Category: Waƙa

  • Ƙungiyar Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ta Kiɗa

    Ƙungiyar Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ta Kiɗa

    Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya samar da ƙungiya ta aiwatar da kiɗa mai zurfin tunani wadda kuma ta amsa sunanta. A wannan ƙungiya Ɗanƙwairo shi ne Jagora, kuma yana ba ‘Y/Amshi nasa damar yin ƙari da ajewa da sauka da saukar sauka da takidi da rakiya ko karɓeɓeniya, wani bi ma da bayayyeniya, sannan da yin takidi na G/Waƙa.

    Haka kuma a rera wasu waƙoƙi Alhaji Musa Ɗanƙwairo yakan tafi da Sanƙirori da wasu hadiman waƙa duk a ƙungiyar kiɗa ta Musa Ɗanƙwairo.

    Da kansa Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya nuna yadda yake aiwatarwa da ƙullawa da rerawa da sadar da ɗiya a waƙoƙinsa a wannan ɗa na waƙarsa ta ‘Yandoton Tsahe Alhaji Aliyu II, mai G/Waƙa:

    Shirya kayan faɗa mai gida Tsahe:

    Jagora: Duk Makaɗan da at Tsahe nai jam’i,
    : Hab baƙi ha ‘yan gida su duka,
    ‘Y/Amshi: Babu mai shirya waƙa kamat tawa,
    Jagora: Ga makaɗi ya ƙulla wuƙatai,
    ‘Y/Amshi: Sai a amsa mashi ba a ƙara mai,
    : In nuk ƙulla waƙa a ƙara man,
    : Mu haɗu duk azanci gare mu,
    : Shin a a mutum guda za ya radde mu,
    : Shirya kayan faɗa mai gida Tsahe,
    : Ali ɗan Iro bai ɗauki raini ba.
    Jagora: Ga mu hwa! Ga mu hwa!!

    (Ɗan’ƙwairo, Waƙar Musa Ɗanƙwairo ta ‘Yandoton Tsahe Aliyu & Gusau, 2003: sh. ɗi)

    Domin haka, Musa Ɗanƙwairo yana ƙullawa da rera ɗiya na waƙoƙinsa a yayin sadarwa kamar haka:
    +Ƙungiya
    + Jagora (+Ƙulli)
    + ‘Y/Amshi (+Ƙari +ajewa +sauka +saukar sauka +takidi +rakiya +karɓeɓɓeniya +/-Bayayyeniya +ciko ko maimaita ko takidin G/Waƙa)
    + Sanƙira (Mai Kalato Ƙarin Bayanai)
    + Hadiman Waƙa

    Ƙungiyar Makaɗa Musa ƊanƘwairo Maradun ta Kiɗan Kotso ta haɗa da:

    i) Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun = Jagora

    ii) Muhammadu, Daudun Kiɗa na Farko, Ya rasu = Kiɗa da Amshi

    iii) Garba, Zawacin Kiɗa, Marafan Kiɗa,
    Daudun Kiɗa na Biyu (2), Ya rasu = Kiɗa da Amshi

    iv) Audu, Wakilin Kiɗa = Kiɗa da Amshi

    v) Ali, Sabon Kiɗa (ɗan Sa’idu Shayi, Wani Ƙanin Musa Ɗanƙwairo) = Kiɗa da Amshi

    vi) Sani, Zaƙin Murya, Marafan Kiɗa, Ya rasu = Kiɗa da Amshi

    vii) Abubakar (Garba), Ciroman Kiɗa (ɗa), Ya rasu = Kiɗa da Amshi

    viii) Ibrahim Sarkin Fada (Ƙane) = Kiɗa da Amshi

    ix) Muhammadu Jikka (Jikka, Halifa 3) = Kiɗa da Amshi

    x) Sani (Jika) = Kiɗa da Amshi

    xi) Muhammadu Gambo (Bara) = Kiɗa da Amshi

    xii) Malam (Bara) = Sanƙira, Kwandon Ɗanƙwairo

    xiii) Ƙanƙahu (Bara) = Tsaron Kaya

    xiv) Sada (Bara) = Sanƙira

    xv) Rabo (Bara) = Kiɗa da Amshi

    xvi) Nabuba (Bara) = Kiɗa da Amshi

    xvii) Bucaca ‘Yarkohji (Bara) = Kiɗa da Amshi

    xviii) Amadu Bakura (Bara) = Sanƙira

    xix) Sallah Kwana (Bara) = Hadimin Gidan Ɗanƙwairo

    xx) Daudu Ɗangaladima (Bara) = Kula da Doki da Gona

    Domin karanta cikakken bayani akan Tattali da Kulawar Ɗanƙwairo da Majiɓintansa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Dangantakar Harshe da Waƙa danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Yin Waƙar Baka ko Sarrafa Waƙar Baka

    Yin Waƙar Baka ko Sarrafa Waƙar Baka

    A lokacin da makaɗi ya zo yin waƙar baka tun a ƙwaƙwalwarsa da tunaninsa yake fara tsara ta. Wannan tsari shi ne na baɗini, wanda yake a rattaɓe a zuciyarsa kuma a cikin jumlolinsa.

    To, tun daga wannan lokaci ne ya riga ya yi waƙarsa ta baka ta bin waɗannan matakai:

    – Matakin Ƙullawa
    – Matakin Kiɗa
    – Matakin Rauji
    – Matakin Kalmomi
    – Gindin Waƙa
    – Layuka ko Saɗaru a Ɗiya 
    -Nuna Farin Ciki
    – Nuna Baƙin Ciki
    -Faɗakarwa
    -Gargaɗi
    -Ilmantarwa
    -Nasihantarwa
    – Isharantarwa
    -Yabawa
    -Yin Zambo
    -Yin Habaici

    Da Sauransu Kamar Kalmomin Azancin Magana

    Matakin Ƙullawa

    Makaɗan baka sukan ƙulla waƙoƙinsu ta azanci da fasahar da suke da su.
    Ma’anar ƙulli ta ƙamus:

    A ƙamus na Hausa-English (Awde, 1996: 102) ya nuna Ƙulli shi ne (1) to knot (2)to plan (3) to conspire; wato (1)ya ƙulla (2) ya shirya ko ya yi dabara (3) ya haɗa kai. Shi kuma Ƙamusun Hausa (CNHN, 2006: 285) cewa ya yi ƙulla, ita ce ɗaura ko ƙudura.

