا كان ليلة إحدى وعشرين وهى اليلة التى يخرج فيها من صبحها من اعتكافه قال : من اعتكف معي فليعتكف العشر الأوخر, وقد رأيت هذه اليلة أنسيتها , وقد رأيتنى أسجد من صبحها فى ماء وطين فالتمسوهافى العشر الأخر والتمسوهافى كل وتر ,قال أبو سعيد فأمطرت السماء تلك اليلة وكان المسجدعلى عريش فوكف المسجد قال أبو سعيد :فأبصرت عيناي رسول الله صلى الله عليه وسلم إنصرف و على جبهته وأنفه أثر الماء والطين , من صبح ليلة إحدى وعشرين .

    An ruwaito daga Ziyadi daga Malik daga Yazidu bin Abdulllah bin Hadi daga Muhammad bin Ibrahim bin Haris Al-tamimi daga Abu-Salma bin Abdullahman daga Abu-Sa’idul Kudri, haƙiƙa shi ne yace, Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) ya kasance yana Ittakafi a goman tsakiyar watan Ramadan, sai ya yi Ittikafi a wannan shekarar, har sai da ya kasance daren ashirin da ɗaya (ta same shi a cikin masallaci) ita ce da ya fita safiyarta, wanda zai yi Ittikafi a cikinta yace “Duk wanda zai yi Ittikafi tare da ni, to a daren goma ƙarshen (Ramadan), haƙiƙa ya ga a cikin wannan daren, sannan sai ya manta da ita, haƙiƙa na ganni ina sujjada a cikin safiyarta, akwai ruwa da taɓo, sannan (sai annabi yace) ku neme ta a cikin kwanaki goman ƙarshen (Ramadan ), sannan (ya ƙara cewa) ku neme ta a cikin kowace rana (na ranar).

    Saboda haka wannan hadisin ya yi magana a kan abubuwa guda biyu Ittikafi da lailatul ƙadri, Ibin Abdulbari yace wannan hadisi shi ne ya inganta a wannan babi, saboda annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) ya kasance yana Ittakafi a kwanakin goman tsakiyar watan Ramadan.

    Haka kuma  imamu Hafiz Ibin Hajar yace, shi ne da yi wa wawin damma da kuma sin sakina (ɗauri ko mara wasali), sannan kuma Ibin Abdulbarri yace wannan ruwarta (ta Manzon Allah) yana Ittikafi  har sai da ya kasance a daran ashirin da ɗaya, ita ce daran da ya fice a cikin ta da safiyarta, domin yin Ittikafi’’.

    Wannan ruwayar tana ɗaya daga cikin ruwayar Yahaya da Abubakar da shafi`i, amma a cikin ruwayar kala biyu ce da ta  Ibin wahabi da Ibin Ƙasim, waɗanda suka fitar da ita (annabi yana Ittikafi), amma kuma basu ambaci safiyar ba.

    Amma kuma shi Ibin Hazim ya faɗa misalin wannan ruwayar, inda yake cewa a cikin huɗubar daran ashirin da ɗaya,  annabi ya shiga Ittikafi, ita ce daran ashirin da biyu, saboda abin da aka faɗa a ƙarshen wannan hadisi.

    Sai ya buɗe idonsa, sai ga  annabi (Sallallahu alaihi wasalla) a gefensa a ranar, sannan kuma sai ga alamar ruwa da taɓo a cikin safiyar daren ashirin da ɗaya.

    Abin nufi a nan shi ne, mutum ya shiga Ittikafi kafin daren ashirin da ɗaya (lailatul ƙadri), sannan sai ya manta da ita, sai yace “annabi ya ga mala’ika da haske da idansa”, sannan kuma ya gani  a farkon wannan daran ya ga kaza da kaza a cikin daren, ya ga masallaci, mai girma kuma ga haske, sannan kuma a saman masallaci, ruwa yana zuba, saboda haka alamomin da ake iya gane daren lailati ƙadri ne.

    Misali kamar su gushewar rana, zubar ruwan sama, washewar sararin samaniya, gari ya yi tsit, rashin jin sautin karnuka ko dabbobi, da sauransu. Sannan kuma ana iya samu daren lailatul ƙadri a ranar daren ashirin da ɗaya ko da uku ko da biyar ko da bakwai, ko da tara waɗannan su ne ranakun da ake iya samun lailatul ƙadri.

    Amma Abi-Sa’id yace, sama ta kece da ruwa a wannan daren, sannan masallacin ya kasance tamkar ginshiƙi, sai masallacin ya tsaya, sannan kuma  Abi-Sa’id yace sai annabi (Sallallahu alaihi wasalla) ya buɗe idanunsa, sai ya juya sai ga goshinsa da hancinsa akwai alamar ruwa da tabo a daren Asubahin da ya shiga na watan Ramadan.

    An ruwato daga Ziyadu daga Malik daga Abudullah bin Dinari daga Abdullah bin Umar (yace) haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalla) yace’’ ku binciki (ku kirdado) daren lailatul ƙadri a cikin bakwai ɗin ƙarshe.

    Abun nufi a nan shi ne a kwanaki ashirin da bakwai ɗin ƙarshen.

    حدثنى زياد عن مالك عن هشام بن عروة عن أبيه : أن   رسول الله صلى الله وسلم قال “تحروا ليلة القدر فى العشر الأخرين من رمضان.

    An ruwaito daga Ziyaddu daga Malik daga Hishamu ‘’ku binciki daran Lailatul ƙadri a cikin (kwanaki) ashirin ɗin ƙarshen watan Ramadan.

    حدثنى زياد عن مالك عن أبى النضر مولى عمر بن عبيدالله : أن عدالله إبن أنيس الجهني قال لرسول الله صلى الله عليه وسلم : يا رسول الله , إنى رجل شاسع الدارفمرنى ليلة أنزل لها , فقال رسول الله صلى الله عليه وسلم ” أنزل ليلة ثلاث وعشرين من رمضان ”

    An ruwaito daga Ziyadu daga Malik daga Abi-nadhir mai yi wa Umar bin Ubaidullah hidima (yace), haƙiƙa Abdullah bin Unaisu Aljuhaniyyu yace da Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalla), ya manzon Allah ni mutum ne mai rushe-shshen gida, ka umarce ni da daren da aka saukar da ita (Lailatul ƙadri), sai Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalla) yace da shi “An saukar da daran (Lailatul ƙadri), ashirin da uku a cikin watan Ramadan”.

    Amma Ibin Abdulbarri yace wannan ruwayar yankakkiya ce, saboda Abi-nadhir bai riski Abdullah bin Unaisu ba, sannan kuma bai gan shi ba, amma haƙiƙa Imam Muslim ya sadar da wannan hadisin ta hanyar Dhahaku bin Usman daga Abidi daga Busra bin Sa’id daga Abdullah bin Unaisu da lafazin Hadisin Abi-Sa’id daga Daud ya sadar da shi ta hanyar Ibin Ishak daga Muhammad bin Ibrahim Attamimu daga Umrata bin Abdullah bin Unaisu daga mahaifansa kamar yadda wannan hadisin na Muwaɗɗa Malik ya nuna haka.

    An ruwaito daga Ziyadu daga Malik daga Humidu Aɗɗawilu daga Anas bin Malik, tabbas ne yace, Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalla) ya fita tare da mu a cikin watan Ramadan, sai yace ‘’ni na ga mutane biyu suna jayayya, sai suka ɗaga ta,(sai yace da su) ku neme ta a cikin (ashirin da) tara ko bakwai ko biyar’’.

    حدثنى زياد عن مالك أنه بلغه : أن سعيد بن المسيب كان يقول : من شهد العشاء من ليلة القدر , فقد أخذ بحظه منها.

    An ruwaito daga Ziyadu daga Malik (yace) haƙiƙa shin labari ya same shi lalle Sa’id bin Musayyibin ya kasance yana cewa, duk wanda ya shaida (ya yi sallah) Isha’i a cikin Lailatul ƙadri (Ai a cikin ranakun da ake sa ran ganinsu), haƙiƙa ya riski daren lailatul ƙadri.

    Haka kuma Ibin Abdulbarri yace, wannan ba zai iya kasancewa ba, sai kawai ra’ayi ne, sannan ba zai riƙi komai ba, sai  dai neman dacewar Allah (Subhanahu wata’ala) a cikin wannan ranar.

    Saboda haka malamai sun ƙarawa junarsu sani a kan daren Lailatul ƙadri, saɓanin mai yawa, daga cikin su akwai maganar baban malamin nan Al-araki, saboda ita (Lailatul ƙadari) ba ta yi dai-dai da sauran shekaru ba ko ranaku.

    Ma’ana ganin wannan daran sau ɗaya ya taɓa faruwa azamanin Manzon Allaah (Sallallahu alaihi wasalla), sannan kuma an faɗa awata maganar, wannan daran yana kewayawa ne a kowace shekara, a wata faɗar kuma an ce Lailatul ƙadri tana cikin rabin watan Sha’aba, sannan kuma wasu sun ce, A’a an keɓance ta ne a cikin watan Ramadan.

    Sannan za a iya samunta a cikin kowanne dare (Ramadan), Bugu da ƙari kuma Sheikh Sabkiyu ya yarinjar da shi, amma malam Sarkhisu ya faɗa a cikin sharhin ‘’ Hidayatu’’. Maganar Abi-Hanifa yace zamu samu ta (daren Lailatul ƙadri) an ciro ta ne a cikin dukkanin Ramadan, haka nan ma abokinsa ya faɗi haka sauransu.

    Haka ma an ruwaito daga Ibin Abi-Asim daga Anas yace, babu wanda ya sani daga cikin mu (ranar ganin Lailatul ƙadri), sai wani malami daga cikinsu yace, A a, Lailatul ƙadri, tana cikin rabin watan Ramadan, sai kuma wani mutum yace, A a tana cikin daren goman sha shida ne, na Ramadan.

    Sai kuma wani yace, A a tana cikin daren goman sha bakwai, sannan sai wani yace, A a tana cikin daren goma sha takwas, sai kuma wani ya ƙara cewa, A a tana cikin daren goma sha tara ne, sai kuma wani ya sake cewa, Aba tana cikin daren ashirin ga watan Ramadan.

    Haka kuma sai wani yace, A’a ita Lailatul ƙadri abar so ce, sannan kuma tana cikin goman tsakiyar watan ramadan, sai kuma wani yace A’a ita kuma abin so ce, sannan tana cikin goman ƙarshe.

    Sai kuma wani yace, A a, Lailatul ƙadri tana cikin daren ashirin da biyu na watan Ramadan har zuwa daren talatin ga watan Ramadan, sannan kuma wasu suka ce Lailatul ƙadri, tana ci kin goman tsakiyar watan Ramadan, wasu kuma suka ce tana cikin goman ƙarshen.

    Amma a cikin mazahabar Imam shafi’i jamhurum Sahabbai (mutanan mu) suka ce. haƙiƙa ita Lailatul ƙadri tana goman ƙarshe watan Ramadan, sannan kuma abar so ce a kan mu, sai dai ita abar ayyanawa ce a kan wannan al-amari, sannan kuma wannan daren na Lailatul ƙadri ba za ta gushe ba, har zuwa ranar lahira, kowanne ranaku goman ƙarshe (na wata) abar ɗaukakawa ce.

    Daga ƙarshe kuma, mazahabar imam shafi’i sun rinjayar da daren ashirin da ɗaya shi ne daren Lailatul ƙadri, sannan kuma dukkanin mazahaban nan guda huɗu sun yi bayani a kan kwanakin sa ran ganin Lailatul ƙadri.

    A takaice, alamomin daren lailatul ƙadri suna da yawa, amma dai idan ana cikin tsananin zafi ko sanyi, to a ranar daren za a samu sauƙi, idan kuma garin akwai duhu, to za a samu haske a garin da sauransu.

    Danna nan don karanta Azumin Watan Ramadan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Wata Mata Mai ’Ya’ya Biyu

    Tatsuniyar Wata Mata Mai ’Ya’ya Biyu

    Ga ta nan, gata nanku.

    Akwai wata mata tana da ’ya’ya biyu, ɗaya mace, ɗaya kuma namiji. Macen ce babba, namijin kuma shi ne ƙarami. Tana nan, tana nan sai wata rana ta kamu da rashin lafiya. Tana cikin rashin lafiyar ta kira ’ya’yanta, tana yi wa macen wasiyya cewa, ko da bayan ranta yaron ya ce zai yi wani abu to kada ta hana shi, ta bar shi.

    Bayan uwar ta rasu sai suka bar gidan, suka kama hanya suka nufi wani gari daban. Suna tafiya a cikin daji kwana da kwanaki, rannan sai wata babbar tsuntsuwa ta ɗauke su ta tashi sama da su, ta yi ta tafiya har suka isa daidai wani babban gari. Sai yaron ya ɗauki tsinke ya ce da yayarsa zai tsokale zumɓutun tsuntsuwar, amma sai ta ce idan ya tsokale tsuntsuwar ai za ta yar da su.

    Da ya ji haka sai ya ce mata ba uwarsu ta ce ta bar shi ya yi duk abinda yake so ya yi ba? Da yarsa ta ji haka sai ta yi shiru. Ya samo tsinke ya tsokali zumɓutun tsuntsuwar nan. Ita kuwa sai ta zubar da su a wannan gari.Can sai suka ga wani gida suka shiga, to ashe na wata tsohuwa ne. Da ta gan su sai ta yi maraba da su, ta ba su ruwa suka sha, ta tambaye su daga inda suke, sai suka kwashe labari suka ba ta.

    Sai ta ce da su za ta riƙe su, amma kuma akwai wani dodo da yakan zo da dare yana cinye mutane kullum a garin. Da dare ya yi aka kulle gida, sai yaron nan ya ce a ba shi ƙarafa guda uku, waɗanda zai yi amfani da su ya soke dodon, kowa ya huta a garin. Da tsohuwa ta ji abin da yaro ya faɗa, sai ta ce da shi ba zai iya ba, amma sai ya dage a kan shi dai a ba shi.

    Tsohuwa ta yi masa yadda ya nema amma ba da son ranta ba. Yaro ya hura wuta, ya zuba ƙarafan a ciki. Da suka yi ja, sai ya ji waƙar dodon yana cewa:

    “Wane ne ya isa ya ja da ni, a garin nan?

    Wane ne ya isa ya ja da ni, ni dodo?

    ”Sai can yaron nan ya ce: “Ni ne na isa na ja da kai a garin nan. Ni ne na isa na ja da kai, Ni Auta, har ma na fi ka.” Da dodo ya ji haka sai ya buɗe bakinsa ya yi wani irin ƙaraji. Sai Ɗan auta ya yi wuf, ya jefa masa ƙarfe ɗaya da ya yi jajir a cikin bakin. Sai dodon ya cafe ya haɗiye ƙarfen, yaron ya jefa masa ƙarfe na biyu, dodo ya cafe ya ƙara haɗiyewa.

    Da yaron ya jefa masa na uku ya haɗiye, sai dodon nan ya faɗi rigija. Nan take ya mutu a ƙofar masallaci, ko shurawa bai yi ba. Ganin haka sai Ɗan auta ya bar takalminsa a wajen mushen dodo. Da asuba ladan ya je ƙofar masallaci domin ya shirya ya kira salla, amma sai ya ga mushen dodon nan shim. Sai ya je ya gayawa Sarki abin da ya gani.

    A cikin murna Sarki ya je ya ga mushen dodo, kuma ya tambaya ko wane ne ya kashe shi, domin an ga takalmin wanda ya kashe dodo, amma ba a san ko na wane ne ba. Abu kamar wasa, sai Sarki ya ce duk wanda ya sa takalmin nan ya yi masa daidai, to shi ne ya kashe dodon, kuma Sarki ya yi alkawari zai ba wanda ya kashe dodon ladan rabin garin nan.

    Masu kwaɗayin wannan kyauta suka ta zuwa suna gwada takalmi, amma bai zauna musu daidai ba. Can sai aka ba Sarki labarin wata tsohuwa da ta yi baƙi, sai Sarki ya sa aka kira ta ta sa takalmi bai yi mata daidai ba. Daga ƙarshe dai Ɗan’auta ya sa takalami, kuma ya yi masa daidai. Da dai aka tabbatar shi Ɗan’auta ne ya kashe dodo, sai Sarki ya cika alƙawarin da ya yi, watau na ba shi rabin garin.

    Yaron kuwa ya karɓi rabin gari ya ci gaba da mulki cikin nasara, shi da yayarsa. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Mai biyayya lamarinsa ba ya ɓaci.
    • Kowa da irin baiwar da Allah ya yi masa a wannan duniya.
    • Duk mai mugunta sai ya gamu da wanda ya fi shi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar ’Yan Mata Masu Kamun Kifi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar ’Yan Mata Masu Kamun Kifi

    Tatsuniyar ’Yan Mata Masu Kamun Kifi

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana wasu ’yan matan ƙauye suka tafi rafi su, watau kamun kifi. Suka kuma yi sa’a suka kamo kifaye, suka kama hanya suka koma gida. A kan hanyarsu ta zuwa gida sai suka haɗu da wata tsohuwa sai ta tsayar da su, ta roƙi su sammata kifin da suka kamo, ko da mai ƙaya ne.

    Sai suka hana ta. Amma sai wata budurwa daga cikinsu ta ɗeba mata kifin. Ta karɓa, ta gode mata suka tafi. Washe-gari da suka koma rafi don kamun kifi, da yawa daga cikin ’yan matan kuma sun kamo kifin mai yawa, ƙoransu cike maƙil. Da tsohuwar nan ta roƙe su, suka hana ta sai waccan budurwa da ta bai wa tsohuwa kifin jiya ta gaya mata cewa yau ba ta samu ba sai wasu ’yan ƙanana guda biyu kawai.