    Ma’anar Ƙulli ko Ƙulla ko Ƙullawa ta isɗilahi wato ta fannin ilimin waƙar baka. Ita ce:

    Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun ya faɗi yadda yake ƙulla waƙarsa a inda yake cewa:

    Jagora: Ga makaɗi ya ƙulla waƙatai,
    ‘Y/Amshi: Sai a amsa mashi ba a ƙara mai,
    Jagora: In naƙ ƙulla waƙa a ƙara man,
    ‘Y/Amshi: Mu haɗu duk azanci gare mu,
    : Shin a a mutum guda za ya radde mu,
    : Shirya kayan faɗa Maigida Tsahe,
    : Ali ɗan Iro bai ɗauki reni ba.

    (Ɗanƙwairo, Waƙar ‘Yandoton Tsahe Alhaji Aliyu II (1960-1991)

    Ƙullawa ta waƙoƙin makaɗan baka tana da matakai biyu. Akwai ƙullawa ta makaɗan ƙungiya, sannan akwai ƙullawa ta makaɗan kaɗaita. Ga su kamar haka:

    i) Ƙullawar Makaɗan Ƙungiya

    Waƙoƙin baka na Hausa waɗanda ake ƙullawa ta ƙungiya, waƙoƙi ne waɗanda ake tunaninsu ta tsakanin Jagora da kuma ‘yan amshinsa. Ita ƙungiya ita ce wadda ta ƙunshi Jagora da kuma yaransa masu yi masa amshi na waƙar baka da kuma yin kiɗa.

    Har wa yau, ƙungiya ta ƙunshi ‘yan ma’abba ko san-ƙirori ko masu kirarin baki. A wannan lokaci, za a haɗa ƙarfi da ƙarfe tsakanin Jagora da ‘yan amshinsa, a dinga tunanin yadda za a shirya waƙa, musamman ta kawo jumloli da yadda za a tsara saɗaru ko layuka, sannan ana yi ana dakatawa ko lumfasawa. Wannan shi ne ƙulla waƙa ta makaɗan ƙungiya.

    Su kuwa makaɗan kaɗaita, su ne waɗanda Jagororinsu kawai za su dinga ƙulla kalmomi da jumloli, amma yaransu, za a sami waɗanda suke yin amshi wato +ciko kawai, sai dai ba su yi musu kowane irin ƙari a waƙa. Akwai wasu jagororin da ba a ce musu ko ƙala, Jagora ne zai ƙulla waƙarsa kuma ya ƙare ta shi kaɗai. Irin wannan ƙulli jagora ne kawai zai yi tunanin waƙa a baɗininta idan ya gama ƙulla ta sai ya zo cikin yaransa ya rera ko ya je wani wuri ya sadar da ita. A irin wannan waƙa, Jagora ne kawai ake jin muryarsa yana rera waƙa, yana sadar da ita ga jama’a.

    A bisa waɗannan matakai ne ake bi, ake ƙuƙƙulla, waƙoƙi na gargajiya ko waƙoƙi na zamani na baka da Hausawa suke yin tunaninsu a baɗini, daga baya su rera su a yayin da suke sadar da su.

    Matakin Kiɗa

    A Ƙamusun Hausa an nuna kiɗa yana nufin bugun ganga ko kalangu ko abun bugawa ko bugun ƙwarya ko goge ko garaya ko taushi ko kotso da hannu ko da makaɗi ko da wani abu (CNHN, 2006: 243).

    A ilimin fannin waƙar baka, kiɗa yana nuni ne da wani amo ko sauti da ake samarwa ta gwama ko haɗa abubuwa biyu kamar dutsi + dutsi ko tafi + tafi ko baki + ƙahon dabbobi ko ganga + gula (makaɗi) ko wani abu + wani abu ko sauransu. Kiɗa kuma yakan zama wani amo ne wanda yakan shiga jikin mai sauraro, ya sa masa karsashi har ya dinga rausayawa, yana tattakawa ko jujjuyawa.

    Gusau (2008: 54) yana ganin kiɗa shi ne wanzar da amo mai shiga jiki wanda kuma ake aiwatarwa ta haɗa abubuwa biyu ta matakin busawa ko tafawa ko bugawa ko kaɗawa ko gogawa ko girgizawa ko kuma wasun waɗannan.

    Akwai kayayyakin kiɗa da dama. Wasu na gargajiyar Hausawa ne, wasu kuma na baƙin wasu al’ummu ne waɗanda Hausawan suka aro, suna amfani da su. A wajen Hausawa akwai kiɗa zallarsa kawai, ba tare da haɗawa da waƙa ba, ko kirari ko kaɗa take. Akwai kuma kiɗa ta amfani da kayan kiɗa wanda ake haɗawa da waƙa, wanda kuma ake yi wa waƙoƙin da makaɗan baka suke yi.

    Kiɗa a wajen Hausawa ya rarrabu zuwa: Kiɗa

    -waƙa +take -take +waƙa
    -Waƙoƙin Gaɗa
    -Waƙoƙin Samartaka
    -Waƙoƙin Manyan Mata
    -Waƙoƙin Manyan Maza
    -Waƙoƙin Makaɗa

    A wajen aiwatarwa ta waƙar baka akan gwama ta da amon kiɗa wanda za su dinga tafiya a tare tsakanin muryar makaɗi da sautin gangar da makaɗin yake amfani da ita. Bisa mahangar makaɗa, akwai wasu hanyoyi da ake ɗora kiɗa na waƙoƙinsu na baka domin su yi daidai da yadda ake sadar da su. Waɗannan hanyoyi sun haɗa da:

    – sadar da kiɗa daidai da nauyi na muryar makaɗi da kuma raujin da aka zaɓa wa matanin waƙa;
    – Dacewar amon kiɗa da gaɓoɓin murya bisa gurabunta na hawa da sauka da kuma faɗuwa;
    – Ƙarfafa madirar gaɓoɓi;
    – Wani bi a kaurara amon kiɗa;
    – Wani bi a sassauta amon kiɗa;
    – Wani bi a ja amon kiɗa;
    – Wani bi a matse ko a tauye amon kiɗa;
    – Wani bi a qwairanta amon kiɗa;

    Sannan kuma yanayin kiɗan yana iya zama:

     Mai diri
     Mai ƙarfi
     Mai kauri
     Mai zaƙi
     Mai kumbura
     Mai kaurara
     da sauransu

    Matakin Rauji

    Ƙamus na Hausa a ɓangaren Hausa-English (Awde, 1996: 131) ya bayyana kalmar rauji da clapping wato yin tafi ko ban tafi (Awde, 1996, 131 & 210). A kuma littafin Ƙamus na Keɓaɓɓun kalmomi wato Hausa Metalanguage ya fassara Rauji da Ingilishi da Rhythems wato Kari ko karin murya (Awde, 1996:361).