    Ga shi kuma tana jin tausayin ’yar tsohuwar. Saboda haka sai ta ba ta ɗaya, ita kuma ta riƙe ɗaya. Kafin su rabu, sai tsohuwar ta gaya mata in ta je gida da wannan kifi guda ɗaya da ya rage a hannunta, kada ta dafa shi ta sanya shi a cikin randar gidansu. Bayan ta isa gida sai ta saka kifin a cikin randar kamar yadda tsohuwa ta ce ta yi. Sai ta shiga ɗaki ta kwanta.

    Da gari ya waye sai ta buɗe randa don ta ɗauki ɗan kifinta, amma sai ta ga randa ta cika maƙil da manya- manyan kifaye. Ta yi ta ɗiba, amma kifayen nan ba sa ƙarewa. Bayan ’yan kwanaki ’yan mata suka koma rafi don su kamo kifi, amma wannan ranar ba su sami komai ba, sai suka koma gida babu kifi.

    Washe-gari sai aka yi shela a gari cewa Sarki yana son ya ci kifi, kuma duk budurwar da ta kamo kifi ta dafa wa Sarki ta kai masa zai aure ta. Gaba ɗayan ’yan matan ƙauyen suka fita kamun kifi, amma ba wadda ta samo sai wannan budurwa da ta taimakawa tsohuwa da kifi. Yadda aka yi ta samo kifin nan kuwa shi ne, da ta kama hanyar rafi
    sai ta haɗu da wannan tsohuwar.

    Sai tsohuwa ta ce mata kada ta je babban rafi, ta nuna mata wata hanya da za ta kai ta har bakin wani ƙaramin gulbi. Sai tsohuwa ta ce ta yashe ruwan. Da budurwa marainiya ta fara yashewa sai ta fara ganin manyan kifaye, ta yi ta ɗiba har ƙwaryarta ta cika, ta koma gida. A duk faɗin garin budurwar nan kaɗai ce ta kamo kifi a wannan rana. Bayan ta dafa kifi ta sa a cikin akushi ta kai fada, mutanen gari da Sarki suka yi mamaki.

    Nan take Sarki ya amince zai aure ta. Bayan ta koma gida sai aka gaya mata ta sanar da iyayenta, za a yi bikinta da Sarki. To da yake iyayenta duk sun rasu marainiya ce, ba ta da kowa, da ta koma gida dare ya yi ta kwanta, sai ta tashi tsakar dare tana kuka domin tana tunanin ba wanda zai yi mata kayan gara. Tana cikin wannan hali na damuwa, sai ta ga kwatsam tsohuwar nan ta ɓullo mata a tsakar ɗaki, kuma ta tambaye ta ko mene ne yake damun ta.

    Sai marainiya ta yi mata bayanin dukkan abin da yake damun ta, har ya zamanto ba ta iya yin barci. Da’yar tsohuwa ta lallashe ta sai kuma ta gaya mata za ta iya yin dukkan abin da take buƙata. Yarinya ta yi ajiyar zuciya cikin murna, ta yi wa tsohuwa godiya. Tun kafin gari ya waye, sai ta ga ɗakinta cike da kayan gara fiye da yadda take zato za ta samu, ta yi ta murna.

    Ta godewa Allah. Ana nan, ana nan, ranar bikinta ta zo, aka ɗaura musu aure ta yi ta murna. Tagode wa Allah aka yi gagarumin biki, aka kai amarya gidan Sarki. Da kayan gara ya ƙare sai tsohuwa ta sake ɓullo mata a ɗakinta, ta kuma kawo mata kayan alatu da na marmari. Tace mata kullum za ta rinka kawo mata kayan ɗadi ta rinka ba Sarki, amma kada ta gaya wa kowa.

    Yarinya ta ce ba za ta gaya wakowa ba. Suka yi sallama tsohuwa ta tafi. Bayan ’yan kwanaki sai matan Sarki suka fara tsegumi cewa amarya ba ta da kowa, amma kullum Sarki yana ƙara son ta fiye da sauran matansa, kuma kayan alatu da take ba Sarki wa yake ba ta? Suka yi ta bincike, amma ba su gano bakin zaren ba, sai suka haƙura, suka bar ta.

    To shi Sarkin bai taɓa haihuwa ba, duk sanda matansa suka ɗauki ciki, sai ya zube. Rannan bayan ’yan shekaru da auren marainiya da Sarki, sai ya tara matansa, bayan ya tabbatar kowacce tana da ciki. Ya ce da su kowacce ta tafi gidan iyayenta, kuma kada ta dawo sai ta haihu. Bayan kowacce ta kama hanyar gidansu, sai ita kuma amaryar
    Sarki marainiya ta tafi gindin wata tsamiya ta zauna, ta kama kuka, tana waƙa tana cewa:

    “Wa zai ba ni yaro a yau?
    Wa zai amshi haihuwa a yau?
    Ni ba ni da uwa, ni ba ni da uba?”

    Tana cikin wannan hali sai tsohuwa ta zo ta sake tambayar ta abin da yake damun ta. Sai ta kwashe labarin yadda suka yi da Sarki ta gaya mata. Sai tsohuwa ta ɗauke ta, ta kai ta gidanta, ta cigaba da kula da ita, tana yi mata albishirin cewa in Allah ya yarda, za ta haihu, cikin ba zai zube ba.

    Suna nan tare da tsohuwahar ranar haihuwa ta zo, ta haifi ɗanta lafiyayye, kowa ya gan shi ya ga ubansa. Amma sauran matan Sarki kuwa ba su sami haihuwa ba, sai ɗaya daga cikin kishiyoyinta ta sami labarin haihuwar amaryar Sarki marainiya. Sai ta fara bin ta a sace, har ranar da aka sa za su koma gidan Sarki. Rannan sai amaryar Sarki ta tafi bakin rafi donta yi wanka tare da ɗanta.

    Da ta je bakin rafin sai ta ajiye jaririn, ta shiga wanka. Sai kishiyar nan tata ta zo ta sace yaron, ta gudu da shi.Da suka koma fada sai amaryar Sarki marainiya ta je ta gayawa Sarki cewa ta haihu, amma an sace abin da ta haifa. Sai aka ƙi yarda da wannan magana. Da kishiyarta wadda ta sace yaron ta zo, sai suka ce ita ce ta haifi yaron.

    Ita kuwa matar Sarki marainiya sai aka sa fadawa da yaran Sarki suka kafa mata ɗaki irin na dawaki, aka ajiye ta a can, bisa cewa ta yi wa Sarki ƙarya. Da kishiyarta ta ba yaron nono sai ya ƙi kamawa. Aka yi juyin duniyar nan, jaririn nan ya ƙi shan nono, sai aka rinƙa ba shi madarar shanu, har ya girma. Ana nan, ana nan, wata rana sai ɗan duba watau Sarkin bokayen Sarki, ya gaya wa Sarki cewa wannan ɗan nasa matar da ta rene shi ba ita ce uwarsa ba.

    Mamaki ya kama Sarki, sai ya nemi Sarkin bokaye da ya gaya masa ta yadda zai gane uwar yaron. Sai mai duba ya ce ya tara matansa ranar kasuwar garin, kuma a tara mutane a fada, sannan duk matansa su yi abinci, su kawo shi bainar jama’a, kuma su jeru a fada. Idan an yi haka, sai a ce da yaron ya zaɓi abincin da matan Sarki suka kai wurin, to duk abincin da yaron ya zo ya ci, tabbas mai wannan abinci ita ce uwarsa.

    Ba tare da nuna wata shakka ba, Sarki ya ce a yi haka ɗin. Sarki ya umarci matansa a kan abin da ake so kowacce ta yi. Duk matan suka yi dafe-dafen kayan daɗi. Ranar kasuwa ta zo, mutane suka taru, fada ta cika ta batse. Amma ita amaryar Sarki marainiya, kuma uwar yaron ta gaskiya, ba ta da abin da za ta dafa.

    Hasali ma tun ranar da aka kai ta ɗakin dawaki ba ta cin komai sai in an zuba wa doki dusa ta ɗiba, ta dama ta sha, ko ta yi tuwo da ita. Da aka ce har ita ma sai ta yi abinci, sai ta ɗebi dusar da aka kai wa dawaki kamar yadda ta saba, ta kama gafiya ta yanka, ta gyara ta da kyau, ta ɗauka ta kai fada.

    Da ta isa fada sai ta tarar duk sauran matan Sarki sun jeru, suka shiga yi mata kallon reni da nuna mata ƙyama. Can da ɗan Sarki ya zo a kan doki aka ce ya zaɓi abincin wadda zai ci daga cikin matan Sarki, sai kawai ya ƙarya linzami ya doshi inda mahaifiyarsa marainiya take. Da zuwa sai ya kama cin abincin dusar nan da ke gabanta.

    Da mutanen da suka yi cincirindo a fada suka ga haka, sai mamakin yadda al’amarin ya kasance ya kama su.Da Sarki ya ga alama lallai gaskiya ce ta yi halinta, sai yasa aka kama matar da ta sace yaron ta ce nata ne, aka fille mata kai. Ita kuwa mahaifiyar yaron ta gaskiya sai Sarki ya ba ta haƙuri, ya nemi ta gafarta masa.

    Ba a daɗe da yin wannan abu ba, Sarki ya kamu da rashin lafiya, wadda ta zama ta ajalinsa. Bayan an gama zaman makokin rasuwar Sarki, sai aka naɗa shi ɗan marainiya a matsayin sabon Sarki. A cikin ikon Allah yaro ya hau karagar mulki. Ya ci gaba da tafiyar da harkar mulki kuma ’yar tsohuwar nan da uwarsa zumuncin da yake tsakaninsu ya ƙara ƙarfi. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Alheri danko ne ba ya faɗuwa ƙasa banza.
    • In Allah ya rufa maka asiri, ba mai tonawa.
    • Karya fure take ba ta ’ya’ya.

    Wannan tatsunya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Biyu)

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Biyu)

    Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Biyu)

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana ’ya’yan Kura sun je yawo gidan Kurege sai suka tarar an yi farfesun Biri. Sai aka ba su suka ci. Da babban cikinsu ya ji daɗin farfesu sai ya ɗebi romon ya shafa a kan gashin kansa ya tafi gida. Da suka koma gida, sai ya je wurin babansa Kure ya ce: “Baba ka dafa kaina mana. ”Da uban ya ji haka sai ya dube shi ya ce: “Ka taɓa jin an cewa uba ya dafa kan dansa ne?

    ”Sai ɗan ya nace shi dai uban ya dafa kansa. Sai ya dafa kan, ya ji danshin romo, ya sa harshe ya lashe. Da ya ji zaƙin romo, a nan take ya tambaye su a inda suka sami wannan abu mai daɗi. Suka amsa masa da cewa a gidan abokinsa Kurege aka ba su. Sai Kure ya sa takalminsa ya tafi gidan Kurege ƙwalama. Da ya isa gidan Kurege sai ya tarar saura kaɗan a tukunya.

    Kurege ya zuba masa ya ci. Da ya ji daɗi sai ya ce da Kurege: “Ina kake samo wannan nama mai daɗi haka?” Sai Kurege ya amsa masa da cewa: “Muna wasa ne a ruwa kullum tare da birrai, sai in daura tarko a ƙafata. Idan mun shiga mun fara kurme a ruwa sai in kama ƙarami a cikinsu, in danne a ruwa har sai ya sha ruwa sosai ya mutu. In sun tafi sun bar shi, sai in ɗauka in yanka mu yi farfesu a gidana.

    ”Da Kure sarkin kwaɗayi ya ji haka sai ya ce: “To in gari ya waye gobe zan bi ka.” Sai Kurege ya amince. Da Kure ya tafi gidansa sai ya kasa barci, ya ƙagara gari ya waye. Can dai da ya ga kamar gari ya ƙi wayewa, sai ya hura wuta ta haske ko ina. Daga nan ya je ya faɗa wa Kurege wai gari ya waye, sai Kurege ya ce: “Haba Kure, ka hura wuta a kan dakinka ka ce gari ya waye?

    Ai gara ka koma gida sai gari ya waye.” Bayan ya koma gida ya ɗan jima gari bai waye ba, sai ya kama zakara ya rinƙa matsa shi har ya rinƙa yin cara. Da Kurege ya fito sai ya ce: “Haba Kure yaya kake damun kanka haka ne? Na gaya maka sai gari ya waye.” Haka dai Kure ya haƙura ala tilas har sai da gari ya waye. Da sassafe ya shirya ya nufi ƙofar gidan Kurege.

    Suka kama hanyar rafi har suka isa, suka tarar da birrai a bakin rafi. Sai Kure da Kurege suka yanke shawarar su shiga cikin ruwa su yi wasan kurme. Da suka shiga tare da birrai sai Kurege ya faki ƙarami daga cikinsu ya danne a ruwa. Shi kuma Kure maimakon ya faki ɗan ƙarami, sai ya nufi kan babba, ya sa masa igiya ya danne shi. Da ya ji Kure zai halaka shi, sai ya yi ƙara, har sauran suka ji, suka watse da gudu.

    Kure da Kurege dai kowa ya kaso Biri daya, amma sai Kuregeya ce: “Kai kuma Kure da muka yi da kai za ka kama karami donkada su gane, sai ka kama babban cikinsu?” Sai Kure ya dubi Kurege ya ce masa ai ƙarami ba zai ƙosar da shi ba, shi ya sa ya kama babba wanda idan ya yi farfesu da shi zai sha ya ƙoshi ya more.

    Washe-gari da suka koma tun safe har yamma suna jira a bakin rafi babu Birin da ya fito bakin rafi. Sai Kurege ya dubi Kure yace da shi: “Kai ka yi mana wannan ɗanyen aiki.” Rannan dai haka suka koma gida, ba su sami nama ba. Sai Kurege ya gaya wa Kure gobe da safe za su je unguwar birrai su gaishe su domin rashin da suka yi na babbansu.

    Da ma birrai sun aika wa Kurege da Kure za su yi taro domin ba su sani ba cewa ko Kure da abokinsa Kurege ne suka kashe musu’yan’uwa. Da gari ya waye suka shirya, sai Kurege ya ce zai hau doki, shi kuma Kure ya hau ɓera. Sai Kure ya ƙi, ya ce tun da shi ne babba shi zai hau doki shi kuma Kurege ya hau ɓeran.

    Haka aka yi; suka kama hanya, kafin su isa sai Kurege yace in sun je shi zai ɗaure abin hawansa a jikin bishiya, sai Kure yace shi ne zai ɗaure a jikin bishiya, domin shi ne babba. Sai Kurege yace to shi zai ɗaure nasa a jikin ciyawa. Da suka isa garin birrai aka yi musu maraba, aka ba su masauki, shi Kure ya ɗaure abin hawansa a gindin bishiya, shi kuma Kuregeya ɗaure nasa abin hawan a jikin ciyawa.

    Suna zaune a masauki aka ce za a kawo musu giya don liyafar baƙunta. Kafin a kawo sai Kurege ya ce ya kamata su yi waƙa. Suka fara waƙa. Kurege yana rerawa yana cewa: “Ni da ƙananan nake wasa, Da ƙananan nake abota.” Shi kuma Kure yana waƙa yana cewa: “Ni da babban nake wasa, Babba na kama, A wasan ruwa mai daɗi” Sai manyan birrai suka ji abin da Kure yake faɗa, sai suka kawo musu giya a ƙwarya.

    Kure yana ta sha, Kurege kuma ya yi kamar tare suke sha amma in ya zuba a ƙoƙo sai ya kwara a jikin shinge, shi kuma Kure ya yi ta shan giya har ya yi tilis. Su kuma manyan birrai suna ta shiri don su rama abinda Kure da Kurege suka yi musu. Nan take birrai suka ƙwala ihu, suka ce a kawo sanduna za su ɗauki fansa. Suka ɗebo sanduna suka nufi kan Kurege da Kure.

    Shi kuma Kure ya riga ya yi tilis da giya ta yadda ba ya jin abinda ake faɗa. Sai ya tambayi Kurege ko me suke cewa a waje? Sai Kurege ya gaya masa cewa an ce a kawo musu farfesun ƙashi da nama. Da Kure ya ji haka sai ya gyara zama, yana dariya da murna wai za a kawo musu nama da ƙashi. A daidai lokacin da birrai suka shigo da sanduna za a fara ma Kurege da Kure, sai Kurege ya kutsa ta jikin shinge, inda yake kwarar da giya, ya gudu.

    Kure kuwa ba zai iya gudu ba, saboda haka suka yi ta jibgar sa. Bayan Kurege ya fita ta baya, kafin su biyo shi har ya hau kan ɓera. Yana taɓa shi sai ya fara gudu. Shi kuma Kure kafin ya fito ya kwance dokinsa daga jikin bishiya, ya rigaya ya sha sanduna har ya faɗi ya suma. Suka ɗauke shi, suka ɗora shi a kan dokinsa, suka kora shi gida. Ya isa gida a galabaice, ya yi ta jinya da kyar ya warke. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Kwaɗayi mabuɗin wahala.
    • Son zuciya, ɓacin zuciya

    Wannan tatsunya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Daya)

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Daya)

    Tatsuniyar Kurege Da Kura (Na Daya)

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wata rana Kurege da Kura suna yawo, sai suka tsinci ƙyallen fatari. Sai Kurege ya ce, bari ya je ya ɗinka musu riguna da shi. Ya je ya ɗinko riguna biyu, amma girmansu ɗaya. Ya bai wa Kura ɗaya. Da Kura ta saka sai rigar ta matse ta, ta shaƙe mata wuya saboda ta yi mata kaɗan.