    A fannin ilimin waƙar baka kuwa, rauji wani sauti ko amo ne wanda yake tashi a sama ko ya sauka ko ya faɗi. Rauji yana iya zama murya ta wata halitta mai rai ko sautin wani abu maras rai kamar ƙara ko doka ƙafafu a bisa ƙasa ko wani tsando ko sauti daga kukan tsuntsaye. Har wa yau kuma akwai rauji mai ɗaɗi, mai zaƙi da kuma rauji maras daɗi, mai-ta-da-hankali, kamar kukan kanari (rauji mai zaƙi) da kuma kukan jaki (rauji maras zaƙi, mai ɗaukar hankali).

    Wata ma’anar isɗilahi kuma, rauji na iya zama masaukar murya a gaba.

    A yayin da aka gwama rauji a waƙar baka ta Hausa ana ɗora shi bisa muryoyi na gaɓoɓi na kalmomi ne waɗanda akan sarƙa su a tayar da saɗara a ɗa na waƙa. Rauji wanda aka zaɓa, aka ɗora wa saɗara ko layi a ɗa na farkon waƙa, shi ne zai dinga daidaita rauji a dukkan layuka da ake ƙullawa a ɗiya na waƙar.

    Nauyin rauji a waƙar baka ta Hausa gajere ne, shi ya sa yake tafiya bisa gaɓoɓi na kalma gwargwadon hawansu da saukarsu da faɗuwansu. Matakai waɗanda ake bi a wajen samar da rauji a waƙar baka ta Hausa sun haɗa da:

    – Rauji mai dogon zango
    – Rauji mai gajeren zango
    – Rauji mai matsakaicin zango

    Sannan gaɓa ta rauji za ta iya zama mai nauyi wadda za ta ƙunshi [bww] ko [bwb], ko kuma ta zama mai sauƙi wadda za ta iya zama gaɓa mai [bw] kawai.

    A wajen furta rauji na waƙar baka ana yi masa waɗannan abubuwa kamar haka:

    – Kaurara gaɓa mai nauyi;
    – Jan gaɓa mai nauyi ko mai sauƙi;
    – Daidaita amsa-amon kari (hawa ko sauka ko faɗuwa) a ƙarshen kowace saɗara ko layi.

    Haka kuma ana yin rauji ne na waƙar baka daga karin murya (na hawa da sauka da faɗuwa) da kuma amon kiɗa tun daga tunanin makaɗi a zuciyarsa. Domin haka, ana samar wa waƙoƙin baka rauji ne ta waɗannan hanyoyi:

     Karin murya daga makaɗin waƙar;
     Amon kiɗa daga kayan kiɗan da makaɗi yake amfani da su, ta la’akari da madiransu na hawa da saukar amo ko kuma faɗuwarsa.
     Daga nan sai a fitar mata da raujinta;
     Rauji zai samar wa waƙar baka wani amo wanda zai fitar da ita kaɗai daga sauran waƙoƙin baka na makaɗin.

    Matakin Kalmomi

    Kamar yadda aka nuna a baya, idan makaɗin baka ya tashi aiwatar da wata waƙa ta baka, yakan fara aiwatar da waƙar ne a cikin zuciyarsa da kuma ƙwaƙwalwarsa tun kafin ya furta waƙar a waje. Haka kuma tunanin makaɗi na kalmomi da yadda zai sarrafa su cikin azanci da hikima shi ne wani abu da zai biyo biyo baya a aiwatar da waƙar baka.

    Sannan kuma dukkan makaɗi na ƙungiya da kuma makaɗi na ƙire duk suna yin aiwatarwa a wajen daidaita waƙoƙinsu da tsawaita su. Matakin kalmomi yakan bambanta dangane da kalmomi da makaɗi ya yi tunaninsu ko kuma ya zaɓo su wajen tsawaita waƙar da zai yi. Wasu daga cikin kalmomi da ake zaɓa a shirya waƙar baka sun haɗa da:

    Kalmomin Shirya Gindin Waƙa

    Gindin waƙa furuci ne na wasu kalmomi masu ma’ana masu nauyin saƙo, masu hikima da balaga da azanci waɗanda ake shiryawa don a gabatar da waƙar baka. Ta gindin waƙa ne ake rarrabe ɗa da ɗa a waƙar baka. Waƙoƙin baka sun kasu kashi biyu. Akwai waɗanda ake yi wa Gindin Waƙa kamar waƙoƙin Alhaji Abdu Karen Gusau. Sannan kuma akwai waƙoƙin da ba a yi wa Gindin Waƙa kamar waƙoƙin Alhaji Babangida Kakadawa.

    Ga Misali na Gindin Waƙa:

    G/Waƙa: A lula ɗan haya,
    : Mai gyaran kekuna.
    (Abdu Karen Gusau; Waƙar Alhaji Alula Ɗanhayar Kekuna, Fagge, Kano)
    Har wa yau kuma, Gindin waƙa yakan bayyana abin da waƙa take nufi tun kafin a shiga cikinta. Gindin waƙa wani ginshiƙi ne ko babban matangali na ginin waƙar baka. Wani kuma harsashe ne ko majingini na farko a waƙar baka, inda duk bai zauna ba, waƙa ba za ta ba da sha’awa ba, balantana har ta yi wani armashi.

    Idan makaɗi ya sami zaunuwar Gindin waƙa, to, zai sami haske ya buɗu a gare shi, ya sami walwala ta zaɓo kalmomi waɗanda suka dace ya saka a waƙa waɗanda za su ba shi damar samun sauran ɗiyan waƙar. Makaɗin baka yakan yi tunani a zuciyarsa idan kuma wanda suke a ƙungiya ne sukan haɗa ƙarfi da azama su samo kalmomi zaunannu kuma mafi girkuwa a waƙar da suke shiryawa ta baka su samar da Gindinta.

    A wajen shirya Gindin waƙa makaɗa sukan yi amfani da waɗannan matakai:

    Yawanci Gindin waƙa bai shige layuka biyu (2) zuwa huɗu (4) ba;
    – Yakan ƙunshi kalmomi masu nauyi da ake sarrafa su cikin azanci da hikima;
    – Gindin waƙa yakan ƙunshi sunan mai waƙa ko laƙabinsa ko alkunyarsa ko wata ƙarina da ke nuna Mai waƙa;
    – Sannan ana wakiltar Gindin waƙa da harafin [X] na ABCD;
    – Ana kuma wakiltar adadin saɗaru ko layuka a Gindin waƙa da alkalumma na [1,2,3,4] kamar haka: [X1] ko [X2] ko [X3] ko [X4] da sauransu;

    – Ga misalai:

    i) Gindin Waƙa; (mai layuka huɗu (4)
    X1: Ka bawai maza,
    X2: Na Magajin Gari Bubakar,
    X3: Kai ad da yanzu,
    X4: Allah ya ba ka Sarkin Kabi.
    (Mamman Inyaga Argungu; Wakar S/Kabi Muhammadu Mera. Wato kalmomin nuna farin ciki).