    Sai Kurege ya ce da Kura tun da rigar nan ta yi mata kaɗan, sai ta bar masa ita. Da Kura ta ji haka sai ta ce masa: “Daman ka cuce ni ne tun da ka ɗinka rigata daidai da taka, sai ka ɗauka.” Kurege ya haɗa duka biyun, suka shiga jeji don su farauto abinda za su ci. Da suka kamo namun daji da yawa sai suka dawo gindin wata bishiya, suna hutawa.

    Kurege yana so ya cinye namanshi kaɗai, amma ya rasa yadda zai yi. Can sai ya hango wasu ‘yanmata a bakin rafi, sai ya dubi Kura ya ce: “Ga ‘yan mata can, mu je mu yi musu magana. “Sai Kura ta yarda, suka je suka tarar da ‘yan matan suna hira. Suka zauna suna sauraron hirar.

    Da Kurege ya ga hira ta fara yin daɗi sai ya ce da Kura su je su dafa naman nasu. Sai Kura tace ita tana nan a wurin hira, ba za ta je ba. Shi kuwa Kurege sai ya je domin ya dafa musu naman. Ashe ya sami abin da yake so, wato sai ya zaɓi nama mai kyau ya zuba a jakarsa, ya ɓoye. Sai ya samo naman mushe ya dafa, ya ajiye wa Kura. Bayan ta dawo sai ya miƙa mata nama.

    Kura ta hau ci ba ta san mushe ya dafa mata ba. Ta ci nama, irin cin haɗama, amma ta ɗan rage ta ɓoye a jakarta. Kura ba ta da masaniyar cewa Kurege ya ɓoye nama mai kyau, ya ba ta mushe. Saboda wayo irin na Kurege, sai ya dubi Kura ya ce: “Kura ki rage mini naman mana. Saboda haɗama irin ta Kura ita ma sai ta harari Kurege tace:
    Ni ba zan ba ka ba tun da kai ne ka dafa, na san sai da ka zaɓi inda ya fi ko ina daɗi ka ci ka ƙoshi, ba zan ƙara maka ba.

    Da rana ta faɗi, kuma dare ya yi sai suka samu wata bukka suka kwanta, can cikin dare sai zawayi ya kama Kura. Ta nemi Kurege ya raka ta, sai da rana ta faɗi, kuma dare ya yi sai suka sami wata bukka suka kwanta ki, ya ce in zawayin yana damunta, to ta fita waje. Ya ƙara da cewa: “Idan ma abin ya dame ki ai sai ki yi shi a kwance ba sai kin tashi ba.

    Amma idan na ji ihu to babu lafiya, idan kuma abin ya yi tsanani, idan kuma kin yi shiru to lafiya kenan. Sai Kura ta fita waje ta yi kwanciyarta. Jim kaɗan sai kunama ta harbe ta. Kura da raki sai ta ƙwala ƙara, haka dai ta kwana tana zawo. Wayewar gari ke da wuya, sai ta je ta faɗa wa Kurege cewa jiya da daddare kunama ta harbe ta.

    Sai Kurege ya ce: “Ai dama mun yi da ke idan na ji shiru lafiya ta samu, idan kuma na Ji ihu to ta yi tsanani sai in fita in taimaka miki. “Bayan Kura ta ji bayanin Kurege, sai ta ce: “To shi ke nan.” Da suka gama maganganunsu, sai Kurege ya rasa yadda zai yi ya ɗauki naman da ya ɓoye ya kai gida, domin ya sani idan Kura ta gani za ta ƙwace. Sai ya yi dabara ya ba Kura shawara ta je ta sha ruwa, ta wanke jikinta kafin su tafi gida.

    Ba tare da zaton wani abu ba, sai ta kama hanyar rafi. Da Kurege ya ga ta tafi rafi, sai ya ɗauko namansa a inda ya ɓoye, ya saka shi a jakar Kura, shi ma ya shiga cikin jakar. Da ta dawo daga wanka, sai ta ɗauki jakarta ta rataya. Ba ta san Kurege yana cikin jakar ba, sai ta kama hanya. Daɗin waƙa ya sa ta kama hanyar gida ta fara tafiya, ta manta da Kurege.

    Tana cikin tafiya sai ta fara yi wa Jakarta waƙa tana cewa. “Sai ni Kura durungu, Na yi farauta, Na cika jakata da nama, Nama sai mun ture, Ga shi a cikin jakata.” Haka ta rinƙa yi wa jakar waƙa. Sai da ta isa gida ta tuna ta bar cikin jakar Kura, riƙe da namansa ya gudu zuwa gidansa. Shi ya sa duk wanda ya je daji zai ga Kura tana ta yawon nema nai. Shi kuma da za ku je gidansa, za ku tarar da gidan cike yake da nama mai kyau, wanda yake ci ya more. Da babu Gizo da na yi muku ƙarya. Ƙurunƙus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Karamin mai hankali ya fi babba mai wauta.
    • Wauta mai janyo wuya.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Kishiyoyi Biyu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Kishiyoyi Biyu

    Tatsuniyar Kishiyoyi Biyu

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    An yi wasu kishiyoyi biyu masu zaman lafiya a tsakaninsu a wani gari. Ba su taɓa ɓata wa juna rai ba. Suna nan, sai wata rana ɗaya daga cikinsu ta kwanta jinya. To da ma kowaccensu tana da ’ya mace, ’ya’yan kuma sun yi kama da juna ainun, yadda ba kowa ne zai iya bambance su ba, tamkar dai ’yan biyu.

    Da mai jinyar nan ta ga alamun ciwon nata ba na tashi ba ne, sai ta kira kishiyarta, ta ba ta amanar ’yarta. Kishiyar ta karɓa, kuma ta yi alƙawari za ta kula da duka yaran biyu kamar ita ta haife su. Da mai jinyar ta rasu, sai kishiyar ta ci gaba da kula da yaran har suka girma, suka zama ’yan mata.

    To amma saboda tsabar so da adalci da take yi wa ’yar kishiyarta, sai ya zamanto ba ta iya gane ’yarta daga cikinsu, domin kamanninsu ɗaya. Sai wata tsohuwa ta ziyarce su da ta lura da yanayin matar ta hanyar adalcin da take nunawa a tsakanin yaran, sai ta rinƙa yi mata faɗa a kan yaya za ta riƙi ɗan wani kamar nata.

    Sannu a hankali, har dai ta fara karkata ga zancen tsohuwa, to amma sai tace ba za ta iya gane ɗiyarta daga cikin yaran ba. Sai tsohuwar nanta ba ta shawara da cewa in sun je ɗaukar ruwa kafin su dawo, ta dafa dambu, ta ajiye a bakin randa, in sun dawo suna jin yunwa za su fara ci.

    To sai ta bari sai sun fara cin dambun sai ta daka musu tsawa, tana cewa: “Kun san yadda yake ne, ba ku tambaya kafin ku fara ci? ”Tsohuwa ta ce mata ta lura da kyau, domin wadda ta fara cire hannunta daga akushin dambun to ita ce ’yar kishiyarta. Wadda taƙi cire hannunta, kuma ta ce suna jin yunwa ne, to ita ce ’yar cikinta.

    Sai kuwa matar nan ta yi hakan. Bayan yaran sun dawo daga ɗaukar ruwa sai suka hangi dambu a bakin randa, suka nufi bakin randa da gudu, suka fara cin dambu. Nan take sai ta daka musu tsawa, tana cewa: “Kun san yadda dambun yake ne, ba ku tambaya ba kafin ku fara ci? ”Nan da nan suka razana, sai ’yar kishiyarta ta cire hannunta daga cikin akushin dambu, ita kuma ’yarta ta cikinta, ta dubi uwarta ce: “Haba mama, muna jin yunwa ne fa.

    ”Daga nan sai ta kama ’yarta ta kai daki, kuma ta kama’yar kishiyarta ta yi mata tsaga a fuska. Daga nan fa sai ta fara gana wa ’yar kishiyar nan tata azaba iriiri, har ya kai ga in za su ci abinci, sai ta ƙi zuba wa ’yar kishiyarta nata abincin a akushi, sai ta zuba mata a ƙasa. Amma kuma maimakon ’yar kishiyar nan ta rame ko ta damu, sai ƙiba kurum take yi.

    Daga nan sai ta daina ba ta abincin sam-sam, har ma dai takore ta daga gidan, wai ta je can kabarin uwarta ta karbi abinci. Da yarinya ta ji haka, sai ta yi ta kuka, ta kama hanya ta tafi bakin kabarin uwarta tana kuka. Ana haka, ana haka, wata rana da ta je kabarin uwar tana kuka, sai uwar ta fito ta rarrashe ta, ta ba ta abinci, ta ci ta ƙoshi.

    Haka dai, kullum sai ta je bakin kabarin uwarta, ta fito ta ba ta abinci. Nan da nan ta sake yin ƙiba, ta yi kuma kyau, ta goge, abin gwanin ban sha’awa. Ita kuwa mai uwa a murhun, sai ramewa take yi. Uwarta ta rasa abin da za ta yi. Wata rana sai wasu samari suka je tambayar uwar cewa ɗaya daga cikinsu yana son ya shiga neman auren marainiyar.

    Maimakon ta yi abin da samarin suka nema, sai ta ce sai dai su auri ’yarta. Su kuma suka ce waccan mai tsaga a fuska suke so. Amma sai ta hana su, ta mare su, ta gaya musu kada su sake zuwa gidan neman aure in ba ’yarta suke so ba. Da marainiyar nan ta ga haka, sai ta gudu, ta shiga uwa duniya. Tana cikin tafiya a dokar daji, sai ta ga shinkafa da nama.

    Sai shinkafa ta yi wa budurwar nan magana, ta ce idan tana jin yunwa ta zauna ta ci. Amma sai yarinya ta ce ta ƙoshi, kuma ta ci gaba da tafiya. Can kuma sai ta ga naman kaza, sai naman ya yi mata tayi, amma sai ta ƙi ci, ta ci gaba da tafiya. Haka ta rinƙa haɗuwa da kayan daɗi iri-iri, amma ta ƙi amsa tayinsu, ta haƙura da yunwar da take ji, ga baƙin cikin da ke damunta.

    Tana cikin tafiya sai ta ga hadari ya haɗu, ita kuma babu inda za ta fake. Ta duba nan, ta duba can, sai ta hangi wata ’yar bukka, nan take ta nufe ta a guje, ta buɗe ta shiga. Bayan ta zauna sai ta ga wani babban kumurci a gefenta. Sai macijin nan ya sulalo ya nufo wurinta, amma ba ta ji tsoro ba sai kallon sa take yi.

    Da ya ji bayaninta, sai ya tambaye ta tana iya gane garin, sai tace ta sani. Ba tare da ɓata wani lokaci ba, sai ya ce ta shirya su je su kai musu ziyara. Jin haka ya sa ta shiga murna da shirye-shiryen tafiya. Ta tanadi kayan sutura da sauran kayan masarufi. Da ranar da suka sa ta zo, sai Sarki ya sa aka haɗa su da dawakai da ’yan rakiya masu yawa, sai ka ce ita ce matar Sarki, suka kama hanya.

    Da suka isa garin, sai ita da mijinta da ’yan rakiyarsu suka nufi gidan iyayenta, suka shiga gidan, mutanen gari kuma suna ta mamakin yadda wannan yarinyar da aka ba wuya a baya ta koma. Da ’yar’uwarta ta gan ta sai ta rungume ta, amma da kishiyar uwarta ta fito sai ta ce ba ita ce ta ɓata ba, to amma saboda tsagun fuska da ta yi mata, sai ta gane ta.

    Nan take suka rungume juna cikin murna. Bayan amarya ta huta sai suka fara hira, ta kwashe labari tun daga barinta gida har zuwa lokacin da ta auri ɗan Sarki. Data gama ganin dangi, sai ita da mijinta suka yi musu sallama, suka kama hanya tare da ’yan rakiyarsu, sai garin mijin.

    Bayan tafiyarta sai kishiyar uwarta ta ce lallai ita ma ’yarta ta je ta auro ɗan Sarki. A kan dole yarinya ta amsa. Da ta kama hanyar tafiyar neman ɗan Sarkin da za ta aura, kamar dai yadda ’yar’uwarta ta yi, tana shiga daji sai ta ga shinkafa da nama. Tun kafin ma a yi mata magana sai ta tsuguna ta fara ci. Sai shinkafa ta ce da ita: “‘Yan mata zo ki ci shinkafa.

    ”Da budurwa ta ji haka sai ta dubi shinkafa ta mayar mata da jawabi: “Da ma ko ba ki yi magana ba, ai ina jin yunwa.” Sai ta ci gaba da cin shinkafa har ta ƙoshi. Daga nan sai ta kama hanyar ta fara tafiya. Ba ta yi nisa ba kuma sai ta haɗu da naman kaza. Nan ma ta zauna ta ci har ta ɗebi cinya da fukafukai da ƙirjin kaza a hannunta, ta yi guzuri. Ta sa kai ta fara ci gaba da tafiya tana lasar baki.

    Ba jimawa sai hadari ya taso, ta rasa yadda za ta yi. Gashi ba gari kusa a baya, kuma ba ta san inda ta dosa ba. Can sai ta hangi wata ’yar bukka, ta ruga a guje ta shiga, sai ta ga wani shirgegen maciji. Tana ganin macijin nan sai ta ƙwala ihu, tana neman hanyar gudu. Sai ɗan yaro ya ɓullo ɗauke da abinci, ya ce ta ba macijin abinci.

    Sai ta ce: “Tabɗi! Ta yaya ina jin yunwa in ga abinci in ba wani maciji?” Sai ta kama cin abinci, ta yi watsi da maciji. Jim kaɗan sai macijin ya fara rikiɗa. Tana ganin haka sai ta faɗi sumammiya, watau ba ta ga ɗan Sarki ba, balle ta san kamanninsa. Bayan ta farka sai ta gan ta a gidan wasu masu sarauta, amma talakawane da wani ɗan yaro ya zo ya gaya mata cewa za a zo a yi mata kitso, amma idan makitsiyar ta ba ta abin ƙwalama kada ta ci.

    Tana cikin haka da macijin nan, sai wani ƙaramin yaro yaɓbullo ɗauke da kayan abinci, ya gaya mata ta ba macijin nan abinci. Nan da nan ta ba shi ruwa ya sha, kuma ta ba shi abinci ya ci. Da ya ƙoshi sai ya rufe baki. Bayan ta kammala ciyar da macijin nan da shayar da shi ruwa, sai yaron ya tambaye ta ko ita ma za ta ci abincin ne.

    Sai tace ta ƙoshi. Sai macijin nan ya sake yin ƙoƙarin razana ta, amma sai tace ita komai ya ga dama ya yi mata, domin ba ta da wurin zuwa, kuma ta riga ta sadaukar da rayuwarta. Da jin haka, sai macijin ya shiga rikiɗa, yana zama namun daji daban-daban, amma duk da haka ba ta razana ba. Maimakon haka ma, sai ta gyara zama tana kallon ikon Allah, har dai macijn nan ya rikiɗa, ya koma yaro matashi kyakkyawa.

    Yarinyar ba ta sani ba, ashe macijin nan ɗan Sarki ne yake neman aure, amma sai ya bi wannan hanya don ya sami mace mai hankali, mai amana. Nan da nan ya sa aka ɗauke ta a kan doki, akakai ta gidan Sarki, aka ɗaura mata aure da shi, aka sha biki. Bayan an gama biki sai aka tura yaro ya gaya wa amarya za a zo a yi mata kitso, to amma matar da za ta yi mata kitson mayya ce, kuma za ta zo da kayan ciye-ciye a hannunta, idan ta ba ta kada ta ci.

    Yaron ya ce mata ta riƙe duk abin da za ta ba ta a hannunta, ko sau nawa ta ba ta kuwa kada ta sa a baki. Yaro ya ƙara bayyana mata cewa, bayan wannan mayya ta gama kitso za tayar da matsefata a gidan, amma kada ta gaya mata, ta kyale ta ta tafi. Bayan ta tafi kuma za ta dawo ta tambayi matsefatar, to sai ta miƙa mata haɗe da kayan ciye-ciyen da ta ba ta.

    Amaryar ta amince. Da makitsiya ta zo gidan, sai aka ce ta je ta yi wa amarya kitso. Da ta fara kitso sai ta miƙa wa amarya kayan ƙwalama, wai ta ɗan lashe bakinta da shi, sai amarya ta karɓa kamar za ta ci, amma sai ta riƙe a hannunta. Jim kaɗan kuma sai
    ta sake miƙa mata wani abincin, sai amarya ta karɓa ta haɗa su a hannunta. Haka dai har sai da suka gama kitso, makitsiyar ta tashi za ta tafi, sai ta yar da matsefin da ke hannunta a tsakar ɗakin amarya, amma amarya ta ƙi gaya mata.

    Makitsiya ta kaɗa kai ta yi tafiyarta. Bayan wasu ’yan sa’o’i da tafiyarta sai ta dawo, wai ta manta matsefinta a gidan, sai amaryata ɗauko mata, ta haɗa mata da kyautar da ta ba ta ta kayanƙkwalama a lokacin da take yi mata kitso. Da mayyar nan ta ga an dawo mata da tarkacenta, sai kawai ta fara zage-zage, ta kama hanya a fusace ta fita abinta. Amarya da mijinta ɗan Sarki suka ci gaba da zamansu cikin jin daɗi.

    Wata rana sai amarya ta kwanta a ɗaki ita kaɗai tana ta rusar kuka. Da mijinta ya shigo sai ya tambaye ta abin da ya faru, sai tace tana tunanin gidansu ne da mahaifinta da kuma kishiyar mahaifiyarta wadda ta riƙe ta. Ta kwashe labarinta gaba ɗaya ta gaya masa. Tana jin wannan ƙa’ida sai ta ce: “Tabdi! Ai ni in har na ga abin daɗi ba zan ƙyale shi ba sai na ci.