    ii) Gindin Waƙa; (mai layuka biyu (2)
    X1: Tankwafau namijin zaki,
    X2: Sa’idu bai taɓa tsoro ba.
    (Idi Ɗangiwa Zuru: Waƙar Sarkin Sudan Sa’idu, Kwantagora. Wato kalmomin nuna farin ciki)
    – Yawancin kalmomi masu nauyin ma’ana da hikimar zance da makaɗa suke tsarawa a Gindin waƙa sun ƙunshi na nuna farin ciki ko na nuna baƙin ciki. Misalin Gindin waƙa na kalmomin nuna baƙin ciki:
    G/Waƙa: X1: Gagarabadon namiji tsayayyen ɗan kasuwa
    (Shata: waƙar ‘Gagarabadau, Mp3)

    – Kuma wani Gindin waƙar yakan ƙunshi kalmomin yabawa ko na zambo ko na habaici da na zugugutawa da makamantansu. Misali:

    G/Waƙa: X1: Ya ci maza ya kwan yana shirye,
    X2: Gamda’aren Sarki Tudu Alu.
    (Narambaɗa, Waƙar Tudu Alu; Kalmomin zuga da kururantawa da yabawa).
    Akwai kuma a wani G/Waƙa:
    X1: Madogara na Malam,
    X2: Iro Uban Bawa,
    X3: Maigida Shinkahi.
    (Narambaɗa, Waƙar Magajin Garin Shinkahi, Ibrahim; Kalmomin zuga da yabawa).

    – Haka kuma wani Gindin waƙar yakan ɗauki kalmomin faɗakarwa ko gargaɗi ko ilimtarwa ko isharantarwa ko nasihantarwa da sauransu. Misali:
    G/Waƙa: X1 “Yan Nijeriya sai Hausa
    (Abdu Karen Gusau; waƙar Harshen Hausa-kalmomin kishin Hausa da na gargaɗi da na ilimantarwa. Gusau, 2015: 64-75).

    G/Waƙa: X1 Mu kama sana’a ‘yan Nigeriya,
    X2 Zaman banza ba namu ne ba.
    (Abdu Karen Gusau, Waƙar Gargaɗi kan riƙo da sana’a – kalmomin gargaɗi da na faɗakarwa da na isharantarwa, Gusau, 2015: 75-78).
    G/Waƙa: X1 Shegiyar ƙafa ke kika saba da gulando,
    X2 Ki tallafe ni, ɗaukar ni ƙafa kar ki gaza ni.
    (Abdu Karan Gusau, Waƙar Shegiyar ƙafa – Kalmomin faɗakarwa da na gargaɗi da na isharantyarwa. Gusau, 2015: 96-97).

    Layuka ko Saɗaru a Ɗiya

    Layuka jam’i ne na layi (tilo). A Ƙamusun Hausa (CNHN, 2016 206-304) an faɗi ma’anarsa kamar haka: (i) Miƙaƙƙen zane (ii) miƙaƙƙiyar hanya ta cikin gari, ko jerin rumfunan kasuwa ko wani abu (iii)majalisar alƙalai ko kotu ko ɗakin shari’a. Amma kuma a ƙamus (Hausa-English) na Awde (1996:106) ya bayyana Layi (p/layuka) da harshen Inglishi da Line. A kuma ɓangaren ƙamus ɗin na English-Hausa, Awde

    (1996: 295) ya fassara line da noun=n=: (1) layi (2) Baiti (3) Telephone line wato waya. Ta Fuskar Saxaru (Jam’i); saɗara (tilo) kuwa – Ƙamusun Hausa (CNHN, 2006: 381) ya fassara ta da layi cikakke na rubutu.

    A cikin layuka ne ko saɗaru waƙar baka take shirya saƙonni tun a ƙwaƙwalwa, sannan ta rera su, ta sadar da su ga al’umma; ta amfani da mataki na kalmomi waɗanda suka haɗa da nau’o’i daban-daban.

    Kuma har gami da kalmomi na maganganun habaici da isharantarwa da gargaɗi da ilimantarwa da tunasarwa da faɗakarwa da makamantansu da yawa.

    A waƙoƙin baka na Hausa akan shirya layuka ko saɗaru masu sauƙi a ƙagi ɗa na waƙar baka wanda zai ƙunshi saƙo ɗaya kawai. Akwai kuma layuka ko saɗaru da ake shiryawa masu tsauri, waɗanda za su haɗu su tayar da ɗa ɗaya na waƙar baka. Shi ɗa ɗaya mai tsauri yakan ƙunshi saƙonni da yawan gaske kamar guɗa huɗu (4) ko ma fiye da haka waɗanda ake wakiltarsu kamar haka:

    Ɗa ɗaya mai tsauri:
    A1:
    A2:
    B1:
    B2:
    B3:
    C1:
    C2:
    C3:
    C4:

    Da sauransu. Za a ba da misali na ɗan waƙa mai sauƙi (Mai saƙo guda ɗaya kawai) kamar haka:
    A1: Ni kam lafiya nit taho salla,
    A2: Lafiya ni ishe Sarki,
    X1: Amadun Bubakar gwarzon Yari,
    X2: Dodo na Alƙali.
    (Narambaɗa, waƙar Sarkin Gobir Ahmadu Bawa (1935-1975).

    Shi kuma ɗan waƙa ɗaya mai tsauri (mai Saƙonni da yawa fiye da ɗaya), ga wani misali kamar haka:

    A1 Na Magaji mai Martaba ɗan Mu’azu,
    A2 Irin assabad Bubakar baba yay yo,
    A1.1 Na Magaji mai Martaba ɗan Mu’azu,
    A2 Irin assabad Bubakar baba yay yo,
    B1 Tsarin gaskiya Bello kai Shehu yac ce,
    B2 Bari masu son duk su maishe ka yaro,
    B 1.1 Tsarin gaskiya Bello kai Shehu yac ce,
    B2 Bari masu son duk su maishe ka yaro,
    B3 Da kyauta da ilimi da neman dalili,
    B4 Da gode ma Allah da istingfari,
    B5 Da su Bello ɗan Shehu yat tsarmo kowa,
    B6 Ka kai kamar Bello ka gadi Moyi,
    B7 Saura ka kai inda mai Hausa yak kai,
    B6.1 Ka kai ka mar Bello ka gadi Moyi,
    B7 Saura ka kai inda mai Hausa ya kai,
    X1: Bajinin gidan Bello Mamman na Yari,
    X2: Sarki Kudu Macciɗo ci maraya.

    (Sa’idu Faru, waƙar Muhammadu Macciɗo lokacin yana a matsayin Sarkin Kudun Sakkwato, ya rasu a 1995 yana Sarkin Musulmi).