    …..”Da makitsiya ta zo ta fara kitso sai ta miƙa wa yarinyar abin ƙwalama, sai ta karɓa ta kai baki ta cinye. Da ta sake miƙa mata na biyu sai ta sake lanƙwamewa. Bayan sun gama kitso sai makitsiyarta yar da matsefinta, sai ta ce da ita: “Ai kin manta matsefinki.” Sai ta juya ta karɓa, ta tafi tana dariya. Bayan wasu ’yan kwanaki sai yarinyar nan, abin tsautsayi ta kamu da cuta, wadda ta zama ajalinta aka binne ta, ba tare da ta auri ɗan sarkin ba. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Munafunci dodo ne, yakan ci mai shi.
    • Mai rabon ganin baɗi ko ana ha maza ha mata sai ya gani.
    • Hassada ga mai rabo taki ce.
    • Mahakurci mawadaci.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Karanta  Tatsuniyar Ƙawancen Kyanwa Da Bera

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Na-Goma

    Tatsuniyar Na-Goma

    ‎Ga ta nan ga ta nan ku.

    ‎Wata rana, an yi wani mutum wanda ya ke da ‘ya’ya goma. Shi kuwa maharbi ne. Kullum ya je daji yawon harbi sai ya kamo tsuntsu guda ɗaya. Shi ke nan kullum ya kamo tsuntsun sai ɗansa Na-Goma ya gasa shi ya cinye shi kaɗai. Kullum haka, kullum haka.

    ‎Ran nan sai ubansu ya ce a tafi kogin rantsuwa a yi rantsuwa a ga wanda ya ke cinye tsuntsun da ya ke kamowa kullum. ‎Shi ke nan. Sai suka ce, ‘To.’ Suka bi shi zuwa kogi. Da suka je kogin, sai na farkon, watau Na-Ɗaya, ya shiga ya ce:

    Ni Na-Ɗaya, na ɗayan Babaye.

    ‎In ni na ci tsuntsun Babaye,

    ‎Ruwa tafi da ni kar ka dawo da ni.

    ‎Sai ruwa ya ƙi tafiya da shi. Sai ya fito. Na-Biyu kuma ya shiga ya ce:

    Ni Na-Biyu, na biyun babaye.

    ‎In ni na ci tsuntsun babaye,

    ‎Ruwa tafi da ni kar ka dawo da ni.”

    ‎Sai ruwa ya ki tafiya da shi shi ma, ya fito. Duk sauran suka yi ba su nutse ba har aka zo kan Na-Goma wanda ya ce:

    Ni Na-Goma, na goman babaye.

    ‎In ni na ci tsuntsun babaye,

    ‎Ruwa tafi da ni kar ka dawo da ni.”

    ‎Shi ke nan. Sai kuwa ruwa ya tafi da Na-Goma.

    ‎Sai ‘yan uwansa suka ce, “To, baba, ka ga wanda ya ke cinye maka tsuntsu.” Uban kuma ya ce, “Na gani. Ku mu tafi gida. ‎Da suka je gida, suka shaida wa uwarsu wannan labari, sai ta fashe da kuka. Ta yi kukanta ta gaji ta share hawaye ta ce, ‘Ba kome. Allah ya ji kansa.’

    ‎Shi ke nan. Ruwa yana cikin tafiya da Na-Goma, sai ya zo gaɓar kogi. A nan ne fa ya ga wata dodonniya tana ta cin kwaɗi. Sai ta kama shi ta ce, ‘Kai yaro mutum ne, ko dodo irina?’ Sai yaro ya ce, ‘Ni mutum ne. ‘Sai ta ce, ‘Kai kuwa me ya kawo ka nan? ‎Sai ya ce, ‘Abin da ya sa na zo nan, shi ne, kullum kullum ubana ya kamo tsuntsu ya kawo gida, sai in ɗauka in gasa in cinye ni kaɗai, ba wanda ya sani.

    Shi ke nan, sai ran nan ya gaji ya ce mu je kogin rantsuwa tare da ‘yan uwana a gwada a ga wanda ya ke cinye tsuntsun da baba ya ke kamowa. Da muka je muka yi rantsuwar, shi ne kogin ya cinye ni ya kawo ni nan. ‘Sai ta ce, ‘To, yanzu ka ga ni dodonniya ce. In cinye ka ko in ƙyale ka?’

    ‎Sai ya ce, ‘Ni dai ina so ki yi mini arziƙi in zama ɗanki. ‘‎Shi ke nan, sai ta ce, ‘To, tashi mu tafi gida. Sai suka tafi gida. Da suka isa gidan, sai ta soma yi masa abubuwa yana sayarwa. Tana yi masa ƙosai yana talla. Kullum haka har yaro ya girma. Sai ta sai masa doki da kayan doki yana hawa yana tallan ƙosai a kai.

    In lokacin cin abinci ya yi, sai ta samo masa irin nasa na mutane. Ita kuma ta samo irin nasu na dodonni. ‎Shi ke nan. Kullum haka, kullum haka, sai rannan ‘yan’uwan Na-Goma suka gan shi yana tallan ƙosai a kan doki. Suka ce, ‘Wannan kamar Na-Goma,’ a zuciyar su. Shi ma kuma ya shaida su. Sai suka ce, ‘Kai mai ƙosai!’

    ‎Sai ya waigo. Suka ce, ‘Ko kai ne Na-Goma? ‎Sai ya ce, ‘I. Ni ne. ‘‎Sai suka rungume juna suna ta kuka. Shi ke nan, sai suka ce, ‘To, mu tafi gidan da ka ke. ‘Sai ya ce, ‘To, ai ni babata dodonniya ce. ‘‎Sai suka ce, ‘Mu tafi haka. Ba kome.’

    ‎Sai suka je suka yi sallama. Suka gaisa da dodonniya, suka ce ‘Mun zo ne mu tafi da ɗan’uwanmu Na-Goma.’

    ‎Sai ta ce, ‘Ni ba zan ba ku shi ba.’

    ‎Sai suka ce, ‘Ki yi haƙuri ki ba mu shi.’

    ‎Sai ta ce, ‘To, ku gaya min dalilin da ya sa ya zo ya same ni a nan.’

    ‎Sai suka gaya mata kamar yadda Na-Goma ya gaya mata, tun farkon haɗuwarsu a bakin kogi. Sai ta ce, ‘To na ji. Amma yanzu sai ku je ku kawo duk irin abin da za ku iya na dangin abincina. ‘Sai suka ce, ‘To.’ Suka tafi gida suka ce wa babansu, ‘Baba, yau dai mun ga Na-Goma yana tallan ƙosai a kan doki.’

    ‎Sai babansu ya ce, ‘Kai ku tafi can masu ƙarya, wanda ruwa ya cinye ina za ku gan shi? ‘Sai suka ce, ‘Ai gaskiya mu ke faɗa. Har ma wadda ta ke riƙonsa ta ce sai mun kai mata kayan abinci, sannan za ta ba mu shi. ‘‎Shi ke nan sai uban ya ce, ‘To a kai mata taikin gero ɗari da gomiya bakwai.

    Taikin dawa ɗari da gomiya bakwai. Taikin shinkafa ɗari da gomiya bakwai. Kai da duk dai irin abincin da mutane su ke ci a yi mata ɗari da gomiya bakwai-bakwai.’‎Da aka kai mata, sai ta ce:

    Ba cina ba, Na-Goma Ba cina ba.

    Je ka ka dawo, Na-Goma Je ka ka dawo.

    ‎Shi ke nan sai suka koma suka ce, ‘Baba, ta ƙi karɓa. Ta ce ba ta cin irin wannan abincin. ‘Sai ya sa aka yi mata taikin ƙuda ɗari da gomiya bakwai. Taikin tsutsa ɗari da gomiya bakwai. ‎Taikin kyankyaso ɗari da gomiya bakwai. Haka kuma taikin su gwano, da na tururuwa, da kiyashi, da jaba, da gafiya, da ɓera, da ƙadangare ɗari da gomiya bakwai-bakwai.

    Sai aka kai mata su. Da ta ga wannan gara zango-zango, tsibi-tsibi na irin abincinta, sai ta ce:

    Ga cinan nan, Na-Goma,

    ‎Ga cinan nan.

    ‎Ga shanu nan, Na-Goma,

    ‎Ga shanu nan.

    ‎Madalladai, Na-Goma,

    ‎Madalladai.

    ‎Dau wandonka, Na-Goma,

    ‎Dau wandonka.

    ‎Sa rigarka, Na-Goma,

    ‎Sa rigarka.

    ‎Sa hularka, Na-Goma,

    ‎Sa hularka.

    ‎Hau dokinka, Na-Goma,

    ‎Hau dokinka.

    ‎Sai wata rana, Na-Goma.

    ‎Sai wata rana.

    ‎Sai wata rana, Na-Goma,

    ‎Sai ka dawo.

    ‎Shi ke nan, sai suka rabu, dodanniya tana kuka, Na-Goma yana kuka. Aka kai Na-Goma gida, ya yi zamansa. Bai sake cinye wa babansa tsuntsu ba. ‎Shi ke nan.

    ‎Kurunƙus kan ɗan ɓera. Ba don Gizo ba da nai ƙarya. Ba don ƙarya ƙarya ce ba, wa zai ci tuntuɓe da tuwon shinkafa, ya dauje baki da tsokar nama, ya faɗa rijiyar zuma, a ciro shi da nakiya da alkaki?

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafi mai taken TATSUNIYOYI DA WASANNI wadda Ibrahim Yaro Yahaya ya wallafa

    Danna nan don karanta Tatsuniya Mai Taken Marainiya

  • Tatsuniya Mai Taken Wani Sarki Da Matansa

    Tatsuniya Mai Taken Wani Sarki Da Matansa

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Wani Sarki ne mai mata uku, amma Allah bai taɓa ba shi haihuwa ba. Ana nan, ana nan wata rana sai ya nemi shawarar fadawansa a kan abin da ya kamata ya yi saboda wannan rashin haihuwa. Sai suka ce ya kamata ya ƙara aure. Shi ko ya ɗauki shawararsu, ya sa aka nema masa budurwa kyakkyawa ya aure ta.

    Bayan wasu ‘yan watanni sai Allah ya ba ta ciki, labari kuma ya gama ko ina, matar Sarki tana da ciki. Su kuwa kishiyoyinta sai suka shiga baƙin ciki, don sun daɗe a gidan Sarki ba tare da ko ɗaya daga cikinsu ta sami ko da ɓatan wata ba. Daga nan sai suka shiga neman hanyar da za su bi su zubar da cikin, amma abu ya gagara, har lokacin haihuwa ya zo.

    Lokacin da suka tabbatar ta kusa haihuwa, sai suka je wurin Sarki suka nemi izini su je shan iska da saran itace a jeji tare da bayinsu. Ba tare da wani mugun zato ba, sai Sarki ya ba su izini, amma da sharaɗi, ba za su je da amaryarsa mai juna biyu ba. Sai suka ce ai za su kula da ita, kuma babu abin da zai same ta.

    Da suka nace, sai Sarki ya bar su suka tafi jeji da ita. A dajin nan naƙuda ta kamata, suka kai ta gindin bishiya, suka kwantar da ita, ta haihu. Da suka ga ta haifi ‘ya kyakkyawa, kuma ba ta cikin hayyacinta, sai suka ɗauki jaririyar suka jefa a kan bishiya. Can da rana ta yi sanyi, sai su da bayinsu suka kama hanyar gida, tare da mai jego.

    Lokacin da suka isa gida, sai matan Sarki suka je turakarsa, suka gaya masa wai matarsa ta haifi wani ɗan itace ne, ba mutum ta haifa ba. Da jin wannan bayani sai ya fusata, domin ya ɗauka gaskiya suka gaya masa, ya sa aka kai amaryarsa wani gida ita kaɗai inda ba kowa, sai abin tsoratarwa, aka bar ta a can.

    Bayan wasu ‘yan watanni sai bayin Sarki suka je daji yankowa dawakin Sarki ciyawa. Suna cikin yankan ciyawa sai wata ‘yar tsuntsuwa ta zo ta sauka a kan bishiya, ta tarar da ‘yar yarinya. Sai ta fara waƙa tana cewa: “Ɗan tsuntsu kar ka faɗa kan ‘yar Sarki, Wadda kishiyoyi suka ce, Wai ɗan itace uwarta ta haifa, Suka jefa ta kan bishiya, Ba ɗan itace ba ne, ‘Yar Sarki ce.

    “Ta rinƙa maimaita wannan waƙa, har bayin Sarki suka ji wakar ‘yar yarinya ta kan bishiya. Wannan ya sa suka fita da gudu, suka koma gari. Washe-gari ma da suka koma yankan ciyawa sai suka ji waƙar. Da suka kasa kunnuwansu da kyau, suka kuma saurari waƙar ‘yar yarinya, sai suka koma gida suka gayyaci mutanen gari masu yawa, domin su ma su je jejin su ji.

    Mutanen gari suka saurari waƙar da tsuntsuwa ke yi wa yarinya. Daga nan fa suka koma gari, suka je suka sanar da Sarki abin da suka ji. Sarki ya tashi da kansa ya nufi jeji inda yarinyar take, yasa aka hau bishiya a ga ko me yake yin wannan waƙa. Da aka hau bishiya sai ga yarinya kyakkyawa mai kama da Sarki, sai ka ce kakinta ya yi.

    Bayan an sauko da ita Sarki ya gan ta, nan da nan ya rungumi ‘yarsa, yana ta salati irin na godiya ga Allah, yana sumbatar yarinyar nan, don ƙauna irin ta ‘ya da mahaifi. Bayan wannan nuna murna ta Sarki da amsar barka da arziki daga jama’arsa da ke wurin, sai ya sa aka kawo masa doki ya hau, aka miƙa masa ɗiyarsa, suka hau doki tare, shi da ɗimbin jama’a suka kama hanyar gari.

    Da suka isa gida sai ya aika aka kawo masa uwar yarinyar da aka kai can wani gida da ke bayan gari, yana cike da nadama, amma kuma a cikin muryar bayyana farin ciki, ya ba amaryar haƙuri, ya nemi ta yafe masa horon da ya yi mata ba tare da laifin ta ba, a sakamakon makircin kishiyoyinta.

    Bayan fada ta cika ta batse da mutanen gari, sai aka bayyana musu miyagun halaye da makircin sauran matan Sarki, da yadda suka sa Sarki ya hori matarsa ba tare da ta yi masa laifi ba, da kuma yadda suka jefa da ‘yar Sarki a daji. Nan take Sarki ya umarci
    Hauni da ya fille musu kawuna, aka je aka zuba su a rami, aka binne. Sarki kuma ya ci gaba da sabuwar rayuwa shi da amaryarsa da’yarsa. Da ba domin Gizo ba da na shara muku ƙarya. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Mugun nufi ba ya kashe ɗan kurciya.
    • Ƙaiƙayi ya koma kan masheƙiya.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Ƙawancen Kyanwa Da Bera

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tatsuniyar Ƙawancen Kyanwa Da Bera

    Tatsuniyar Ƙawancen Kyanwa Da Bera

    Ga ta nan, ga ta nanku.

    Kyanwa da Bera dai ne suka yi ƙawance, suka kuma yi shawarar cewa ya kamata su tara kayan abinci da za su rinƙa ci idan lokacin hunturu ya zo. Suka kuwa zartar da wannan shawarar.

    Suna nan, sai rannan Ɓera ya ce da Kyanwa zai je bikin ƙanwarsa. Da ya fita sai ya nufi rumbun abincin da suka tara, ya ci har sai da ya ƙoshi. Da ya dawo gida sai Kyanwa ta yi masa maraba, ta tambaye shi, “Me aka samu ne?” Ɓera ya dubi Kyanwa ya ce: “Abin da aka samu shi ne, wuyar aiki ba a fara ba!” Aka yi murna aka watse.

    Bayan ’yan makwanni kuma Ɓera ya je wani sunan, ya bi ta rumbu ya ci har ya ƙoshi. Da dawowa gida sai Kyanwa ta tambaye shi: “Yau kuma wa aka samu?” Sai Bera ya dubi Kyanwa yana murmushi ya ce: “Yau kuma an sami kwanci-tashi ba ta bar komai ba.” Duk abin da Ɓera ke yi dai Kyanwa ba ta sani ba.

    Da Ɓera ya je gidan suna na uku ya dawo, sai Kyanwa ta nemi sanin abin da aka samu. Sai ya harare ta ya ce: “An sami ta-faru-ta-ƙare.” A tafiyar suna na huɗu Ɓera ya dawo da fuska a murtuke. Ita ko Kyanwa ta tambayi sunan jariri da goron suna. Maimakon Ɓera ya ba ta jawabi kamar yadda ya saba, sai ya fara yi mata wani kallon raini, kuma ga shi tana jin yunwa, tana jiran ya kawo mata abincin suna.

    Da ta ga alamun babu abincin nan, kuma Ɓera yana yi mata kallon raini, sai haushi ya kama ta ta fusata ta ce: “Kai ka cika surutu da fitina.” Kafin a ce haka, ta yi carab ta far masa, ta kama shi ta cinye. Ƙarya daɗin ji, amma ba na yi tun da Gizo yana nan. Kurunkus.

    Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa

    • Ruwa ba sa’an kwando ba ne.
    • Duk wanda ya ci amana, sai amana ta ci shi.

    Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.

    Danna nan don karanta Tatsuniyar Kaza Da Muzuru

    Edita@rumasau-kallamu