    A layi na ɗan waƙa ana wakiltar sa da alƙalumma na [1-0], da haruffa na ABCD ban da [X] kamar yadda aka gani a misalan da suka gabata. Har wa yau kuma ana iya wakiltar ɗan waƙa ta jan layuka kawai. Misali:

    Ɗanwaƙa mai layuka biyu ko uku
    Xa: 1 ____________________
    2 _______________________
    3 _______________________
    X1 ______________________
    X2 ______________________

    Ko ɗa mai layuka biyu
    Xa: 1 ____________________
    2 _______________________
    X1 ______________________
    X2 ______________________

    Saƙonni a ɗa na waƙa, bisa yawanci ba su shige layuka guda biyar (5). Misali: A1, B1, C1, D1, E1, wato saɗo na ɗaya (1) zuwa na biyar (5).

    A layuka ne kuma ko saɗaru ake tunani a zuciya a gina saƙo na farin ciki ko na baƙin ciki ko na faɗakarwa ko na tunasarwa ko na gargaɗi ko na ilimantarwa ko na isharantarwa ko na yabawa ko na zambo ko na habaici ko na wani saƙo da makaɗi yake son ya gaya wa al’ummarsa a harshen waƙar baka.

    Alalmisali:

    Jarora: Yara farau-farau farar tabarma,
    : Farin cikin mai baƙunta,
    Y/Amshi: Gagarabadon namiji tsayayyen ɗan kasuwa.
    (Shata, Gagarabadau; Gusau, 2018:20)
    Akwai kuma
    Jarora: Ga wani ya yi ilimi babu hankali,
    : Ga dai ilimi babu nutsuwa,
    : An kira shi Dabtan ya amsa,
    : Da ganin ƙurji sai ya yaɓa wuƙa,
    Y/Amshi: Na gode wa Amadun Gaya.

    (Shata, Waƙar Amadun gaya; Gusau, 2018: 23)

    A lokacin da makaɗa suke yin tunanin baɗini na wata waƙa da za su shirya sukan bambarta a wajen yin wannan tunani da kuma samo kalmomi na waƙa.

    i) Wasu makaɗan sukan zauna a ƙarƙashin wata inuwa kamar ta wata bishiya, su kwanta su lulluɓe kansu, suna tunanin wata waƙa. Alalmisali, Alhaji Ibrahim Narambaɗa, idan yana tunanin waƙa har zana tunanin nasa yake yi a ƙasa, ya dinga shata wani zani ko zane-zane kamar zai zana wani hoto na musamman. Zai dinga zanawa a ƙasa a cikin layuka, ya dinga yin zane-zane, yana tsara saɗaru na waƙa.

    ii) Wasu kuma makaɗan sukan dinga jefo wasu kalmomin suna sarƙawa suna kuma zubar da wasu, suna warwarewa, har su haɗa kalmomin da suke buƙata na waƙar. Wasu makaɗan, kamar Salihu Jankiɗi, har tattaka ‘yan amshinsa yake yi, suna zazzaune, idan sun jefo wasu kalmomi da ba su dace ba.

    Ta haka dole ɗan amshi ya yi taka-tsantsan da abubuwan da yake ba da tasa gudummawa.

    iii) Wasu makaɗan, musamman makaɗan ƙire (kaɗaita) sukan sami saulin yin tunani ne a yayin da ‘yan amshinsa suke maimaita kiɗa, su kuma makaɗan sukan yi shuru, suna numfasawa. A lokacin da kuma sanƙirorinsu suke ba da tasu gudunmawa, su kuwa makaɗan (Jagororin) suna yin shuru, suna saurarensu. Da sauran halayen makaɗan kaɗaita. A duk lokacin da makaɗan suka yi shuru suna tunani ne a kan abubuwan da za su ƙara ƙulla waƙoƙinsu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Sadarwa a Waƙar Baka danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Aiwatarwa Da Sadarwa A Waƙƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita, RMK

  • Iƙirarin Simpanci

    Iƙirarin Simpanci

    Ni basimpe ne ku ganni
    Ba taƙiyya zo ka ganni
    Ba ni kunyar yin bayani
    Tunda da ai ban faɗo hakan ba.

    Babu mai sa in yi ridda
    Daga Simphanci ku shaida
    Na yi wasa kam a can da
    Yanzu kam ba a kaini yin riƙo ba.

    Sheik nake so ma a ba ni
    A ɗariƙar Simp a kai ni
    Matsayin Mufti na ƙarni
    Ko kwa Ayatul-ilahi babba.

    Ko na yo digirin digirgir
    Har na farfeshe a koyar
    Da mutane don a samar
    Da tsayayyen Manhaji na babba.

    Ga nasiha ta ga Simpis
    Kar ka yarda ta ɗanji ko dis
    A cikin rai nata ko ɗis
    Wai da sunan ranta yai baƙi ba.

    Lallaɓata a ko da yaushe
    Kar ka ba ta kaɗan ta lashe
    Ba ta duk malam Abashe
    Haka ne ya fi ba fa hancini ba.

    In ka ba ta ta ce ka ƙaro
    Je ka deɓo du a baro
    Ajiye a gabanta jero
    Sai ta zaɓa yin hakan da riba.

    In ka zo ka gida ka ganta
    Ranta ɓace tsaya gabanta
    Kai ta cewa shugaba ta
    ISBIRI ban yo ina sani ba.

    In ta bayyana ba ka lefi
    Kar ka ƙyale ɗaukin lefin
    Yi wa kanka hukunci ya fi
    In ta sauko kai ne kacci riba.

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Tsarabar Makon Sahabbai 2025

    Tsarabar Makon Sahabbai 2025

    SHIRYAWAR GIDAUNIYAR ALHAWARIYYUN KANO

    Ya Ilahu ka ba ni baiwa,
    Nai bayani babu tsaiwa,
    Wanda za ni faɗa wa kowa,
    Za a ji shi a yo riƙewa,
    In ko na mutu ai tunawa.

    Ƙara tsira gun Rasulu,
    Wanda bin Sa fa ba hululu,
    Sa sahabbai har da alu,
    Bin su ba wai ko kwa ƙilu,
    Gaskiya zancen riƙewa.

    Yau Kano ta yo cikowa,
    Ba wurin tsinke sakawa,
    Ga magada annabawa,
    Malamai ‘yan girmamawa,
    Gaskiya suka ambatawa.

    Alhawariyyuna su dai,
    Sun kira Makon Sahabbai,
    Har da mu ‘ya’yan adibai,
    An ware komai na baibai,
    Gaisuwa ce ke fitowa.

    Ga mutane sun halarta,
    Wasu na parking a kwalta,
    Don su kwashi abin buƙata,
    In da mai ja zai jigata,
    Gun magada annabawa.

    Kun kwa san darajar mazaje?
    Ko na kawo nan mu ɓarje,
    Har a kau da ɗiyan garaje,
    Masu kai duk fal ƙuraje,
    Ba su ƙaunar annabawa.

    Na sani kun ɗauki haske,
    Kan bayani na a waƙe,
    Zan bayanina da gaske,
    Babu mai sa wa na waske,
    Kar ku ce na yo zaƙewa.

    Kan su Manzo yai bayani,
    Babu mai ƙi ko kwa raini,
    Gun su ko zagi na muni,
    Shi da su suka rayu ƙarni,
    Sun ci sun sha sun ficewa.

    Sun karanto wanga dini,
    Gun Rasulu da kyan bayani,
    Sunka ɗauka har da nuni,
    Babu saɓani na launi,
    Sai fahimtar girmamawa.

    Sun yi auren ‘ya ga Manzo,
    Ya biɗo aure da ƙwazo,
    Rayuwa suka yo ta ƙwazo,
    Ba hijabi ko kwa hazo,
    Sun aminta da girmamawa.

    Shi fa ja-gaba ne gare su,
    Ko a sallah ko gidansu,
    Har a nau’in kasuwarsu,
    Ba gaba-gaɗi rayuwarsu,
    Sai da amsar tambayawa.

    Son su dinin Annabina,
    In ka bi su ka doshi Janna,
    In ka ƙi su wuta ka zauna,
    Hawuyar nan mai gudana,
    Nan zama nan dauwamewa.

    Da ɗayanku fa zai yi kyauta,
    Duk da girman ambaton ta,
    Ko Uhud dutsen bajinta,
    Ba ta kai mudun awonta,
    Ko rabin sa ana zubawa.

    Wanga zance nai quotation,
    Sai ku ɗauka babu tension,
    In kuna son education,
    Zo Kano nan na yi mention,
    Har a Sakkwato ba ragewa.

    Rijiya bakinta gane,
    Ba wurin wasan su wane,
    In ka ja kuma ka ji hau ne,
    Za ka zame babu aune,
    Rayuwarka ta zam ruɓewa.

    Ai maza gumbarta dutse,
    Maganin duk masu kutse,
    Kan ka ce tak za su rotse,
    Babu hujjar rantse-rantse,
    Sunka kar arna bajewa.

    In kana neman ka tsira,
    Kar ka yo aikin fitsara,
    Har a ce maka ɗan tijara,
    Rayuwarka cikin larura,
    Kun ji ‘ya’yan Rafilawa.

    In kana neman bugagge
    Jahili mai shirya ƙage,
    Wanda bai ƙwalwa ta hange,
    Sai yawan haushi da zarge,
    Ba su fatan girmamawa.

    Kai ina wancan na mushe,
    Mai gaba-gaɗi wa a tashe,
    Mai faɗin kalma a yashe,
    Yau yana can rai a toshe,
    Wai yana neman sakowa.

    Ko a Zariya an rutsawa,
    An ka dirtse mai haɗawa,
    Masu zagin sahibawa,
    Ba su ƙaunar annabawa,
    Sai jidalin jahilawa.

    Gaisuwa gun malamaina,
    Dakta Sani maza gabana,
    Rijiyar ilimi a raina,
    Malami mai kau da ɓarna,
    Ba ya tsoron ambatawa.

    In ana magana ta lugga,
    Ko hadisi babu birga,
    Har a tafsiri ka hanga,
    In ka ce shi toshe taga,
    Dole sai an sallamawa.

    Ga Bashir masani faƙihi,
    Ɗan Aliyu Umar fasihi,
    Ga bayani gun sa sashi
    Ko a lugga Ingilishi,
    Zo gaban sa ya kau da wawa.

    Dakta Mansur Malamina,
    Ba shi son wargi a Sunna,
    Ko a Sakkwato in ya zauna,
    Babu mai zowa da ɓarna,
    Zai baje su da tabbatarwa.

    Ga na Labɗo Umar Ubana,
    Mai rubutun kau da ɓarna,
    Ba shi wasa kare Sunna,
    In ka ce kule zo ku zauna,
    Ba shi sassauta wa wawa.

    Ga Jameel Daktan ƙadimi,
    In yana zancen sa ƙaimi,
    Za ya ja ka ka kauce rami,
    Ga bayani babu lami,
    Jinjina gun Zazzagawa.

    Ga Ubanmu uban mazaje,
    Malaminmu da ke da saje,
    Ba ya lamuntar garaje,
    Sheikh Wahab Abdul mazaje,
    Gaisuwar ka na zazzagowa.

    Ai Bahaushe na fa cewa,
    Kuskuren daɗi katsewa,
    Shi ko sabo ɗauri wawa,
    Za mu rarrabu ba jimawa,
    Ni fa Hausa nake taɓawa.

    In kana neman bayani,
    Nawa ni nan zo gare ni,
    Ba na gaba ko kwa raini,
    Ko gudun mai son ya gan ni,
    Don mu gana ba musawa.

    Je garin Guru ko Kaduna,
    Ko Kano wataran ka zauna,
    Ɗan jira ni kaɗan da kwana,
    Za ka risken ko da rana,
    Ba na ƙyamar mui gamewa.

    Ni Nayaya na ce wa dangi,
    Bissalamu a wanga ƙangi,
    Na sako kowa a tagging,
    Ban da mai zargi da zagi,
    Gun sahabban girmamawa.

    Ibrahim Garba Nayaya,
    Asabar 18 Rajab, 1446 (18 Janairu, 2025)

    Danna nan don karanta Bikin Karrama Gwarazan Gasar Hukumar Tace Fina-finai Ta Jihar Kano

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Waƙar Ilimi

    Waƙar Ilimi

    Waƙar ilimin zamani ta Mu’azu Haɗeja

    1. Gishiri in ba kai ba miya,
    Ilimi mai gyaran zamani.

    2. Jama’armu ku jawo hankulanku,
    Mu lura da halin zamani.

    3. Iko, mulki, ƙarfi, duka,
    Na ga wanda ya ƙaddari zamani.

    4. Ilimi shi ke gyaran ƙasa,
    Har a santa a wannan zamani.

    5. Babu jin kunya gun mai limi,
    Jahili shi ke ta wuni-wuni.

    6. Yanda kaska ke tsotsar jini,
    Haka jahilci gun zamani.

    7. Da tsiya da talauci duk suna,
    Gun da jahilci ya yi sansani.

    8.Wa’azinmu ga mai karɓa duka,
    Masu murnar gyaran zamani.

    9. Masu son lardinmu ya ɗaukaka,
    Bisa kan juyawar zamani.

    10. Kar su fara faɗar da-na-sani,
    Da mun yi karatun zamani.

    Allah ya gafartawa Malam Mu’azu Haɗeja da sauran magabata.

    Danna nan don karanta saƙo cikin waƙa

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Waƙar Baƙar Rama (Ta Haruna Uji)

    Waƙar Baƙar Rama (Ta Haruna Uji)

    Wanda ya yi ma masoyiyar Khadija, wacce aka fi sani da suna “Dije. A inda ya kamanta ta da suna “baƙar rama”. Saboda ita rama, tana da farin jini sosai a wajen Bahaushe. Ga baitin waƙar nan kamar haka;

    Ibrahim Sheme
    Home Columns Online Musings
    Waƙar ‘Baƙar Rama’ ta Haruna Uji
    By IBRAHIM SHEME July 24, 2018

    Haruna Uji ya na kaɗa gurmin sa
    Na rubuta wannan waƙar daga wani faifai na Alhaji Haruna Uji a ranar 21 ga Mayu, 2015. A lura da cewar da yake Uji ya rera wannan waƙar a lokuta daban-daban, mai yiwuwa ne ka ji wani samfur na waƙar wanda ya bambanta da wannan da na rubuto.

    Waƙar “Baƙar Rama” dai Haruna Uji ya yi wa matar sa Tasalla ne, don nuna shauƙin soyayya da ke tsakanin su. Bismilla:

    Ruwa isa gayya, Baƙar Rama,
    Ruwa isa gayya, ya ki!
    Allah Sarki, Baƙar Rama,
    Ke ‘yar masara mai yawan zani,
    Sannu da rana, Tasalla!

    Na kaɗa gangar Baƙar Rama
    Wa’yansu mutane suna faɗi: “Baƙar Rama ko ba mutum ba ce?!”
    Na ce musu, “A’a, ku bar faɗi, Bakar Rama amma mutum ta ke.”

    Ai sai suka ce min: “Haru Uji, Baƙar Rama in dai mutum ta ke,
    Ka yi mana taɗin Baƙar Rama.”
    Sai na ce “Na yarda!”

    Sai ku matso zan gaya muku,
    Na farko zancen Baƙar Rama,
    Mai son ‘yar nan Baƙar Rama,
    In gan shi ga kogo kamar guza kamar gansheƙa, ya ja ciki,
    Ta ce ba ta so, ba za ta ba.

    Ina mai son ki?
    In kai shi ga kogi,
    Iy yi nutso ya ɗebo yashi,
    Sai ya ƙirge yashi,
    Baƙar Rama ta ce ba ta so, ba za ta ba!

    In ya haɗa wannan,
    In kai shiga rairai ya tandara,
    Ta ce ba ta so!
    Ya hau kan rimi,
    Sai ya kere rimi, ya faɗi da ƙirji,
    Baƙar Rama ta ce ba ta so, ba za ta ba!

    Mai son ‘yar nan Baƙar Rama,
    Ya zabura sosai,
    Ya je dawa ya samu giginya,
    Ya hau giginya da baya,
    Baƙar Rama ta ce ba ta so!

    In ya haɗa wannan,
    Ya zauna ya yi mata kukan wata bakwai da kwana hamsin,
    Sai ta ce ba ta so, ba za ta ba. Allah Sarki, Baƙar Rama!

    Danna nan don karanta waƙar ban mutu ba ta Fati Niger

    Edita; Rumasa’u Muhammad kallamu

  • Lokacin Sanyi

    Lokacin Sanyi

    Maganar gaskiya ana sanyi yau garin
    Tin a daren jiya na san yau za ai abin
    Iska ce kamar da rani ta game garin.

    Daga jin fil-fifil na iska sai tausayin
    Kaina Auwalan ya zo mini tin Ajiyan
    Dan na san abin da zai faru da ni kurin.

    Yo ɗakin da anka ba ni gida dukkanin
    Bango nai ina zaton sanyi nan yakan
    Zauna yai watanda kafin ya game garin.

    Ga tagarsa babu ƙofa sai labulan
    Da idan nai fishi aradu ina cinye ɗan
    Malafar uba da bai kare sanyi ko kaɗan.

    Ga ƙofarsa ba ta rufuwa gam wai dukan
    Wanda ya ce fa zai rufe ta rubuk sai idan
    Zai ƙarawa kansa caji na rabin galon.

    Da ma can samansa lau ne to da da ɗan
    sauƙi dan kwa na yi imani zai ragen
    Sanyi tinda ai rufi da silin ba sa barin.

    To fauƙas-samawatin ma tin jiyan
    Na ji ta fara ba ni saƙon kar nai jiran
    Sai wani ya yi min bayani kan nai iyon.

    Ga bargon da ke yi min hidima ya yi min
    Ƙanƙanta dan kwa ƙwabrina ko kaɗan
    Bai samun shiga cikin halara ko kaɗan.

    In na sanya kai ƙafata ita ke wajen
    In kwa na sa ƙafar fa to kaina sai ya zan
    Ya bullo ta ɓangaren titin shonekan.

    An ce ba ku jin dukan sanyi wai hakan?
    Tattabaru da ku nake magana kun yi jim!
    Ko dan na mu lokacin muma is kwamin.

    Allah ga su Abba Yusuf nan na biɗan
    Canjin rayuwa da Bargo Ɗanlibiyan
    Da idan na shige ciki bai mai takuran.

    Danna nan don karanta waƙar halin da muke ciki

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Halin Da Muke Ciki

    Halin Da Muke Ciki

    Sun dai kai mu sun bari sun dawo
    Kuma ni sai nake ga mu muka jawo
    Wani sunansa Baba wani Babawo.

    Alƙawari sukai na za su yi aiki
    Har ma rantsuwar mutanen kirki
    Yau mun wayi kanmu ba imfaƙi.

    Babu tsaro ƙasarmu komin haske
    To in kai dare kwa sai dai waske
    Sai a siye ka tsaf kamar ɗanwake.

    Yau mun wayi kanmu ba jin daɗi
    Wai kuma gwamnati akai tajdidi
    Ko mu sai a lahira jin daɗi?

    Wancan shi ya fara kai mu kushewa
    Muka jure mukai ta daddagewa
    Har ya gama ya bai wa ɗan yarabawa.

    Al’umma tana cikin lahaula
    Babu abinci kana babu sulalla
    Ba nutsuwa gare mu bayin Allah.

    Magidanci babu ba mai ba shi
    Ba mai ba shi sadaka ko bashi
    Kai wallahi dole sai an tashi!

    Yau talakan ƙasarmu ba shi da hali
    Na siyan taliya catorn ko kwali
    Ko shinkafa-kaza ba shi da hali.

    Yau in ya siya ana daɗa kuɗɗi
    Gobe siyanta sai su Alhaji Mudi
    Jibi kwa sai irin gidan ɗanmoɗi.

    Mun ji kuna da bindigar hana bore
    Kuma ku ne da kurkuku mai ƙyaure
    Naman ‘ƴan maza fa shi ne gyare.

    Ku ba kwa sanin muna ƙunci ne?
    Ba ku ganin abin yana yin worse ne?
    Anya ku kwa ma mutane ku ne?

    Ku yi sata amma ku bar mu mu rayu
    Amma kun ci kun hana mu mu rayu
    Ko so duk kuke mu zamma marayu?

    Yanzu a ce abinci ya wuce kanmu
    Ba mu babu cin abin ƙaunarmu
    To wa za ya share duk kukanmu?

    Ba doka ƙasarmu sai kurari
    Sai cewa anai kamar mai bori
    Mu fa aradu sai mu ɗau gorori.

    Abban Marke

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Yaushe Tura Za Ta Kai Bango?

    Yaushe Tura Za Ta Kai Bango?

    Jama’a wai kwa du kuna iya ji na
    Na ga kamar fa ba ku saurare na
    Ya na gane ku ne a zaune a rana
    An ya ma kwa za ku so waƙe na.

    Da dai na mayar wuƙar ƙuguna
    Na ajiye dukka al-ƙalumana
    Domin ni fa ko? Akwai hange na
    Shi nassa gidan ga ba waƙe na.

    Yanzu hakan ga za ku zauna ni kam?
    Wasu gommai suna zuba muku poison
    Ko sai sun fara dangana ku da prison
    Ƙarni CENTURY decade kuma season.

    Ba ni da arzuƙin zama a gidana
    Ba ni abin da zani bai ‘ƴa’ƴana
    Balle ma na kai gidan surukaina
    Haka kullum nake barin matana.

    Yanzu ƙasar ga babu canji kenan
    Ba mai tausayin da zai ce uffin
    Sai wahala ake ta sha ni wai kam
    Ko sararin ga mun fi kowa more than.

    Sai an ambata ku ce watarana
    In komai ya kai mahudar rana
    Akuya in ta dangana bangona
    Cizo za ta dunga yi ɗan Chana.

    An zo an kashe iyayen wancan
    An ɗau wane sai kace Al-kakin
    Wane kwa an kashe hi can ba haƙƙin
    Matar wane ko gabansa ka haiken!!

    An sace ɗiyar mutum fa da rana
    Ni kuma an kashe ɗiyata gidana
    Haka an sace wance du a idona
    Dan Allah ku kai kuɗin fansana.

    Na kai shekara rabon a gidana
    Da Tukunya ta doshi kan murhuna
    Kuma wallahi babu ko son raina
    Tsabar an ci ne da haƙƙoƙina.

    Na je Hospital a ban haƙƙina
    Ba komai cikinsa duk sai yana
    Ba daktas da sunka kai saba’una
    Kuma adadin garinmu ya fi a auna.

    Ba mai faruwa a bayan wannan
    Akuyar ta shige ta bayan bangon
    Ta ma tsallake ginin har zauren
    Ta manta ashe fa an zo bangon.

    To ko dai mu tashi ko kwa mu zauna
    Ko kwa mu dunga shan bugun fir’auna
    Ba baƙon da za ya zo shi gidana
    Ya yi aikin da ban iya ba ku auna!!

    Sai gyara ake a wassu ƙasashen
    Amma mun yi shu kamar ba ma nan
    Kuma mun fi su ma karmar mu yi wannan
    Dan kwa da mai kama ake yin ƙotan.

    Abban Marke.

    Edita: Rumasa’u Muhammad Kallamu

  • Duka A Murɗe

    Duka A Murɗe

    Afwan yau jikin kamar wani mai laulayi

    Haka na yini ta har daren Allah haka na yi

    Ban aika ba babu wanda kuma nace ya yi

    Shi ai so fa ba abin dama ba ya yi.

     

    Ita waccen tana faɗin ni ce taka ɗai

    ‘Ƴar dangi na faɗin ba mai min kwaɗai

    Abba fa nawa ne ki jini na ni ni kaɗai

    Gogan naku ko yana kwance kishingiɗe

     

    Babu fa wanda za ya ce bai son nasa kam

    Sai dai in ya zam yana ɓoyewa kurum

    Ba a makara idan handset kwai alarm

    Babu ruwansa sai ya yo ma ƙara daram.

     

    Maganar gaskiya fa waccen na riƙa sila

    Tun da kamar muna ƙanana fa ya ‘ƴan shila

    Ba ko hantara bare zancen matsala

    Tun ma kan tsayinta ɗinnan fa ya kammala

     

    Haka siddan ki zo ki ce sai min banƙara

    Daga haddar izawaƙa kika nufi baƙƙara

    Kika bar nan kika wuce ƙarshen saɗɗara

    Fazuƙu falan-nazidkum ki yi hattara.

     

    Maganar gaskiya kamata fa ki hanƙura

    Tinda gidanku na sani ba mai takura

    Ba mai ji kama da kamun da ta kumbura

    Ko mai na ci ya beban da ya ke bara.

     

    Kin ga fa ni gidanmu ni ne ɗai salimi

    Kar fa ki sa mutan gidajenmu a zullumi

    Kar ki bari na dinga jin zafi ba gumi

    Sai dai in jikin ga nau to da akwai shimi

     

    Kin ga idan akwai rabo wataƙil za ya zo

    Ko duk duniya su taru su yo dandazo

    In dai Rabbi ya hana to dai ba ya zo

    Ba na son kira a ce min to je ka zo.

     

    Tabbas na sani kina so na Mahira

    Kuma ni ma fa da hakan take ya Ɗahira

    Amma yanzu kam a ƙyale ni na tsahira

    Ɗandagus da shi da Ɗanbello Jira! Jira!!

     

    Afwan ni fa ba na yin ƙusƙus duk dare

    In ka ganni kan icen kuka maza ɗare

    Ba akuya kana sannan kuma ba kare

    Sai ‘ƴa’ƴan fire a mota fal maƙare.

     

    Afwan duk da na sani ba kya jin bari

    Mai suna Karima ce aka cewa Kari

    Mai son shi a kai shi police bai jin bari

    Sai ya je shi dole wata ƙila da ma mari.

     

    Allah ya sani fa ba so ne ba na yi

    Da harawa da garera a haɗa da ƙamayi

    Duk akuyar da tai ta kushe haka so ta yi

    Tattauna shi gunta ko ba ranar ta yi.

     

    Domin ni fa ɗan titis nake sam ba nawi

    Ba Li’irab bare a ce mini annahawi

    Shi farce yana da aiki ran ƙaiƙayi

    Allah dai ya sa abin da ake so na yi.

     

    Abban Marke

    Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu