Category: Waƙa

  • Rataye Na 1: Waƙar ‘Yar Maye Ta Ahmad Tijjani Gandu

    Rataye Na 1: Waƙar ‘Yar Maye Ta Ahmad Tijjani Gandu

    Ahmad Tijjani Gandu

    ‘Yar Maye ‘yar maye,

    ‘Yar maye ya kamata ki bar shaye-shaye, Shaye-shaye, Ya kamata ki bar shaye-shaye.

    Amshi

    ‘Yar uwa ki lazumci karamci kada ki sa ni na zub da hawaye,

    Ta zamo, mai kayan maye mujiya a cikinsu ƙawaye.

    Namiji

    Ni kalar ki tana burge ni,

    Kina da kyau a cikin mataye,

    Nai zaton ki kina da mutunci,

    Sai na gan ki kina shaye-shaye,

    Ga shi ƙauna ta kuma kullu,

    Ƙafa jikinmu zuwa hannaye,

    Da ina murna na dace,

    Ga shi yanzu ina ta hawaye.

    Mace

    Dakata ka ji labarina,

    Na kasance ‘yar shaye-shaye.

    Kuma iyayena sun nunan,

    Tarbiyyarsu da kyan halaye.

    Yau da gobe a kwana a tashi,

    Saurayi ya kira ni kiranye.

    Shi ya ce na raka shi wurin party,

    Can na tadda dukan ‘yan maye.

    Namiji

    Na ji zancan yai mini muni,

    Duk da dai na so ki a ɓoye.

    Yanzu ne na fito in gaya maki,

    ‘Yar’uwa buɗe kunnaye.

    Shi halin da kike kai yanzu,

    Bai da kyau a cikin sunaye.

    Shawara ce yau zan ba ki,

    Ya kamata ki bar shaye-shaye.

    Mace

    Ni fa zancena a taƙaice,

    Ba na so ka gaya wa ƙawaye.

    In kana so mu yi soyayya,

    Za mu yi amma fa a ɓoye.

    Ga waya ta sai ka buga mini,

    Za ka ganni ina nanaye,

    Kar ka damu ka bi ni masoyi,

    Kar ka ce in bar Shaye-shaye

    Amshi

    ‘Yar Maye ‘yar maye,

    ‘Yar maye ya kamata ki bar shaye-shaye, Shaye-shaye, Ya kamata ki bar shaye-shaye.

    Namiji

    Hafsa ke na riƙa zan aura,

    Taimake ni ki bar shaye-shaye.

    Kuma ki tuba zuwa Allahu,

    Yai maza shi yai mataye,

    Hailala da Salati sannan,
    Tarbiyya ki yowa iyaye.

    Kuma ki kamu da istigifari,

    Ba ƙawa da dukan ‘yan maye.

    Mace

    So da ƙauna ta kama ni,

    Ɗan uwa mai kyan halaye.

    Tarbiyyarka tana burge ni,

    Kai daban da zubin wawaye.

    Ko ina na yi sai a gaya min,

    An gan ka kana ta hawaye.

    Mai kake so in maka sahibi,

    Ba ni son ka da zubda hawaye.

     

    Na bi na ɗauka kuma ɗan uwa,

    Karɓi wannan share hawaye.

    Ga jikina har ya canja,

    Nai daban a cikin mataye.

    Da ana ta kira na Hafsat,

    Yanzu na koma ‘yar maye.

    Na shiga uku wayyo Allah,

    Dan’uwa saitan halaye.

    Namiji

    Hafsa ɗan natsu kadda ki damu,

    Rabbi zai yafe halaye,

    Tun da dai kin daina babu ji,

    Yau ido ya daina hawaye,

    Godiya gun Sarkin Allah,

    Shi ya gyara dukan halaye,

    Mu yi zaman aure da mutunci,

    Mun shigo hanyar angwaye.

    Danna nan don karanta Illolin Shaye-Shaye

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Mata Da Shaye-shayen Kayan Maye: Ina Mafita? Wanda Ado Ahmad Gidan Dabino MON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Siyasa

    Siyasa

    GABATARWA

    Adabi sha kun dum ne cikin al’amuran rayuwar al’umma, kama daga abincinsu, abin sha, tufafi, kai har siyasa adabi bai bari ba, ya ratsa cikin rassan adabin nan uku, wato:Zube, Waƙa da kuma Wasan kwaikwayo.

    MA’ANAR SIYASA

    Siyasa hanya ce da mutane ke bi wajen rayuwa a haɗe, ko a tare, ko a ƙungiyance cikin manufa ɗaya. Siyasa na nufin haɗa yarjejeniya tsakanin mutane domin su zauna tare duk da maban-bantan ra’ayoyi, ƙabilu da addinai, a birane da ƙasashe.

    MA’ANAR SIYASA DAGA BAKIN MASANA

    Manzur (1978) Ya kawo asalin inda kalmar siyasa ta samo asali. Inda ya ce”Ta samo asali ne daga “sa’asa” sai ta koma “siyasa” wato ma’anarta tafiyar da shugabancin jama’a ko kuma july away kan wani al’amari ko yarda da wani abu ko jiɓintar al’umma tare da saninsu ko kuma ba su sani ba”

    Bargery (1934) Ya ce”Siyasa na nufin ko dai rangwame a farashin kowane abu, ko kuma tausayawa a cikin al’amura”

    Manzur (1978) Ya ce “Siyasa na nufin ilimi ne dake nuni da kuma gabatar da hanyoyi da manhajoji mabanbanta a cikin gida da kuma alaƙanta da al’umma a waje”.

    NAU’O’IN SIYASA

    Dangane da yadda zamani yake tafiya, haka nau’in siyasa ya dinga ratsuwa a tsakani har aka samu nau’i kamar haka:

    -Siyasar Gargajiya.

    -Siyasar Addini.

    -Siyasar Mata.

    -Siyasar Jami’a .

    -Siyasar Jam’iyya.

    Ga taƙaitataccen bayaninsu.

    * Siyasar Gargajiya: Idan aka ce “Gargajiya”wato abin da al’umma ta gada tun daga kaka da kakanni kafin wasu al’ummu su yi kutse cikinsu.

    Siyasar Gargajiya siyasa ce da aka samo ta daga addinin gargajiya, wanda wasu na ganin bauta ta gargajiya da imani da iskoki dodanni ita ce tsari na samar da shugabanci a tsakanin al’ummar Hausawa, wanda duk wani mai ƙarfi ko jarumi a wurin bauta da alaƙa da dodanni ko iskoki to shi ne jagorancin kuma shugaba, don kuwa babu wani mai iya taka shi ko mai musu da shi.

    *Siyasar Addini: Nau’in wannan siyasa ita ce wacce ta shafi addinin musulunci, wanda ake samun shugaban da hukunce-hukunce daga Alƙur’ani da Hadisi.

    *Siyasar Mata: Ƙwarai su ma mata ba a bar su a baya ba, don tun lokacin da aka haɗa kudancin Nijeriya da Arewa a shekarar 1914 mata suke taka rawar gani a siyasar jam’iyya. Ko a yanzu za mu ga a Jihar Kaduna Dr. Hajiya Hadiza Balarabe ita ce mataimakiyar Gwamnan Jihar a 2019 zuwa 2023. Haka kuma ita ce za ta yi wa zaɓaɓɓen Gwamnan wato Sanata Uba Sani a shekarar 2023 zuwa 2027.

    Haka Hajiya Aisha Binani, ita ce Waƙiliyar Majalisar Dattawa a yankin garin Adamawa, haka kuma ta fito takarar Gwamna, wanda ita ake tsammanin cin ta, sai dai abin akwai ruɗani, sai an sake fafata zaɓen Jihar.

    *Siyasar Jami’a:Irin wannan siyasar ita ce wacce ake gudanar wa a farfajiyar Jami’o’i, kuma ana gudanar da ita ne irin tsarin siyasar Damukuraɗiyya, akwai tsarin Kwansutushon da komai.

    Babban misali kuwa idan muka kalli wannan Jami’ar da muke ciki ta Jihar Kaduna (KASU) za mu ga ita kanta ana fafata siyasar a cikinta. Shugaban ɗalibai na shekarar 2021/2021 shi Abdulhamid Umar, bayan shi kuwa Abubakar Abdullahi ne ya hau a shekarar 2021/2022.

    *Mashi (1986) ya bayyana siyasar jam’iyya da cewa “Jam’iyya tana nufin wata ƙungiya mai wakiltar wani ra’ayi na neman mulkin al’umma, irin wannan ƙungiya akan same ta a ƙasa ɗaya ne, kuma sukan yawaita yadda manufofinsu suka kasance, wannan shi ne ya jawo samun hanyoyin siyasa iri-iri, wato akan sami salon siyasa na Damukuraɗiyya, wato mulkin al’umma ta hanyar abin suke buƙata, kuma suke da ikon tarfe ra’ayinsu cikin lamarin tafiyar da mulki” Wannan ke nuna siyasar jam’iyya tana nufin irin gwagwarmayar da jam’iyyan suke yi don neman kafa gwamnati da saman mulkin al’ummar ƙasa.

    A taƙaice ma iya cewa siyasar Jam’iyya dai wata ƙungiya ce da take gudanar da siyasarta a jam’iyya ɗaya da samun haɗin kai don su kayar da wata jam’iyya daban wato ta abokan hamayya.

    A ƙarƙashin wannan siyasar ta jam’iyya akwai Jamhuriyya har huɗu, inda kowacce Jamhuriyya akwai rawar Jam’iyyu da dama da suka taka rawa a ƙarƙashinta.

    *Jamhuriyyar Najeriya ta farko (1963 – 1966)

    Akwai jam’iyyu kamar su :

    AG, BYM, DP, KPP. Da sauransu

    *Jamhuriyya ta Biyu (1979 – 1983)

    Akwai jam’iyyu kamar su:

    PRP, NPP, NAP, NPN, Da sauransu.

    *Jamhuriyya ta uku (1993)

    Akwai jam’iyyu kamar su:

    SDP, NRC.

    *Jamhuriyyar Najeriya ta Hudu (1999 – yanzu)

    Akwai jam’iyyu kamar su:

    CND, JP, CNC, APC, CPC, PDP, Da sauransu.

    Yanzu za mu ɗauki ɗauki waƙa ta Jamhuriya ta farko don fito da hoton siyasa a ciki.

    WAKAR ‘YAN SAWABA GAMBO HAWAJA JOS.

    Wannan waƙa ta ƙunshi hotunan siyasa da dama kamar su: son yunƙurin canja jam’iyya yayin da aka gane zaluncinta, kamar yadda ya faɗi a baiti na 10 zuwa na 17.

    AMSHI: Allahu Taimaki NEPU Kan Azzalumai

    10. Albarkacin Manzonka zan yabi jam’iya,

    Mai son ta tunɓuke zaluman Nijeriya.

    11. Mu ne mutanan nan da munka fito biɗar,

    ‘Yanci ya samu a tsarkake Nijeriya.

    12. Ita jam’iyar NEPU ta ɗau aniya,

    Sai ta ga bayan zalumanga masha giya.

    13. Ta ɗau makamai sun fi bom har bindiga,

    Kun san su ko in faɗe su su ne gaskiya.

    14. Iggwa da bom bai magani in sun zaka,

    Wa ke da ikon dankwafe wa gaskiya.

    15. Kai fankashali shazumami ka dakata,

    Koron da ba shi da nasa sai ƙwalamar tsiya.

    16. Kai baka noma ba fatauchi ko kaɗan,

    Kuma ba sana’a sai yawan faharin tsiya.

    17. Na tabbata ɗan NEPU ba zai so ka ba,

    Tamkar ƙudan shadda ya sauka a kan miya.

    Haka daga baiti na 18 ya yabi jam’iyyar,kuma ya nuna da su za su samu nasara gami da kirari ga jam’iyyar ta NEPU har zuwa 20.

    18. Mu NEPU mu ne kainuwa bisa kan ruwa,

    Wawan da zai taka mu shi zai dulmiya.

    19. Ga NEPU dutse ba a far maka nan da nan,

    In munka far wa zalumi zai sha wuya.

    20. Mu ne tsakin tsakuwa a gun azzalumai,

    Kafin a ci mu aradu sai an sha wuya.

    Haka tun daga na 21 zuwa na 40 Ya fito da nuna addinanci ne a siyasa, don kuwa ya bayyana yadda za a tsani wanda ba musulmi ba kwata-kwata da shugabanci, don kuwa munanan halayensu da ɗabi’unsu marasa kyau.

    21. Kai turdimi jaki daƙiƙin duniya,

    Ƙaton cikin wofi na cinye haramiya.

    22. Ni zan gaya maka gaskiya in za ka ji,

    Bar sa Wali a cikin a batun dab a shi da gaskiya.

    23. Don Shehu bai ja kafiri a jikinsa ba,

    Shi sai musulmi wanda ke riƙe gaskiya.

    24. Bai je cikin hotel ba Shehu Mujaddidi,

    Kuma ba shi ƙarya bai zama da masha giya.

    25. Har yai wafati Shehu bai cuce mu ba,

    Allah Ya gafarce shi Shehu mazan biya.

    26. Ku jakunan Sheɗan ba za ku ga Shehu ba,

    Bar sanya Shehu cikin batunku na jam’iya.

    27. Kaka, uba bai fidda dan sa ga hallaka,

    In dan yace bai kama hanyar gaskiya.

    28. Kuma ga misali jalla Ya saukar mana,

    Aya a kan Kan’ana inda ya dulmiya.

    29. Kai mai kirarin martabar kaka tsaya,

    Ka tuna Hassan da Hussaini sun riƙe gaskiya.

    30. Bar taƙamar kakanka ban ga fitar ka ba,

    Kakanka baya yin hannu da baturiya.

    31. Kuma bashi cewa goro ai masa jangali,

    Shi bai kawa da Nasara ba ya shan giya.

    32. Gemunka har sajenka ba shi da martaba,

    In dai ya zam aikinka babu na gaskiya.

    33. Ɗan wane jikan wane ba ta isar maka,

    Allahu Ya ce sai kana bin gaskiya.

    34. Mai ɗaura bante in ya bayyana gaskiya,

    Ya zarce mai rawanin da ke son dulmiya.

    35. Da martabar kaka ka mulkin duniya,

    Awolowo shi kuma wa ya ba shi Firimiya?

    36. Kai gafara sa ya ishe ni ku dakata,

    Ba na gudu sai na ga goshin saniya.

    37. Sun raina hanyar Shehu sun bijire masa,

    Ba sa buƙatar lahira sai duniya.

    38. Su dai su hau mota su sauka a hil tasha,

    Ran Jumu’a ran nan suke shagalin giya.

    39. Da ya yi imani ya dubi mazan gaba,

    Da sukai sarautar duniya baki ɗaya.

    40. Ba su shuka sharran don su cuci waninsu ba,

    Su sai shirin da sukai a taimaki gaskiya.

    Haka daga 40 zuwa 58 ya suka jam’iyyar hamayya wato NPC da kuma waɗanda suke cikinta.

    46. Ba na cikin NPC ba na son shiga,

    Manyansu ba sa taimakon Nijeriya.

    47. Na raina jam’iyarsu masu abin faɗa,

    Ni na tsaya kan NEPU tutar gaskiya.

    48. Tutar da ba ta da jahili ko zalumi,

    Da baƙi da ja kore farar taurariya.

    49. In ban da wawa jahili da rashin shina,

    Wai zai bi jam’iyar da ba ta da gaskiya.

    50. Wallahi Allah zan faɗa muku ‘yan uwa,

    Talakan da ke NPC ba shi da zuciya.

    51. Daga dai kawali sai maroƙi ke shiga,

    Sai wanda zai ƙi ubansa don kwaɗayin miya.

    52. Kuma mai kuɗin da ka ganshi ya shiga tabbata,

    Ya raina nasa yana biɗar na haramiya.

    53. Ku ne talakka uba talakka uwa haka,

    Wai har da ɗan sarki kuke gama jam’iya.

    54. Kurdinku ya ruɗe ku kunyi abin faɗa,

    Don kun ki bin asalinku kun bi masha giya.

    55. Ko mai kuɗi ko malami da ya karkata,

    Allahu shawo kan sa mui masa fatiya.

    56. Asirin cikin riga jama’a na tuna,

    Zan bar uba domin ɗiyansa na gaskiya.

    57. Na ‘yanta rand don ruwan da yake ciki,

    Ba don wadansu ba wane da ya sha wuya.

    Tun daga na 89 zuwa na 117 duk yana shimfiɗa habaici da zage-zage da zambo kan ‘yan jam’iyyar adawa.

    89. Babban abin kunyar da sunka yi zan faɗa,

    Wasu tajirai suka je su gai da Firimiya.

    90. Police ya ce babban su, Alhaji dakata,

    Koma, idan kuwa ka ƙi yanzu ka sha wuya.

    91. Wani turdumi dunan amale kututtuɓi,

    Kun san shi ko in faɗe shi, gara mu sakaya.

    92. Ya tattare cuna ya gangare hel tasha,

    Ya dafe kansa yana gudu ba waiwaya.

    93. Ya manta rancen dukiyar da ya tambaya,

    Ya tuna da kwanan yari, gara ya sakaya.

    94. Im ban da jahilcinka ba ka da hankali,

    In anka cinye kuɗinka sui maka dariya.

    95. Bayan watanni ‘yan kaɗan suka tabbata,

    Kurɗinka sun kare su sa ka a jam’iya.

    96. ‘Yan NEPU don ba su ce a cinye kuɗinka ba,

    NPC ba ta biyanka wannan dukiya.

    97. Na tabbata ɗan NEPU bai ci kuɗinka ba,

    Ɗan NPC ne ya ci dukiyarka ta dulmiya.

    98. Mai son yana da sule biyar a yi mai jaka,

    Ba na saka shi cikin mutanen gaskiya.

    99. Koma Kaduna ka nemi mai maka tsibbu can,

    Kuma na ji ba shi Kaduna ya tafi Zariya.

    100. Jama’a takarda na gaba ta mantuwa,

    Na gan ta na tuna jahilin tsohon tsiya.

    101. Duk fasiƙin tsohon da bai tsare kansa ba,

    Wallahi in muka gauraya zai sha wuya.

    102. Wani ɗan farin tsoho cikinsa baƙinƙirin,

    Ya manta Allah ya ji ruɗin dukiya.

    103. Mai shekara saba’in ka gan shi da daduro,

    Me zan kira shi ku ce da shi tsohon tsiya.

    104. Tsohon da bai san Fatiha ba munafiki,

    Bakinsa na kumfa ya bakin saniya.

    105. Duka fasikin tsohon da ba zai tuba ba,

    Wallahi zai tozarta tun daga duniya.

    106. Kai danƙaro mai danne tsaba, ka ɓata,

    Sha talla doki ba ido wa zai saya.

    107. Ɗaukar macuci ban ga amfaninta ba,

    Noman kisan gero a kewaye harkiya.

    108. Yau duk mutan NPC in na ƙididdige,

    Maciya amana sai ɓarayin tunkiya.

    109. Sai wanda zai baki ya kai su cikin tasha,

    Ya gama da ‘yan sane su ɗauke dukiya.

    110. Wa ke shiga NPC ban da munafiki,

    Sai Alhajin da ya kasa ƙarasa Fatiya.

    111. Ko yai karatu in ka bi shi a hankali,

    Ka tadda imaninsa babu a zuciya.

    112. Jama’a masoya NEPU kar ku yi fargaba,

    Wallahi ƙinsu da sonsu ma faɗi gaskiya.

    113. Duk mai abin kunya ba zai shiga NEPU ba,

    Wallahi ko da ya shigo ta da sakiya.

    114. Kai kyankyaso kwaɗayinka bai fishshe ka ba,

    Koma cikin shadda, fito daga tsariya.

    115. Wani sakarai maganarsa in muka bincika,

    Muka buɗa tarihinsa sai a yi dariya.

    116. Don sai da tsohon yai shiri yai gangara,

    Sannan ya nemi shiri da shi don dukiya.

    117. Jama’ar garin muka taru dai aka lallaɓa,

    Mutuwarsa ke da wuya ya kwashe dukiya.

    Idan muka dauba, za mu ga cewa lallai a wannan waƙa an fito da wasu ƙaɗan daga cikin hoton siyasa dangane da adabi, kamar yadda muke shantalo wasu baitika mu tsatso ma’anonisu a dunƙule.

    Ga wasu halayyan ‘yan siyasa ko abin da ya shafi siyasa a wannan waƙa kamar haka:

    -Yabon jam’iyya, wato ta NEPU.

    -Kirari wa jam’iyya don janyo ra’ayin mutane.

    -Nuna Addinanci don a samu damar sukar jam’iyyar adawa.

    -Sukar jam’iyyar Adawa wato NPC

    -Zambo da zagi da habaici wa jam’iyyar adawa.

    KAMMALAWA

    Duba da yadda muka tsatso hoton siyasa a wannan waƙa ta NEPU, za a ga cewa lallai ana tsintan abubuwa da dama da suka shafi siyasa a rubutaccen adabi ko kuma adabin baka.

    MANAZARTA

    -TARIHIN SIYASARNIJERIYA,FACEBOOK GROUP.

    -Bawa S 2021


    ,Siyasa da adabi ;nazari daga wasu rubutattun labaran Hausa.Sashen harsunan Nijeriya da kimiyyar harshe Jami’ar Jahar Kaduna.

    -C.N.H.N(2006) Ƙamusun Bayero.Jami’ar Bayero Kano.

    -Waƙa a bakin mai ita1,center for nigerian languages,Bayero University,Kano.

    Danna nan don karanta Haɗuwar Harshe

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Waƙoƙin Fada Da Wasu Waƙoƙi Game-Gari

    Waƙoƙin Fada Da Wasu Waƙoƙi Game-Gari

    1.1 Abdu Inka Bakura : : : : : :

    ‘Shi mika dibi Mujaddadi.’
    Sarkin Musulmi Alhaji Sir Abubakar III : : :
    ‘Akwai Haƙuri ga Shehu Majidaɗi.’
    Waƙar Alhaji Shehu Majidaɗi : : : :

    1.2 Muhammadu Sani Dodo Maitabshi, Wurno : :

    ‘Ki Sake Sarkin Sudan.’
    Waƙar Sarkin Sudan na Wurno, Alhaji Shehu Malami :
    1.3 Sani Mamman Inyaga Argungu : : : :
    ‘Mamman Sadaukin Sarakuna.’
    Waƙar Sarkin Kabin Argungu, Alhaji Muhammadu Mera :

    1.4 Aliyu Gurso Talatar Mafara : : : :

    ‘Bajini ɗan Moyi na Amadu.’
    Waƙar Sarkin Musulmi, Alhaji Sir Abubakar III
    (1938-1988) : : : : : :
    ‘Bi da Maza Uban Zagi na Sanda.’
    Waƙar Sarkin Maru, Banaga Muhammadu Bature :
    ‘Namijin Zaki Tsayayyen Maza.’
    Waƙar Sarkin Maru, Banaga Muhammadu Bature :

    ‘Faskara koyo Mamman maqi garaje.’
    Waqar Sarkin Maru, Banaga Muhammadu Bature :

    1.5 Sa’idu Maidaji Sabon Birni : : : :

    ‘Gagara gasa ‘yak Kaso.’
    Waqar Sa’idu Maidaji ta Innar Gobir Sabon Birni :
    ‘Ƙi Garaje Uban Meli bai Ɗauki Wargi ba.’
    Waƙar Sa’idu Maidaji ta ‘Ƙi Garaje’ : : :

    1.6 Sa’idu Faru : : : : : :

    ‘Kana shire baban ‘Yanruwa.’
    Waƙar Sarkin Kudun Sakkwato, Alhaji Muhammadu
    Macciɗo : : : : : :

    1.7 Idi Ɗangiwa Zuru : : : : : :

    ‘Tankwafau namijin Zaki.’
    Waƙar Sarkin Sudan na Kwantagora Sa’idu : :
    ‘Gwauron giwa shirinka yai kyau.’
    Waƙar Sarkin Zazzau Muhammadu Aminu : :
    ‘Qi garaje bai ɗau Wargi ba.’
    Waƙar Sarkin Zazzau Muhammadu Aminu : :

    1.8 Muhammadu Dodo Maitabshi : : : :

    ‘Ya ci dunun yaƙi.’
    Waƙar Sarkin Gobir na Gwadabawa, Alhaji Muhammadu
    Maiturare : : : : : :
    ‘Ya Ɗau Girma na Hwaɗa.’
    Waƙar Sarkin Gobir na Gwadabawa, Alhaji Muhammadu
    Maiturare : : : : : :

    1.9 Ibrahim Gurso Talatar Mafara : : : :

    ‘Mai taimakar Musulmi Kullum.’
    Waƙar Sarkin Musulmi, Alhaji Hassan ɗan Mu’azu :
    ‘Gwarzo mai Saje.’

    Waƙar Sardauna Abubakar III, (Kafin ya zama
    Sarkin Musulmi) : : : : :
    ‘Mijin maza jikan Mu’azu’
    Waƙar Sardauna Abubakar III, (Kafin ya zama
    Sarkin Musulmi) : : : : :

    1.10 Alhaji Bala, Sarkin Taushi Sarkin Kano : :

    ‘Lamiɗo mai rabo da yawa Ɗanmaje.’
    Waƙar Ɗanmajen Kano, Alhaji Muhammadu Sanusi II
    (Kafin ya zama Sarkin Kano) : : : :
    ‘Shi a gaba ya wuce gwangwani.’
    Waƙar Danmajen Kano, Alhaji Muhammadu Sanusi II
    (Kafin ya zama Sarkin Kano) : : : :

    1.11 Ibrahim Narambaɗa, Tubali-Isa (ya Rasu 1960) : :

    ‘Tattaki Maza ɗan Shehu na Babba.’
    Waƙar Magaji Shadawu ta Dagacin Tubali, Isa :
    ‘Bajimin ɗan Jika.’
    Waƙar Sarkin Rahi, Muhammadu na Rahi : :
    ‘Yai Halin Mazan Jiya.’
    Waƙar Sarkin Kwatarkwashi, Alhaji Amadu : :
    ‘Gagarau mai Buge Kangara.’
    Waƙar ‘Yandoton Tsafe, Alhaji Aliyu (1960-1991):
    ‘Mai Gusau Raba Kaya.’
    Waƙar Sarkin Kudan Gusau, Alhaji Sulaiman :

    1.12 Alhaji Dr. Mamman Shata Katsina : : :

    ‘Da Akwai Daɗi Zaman Ƙauye.’
    Waƙar Zama a Ƙauye : : : :
    ‘Bawan Allah Yakubu Gawon.’
    Waƙar Tsohon Shugaban Ƙasa, Dr. Yakubu Gowan:
    ‘Gagarabadau Namiji Tsayayyen ɗan Kasuwa.’
    Waƙar Sarkin Musawa, Alhaji Usman (1949-1965) :

    1.13 Muhammadu Isa Gawo-Haraɗo (Mamman Gawo) :

    ‘Ya Allah Gyara.’
    Waƙar Mamman Gawo ta Jamhuriyyar Nijar :
    ‘Nijeriya da Nijar Daidai Suke.’
    Waƙar Mamman Gawo ta Nijeriya da Nijar ta
    ‘Ya Rabbi Sarki mai Jama’a’ : : : :
    ‘Allah shi ba mu Sa’a.’
    Waƙar Mamman Gawo ta ‘Allah Shi ba mu Sa’a’ :
    ‘Sannu Yalwa Ɗiyar Malam.’
    Waƙar Mamman Gawo ta ‘Sannu Yalwa’ : :
    ‘Muna Murna ‘yan Nijeriya Duka Baki ɗai.’
    Waƙar Mamman Gawo ta ‘Muna Murna ‘yan
    Nijeriya.’ : : : : : :
    ‘Yau mun kai ga Daɗi da Mulkin Soja yaz zo.’
    Waƙar Mamman Gawo ta ‘Allah Kai Ruwa’ ta
    Mulkin Soja Shugaba Sani Ƙunci : : :

    1.14 Auwalu Nahabu Ibrahim : : : : :

    ‘Kiɗin Siti Ilorin.’
    Waƙar Auwalu Nahabu Ibrahim ta ‘Kiɗin Siti Ilorin :
    ‘Tambarin RDPC.’
    Waƙar Auwalu Nahabu Ibrahim ta ‘Tambarin
    RDPC’: : : : : : :
    ‘Tambarin Auwal Nahabu Ibrahim.’
    Waƙar Auwalu Nahabu Ibrahim ta ‘Tambari’ :

    1.15 Makaɗiya: Hajiya ‘Yargado Mai’amada

    ‘La’ilaha illallah’ : : : : : :
    ‘Lale – Lale in Dire’ : : : : :
    ‘Dangwale Yarinya Dangwale : : : :
    ‘Yargadagar Gadagalle’ : : : : :

    1.16 Hajiya Sa’adatu Barmani Coge : : : :

    ‘Allah ka ba mu Nairori.’
    Waƙar Barmani Coge ta ‘Allah ka ba mu Nairori.’ :
    ‘Gangar Ɗa’a.’
    Waƙar Barmani Coge ta ‘Gangar Ɗa’a : : :

    1.17 Bawa Namiji Jega : : : : :

    ‘Gyara Gari Rambo Sarkin Aiki.’
    Waƙar Bawa Namiji Jega ta ‘Gyara Gari Rambo’ :
    ‘Ba yaƙi Ɗai ay Yaƙi ba.’
    Waƙar Bawa Namiji Jega ta ‘Ba Yaƙi Ɗai ay
    Yaƙi ba.’ : : : : : :

    1.18 Haruna Uji Haɗeja : : : :

    ‘Kainuwa Dashen Allah.’
    Waƙar Haruna Uji ta ‘Kainuwa Dashen Allah’ : :
    ‘Shamuwa’
    Waƙar Haruna Uji ta Shamuwa’ : : :

    1.19 Sani Ɗan’indo Gusau : : : : :

    ‘Yangayu.’
    Waƙar Sani Ɗan’indo ta ‘Yangayu’ : : :
    ‘Mu koma Sakkwato.’
    Waƙar Sani Ɗan’indo ta ‘Mu Koma Sakkwato’ :

    1.20 Alhaji Ɗanjuma Ɗanƙwairo Maradun : : :

    ‘Na Sarkin Bai ba a ja ka ba.’
    Waƙar Ɗanjuma Ɗanƙwairo Maradun ta ‘Na Sarkin
    Bai ba a ja ka ba.’ : : : : :
    ‘Uban Inuwa ɗan Indo’
    Waƙar Sarkin Kiɗa Ɗanjuma Ɗanƙwairo Maradun ta
    ‘Uban Inuwa.’ : : : : : :

    1.21 Malam Ashana Ɗankama, Kano : : :

    ‘Mr. Ojuku (Sojojin Tuwo).’
    Waƙar Malam Ashana Ɗankama ta ‘Mr. Ojuku’ :
    1.22 Nura S. Fada : : : : : :
    ‘Sarkin Jeganmu, Zaki Kake ba a yi Maka Ɓamɓarma.’
    Waƙar Nura S. Fada ta ‘Sarkin Jeganmu’ : :

    1.23 Amadu Mailauni Bakura : : : :

    ‘Shugaban Ƙasa mai ban Tsoro.’
    Waƙar Amadu Mailauni Bakura ta ‘Shugaban Ƙasa’
    Alhaji Shehu Usman Aliyu Shagari : : :
    ‘Za mu Shirin Waƙar Jam’iyyar NPN mai Haske.’
    Waqar Amadu Mailauni Bakura ta ‘Za mu Shirin
    Waƙar Jam’iyyar NPN mai Haske’ : : :

    1.24 Usman Sarki Shiyar Fada Birnin Kebbi : : :

    ‘Yan Zanzari Shahada Ƙarya ku kai.’
    Waƙar Usman Sarki Shiyar Fada ta ‘Yan Zanzari’ :
    ‘Yan Zanzarin Shiga Wuta a yi Hattara.’
    Waqar Usman Sarki Shiyar Fada ta ‘Yan Zanzarin
    Shiga Wuta’ : : : : : :
    ‘Sakamakon Janar Buratai Nijeriya ta Zamo Tsaf-Tsaf.’
    Waƙar Usman Sarki Shiyar Fada ta ‘Sakamakon.

    Domin karanta cikakken bayani akan Wasu Waƙoƙin Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau danna nan.

    Domin karanta cikakken bayan a kan Tarihin Magabata da Haihuwar Ɗanƙwairo danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Diwanin Waƙoƙin Baka Juzu’i Na Biyar (Matanonin Wasu Zaɓaɓɓun Waƙoƙin Makaɗan Baka); wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Roƙo a Wasu Waƙoƙin Kamilu Almajirin Mawaƙa

    Roƙo a Wasu Waƙoƙin Kamilu Almajirin Mawaƙa

    Kamar yadda tarihi ya hakaito cewa roƙo na daga cikin muhimmin abu a wurin Bahaushe; wannan ya sanya har ake samun maroƙa a ƙasar Hausa; kuma da wannan sana’a ta roƙo suke yin dukkanin wata ɗawainiya ta rayuwarsu.

    Mawaƙa sun fi kusa da maroƙa, domin wasun su ma sukan yi roƙo ne ta hanyar waƙa. Kamilu ɗaya ne daga cikin mawaƙan Situdiyo wanda yake waƙar siyasa; wanda a mafi yawan waƙoƙinsa za a riski salo daban-daban na roƙo.

    Cikin wuraren da aka sami wannan roƙo a waƙoƙin da aka nazarta akwai:

    1. Waƙar Hon. Alhaji Baba Bukar Mashina

    Gindin waƙa : Baba na Mashina kowa ya bi.
    Jagora : Baba na Mashina nai waƙa baba kaƙara mini ƙarfi na ba,
    Babu gida kuma ba ni da mota ban je Saudiya na dawo ba,
    Masu gida na haya sun tashen ban miƙa musu ‘yan kuɗi ba,
    Baba na Mashina ya ci ka duba ni ma ga ni gwanin talakawa.

    Idan aka lura a wannan baiti, za a ga Makaɗi Kamilu ya fito da gayar roƙo ta sigar bayyana wa wanda yake yi wa waƙa wasu matsaloli nasa. Wato ya nemi a ƙara masa ƙarfi, wato a ba shi kuɗi ko dai wani abu mai daraja. Sannan ya bayyana ba shi da gida da mota, kuma bai je Saudiya ba (aikin Hajji ko Umara), wanda hakan na nufin a ba shi gida da mota sannan a kai shi Saudiya. Sannan ya bayyana cewa masu gidan haya sun tashe shi, saboda ya kasa biyan kuɗin haya. A nan, idan an saya masa gida, shi ne abin da ya roƙa a farko, amma idan haka ba ta samu ba, to sai a biya masa kuɗin haya na tsawon wasu lokuta.

    2. Waƙar Alhaji (DR.) Ibrahim Geidam ta Ruwa Baba

    Gindin Waƙa : Ruwa Baba, Sannu Baba Gwamna Bra-Bra.
    Jagora : Ahmad Lawan ka duba mini ya Maigidana,
    Maganar rashin gida ɗazu a mota na kwana,
    Fili nake buƙata na biya Maigidana,
    Kaza gare ta gashi na biɗa ba jini ba.

    A wannan waƙar, Makaɗi Kamilu ya bi wani salon yin roƙo ta yadda ya fara neman Ahmad Lawan da ya dube shi. A nan, da ya ce, yana nufin a yi masa wani alheri, amma a layi na gaba sai ya bayyana matsalarsa ta farko, wato rashin gida wanda ya sabbaba kwanansa a cikin mota yayin da ya je Abuja.

    3. Waƙar Gafara Koko

    Gindin Waƙa : Gafara Koko, tunda mun taɓa mun ji Fura.
    Jagora : Yanzu waƙa ta tashi sai gurin Gwarzona,
    Jinin sharifai ba ka san ɗumi ba balle ƙuna,
    Dutsin cikin ruwa ba ka yamutse ba domin rana,
    Mu gaida Babagoni dole na yaba Gwarzona,
    Fage na kyauta wallahi ka fi wancan suna,
    Batun siyasa bana o’o ya ware da suna,
    Mu gaida SSG Jarumi na ce Gwarzona,
    Fage na alƙawari duk a duniya kai suna,
    Idan ya ce zai mana ai kamar yana hannuna,
    Mu gaida Babagoni Jalla ya tsare Gwarzona,
    Ka duba lambata kuma ka je zuwa sunana,
    Ka ban kujera ni ma na je Gabas ɗan baiwa.

    A nan kuma, ya yi ƙoƙarin yin roƙo ta sigar ambato Babagoni Mashina da jarumi wanda muddin ya ce zai bayar, to tamkar ya bayar ɗin. Sai ya shiga fagen roƙonsa nan take, a inda ya roƙi ya ba shi kujerar Hajji. A nan dai, ya roƙi kujerar Hajji ce a taƙaice.

    4. Waƙar Masassara Mai Saurin Duka

    Gindin Waƙa : Masassara mai saurin duka, kun ji kunya ‘yan PDP.
    Jagora : Abdul’aziz Yari yau na zo ni wajen ka waƙa ta kawo ni,
    ‘Yan amshi : Masassara mai saurin duka
    Jagora : Mota nake so amma ta hawa zan hau na tuƙa in ka ba ni,
    ‘Yan amshi : Kun ji kunya ‘yan PDP,
    Jagora : Birnin Gusau za ni gun sa kwa nan ne ya ba ni motar in ya ji ni,
    ‘Yan amshi : Masassara mai saurin duka,
    Jagora : In ya ce ga ta ba shakka wallahi waqa ta tai riba.
    ‘Yan amshi : Masassara mai saurin duka
    Jagora : Kun ji kunya ‘yan PDP,
    ‘Yan amshi : Dukkanin mutumin da ya bar ku a ko’ina ne shi ya ci riba.

    A nan, ya roƙi mota a wurin Abdul’aziz Yari da ya ba shi mota, har ma yake nunawa cewa fa, idan aka ce ga motar; to fa waƙa ta yi riba, ma’ana roƙon da ya yi ya amfanar.

    Jagora : Mai Mala Maigidana wai shin ni da kai me yai zahi ne?,
    ‘Yan amshi : Masassara mai saurin duka
    Jagora : Ni so nake yi na je ni Haji ga kuma lokacin tsadar jirgi ne,
    ‘Yan amshi : Kun ji kunya ‘yan PDP,
    Jagora : Ka ce da Gwamnanmu B.B yai mini agaji Oga ka gane,
    ‘Yan amshi : Masassara mai saurin duka,
    Jagora : In ban da Barno zuwa Legas na tabbata ban hau jirgi ba.
    ‘Yan amshi : Masassara mai saurin duka
    Jagora : Kun ji kunya ‘yan PDP,
    ‘Yan amshi : Dukkanin mutumin da ya bar ku a ko’ina ne shi ya ci riba.

    Duk a cikin waƙar, sai ya ƙara yin wani roƙon ga Mai Mala Buni inda ya nemi ya nemar masa kujerar Hajji a wurin Gwamnan Jihar Yobe, wato Alhaji Ibrahim Geidam, har ma yake nuna shi fa in ban da daga Borno zuwa Legas bai taɓa hawa Jirgi ba. A Taƙaice dai a nan ma ya roƙi kujerar Hajji ce.

    5 Waƙar Na Je Buni

    Gindin Waƙa : Na je Buni, Mai Mala ba ya gida
    Jagora : Zuwa da wuri mutanenmu ya hi zuwan wari,
    Idan Kura ta kuɓuce a nemo sasari,
    Hausawa sun ka ce walla guntun gatari
    Shi yaf fi ka je ka ce wane yi min haƙƙuri,
    Akwai wahala da nomansa kun san tsaddari,
    Idan har za ka nome shi sai kai haƙƙuri,
    Gwani ɗan Boni mai maganin ‘yan tunziri,
    Idan dai ga ƙuli gehe saura ƙahuri,
    Kujerar Hajji aka ba ni saura guzziri,
    Ka ba ni dala dubu ukku na bar damuwa.

    A wannan ɗiya, ya bayyana cewa an riga an ba shi kujerar Hajji, to abin da yake son Mai Mala Buni ya masa, shi ne ya ba shi guzirin da zai bari a gida da abin da zai yi ɗawainiya yayin aikin Hajji, har ma ya yanke adadin abin da yake so, wato dala dubu uku. A taƙaice a nan, ya roƙi a ba shi kuɗi domin samun tafiya aikin Hajjin da zai tafi wanda tuni an biya masa ko kuma dai ya biya wa kansa.

    6 Waƙar Daga Geidam Sai Buni

    Gindin Waƙa : Daga ya ƙare Gwamna Geidam sai Buni.
    Jagora : Wai Mai Mala ya za a yi ne to ni dai ga ni,
    Da ka canjan mota da ka birge ni,
    Domin waccan motar Oga tai rauni,
    In za ka sayan wata to in zo har Buni,
    Da ka ƙi sayan motar da an nuna ni,
    Sarki Allah Shi ne mai kakkare ni,
    Da ‘yan bangar wancan da sun yanka ni,
    Kyautar nono ita ce kyauta ta Hilani,
    Kyautar mota ita ce kyautar ɗan Buni,
    Iyakar su yi kuwwa ban hau motar ba.

    A wannan ɗiya kuwa, Makaɗi Kamilu Almajiri ya roƙi Mai Mala Buni da ya canja masa mota, inda har ma yake shaida masa cewar motarsa ce fa ta yi rauni, wato ta lalace.

    Sannan ya yi nuni idan fa ya ƙi saya masa motar, to fa za a nuna shi, ma’ana maƙiya ko ‘yan adawarsa za su rinƙa yi masa dariya, domin ga shi ya yi roƙo amma an ƙi amsa masa, kuma alhali ya cancanci a amsa masan.

    ‘Yan amshi : Daga ya ƙare Gwamna Geidam sai Buni,
    Babban Zaki ba ya tsoron kuraye,
    Ga ƙarfi ga ƙarfe ba mu ɗau roba ba.

    Jagora : Kura har limamin tsoro ban tsoro,
    Ga Kura na yawo ga Giwa toro,
    Jiya na ga zuwan Gwamna taro yai taro,
    Ga nan shukar Malum ga shanun Jauro,
    Wasa za ai ko ko zancen ‘yan horo,
    In Mai Mala na gwamna da mun yi ta voro,
    Sabon shuka taka waccan kuma gyauro,
    Waken Suya shi ne ƙarshen duk ƙwaro,
    Kai sarkin kyauta ne Ogana ƙaro,
    Ni dai mota ita ce ba ka ɗan miƙan ba.

    A wannan ɗiya ma, ya roƙi mota ce daga wurin Mai Mala Buni, inda a sigar roƙon yake nuni da cewa fa ya masa wani abu, amma bai miƙa masa mota ba, ma’ana bai ba shi kyautar mota ba.

    7. Waƙar ‘Yan Jo’aye

    Gindin Waƙa : Komai munaƙisa
    Jagora : Gida nake biɗa Damaturu dan ni ma na sha kwana,
    ‘Yan amshi : Talakawa,
    Jagora : In dai akwai Bukar Dauda ku ma kanku kun shina,
    ‘Yan amshi : Talakawa,
    Jagora : In dai gyaɗa tana waje ba a zance da geguna,
    ‘Yan amshi : Talakawa,
    Jagora : Na gaida Maigida Bukar bin Dauda ban da shi gudun talakkawa.

    A nan kuma, sai ya roƙi gida a wurin Hon. Bukar Dauda, inda ya nemi a ba shi gida a Damaturu Fadar Gwamnatin Jihar Yobe. Kasancewar Makaɗi Kamilu ɗan Nguru ne, ya sanya kuma ga Damaturu inda nan ce gidan mulki, sai ya nemi a ba shi gida domin shi ma ya zama yana da gida a can, ko kuma ma ya tare ya koma can gaba ɗaya.

    Jagora : Kowa ya zo gaban ka Sarki sai ya doka tambura,
    ‘Yan amshi : Talakawa,
    Jagora : Na gaida shi Sanate President mai ƙaunar mu nai ƙira,
    ‘Yan amshi : Talakawa,
    Jagora : Zan je da tambura gaban Sardauna na ba da shawara,
    ‘Yan amshi : Talakawa,
    Jagora : Oga ka taimaka ka ban matsayi ni ma a san ina gidan Giwa.

    A nan kuma, sai ya roƙi Shugaban Sanatocin Nijeriya da ya ba shi aiki. Wani abin mamaki a nan, mafi yawan roƙon mawaƙa, sun fi roƙon gida, kujerar Hajji da mota, amma a nan, sai Kamilu ya roƙi a ba shi aiki.

    Jagora : Sai Baba Malam ina S.S.G namu na yaba,
    ‘Yan amshi : Talakawa,
    Jagora : In dai akwai dala hannun dogo ba a kai shi ungo ba,
    ‘Yan amshi : Talakawa,
    Jagora : Kyauta da igiya ta lilo ya fi a ba ni tak kaba,
    ‘Yan amshi : Talakawa,
    Jagora : Kahin da rana in yi ɗanwake gara tun da sahe in biɗo kanwa.

    A nan, Kamilu ya bi wani salo a saye domin yin roƙo. Domin da farko bayan ya yaba wa Baba Malam , sannan sai ya nuna ita kyauta idan za a yi da babban abu ita ce kyauta, wato idan za a ɗaure wani abu domin a yi kyautarsa da igiya, to muddin wannan abin mai yawa ne, to fa da lilo za a ɗaure, domin igiya ba za ta iya ɗaure shi yadda ake so ba, misali kuɗi. To wannan ɗabi’a ce ta Baba Malam Wali. Sannan sai ya nuna idan fa zai nemi wani abin da zai yi amfani da shi da safe, to tun rana ko dare zai nema domin da safe ya samu ya yi amfani da wannan abin. Sai a nan ya yi amfani da kanwa idan ana son yin ɗanwake.

    8. Waƙar Rtd. Hon. Adamu Dala Dogo

    Gindin Waƙa : Sannu Adam Dala Dogo.
    Jagora : Taimaka Difiti ka ban wata mota mai kyawu kalar birni,
    ‘Yan amshi : Sannu Adam Dala Dogo,
    Jagora : Saboda mahassada in na zo na wuce sai sui ta ruɗani,
    ‘Yan amshi : Sannu Adam Dala Dogo,
    Jagora : Kullum magana suke maja ma bai samu ba balle ni,
    ‘Yan amshi : Sannu Adam Dala Dogo,
    Jagora : Ni dai Allah na roƙa Tabaraka ba gunki na roƙa ba,
    ‘Yan amshi : Sannu Adam Dala Dogo,
    Jagora : Dubban jama’a muna sai kai,
    ‘Yan amshi : Bana ma mun nemi alfarma Difiti ka wuce muna fata.

    Jagora : Da sanda muna qanana muna tashe tsaba muke nema,
    ‘Yan amshi : Sannu Adam Dala Dogo,
    Jagora : Amma kuma yau a tashen da za mu yi Toyota muke nema,
    ‘Yan amshi : Sannu Adam Dala Dogo,
    Jagora : Difiti bari dai na zo kusa in zauna dan in kwatanta ma,
    ‘Yan amshi : Ɗan duƙununu,
    Jagora : Sai an ba shi,
    ‘Yan amshi : Ba ya tashi,
    Jagora : Sai da tsaba,
    ‘Yan amshi : Kamilu kai fa?,
    Jagora : Sai an ba ni,
    ‘Yan amshi : Kai ma ba ka tashi, × 4
    Jagora : Sai da mota, × 4
    ‘Yan amshi : Sannu Adam Dala Dogo,
    Jagora : Dubban jama’a muna sai kai,
    ‘Yan amshi : Bana ma mun nemi alfarma Difiti ka wuce muna fata.

    Idan aka lura da waɗannan ɗiya biyu da suka gabata, za a iske nan ma Kamilu Almajirin Mawaƙa ya yi roƙo, roƙon kuwa a fili; inda ya nemi a saya masa mota kai tsaye.

    A wannan salo, ya bayyana ƙarara nau’in motar da yake so, wato nau’in motar da ake shiga a birni, sai kuma ya bayyana dalilansa na neman mota. Idan muka koma ga ɗa na gaba, sai kwatanta abin da suke roƙa a yayin wasan tashe , kuma har ma ya kawo ɗaya daga cikin wasannin, wato wasan Ba Ma Tashi . Amma shi a nan, sai ya bayyana abin da yake so, wato mota, kuma ma sai ya bayyana ƙirar motar da yake so Toyota. A lura, a nan Kamilu ya haɗe wasanni guda biyu wuri ɗaya, wato ‘Ɗan duƙununu’ da tashen ‘Ba na tashi’, waɗannan tashe ne guda biyu mabambanta, amma sai ya haɗe su a matsayin tashe guda.

    9. Waƙar Hon. Alhaji Shu’aibu Ɗanladi Hamza

    Gindin Waƙa : Sai Baba Shu’aibu mun gamsu.
    Jagora : Jamilu zan kira Cross Fire zauna daram ka ƙyale sokaye,
    ‘Yan amshi : Mu dai ba za mu fasa canji ba,
    Jagora : Jamilu Rabbana ya kare ka bar banza da shi da ɓallaye,
    ‘Yan amshi : Mu dai ba za mu fasa canji ba,
    Jagora : Akwai batu da ni da kai babba Jamilu dan ka ba ni filaye,
    ‘Yan amshi : Mu dai ba za mu fasa canji ba,
    Jagora : Addu’a nake gami da fata Jamilu ban so ka bar ni ‘yamti ba.
    ‘Yan amshi : Sai Baba Shu’aibu mun gamsu,
    Jagora : Guru Central ka zo ka gyara ta,
    ‘Yan amshi : Wuce mu bi ka 2011 ba za mu fasa canji ba.

    Jagora : Na gai da Nura sai Oga wataƙil Nura za ya duba ni,
    ‘Yan amshi : Mu dai ba za mu fasa canji ba,
    Jagora : Domin kwa maigidan haya ne Nura yake ta ƙoƙarin ya ta da ni,
    ‘Yan amshi : Mu dai ba za mu fasa canji ba,
    Jagora : Jiya ma ya shigo da ‘yan sanda ya turo su zo su kama ni,
    ‘Yan amshi : Mu dai ba za mu fasa canji ba,
    Jagora :Wannan wata ga shi yai nisa kuma ga shi ban biya su wancan ba,
    ‘Yan amshi : Sai Baba Shu’aibu mun gamsu,
    Jagora : Guru Central ka zo ka gyara ta,
    ‘Yan amshi : Wuce mu bi ka 2011 ba za mu fasa canji ba.

    Idan aka bi waɗannan ɗiya guda biyu da suka gabata, za a ga Kamilu ya yi roƙo ta wasu sigogi mabambanta guda biyu.

    Siga ta farko, sai ya nemi Jamilu ya ba shi fili, amma fa idan har filin bai samu ba, to kar ya bar shi hannu-rabbana, ma’ana ya ba shi wani abu. A taƙaice a nan, ya bayyana abin da yake son a ba shi kyauta. A sigar roƙo ta biyu, sai ya nuna gida yake buƙata, domin a roƙon ya yi saye inda ya nuna masu gidan haya ne suka azazzale shi; har ta kai ga suna ta ƙoƙarin sai ya tashi la’akari da yadda suke takura masa.

    A nan, ya nuna cewa, bai biya su kuɗinsu na haya ba, to ka ga kenan idan ana son faranta masa, shi ne a ba shi gida ko a saya masa wani, ko kuma a biya masa kuɗin hayar gaba ɗaya.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Wayon Roƙo a Adabin Baka: Nazarin Roƙo a Wasu Waƙoƙin Kamilu Almajirin Mawaƙa wanda Ibrahim Baba (Nayaya) ya wallafa shi.

    Domin karanta bayani a kan Nazarin Yabo Daga Cikin Waƙoƙin Ala dannan nan.

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Nazarin Yabo Daga Cikin Waƙoƙin Ala

    Nazarin Yabo Daga Cikin Waƙoƙin Ala

    Jigon yabo baduniyen jigo ne da ke yaba mashahuran mutane irin su; sarakuna da shugabanni da attajirai da ma’aikata da manyan malamai da masu ilimi ko ba na addini ba ne.

    Irin waɗannan waƙoƙi sun fara samun tagomashi bayan zuwan Turawan Mulki, kuma sun haɓaka daga wajen 1950 zuwa yau. Waƙoƙin yabo suna taimakawa wajen ƙara wa waɗanda aka yi wa yabo gwuiwa don sun ƙara hoɓɓasa kan irin gudunmawar da suke bayarwa, domin yaba musu kamar ƙaimi ne wato ke nan an ga fa’ida da muhimmancin abin da suke yi.

    Waƙoƙin kuma sukan zama kamar matashiya ga wasu daban domin; sukan sa wasu mutanen su ma su tashi tsaye su yi hoɓɓasan da su ma; wasu mawaƙan za su gani su ma su yi musu irin waɗannan waƙoƙin yabo don yaba musu (Abdulƙadir, 2014: xx).

    Makaɗan baka na zamani sun yi waƙoƙin yabo da zuga daban-daban ga malaman Hausa musamman waɗanda suke jami’o’in ƙasar nan, inda waƙoƙin nasu suka fi karkata ga farfesoshi.

    A wannan gaɓa, za a bayyana wasu muhallai da aka yi irin wannan yabo ga wasu manyan malaman Hausa; sannan a yi ƙoƙarin yin sharhin wannan yabo a taƙaice.

    1. Salon Yabo ga Farfesa Ɗandatti Abdulƙadir

    Farfesa Ɗandatti Abdulƙadir yana cikin jerin malamai, masana kuma manazarta harshen Hausa ‘yan Ƙasa na farko, masanin harshe da adabi da al’adun Hausa ne. Gudumawarsa ba ɓoyayyiya ba ce; musamman a fagen waƙa.

    Makaɗi (Dr) Aminuddeen Ladan Abubakar (Alan Waƙa), ya yi wa Farfesa Ɗandatti waƙa, inda a cikin waƙar ya yabe shi a wasu baituka. Ga yabon da ya masa:

    G/Waƙa : Ɗandatti Dattijo Abdulƙadir Furofesa,
    Ka ji masu umarni da hani bisa sha’anin Allah,

    Misali na I

    Jagora : Ka ji masu umarni da hani bisa sha’anin Allah,
    Ɗandatti Dattijo Abdulƙadir Furofesa,
    Yau gida na malanta na taho za na yi wa ƙasida,
    Yau jinin sarakai zan waƙe in rubuta nashida,
    Bahari na taso in wa yabo masani na al’ada,
    Bahari na fannonin adabi na gama da al’ada,
    Ɗan Abdulƙadir Abdulƙadir ku min shaida,
    Baitukan na yo wa ne atafa ko in ce farar tsada,
    In zubo ɗiyan waƙa wane dirhami fagen tsada,
    In yabon Furofesa Abdulƙadir a ƙasida,
    Datti masu umarni da hani bisa sha’anin Allah.

    Idan aka dubi matashiyar wannan waƙa, za a ga Makaɗin ya buɗe waƙarsa da wannan ɗiya; wanda hakan ɗaya ne daga cikin salon da Alan Waƙa ke bi yayin buɗe waƙoƙinsa musamman waɗanda suka shafi yabo. A wannan ɗiya, ya yi yabo ga Farfesa Ɗandatti ta amfani da kalmomi da dama. Misali, ya ambace shi da “masu umarni da hani”, a nan sai ya yabe shi da wata kyakkyawar sifa ta koyarwa. Sannan ya ambace shi da “masanin al’ada”, da “bahari a fannoni”, ma’ana mutum ne wanda yake da ilimi a ɓangarori da dama, inda har ma ya keɓanci wasu ɓangarori, wato masanin adabi da kuma al’ada.

    Misali na II

    Jagora : Gaisuwa gurin Allah arraziƙi mai azirtawa,
    Mai aro na ilhama hikima kyauta gurin bawa,
    Taimake ni min lamun na zo a gare ka don ƙwawa,
    Zan yabon wurin jigon adabi mai hali na madalla.

    A wannan ɗiya na farko, bayan ya yi gaisuwa ga Allah da roƙon lamuni. Sai ya bayyana zai yi yabo ga “jigon adabi”. Jigo a nan, na nufin ginshiƙi, wato ginshiƙin adabi. Shi kuwa adabi sanannen abu ne ga masu nazari da ɗalibai.

    Misali na III

    Jagora : In ana dara dangi ai fid da uwa ake gefe,
    Yau uban iyaye ne na tashi yabo fa zan tsefe,
    In ana batu na sani Abdulƙadir ku kai gefe,
    Bahari fa kogi ne na masu iyo fa don Allah.

    A wannan ɗiya na uku, ya yabe shi ta hanyar ambatarsa da ‘uban iyaye’ da ‘kogi’. Uban iyaye na nufin kakan jikoki amma a fuskar ilimi. Sannan ya ambace shi da kogi, wato iliminsa yalwatacce ne ta yadda ganin ƙarshensa akwai matuƙar wahala.

    Misali na IV

    Jagora : Rukunin dukkan daraja da ke ɗaga martabar bawa,
    Ilimi da sarauta sai alatu halin bawa,
    Ka haɗa mu’amilla yakana mai izo gurin bawa,
    Babu wanda ɗan Audu bai taka ba ibadul Lah

    A wannan ɗiya na huɗu kuwa, ya yabe shi ta hanyar amfani da rukunan da suke sanyawa a yabi mutum, wato ilimi ko sarauta ko dukiya ko kuma wata kyakkyawar mu’amala ga mutane. To a nan, sai yake ƙoƙarin nuna cewa duk waɗannan dalilai da suke sanyawa a yabi mutum, to fa Farfesa Ɗandatti ya haɗa su.

    2. Yabo ga Farfesa Abdulƙadir Ɗangambo

    Farfesa Abdulƙadir Ɗangambo yana cikin rukunin ‘yan Ƙasa rukuni na uku a fagen Hausa, fitaccen masani ne a ɓangaren adabi da al’adu, musamman yadda ya zama manazarci mai son ganin an haɗa hanyoyin nazarce-nazarce su tafi bai ɗaya. Farfesa ya taimaka wajen samar da hanyar fiɗar waƙa, sannan ya fassaro kalmomin nazari tare da ƙirƙiro wasu. (Gusau, 2008: 56).

    (Dr.) Alan Waƙa ya gwangwaje Farfesa da waƙoƙi, cikin waƙoƙin an bibiyi guda ɗaya, sannan aka zaƙulo yabon da ya yi ga Farfesa.

    G/Waƙa : Garkuwar Adabin Hausa sannu Farfesa,
    Sannu Ɗangambo na taho in gaishe ka.

    Misali na I

    Jagora : Za ni hau sarari na yabo da baitukka,
    : In yabanta gwani turmi ma-sha duka,
    : Nemi Ɗangambo ka ji rairayar waƙa,
    : Rariyar adabi ce matankaɗar waƙa

    A wannan ɗiya, ya yabe shi da kalmar ‘gwani’, wato ƙwarrarre a kan abu, sannan kuma mai juriya. Har wa yau, ya yabe shi ta hanyar gwarzantawa wajen nuna cewa dukkanin abin da ya shafi adabi, to shi yake tantancewa.

    Misali na II

    Jagora : Maliyar malala dole sai fa an sha ka,
    : Ko cikin birni ko a sha a ƙauyuka,
    : Ga ni nai girshe ginshiƙi fa zan waƙa,
    : Matsirar masana Hausa sai fa labbaika.

    A wannan ɗiya, Makaɗin ya yi ƙoƙarin amfani da salon kambamawa ga Farfesa a yayin yabo, sannan sai ya ƙara bayyana cewa shi Farfesa Ɗangambo tushe ne na masana Hausa. A taƙaice a nan, ya yabe shi da kasancewarsa mai yalwar ilimin Hausa, sannan kuma tushe ga dukkanin wani masani ga Hausa.

    Misali na III

    Jagora : Na kira ka daƙu a fagen nazar naka,
    : Hausa dai wannan sai in ce a kalle ka,
    : Za a gan ta tafe a ƙasan ƙafafunka,
    : Godiya Bakano ke ta yi da samun ka.

    A nan kuwa, ya yabe shi ne ta hanyar kwatantawa, inda a layin farko na ɗa, sai ya ambace shi da ‘daƙu ‘. To a fagen ilimi ma ya ambace shi da ya san komai ko ya taɓa kowane ɓangare na ilimi.

    Masali na IV

    Jagora : Bishiyar rimi ko na nesa ya ganka,
    : Mai firirita sai in ce ki yai kanka,
    : Haka nan Jamus na ga ɗalibai naka,
    : Da na je Oxford na ga ɗalibai naka.

    A wannan ɗiya ma, sai ya sake yabonsa ta hanyar kwatantawa, inda ya kamanta shi da ‘Bishiyar Rimi’. Rimi wata ƙatuwar bishiya doguwa mai kamar kuka, tana da ‘ya’ya da ake samun audugar da ake katifa da matashin kai da ita (CNHN, 2006: 372).

    Domin ya bayyana faɗaɗuwar ilimin Farfesa Ɗangambo da yadda ya kewaya ko’ina ta yadda kuma kowa na iya kwankwaɗa daga ciki, sai ya kwatanta shi da wannan bishiya. Abin nufi, duk yadda mutum yake son bincike a ɓangaren Hausa, a ko’ina yake, to fa sai ya ci karo da ilimin Ɗangambo a wannan fage. Domin ya tabbatar da abin da ya faɗa, sai ya bayyana cewa a Jihar Oxford ma ya ga ɗaliban da Farfesa Ɗangambo ya koyar.

    Masali na V

    Jagora : Malami tammi masani na fannoni,
    : A adon harshe zai zame maka tsani,
    : A fagen tarke ka biyo shi ladani,
    : Ya faɗa ka faɗa ya sanar ka allonka.

    Jagora : Yadda Jami’atu ke alam ya shaide ka,
    : Ba ka satifiket wanda ke alamta ka,
    : Haka nan Ala ke alam na shaidarka,
    : In kiraye ka gwargwadon nagartarka.

    Jagora : Ɗauraya ta fadon feɗiya a kan waƙa,
    : Ka yi rabbe-rabben Adabi na Hausarka,
    : Kai Kitsen Rogo ƙirƙira ta kwanyarka,
    : Godiya wannan ya ci ai yi ma waƙa.

    A waɗannan ɗiya uku da suka gabata, Makaɗin ya yi masa yabo ta hanyar tabbatar da ilimi da nagartarsa, ta yadda har Jami’a ta ba shi shaidar yabo ta satifiket, wanda samuwar wannan satifiket ne ya sanya shi kuma Makaɗin ya yabe shi gwargwadon wannan nagarta tasa. Sannan sai ya bayyana wasu ayyuka cikin muhimman rubuce-rubucensa da ya yi.

    3. Salon Yabo ga Farfesa Ahmadu Bello Zaria

    Farfesa Ahmadu Bello Zariya shi ma na cikin ‘yan Ƙasa rukuni na uku a Hausa, masani ne kuma manazarci a ɓangaren Harshe. Farfesa Ahmadu Bello ya yi rubuce-rubuce da dama a ɓangaren harshe; waɗanda suka fi karkata ga Nahawu da ƙa’idojin rubutun Hausa da Arulin Hausa da kuma kare-karen harsuna.

    Makaɗi (Dr.) Alan Waƙa ya yabe shi musamman kasancewarsa ƙwararre a fagen Arulin Hausa. Ga wasu baituka da ya masa a wata waƙa.

    G/Waƙa : Ahmadu Bello Farfesa kai ne mizanin Arulinmu,
    A.B.Z Furofesa tartibi na awo a waƙenmu.

    Misali na I

    Jagora : Ahmadu Bello Farfesa ABZ babban kadarkonmu,
    Ahmadu Bello Farfesa gwadabe ɗoɗar na sani namu,
    :Farfesa hanyar ilimi ne a waƙenmu,
    :Farfesa alfijiri mai haska harkarmu,
    ABZ Furofesa mudu na awon sha’irai namu,
    :hanyar gane dukka lagonmu,
    :hanyaar turke a ƙasidarmu,
    :hanyar fiɗar abbiyat namu.

    Makaɗi Alan Waƙa ya buɗe wannan waƙa tasa da waɗannan ɗiya, inda a cikin su ya yi amfani da wasu kalmomi domin yabo na sani da maƙura a ilimi ga Farfesa Ahmadu Bello. Kalmar ‘kadarko’ na da ma’anoni biyu, amma a nan mun kalli ma’anar wata ‘yar ƙaramar gada wadda yawanci ake yi da katako a kan hanya don kwararar ruwa (CNHN, 2006: 223). To a nan, an yi amfani da ita ga Farfesa Ahmadu Bello a matsayin babba duk da cewa ƙarama ce, mai makon ruwa da take kwarararwa, to a wurin Farfesa sa kuwa hanya ceta kwararar da ilimi.

    Ambatarsa da gwadabe ‘godabe’ kuwa, an siffanta shi da babbar hanya ta sani ga ilimin waƙa. Sannan Makaɗin ya ƙara yabon shita hanyar siffanta shi da alfijir, wanda alfijir wani haske ne da ke fara fitowa domin yaye duhu. To haka shi ma hasken ilimi ne da yake yaye duhun jahilci. A wannan ɗiya dai, duk ya yabe shi da ilimi da sani a tsarin waƙa.

    Misali na II

    Jagora : Ya Jabbaru Ƙahharu mai ikon duka lammura namu,
    : Ban hikima da tarbiyya za ni yaba wa gwaddabe namu,
    : Za ni yabon Imaminmu Limamin da ya zamma gatanmu,
    : Shehun Shehunai namu Ahmadu Bello qafar sani namu,
    : Madalla da jagora mai fitilar haskawa dubanmu.

    A wannan ɗiya kuwa, ya ambace shi da imam, wato ja-gaba. Sannan ya ba shi babban suna na malamin malamai, wanda idan aka ce ‘shehi’ babban malami ne, to shi kuma sai ya ambace shi da ‘shehun shehunai’.

    Misali na III

    Jagora : Amma na sani tunda na yi tawassil gunsa mai iko,
    : Zai fisshe ni jin kunya inda na yo lam’a da mamako,
    : Baiwa ta Jibulliya ba ta tsumayi ba ta yin dako,
    : Allah ba ni ilhama lamunce Ka saka ni nai ƙarko,
    : Za ni yabon madubinmu masanin waƙa har irin tamu.

    A wannan baiti na huɗu, ya yabe shi da kalmar madubi masani. ‘Madubi’ na da ma’anoni da dama, amma a nan za mu ɗauki ma’anarsa ta ‘ƙarau da aka shafa wa wani abu mai ɗaukar ido da yake nuna surar duk abin daya bayyana a gabansa; mutane kan yi amfani dashi domin duba fuskokinsu’. To shi ma Farfesa a fagen ilimi, an siffanta shi da madubi ta yadda suke duba zuwa ga rumbun iliminsa a game da waƙa.

    Misali na IV

    Jagora : Na yi shiru na tsahirta na gyaɗa kai wayyo ni wayyo ni,
    : Ya zan su fahimce ni na ga kamar malam suka riƙe ni,
    : Mai nazari da mai waƙa ba ɗaya suke ba ko a mizani,
    : Ba lalle ga mai waƙa yai nazari balle ya hau tsani,
    : Ko bishiyar Galadanci sai Ahmadu AB madubinmu.

    Bishiyar Galadanci, ita ce bishiyar li’irabi ta jimla a Hausa. Wannan bishiya aba ce mai matuƙar muhimmanci a tsarin jimlar Hausa. Akan ɗauki jimla a yanka, a feɗe ta sannan a rataye ta a bishiyar. Farfesa M.K.M Galadanci ɗaya ne cikin malaman Farfesa Ahmadu Bello Zariya, wanda ya yi littafin kan wannan tsari na bishiya, duk da wahalar hawanta. To Farfesa Ahamdu ya naƙalci hawa wannan bishiya domin rataye jimla.

    4. Salon Yabo ga Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau

    Farfesa Sa’idu Gusau na cikin ‘yan Ƙasa rukuni na huɗu, masani ne manazarci da ya yi rubuce-rubuce a kan abin da ya shafi adabi da al’adu, sai dai ya fi karkata zuwa waƙar baka. Farfesa Gusau ya bayar da gagarumar gudumawa a fagen waƙar baka, ya fito da hanyoyin nazarin waƙar baka, ba ya ga gata da ya mata na bincike da lalubo tushenta.

    Aminuddeen Ladan Abubakar (Alan Waƙa) ya yi wa Farfesa Gusau waƙoƙin yabo da dama, amma a wannan takarda an bibiyi waƙa guda ɗaya sannan aka zaƙulo wurin da ya masa yabo, wato waƙar ‘Shehin adabi da al’ada’. Ga wasu ɗiya da ya yi yabo a cikin su:

    G/Waƙa : Shehin adabi da al’ada,
    : Sa’idu Gusau Furofesa mafakar mazaje

    Misali na I

    Jagora : Malam na Gusau kadarko ne,
    ‘Y/amshi : Ɗan maƙi garaji,
    Jagora : Tsanin ilimi adibi ne,
    ‘Y/amshi : Namijin mazaje,
    Jagora : Kambin adabi na ilmi ne,
    ‘Y/amshi : Ɗan maƙi garaje,
    Jagora : A yau a fage karimi ne,
    ‘Y/amshi : Namijin mazaje,
    Jagora : Ya zam fitilar adibbai ne,
    ‘Y/amshi : Ɗan maƙi garaje,
    Jagora : Farfesa Gusau gadon bai ne,
    : Mabiyar mazaje.

    A wannan ɗa, Makaɗi Alan Waƙa ya yi wasu kalmomi ga Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau, waɗanda kalmomi ne da suka bayyana yalwar ilimi da yadda shi Farfesa Gusau ya zama mai yi wa ilimi hidima a kowane ɓangare. Cikin kalmomin da ya yi amfani da su wajen wannan yabo akwai kalmar ‘kadarko’.

    Kalmar ‘kadarko’ na da ma’anoni biyu, amma a nan mun kalli ma’anar wata ‘yar ƙaramar gada wadda yawanci ake yi da katako a kan hanya don kwararar ruwa (CNHN, 2006: 223). A nan, Alan Waƙa ya yi amfani da kalmar, maimakon ruwa da take kwarararwa, to a wurin Farfesa Gusau hanya ce ta kwararar da ilimi.

    Har wa yau, ya sake yabon shi ta hanyar kambama iliminsa da cewa ‘Tsani ilimi’.

    Tsani shi ne wani abu da za ka taka domin ya sada ka da wani abu; wanda ba za ka iya kai wa gare shi ba, dole sai ta wannan hanya. A nan, sai ya yabe shi ta hanyar kwatantawa, inda ya nuna Farfesa Gusau tsani ne ga wanda yake son ilimi, wato duk wanda ke son ilimi, to ga wanda zai haxa shi da ilimi, ma’ana zai karantar da shi ilimi.

    Kambi na nufin hula ta zinare da sarakunan Turai kan sa. Ko kuma wata lamba ta girmamawa (CNHN, 2006: 229). A nan, sai ya kwatanta Farfesa da kambi, amma a fagen ilimi, domin a fagen ilimin, wani mutum ne da ake girmamawa.

    A ci gaba da yabon, sai ya bayyana shi da ‘karimi’, wato mutum mai yawan kyauta.
    Alan Waƙa, ya ci gaba da yabo, inda ya ambaci Farfesa Gusau da ‘Fitilar adibbai’. ‘Fitila’ na nufin abar da ake haskaka wuri ko ɗaki da ita (CNHN, 2006: 143). A nan, sai ya bayyana Farfesa Gusau da cewa fitilar adibbai ne, wato shi ne ke haskaka wa duk wani adibi domin ganin hasken ilimin adabi.

    Domin ƙara fito da wani nauyi na ilimi da ke kan Farfesa Gusau, sai Makaɗin ya ambace shi da ‘Gadon bai’. A nan, kalmomi guda biyu ne aka mayar da su ta hanyar samar da harɗaɗɗen suna, wato ‘gado’ da ‘baya’. Amma a ginin kalmar, sai aka yi gutsirewa, wanda sanannen abu ne a tsarin nazarin kalma ko ilimin kalma, wato maimakon a ce ‘gadon baya’, sai a ce ‘gadon bai’, ko dai don shi mai waƙa ya sami kalmar ta shiga waƙarsa, ko kuma domin taƙaita kalmar. Gadon bai da ya ambace shi da shi, yana nufin shi sha-nauyi ne a fagen ilimi.

    Misali na II

    Jagora : Ruhin adabi da al’ada,
    ‘Y/amshi : Ɗan maƙi garaje,
    Jagora : Ƙigon adabi da al’ada,
    ‘Y/amshi : Namijin mazaje,
    Jagora : Jigon adabi na al’ada,
    ‘Y/amshi : Ɗan maƙi garaje,
    Jagora : Domin ka a yau muke tsada.

    Domin bayyana ƙarfin ilimin Farfesa Gusau a ɓangaren adabi da al’ada, sai ya yabe shi da ‘ruhin adabi da al’ada’, wato rai ne shi a adabi da al’ada, ta yadda idan babu shi; to babu waɗannan abubuwa biyu. Sai kuma ya yi masa kirari da irin kirarin da ake yi wa sarki ko ango, amma shi ya keɓanta shi da adabi da al’ada, wato ‘ƙigon adabi da al’ada’. Sannan kuma sai ya yabe shi ta hanyar ambaton sa da ‘jigon adabi na al’ada’. Imma dai jigo da ma’anar shugaba, ko kuma jigo da ma’anar itatuwan da ake kafawa su tallabi gugan ban ruwa (CNHN, 2006: 216). To amma shi a nan, shi ake kafawa domin a tallafi ilimi, ma’ana tsayuwarsa ce ke samar da wannan ilimi.

    5. Salon Yabo ga Farfesa Salisu Ahmed Yakasai

    Farfesa Salisu Ahmed Yakasai sanannen masani ne a ɓangaren harshe, ya yi rubuce-rubuce da dama waɗanda suka fi karkata ga kare-karen harshen Hausa, harsunan da ke maƙwabtaka da Hausa. Haka zalika ya yi rubutu a ɓangaren tatsuniya. Makaɗi (Dr.) Aminuddeen Ladan Abubakar ya yi wa Farfesa waƙoƙi, cikin waƙoƙin mun nazarci waƙa guda, inda muka ciro yabon da ya yi masa. Ga irin yabon nan biye:

    G/Waƙa : Jagoran ilimi Salisu ɗan Amadu Furofesa,
    : Darajar ilimi Salisu jigo na walwalar harshe.

    Misali na I

    Jagora : Ga ruhin ilimi Salisu in dai ana batun harshe,
    : Ga rayin ilimi Salisu tsari na sautukan harshe,
    : Ga gidan ilimi al’umma sauti na samuwar harshe,
    : Ginshiƙin ilimi Salisu gado na sarrafar harshe,
    : Falsafar ilimi Salisu na ɗaufare a kan harshe,
    : Dakata ka jiya Salisu yau zan rawa rawar harshe,
    : Ka yi min uziri Salisu rumbunka zan shige harshe,
    : Zan yi ma tage Salisu jigo na walwalar harshe.

    Kamar yadda ya gabata a bayanan sama, mafi yawa ire-iren waɗannan waƙoƙi Makaɗi Alan Waƙa kan buɗe su da wasu ɗiya, sannan daga baya gindin waƙa da amshi ya zo. A wannan matashiya, ya buɗe da yabon Farfesa Salisu Ahmed Yakasai inda ya bayyana shi da ‘ruhin ilimi’, da ‘rayin ilimi’ wanda dukkaninsu ma’ana ɗaya suke ɗauka. Sannan sai ya ambace shi da ‘gidan ilimi’ da ‘ginshiƙin ilimi’.

    A waɗannan yabo da ya yi ta hanyar gwarzantawa, ya yi ƙoƙarin bayyana fagen da Farfesa Yakasai ya fi shahara, wato fagen ilimin harshe. Sannan a layi na ƙarshe, sai ya bayyana shi da ‘jigo na walwalar harshe’. Wannan sai ya ƙara fito da fagen da Farfesa Salisu Yakasai ya fi shahara.

    Misali na II

    Jagora : Jami’a na nufa aradu wanshekare batun harshe,
    : Jami’ar ilimi zan je ga tushe maɓuɓɓugar harshe,
    : Jami’ar su Kware autansu jika ga Shehu kau reshe,
    : Ga Baba Gwani Salisu Amadu maigidan harshe,
    : Walwala nika so Salisu za mu yi a kan batun harshe.

    A wannan ɗiya kuwa, ya kira shi da ‘Baba’ da kuma ‘gwani’. Wato uba ne a ɓangarensa na harshe, sannan gwani ne ta yadda ya san wannan fage sosai da sosai.

    Misali na III

    Jagora : Sanadin su uba Salisu ɗan Amadu Furofesa,
    : Daraja tasa ce ta hana Ala ya rinƙa Ingausa,
    : Sababin ilimi wanda nake bibiya a rumbunsa,
    : Daraja tasa ce ta hana Ala ya rinqƙa Arausa,
    : Vurbushin ilimi ya ba ni dama ta walwalar harshe.

    Domin ya ƙara nuna gogewar Farfesa Salisu Yakasai a wannan fage na harshe, sai ya bayyana wa duniya ta hanyar yabo cewa, shi kansa idan ba domin Farfesa Salisu ba, da ba zai rinƙa tafiyar da waƙarsa da tatacciyar Hausa ba, sai dai ya rinƙa haɗawa da Ingausa, wato ya rinƙa ɗaukar wasu kalmomi na Turanci yana kiran su da Hausa, ko kuma Larausa, shi ne Hausantar da kalmomin Larabci. To amma albarkar karatun da ya samu a rumbun Farfesa Salisu, sai ya san abubuwa da dama, kuma ya iya tantance kalmomi.

    Misali na IV

    Jagora : Zan yabon ka gwani ko da a kan bishiya a kan reshe,
    : Zan yabanta gwani ba zan amai ba balle fa in lashe,
    : Ko in na sarari ko ko ina a hukunce ga harshe,
    : Za a ji ni da kai Salisu ƙaunarka na cikin tushe,
    : A jinni take ma Salisu tun fil’azal cikin tushe.

    Duk domin dai gwarzanta Farfesa Yakasai, sai ya ci gaba da yabonsa da kuma bayyana cewa ko a ina zai iya yabon sa, sannan ƙaunarsa daman can akwai ta tun a tsatso.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Masana A Bakin Makaɗa: Nazarin Yabon Masanan Hausa A Cikin Wasu Waƙoƙin Aminu Alan Waƙa wanda Ibrahim Baba (Nayaya) ya wallafa shi.

    Domin karanta cikakken bayani akan Taƙaitaccen Tarihin Samuwar Waƙoƙin Baka a Ƙasar Hausa danna nan

    Edita:@rumasau-kallamu

  • Makaɗi a Sarrafa Harshen Waƙa

    Makaɗi a Sarrafa Harshen Waƙa

    Kamar yadda aka yi bayani a baya, makaɗi yana amfani da gurbin furuci na gaɓoɓi a cikin kalmomi da jimloli ya samar da zubin waƙa.

    Ta haka makaɗi yake sarrafa harshe, ya harhaɗa ƙwayoyin sauti da amon kiɗa, ya saƙa saɗaru cikin ɗiya, ya rera wa masu ji da sauraro saƙonni masu ɗaga hankali, masu cika fuska, masu daɗi, masu garɗi masu shaguɓe da baƙar magana, masu fallasa muruwa da soke daraja, masu barkwanci, masu tumasanci, masu nuna kasawa, masu ƙasƙantawa da sauransu waɗanda kuma suke yi domin manufofi mabambanta.

    A wajen ɗorawa da tafiyar da harshen waƙa, makaɗan baka na Hausa suna bin hanyoyi iri-iri waɗanda muhimmai daga cikinsu suka haɗa da:

    4.1 Harshe na Nuna Hikima

    Hikima a harshe ta shafi iya magana bisa dacewa da manufa ba tare da tsawaitawa ba. Hikima kuma takan danganci ƙarfin ƙwaƙwalwa ko ƙarfin basira wajen gina zance mai ma’ana tare da ayyana manufa daga mutum ɗaya-ɗaya ko al’umma. A wani bi ma manufar hikima ba takan bayyana a sarari ba, takan zama a sakaye ta yadda a kullum za a dinga ƙoƙarin fahimta ko ganowa.

    Hikima kuma takan zama yin wani abu wanda zai birge mutane (CNHN, 2006: 200). Yahya (2012: 238) shi kuma yana ganin hikima wadda ta jiɓinta da harshe takan shafi hanya ko matsalolin rayuwa ta bayyana su cikin zaɓen kalmomi da za su ɗora a kan zance mai armashi.

    Makaɗan Hausa sukan yi amfani da harshe mai hikima domin sakaya zance ko su kaifafa tunani ko su zurfafa tunani ko su taƙaita ma’ana ko su saka galmi a zance ko su kawar da gwangwani ko su saka gwangwani ko su yi barkwanci ko su dagule tunani ko su ƙawata rai ko su saka jin daɗi ka su burkuta zuciya ko su tayar da hankali da sauransu.

    Sau da yawa kuma makaɗan sukan saka wasu maganganu na hikima ko azancin harshen Hausa kamar karin magana da baƙar magana da ba’a da shaguɓe da zambo da habaici da kirari da makamantansu waɗanda makaɗan suke ƙawatawa tare da taƙaita tunaninsu a waƙoƙinsu.

    Haka kuma makaɗa sukan yi amfani da dabaru na jan hankali waɗanda suke raɗe da hikima cikin kwatantawa da ƙarfafawa da jaddadawa da shirɓacen kalmomi ko na ma’anoni duka a mabambantan zubi na ɗiyan waƙoƙinsu. A wannan ɓangare, makaɗan sukan yi kamantawa da siffantawa da jinsintarwa da alamtarwa da kinaya da gamin bautar kalmomi da jaddadar ƙarfafawa da zubi mai jan rai da baubawan burmi da sauransu (Ɗangambo, 2007: 43-54).

    Misali, idan aka dubi waƙar Shata ta ‘Sani Audi’ da ta ‘Habu na Habu’ da ta ‘Ummaru ɗan Ɗanduna na Gwandu’, za a ga Shata ya sarrafa hikimomin harshe iri-iri cikin mabambantan manufofi.

    Tabbas harshe na nuna hikima a wajen ciro kalmomi na gwaninta da kwatance na ayyana wani yanayi ko siffa ko hali za a iya ganin misalin haka a wannan ɗa na waƙar ‘Gwabron giwa uban Galadima ɗan Sambo, ginshimi, Ginshiƙan Amadu na Maigandi kai a uban Zagi’:

    Jagora: Ɗiyan Alibawa ku hanƙure,
    ‘Y/Amshi: Don Allah ya yo uban zagi, x2
    : Domin kura ta wuce,
    : Ana ɓacin laka kamar ita,
    Jagora: Domin,
    ‘Y/Amshi: Kura ta wuce, ana ɓacin laka kama ita.
    Jagora: Ko jiya na iske gamdayaƙi da tuji,
    : Sun iske jinjimi,
    : To sun ko mirɗa gardama,
    : Sun iske su bubuƙuwa ruwa,

    ‘Y/Amshi: Dannan ni kau ina gaton gaɓa,
    : Sai niƙ ƙwala gaisuwa,
    : Su ko sun daƙile ni duk,
    : Ni ko niƙ ƙara gaisuwa,
    : Dannan gurbin da a cikin gurbi,
    : ya amsa gaisuwa.
    Jagora: Dannan sai jinjimi da yas sullata,
    : Yas suntule su dut,
    ‘Y/Amshi: Shi ko tuji da ad da girman baki,
    : Yak kwashe jinjimi,
    : Dannan bubuƙuwa da tur rura,
    : Tag gangame su dut,
    : Rannan nis san duniyag ga,
    : Komina ne wani mayin wani,
    Jagora: Rannan,
    ‘Y/Amshi: Nis san duniyag ga
    : Komina ne wani mayin wani.
    (Gusau, 2009:145)

    4.2 Harshe na Nuna Fasaha da Nagarta

    A Ƙamusun Hausa an bayyana fasaha ita ce gwaninta ko ƙwarewa (CNHN, 2006:136). Ita kuma kalmar nagarta tana nufin kyawun abu ko ingancinsa (CNHN, 2006: 355).

    Makaɗan baka na Hausa sukan yi amfani da harshe mai nuna fasaha ta fito da gwanintar abu ko ƙwarewar wani abu kan wani ko kuma harshe mai fitar da nagarta a kan kyawo ko inganci na wani abu. Yanayin harshe na nuna nagartar abubuwa a rayuwa ya mamaye zubi na waƙoƙin baka na Hausa har ma wasu daga cikin makaɗan sukan bayyana nagarta da zubi na fasaha na waƙoƙinsu.

    Bawa Namiji Jega a wani ɗan waƙa ya tabbatar da fasahae harshe ita ce ke gaba, mai yin jagoranci a wajen shiryawa da rera waƙa mai ma’ana, mai garɗi.

    Dubin abin da yake faɗa:

    Jagira: Kalangu na da daɗi,
    : In ga fasaha ta yi.
    ‘Y/Amshi: Shalla Barayar Kada,
    : Fadama da sanyi take.
    (Bawa Namiji Jega: Waƙar ‘Shalla Barayar Kada’)

    Ibrahim Narambaɗa ya nuna fasaha tana daga cikin hanyoyin sarrafa harshe da ke nuna darajar makaɗi a fagen waƙa. Yana cewa:

    Jagora: Ai ba a gama ni da yaro,
    : Na san yaro bai yi mƙamina ba,
    : Ka ku gama ni da yaro,
    : Na san yaro bai yi zalaƙata ba,
    : Ka ku gama ni da yaro,
    : Na san yaro bai yi fusahata ba,
    : Ka ku gama ni da yaro,
    : Ƙaryab banza,
    : Yaro bai kai inda Narambaɗa,
    : Mai tabarukun Sarki,
    : Gogarman Tudu jikan Sanda,
    : Maza su ji tsoron ɗan mai Hausa.
    (Gusau, 2003: 74).

    Fasaha da nagartar harshe sun bayyana a zubin wannan ɗa na waƙar ‘Abin duniya tahowa na’:

    Jagora: Na ji an ce a daina ma al’ada,
    : Al’ada tana nan tana aiki,
    : Karatun mutum bai wuce salla,
    : Dole sai an yi Alhamdu Lillahi,
    : To, ashe ko kana nan ga al’ada,
    : Kowaɗ ɗauki kayan da bai ima,
    : Bawa tilas ya dawo ya yasshe su,
    : Abin duniya mai tahowa na,
    : Ran da duk ya wuce sai ga labari,
    : Sai ga labarin nan a tashe shi,
    : Wane ai yayi irin tashi.

    Jagora: Rigimar mutum dut ta rai nai ta,
    : Ran da dut babu rai tashi ta ƙare,
    : Kur’ani babu gamtsi ciki,
    : To Hadisi da ko ba a ruwaito ba,
    : Abin ga ko ko zari na mu tanye ku,
    : Abin duniya mai tahowa na,
    : Ran da duk ya wuce sai ga labari,
    : Sai ga labarin nan a tashe shi,
    : Wane ai yayi irin tashi.
    (Bawa Namiji Jega: Waƙar ‘Abin Duniya’)

    Daga cikin waƙoƙin da makaɗan Hausa suka aiwatar masu ɗauke da harshe na fasaha da nuna nagarta akwai waƙar ‘Ɗan’adam’ da waƙar ‘Aiki duka aiki ne’ da waƙar ‘Tica uban karatu’ na Ɗanmaraya Jos da waƙar ‘Mai Martaba ɗan Bayero’ da waƙar ‘Kano garin saye da sayarwa’ da waƙar ‘Na ɗauki angara na saƙala’ na Aminu Ladan Abubakar, Alan Waƙa da makamantansu.

    4.3 Harshe na Nuna Yanayi

    A luggance kalmar yanayi tana iya zama hali irin wanda ake ciki, kamar damina ko sanyi ko zafi ko bazara da sauransu (CNHN, 2006:478). A ma’ana ta fannu, yanayi yakan nufi bayyana halayyar abu ko halin aukuwar abubuwa ko nuna kamanni na abubuwa (Gusau, 2008:463).

    Sau da yawa, makaɗan Hausa sukan zaɓo kalmomi su sarrafa su a waƙa su kuma dace da halayyar aukuwar abubuwa da wuri da lokaci da fasalin abu. A waƙar ‘Haji Garban Bichi ɗan Shehu’, Shata yana gaya wa Alhaji Garban Bichi game da harkokinsa na ciniki cewa:

    Jagora: kaka ta matso uban Nura,
    : Gyaɗa ta fara jar fata,
    ‘Y/Amshi: Haji Garban Bichi ɗan Shehu.

    Jagora: Auduga ta fara kitse Garba,
    : Gyaɗa ta fara jar fata,
    ‘Y/Amshi: Haji Garban Bichi ɗan Shehu.

    Jagora: Gabas riƙa yamma ta kama,
    : Gusun riƙa arewa ta samu,
    : Baba gabas riƙa na yamma sun samu,
    : Gusun riqa arewa ta kama,
    :Kaka ta yi uban nura,
    ‘Y/Amshi: Haji Garban Bichi ɗan Shehu.
    (Gusau, 2009:340-341)

    4.4 Harshe na Gwagwarmaya

    A wata ma’ana an nuna gwagwarmaya tana nufin yin fama ko karawa da wani (CNHN, 2006: 180). Wata ma’ana ta gwagwarmaya takan ƙunshi bijirereniya ko fanɗarewa ko kangara. A gwagwarmaya akan ƙarfafa hanyoyin ƙwatar rayuwa kamar neman abinci ko kiyaye haƙƙi ko neman waraka daga wata cuta ta bayyane ko ta ɓoye ko kishin ƙasa da al’adu ko kishin addini ko makamantan waɗannan hanyoyi.

    Wasu makaɗan Hausa sukan shirya waƙoƙi bisa harshe na gwagwarmaya da ke neman daidaito a rayuwar al’umma. Wasu daga cikin waƙoƙin baka waɗanda aka shirya su ta harshen gwagwarmaya sun haɗa da waƙar ‘Buɗaɗɗiyar Wasiƙa’ da ta ‘Raba Gardama Ɗansani’ da ta ‘Alƙalami ya zarce takobi’ da waƙar ‘Jami’a Gidan ban Kashi’ 1-3 na Aminu Ladan Abubakar, Alan Waƙa.

    Akwai waƙar ‘Shegiyar uwa mai kashe ‘ya’yanta PDP’ ta Haruna Aliyu Ningi da Waƙar ‘Haɗa kan Nijeriya’ ta Musa Ɗanba’u da waƙar ‘Babbar Ƙasar Shehu Ɗanfodiyo’ ta Alhaji Mamman Sarkin Taushin Katsina da waƙar ‘Haɗa kan Nijeriya’ ta Ɗanmaraya Jos da waƙar ‘Allah rayan jihar Katsina’ da ta ‘Muriki Abincinmu’ na Gargajiya na Alhaji Mamman Shata Katsina da makamantansu.

    4.5 Harshe na Faɗakarwa

    Kalmar faɗakarwa tana nufin faɗakarwa ko luraswa ko yin nuni ko ishara domin a lura. Kalma ce wadda take daga faɗaka wato farka ko lura ko kula (CNHN, 2006:129). Maganar Hikima wadda Hausawa suke cewa, ‘nuni cikin nishaɗi’ tana nufin yin faɗakarwa cikin wata siga ta raha ta amfani da harshe mai karsashi, mai daɗin ji, mai motsa rai.

    A faɗakarwa ana tunatar da mutum ne a kan waɗansu al’amuran rayuwa waɗanda suke yi masa tambihi ya aiwatar da su ko kuma ya guje musu. Yawanci a faɗakarwa akan ƙara tunasarwa ne, ko a lura da wasu abubuwa, ko a janyo hankali zuwa gare su (Auta, 2008:75-76).

    A harshen waƙa makaɗan Hausa sukan yi faɗakarwa a kan wasu abubuwa na al’umma domin su tunashe su, su lurar da su ta amfani da kalmomi na nasiha da wayar da kai da jawo hankali, musamman akan yin aure da neman aure da zaman aure da zawarci da haƙƙoƙin iyaye da na ‘ya’ya da yaran gida da faɗakar da matakan zamantakewa a gida da unguwa da gari da ƙasa da tuni kan matsayi da halayen sababbin abubuwa masu faruwa a rayuwar al’umma da sauran abubuwa na zamantakayya.

    Akwai waƙoƙin baka da yawa matuƙa a kan harshen faɗakarwa, kuma har wa yau makaɗa na ta aiwatar da su. Misalan waƙoƙin harshen faxakarwa sun haxa da waqar ‘Jawabin Aure’ da waqar Kwalara’ da waƙar ‘Gulmawuya’ na Ɗanmaraya Jos da waƙar ”Don salla da Salatil-Fati’ da waƙar ‘Noma aikin ‘Yan’arewa’ na Alhaji Mamman Shata da waƙar ‘Cutar Taɓin Hankali’ da waƙar;’Irin Ginin Sakarkari’ na Alan Waƙa da waƙar ‘Naira da Kwabo Sabon Kuɗi Haruna Uji da sauransu.

    4.6 Harshe na Nuna Alhini

    Kalmar alhini tana nuni a kan juyayi ko tausayawa a kan wani rashi na mutuwa (CNHN, 2006:12). Harshen alhini, harshe ne wanda ake ɗura wa kalmomi na yin ta’aziyya tare da sanyaya wa mutum da aka yi wa rashi tare da ba shi haƙuri da yin addu’a.

    Makaɗan Hausa sukan yi alhinin mutuwa a zubin waƙoƙinsu, musamman ma waƙoƙin turken ta’aziyya. Tubalan ginin harshen alhini ya ƙunshi kalmomi na tausayawa da juyayi da nuna jimami da addu’a da ba da haƙuri da kalmomin sambarka a kan halayen mai mutuwa ko kalmomi masu tuna ayyukan da ya yi kyawawa, ayyuka na taimako, ayyuka na inganta rayuwa da sauransu. Misalan waƙoƙi na harshen alhini sun hada da waƙar ‘Allah jiƙan Ciroman Gwambe’ ta Mamman Shata da waƙar ‘Mutuwa ba ki da sabo’ ta Abdussalam, Shatan Nijar da waƙar ‘Ɗamarar ko ta Kwana’ ta Alan Waƙa da sauransu.

    Dubi abin da Shata ya faɗa a harshen ta’aziyya cikin alhini:

    Jagora: Kowa yam mutu bai sauri ba,
    : Mu da muke nan ba mu daɗe ba,
    : Sai mun zo Ciroman Gwambe.
    ‘Y/Amshi: Allah jiƙan Ciroman Gwambe.

    A wani ɗa Shata yana cewa:
    Jagora: Ni me zance ma Sarkin Gwambe,
    : Sarkin Gwambe ya yi rashi,
    : Haka ni ma Mammalo mai ganga,
    ‘Y/Amshi: Allah jiƙan Ciroman Gwambe.
    (HBTKA, 2003:32&38).

    4.7 Harshe na Sanya Sambarka

    Sambarka, kalma ce wadda ake amfani da ita don nuna godiya ko yabo ko murna, takan ɗauki ma’anar ‘Allah ya sa albarka. Haka kuma takan nufi tubarkalla ko madalla ko sanya albarka (CNHN, 2006:386).

    Waƙoƙin Hausa suna cike da harshe cikin kalmomi masu yabo ko yabau ko bege, kalmomi na nuna sambarka, kalmomi masu saka jin daɗi, kalmomi na ayyana soyayya ko ƙauna, kalmomi masu nuna yanayi na farin ciki ko sakin fuska ko sakin jiki ko farar zuciya ta yin magana kwakkyawa, ta baza alheri, ta baza kyauta, ko nuna hannun baiwa da sauran maganganu masu saka wa jiki annashuwa, ita kuma zuciya ta faranta har a wani lokaci ta ɗimauta, idanu su dinga zubar da hawaye domin daɗi.

    Harshe mai saka tsima ta sambarka ya ƙarfafa a waƙoƙin baka na Hausa waɗanda ake yi wa masoya da waɗanda ake ƙauna kamar malamai da sarakuna da attajirai da iyaye, maza da mata, da sauran mutane masu ayyukan bajinta, masu ɗaukaka darajar al’ummar Hausawa.

    Mai waƙa Yakubu Muhammad ya yi ishara wadda ya nuna yabo, ta amfani da kalmomin sambarka, yakan saka daɗin zance ya jaddada ƙauna a inda ya ce:

    Jagora: Imbambaliba imbambalibo,
    : Biyayya daraja ce,
    : Yabo daɗin zance,
    : Ƙauna ai ƙima ce,
    : Son ki gare ni ai hujja ce,
    ‘Y/Amshi: Alambiyo-biyo yaran badali,
    : An yi bibiyo sai in da dalili.
    (Yakubu Muhammad: Waƙar ‘Imbambaliba’)

    Wannan fage mai faɗi ne wanda yake da waƙoƙi masu ɗimbin yawa, kila waɗanda ma baza a iya gane adadi na yawansu ba. Wasu daga cikin waƙoƙi na harshen nuna sambarka su ne waqar ‘Abdullahi shugaban sahu’ da waƙar ‘Mai yawuri bangon daniya’ da waƙar ‘Babban bijimi Muhammadu Sama’ na Aliyu Ɗandawo da waƙar ‘Amadun Bubakar gwarzon Yari’ da waƙar ‘Gogarman Tudu jikan Sanda’ na Ibrahim Narambaɗa da waƙar ‘Mai dubun nasara garnaƙaƙi sardauna’ da waƙar ‘Zaki ba a ja ka wasa ba’ da waƙar ‘Babban jigo na Yari’ na Musa Ɗanƙwairo da waƙar ‘Bijimin gidan Bello Mamman na Yari’ da waƙar ‘Tsakin Tama na Abashe’ da sauransu.

    Sa’idu Faru ya gaya wa Sarkin Musulmi Alhaji Muhammadu Macciɗo wasu halaye nasa tun a lokacin da yake riƙe da sarautar Sarkin Kudun Sakkwato har yake gaya masa Sarkin Musulmi ne na wata rana. Ga abin da ya ce:

    Jagora: Maganag ga da za ni faɗa maka,
    : Gagarau ɗan Aliyu kai mana gafara,
    : Wada duk aka gadon ƙasura,
    : Wada duk aka gadon ɗaukaka,
    : Wadda duk aka gadon ci gaba,
    : Mamman ka gaji Abubakar
    : Ko da sayen halin nan akai,
    ‘Y/Amshi: Baba halin da ka kai kuɗɗi shikai.

    Ya ci gaba da cewa:

    Jagora: Diba ƙafarka zuwa bisa hannuwa,
    : Zaman Shaihu na ba wata sa’ida,
    : Sarkin Musulmi wataran kake,
    : Da imani da mu’ujjiza,
    ‘Y/Amshi : Na nan ga Malam Macciɗo,
    Jagora: Tun ga Aliyu Maisango naj jiya,
    : Halin ga da Bubakar yar riƙa,
    ‘Y/Amshi: Macciɗo kai ka shirin gado haka.
    (Gusau, 2009:154).

    4.8 Harshe na Tarihi

    Tarihi wani fannin ilimi ne wanda yake ba da labarin al’amura da suka faru a zamanin da ya wuce wato labarin abubuwan da suka shuɗe (CNHN, 2006: 49).

    Makaɗan baka na Hausa sukan yi amfani da harshe mai nuna tarihi su gina waƙoƙinsu. Misali, Alan waƙa ya rera wata waƙa a kan, tarihin cinikin bayi a tsakanin Hausawa mai gindi ‘Rayuwar Afirkawa, ga waƙar ‘Mu so Allah Sarkin makaɗa ‘ta Danmungai Daura wadda ya rera game da tarihin, zuwan Bayajidda ƙasar Hausa. Dubi kuma waƙar ‘Ga darajjar Amadu Bello’ ta Sarkin Taushi Salihu jankiɗi wadda ya bayyana tarihin zaman Turawa Nijeriya ta Arewa da hanyoyin da suka biyo da shekarun da suka yi kafin su miƙa mulki a 1960 da kuma bayan tashinsu.

    Dubi abin da yake faɗa a wani ɗa:

    Jagora: Zakkuwar Turawa nan Tudu,
    ‘Y/Amshi: Shekara hamsin da tara,
    : Ta inda sunka biyo Bidda,
    : Sai Kafin-Ɗanyumusa da Makurɗi,
    : Kwantagora garin Ibrahim,
    : Gwanga ya yi faɗa da Nasara,
    : Ga darajjar Amadu Bello,
    : Da arziki na mazan jiya yay yi.

    Jagora: Dagga Zariya sai Birnin Kano,
    ‘Y/Amshi: Ƙoramar Zorori wajen faɗa,
    : San Kano ya tarbi Nasara,
    : Ga darajjar Amadu Bello,
    : Da arziki na mazan jiya yay yi.
    (Gusau, 2012:119-120)

    4.9 Harshe na Koyar da Addini

    Addini hanya ce ta yi wa Allah bauta, ko kuma kamar yadda Ƙamusun Hausa (CNHN, 2006:3) ya bayyana, addini shi ne hanyar bauta wa Ubangiji. Akwai dabaru iri-iri waɗanda al’ummu suke amfani da su wajen yi wa Allah bauta. Mutum, ɗan’adam, ya shirya wa kansa wasu hanyoyi na bautar ubangiji na maguzanci, Allah kuma ya saukar wa ɗan’adam da daidaitacciyar hanya ta yi masa bauta a inuwar addinin Musulunci.

    Addinin Musulunci yana ƙunshe da sharuɗɗa da hukunce-hukunce da ake neman kowane mutum Musulmi ya san su, ya yi aiki da su wajen yin wannan bauta ko ibada (Gusau, 2008:389). Haka kuma dole ne a sami wasu mutane daga cikin al’umma waɗanda za su tsayu a wajen koya wa sauran jama’a hanyoyi waɗanda suke yin jagoranci ga sanin matsayin bauta da kaifiyyarta da siffofinta da hanyoyin gudanar da ita.

    Bisa wannan aiki ne aka sami wasu suka himmatu wajen koyar da abubuwan da suka shafi bauta ko ibada a addinin Musulunci tun daga Manzanni da Annabawa da malamai da sauransu.

    Makaɗan baka na Hausa sun sami dama ta baiwar waƙa wadda suka dinga koyar da ayyukan ibada ta harshen waƙa domin ilmantar da mutane wasu sassa na sha’anin addininsu na Musulunci. Misali, waƙar ‘Fara ba mu ye Allah’ ta Uwaliya Mai’amada an zuba ta a kan harshe mai neman a kaɗaita Allah, waƙar ‘Mu je mu je ba mai yi kamar Allah’ ta Uwaliya ita kuma tana koyar da aikin hajji da kuma waƙar Ɗanyaya ta ‘Allah kai ni Madina’.

    Ita waƙar ‘Don salla da Salatil-Fati’ ta Alhaji Mamman Shata Katsina ya gina ta ne bisa harshe na sunnar aure. Dubi kuma waƙar ‘Azumi watan bautar Allah’ ta Alan Waƙa wadda ya sarƙa ta bisa harshe mai yin bayani a kan ibadar Azumi ta watan Ramalana. Ga waƙar ‘Allah ba ku mu samu Alhaji Alhajiya’ har wa yau ta Alan waƙa wadda take karantar da matsaloli na almajirci irin na Ɗankulodu. Kila ko wannan ne ya sanya Alan Waƙa ya ba ta suna Muhajira wato waƙa wadda take ƙaurace wa bara da almajirci irin na ɗanƙolo domin ta zama wata hanya ta koyarwa cikin harshen waƙar baka, da sauransu.

    4.10 Harshe na Bara-Gurbi

    A hikimar magana ta Bahaushe ne yake kiran sauran ƙwai wanda kaza ta yi kwanci, bayan ta gama ƙyanƙyasa ta bar su da bara-gurbi. Irin ƙwai bara gurbi yakan zama ya ruɓe ko ya ƙafe ko ya zama gunya ko dai wata illa ko lalura ta same shi (Bargery, 1934&1951:81). Ƙwai bara-gurbi yana fita ne daga ƙwayaye masu lafiya waɗanda ake ƙyanƙyashewa su zama ‘yan tsaki.

    Harshe bara-gurbi, harshe ne maras kyau, maras daɗi, mai ban haushi wanda wasu makaɗa suke jefawa a cikin wasu waƙoƙinsu. Abincin harshe bara-gurbi a waƙa shi ne zagi da batsa da baɗala da alfasha da munanan kalmomi, musamman irin na bara a kufai (Alan Waƙa: ‘Gara nai bara da bulayi, bara a kufai) da wasa da nassi na Alƙur’ani ko Hadisa ko musanta wani hukunci saukake ko ƙarfafa al’adu munana waɗanda suke kauce wa tubalai kyawawa na gina ingantacciyar al’ummar Hausawa. Lalataccen harshen waƙar baka tamkar lalataccen ƙwai ne wanda yake zama bara-gurbi (CNHN, 2006:37) a cikin ƙwayaye.

    Wasu misalai na harshe bara-gurbi a waƙoƙin baka na Hausa sun haɗa da wani ɗa wanda Muhammadu Gambo ya rera inda yake cewa:

    Jagora: Ba azumi nika wa gudu ba,
    : Yawan sallan nan yau da gobe,
    : Ba sallan nan nika wa gudu ba,
    : Yawan duƙin nan yau da gobe,
    : Ba shi barin mai rai da wando.
    (Gambo mai waƙar Ɓarayi)

    A wani ɗa ma yana cewa:

    Jagora: Ba Allah nika wa tambaya ba,
    : Wai laihin mutuwa ɗaukar ɓarayi,
    : Ta bar mai kurɗi lahiya lau,
    :Shin Allah mis sa hakan ga?
    (Gambo mai waƙar Barayi)

    A wani ɗa ma yana cewa:

    Jagora: Ni dai in ga asara danya-danya,
    : Ko ba a ban ko sisin kwabo ba,
    : In ishe tsohi sun yi lanƙwat,
    :Sai in ji kamar na taki Arfa.
    (Gambo Fitilar Sarri mijin Kulu)

    Wasu daga cikin waƙoƙi da aka yi su bisa harshe bara-gurbi su ne waƙar ‘Buwayi gasa na Shehu’ ta Ɗangaladima Labbo, Magajin Jankiɗi (Gusau, 1980:57) da waƙar ‘Ɗan’ali’ ta Muhammadu Bawa Ɗan’anace da waƙar ‘Gagaragadon namiji tsayayyen ɗan kasuwa’ da waƙar ‘Habu na Habu’ da waƙar ‘A sha ruwa ba laihi ba ne’ na Alhaji Mamman Shata da waƙar’ Yau huɗu ga wata’ da waƙar ‘Jirgin sama za ya wuce’ na Aliko Makaho da wasu waƙoƙin Illon Kalgo da wasu na Isa Ɗanmakaho da wasu na Ɗanqurji da wasu na Musa Ɗanƙwairo tun ma ba wasu waƙoƙinsa na noma ba da sauransu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Dangantakar Harshe da Waƙa danna nan

    Domin karanta cikakken bayani akan Yin Waƙar Baka ko Sarrafa Waƙar Baka danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Waiwaye Kan Harshen Makaɗi A Zubin Waƙar Baka; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakkken Littafin danna nan.

  • Iyalin Musa Ɗanƙwairo

    Iyalin Musa Ɗanƙwairo

    Iyali suturar mutum, iyali suturar gida. A bisa yanayin zamantakewar bil Adama da aljannu, cikar ɗa, mutum namiji ko ‘ya, mutum mace ita ce yadda Allah ya hore musu, ya ba su dama, suka assasa zuriya ta kankin kansu.

    Ta haka za su sami nutsuwa, da samun ayyukan yi a duniyarsu da lahirarsu, musamman ma idan suka yi aiki da hukunce-hukuncen addini da matakan zamantakewar rayuwa bisa kyakkyawan zaɓi da dacewa. Haka kuma aure yana a kan gaba wajen tsayar da usra ko iyali da za su iya zama ƙwarara, ina ma a ce an bi sharuɗɗa da kyawawan dangogi na yin sa.

    Alhaji Musa Ɗanƙwairo wanda aka fi sani kuma ake kira da Maradun, ya sami jagoranci na iyaye wajen yin matar farko 21. A yayin zaman Ɗanƙwairo a doron rayuwar duniya bayan matarsa ta fari, ya auri mata da yawa kuma wasu daga cikinsu ne suka haifa masa ‘ya’ya har goma sha bakwai (17).

    Matan Aure na Musa Ɗanƙwairo

    Mata waɗanda Alhaji Musa Ɗanƙwairo ya aure a rayuwarsa ta duniya su ne:

    i) Hauwa Taladan
    ii) Hajiya Hadiza (Ikka/Tashikka)
    iii) Amina
    iv) Tumba
    v) Rabi (‘Yar Zuma)
    vi) Maryam (Amarya)
    vii) Hauwa
    viii) Maimuna

    ‘Ya’yan Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maza da Mata

    Ga tsarin sunayen ‘ya’yan Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun ta bin ɗakunan iyayensu mata da suka haɗa da:

    i) Ɗakin Hauwa (Taladan)

    ii) Ɗakin Hajiya Ikka (Tashikka)
    a) Muhammadu Ɗanmakaɗa, Dauda na ɗaya (1)
    b) Alhaji Garba, Zwacin Kiɗi, Marafa, Daudu (2)
    c) Audu Adodo, Wakilin Kiɗa
    d) Zulaihat
    e) Habiba

    iii) Ɗakin Amina
    f) Ummaru Ka-ji-Dama (Makaɗin Noma)
    g) Amina (Kassu): Tana aure a Maradun

    iv) Ɗakin Tumba
    h) Sanin Ɗanƙwairo, Zakin Murya

    v) Ɗakin Maryam (Amarya)
    i) Sa’adatu
    j) Muhammadu Balarabe
    k) Umaru

    vi) Ɗakin Rabi’a (‘Yarzuma)
    l) A’ishatu (Indo)
    m) Malam Musa Tunau (Malamin Makarantar Allo)

    vii) Ɗakin Hauwa
    n) Abubakar, Ciroman Kiɗa
    o) Amina, Ige
    p) Ibrahim Ɗan’auta22

    viii) Ɗakin Maimuna
    Ba ta Haihu ba.

    Bishiyar Iyalin Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun

    Kaka Maiganga
    Usman Ɗankwanagga = Yarnunu
    Musa Ɗanƙwairo23 Amina Binta (Maryam)

    = Hauwa = Haj. Hadiza =Amina = Tumba = Maryam =Rabi = Hauwa =Maimuna
    (Taladan) (Ikka Tashikka) (Amarya) (‘Yar Zuma)
    Malam Musa Ba ta
    Tunau haihu ba
    Umaru Amina (Kassu)
    (Ka-Ji-Dama) Tana Aure Sa’adatu Muh Umaru
    a Maradun (‘Yabbata) Balarabe
    Muhammadu Sani (Zaƙin Murya)
    Ciroma Amina Ibrahim Ɗan’auta
    Abubakar (Ige) (Harkokin
    Magaji na (2) Kasuwanci)
    Muhammadu Garban Audu Zainabu Habiba
    (Ɗanmakaɗa) Ɗanƙwairo (Adodo)
    Magaji na (1)

    = Salame = Baraka
    Muhammadu Muh Tamaikiɗi
    Ɗanjimma Basiru
    Magaji na (3)

    Domin karanta cikakken bayani a kan Kiɗa da Waƙoƙin Makaɗa Musa Ɗanƙwairo danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ma’anar Kiɗa da Makaɗi danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Wuraren Sadawar Waƙar Baka

    Wuraren Sadawar Waƙar Baka

    Makaɗan Hausa sukan sadar da waƙoƙin da suka yi bisa maƙasudai ne daban-daban gwargwadon waɗanda aka yi domin su. Waɗannan wurare da ake yin sadawar sababbin waƙoƙin baka sun haɗa da:

    i) Gidajen al’umma na ɗaiɗaikun mutane kamar gidajen sarakuna da gidajen malamai da gidajen attajirai; da gidajen masu jarumta da sauran gidajen masu sana’a da kuma sauran gidaje na ɗaiɗaikun al’umma.

    ii) Wurare na bukukuwa; kamar bikin aure da bikin suna da bikin kalankuwa da bukukuwan sarauta na al’adar Hausawa da bukukuwan masu sana’o’i da bukukuwan nunin amfanin gona da bukukuwan murna da bukukuwan da akan shirya na musamman da sauransu;

    iii) Dandali na shirya wasannin yara; tun a musamman lokacin kiɗan kalangu na ‘yan mata da na asauwara da kuma kiɗan duma da makamantansu.

    iv) Wuraren farauta; a fagagen da ake farauta a cikin dazuzzuka akan yi wa mafarauta sababbin waƙoƙi; kuma ana sadar da su da waƙoƙin ne a lokacin farautar a cikin dajin farauta, musamman a yayin da alalmisali, farauta ta rincime; ana buga in buga.

    Waƙoƙin da Kassu Zurmi ya yi sababbi; na farauta ya rera su ne kuma ya sadar da su kai tsaye a fagen farauta.

    v) Wurin noma, haka abin yake wurin manoma, musamman a yayi na gayyar noma a wata gona; kamar a Gandun Sarki, ko a gonar wasu Sarakai, ko a gonakin taimakon sauran talakawa. Nan ake sadar da sababbin waƙoƙi ga manoma, musamman waɗanda suke da sarautun noma kamar; Sarkin Noma da Madakin Noma da Gojen Noma da Kayayen Noma da sauran jaruman noma da makamantansu;

    vi) Wurin wasanni; Wurin wasannin al’ada a ƙasar Hausa wuri ne da ake rera sababbin waƙoƙi, a kuma sadar da su ga waɗanda aka yi wa su da sauran jama’a masu sauraro.

    Wurin wasannin al’ada sun haɗa da:

    – Wasan Asauwara wadda ake yi a kowace ranar kasuwa ta gari. Ana yin wasan Asauwara a ranar cin kasuwa ta wani gari da yammaci ne, gab da kamar la’asar sakaliya wato kasuwa za ta watse. A wasan Asauwara ana yin waƙoƙi ne tsakanin matasa-‘yan maza da ‘yan mata ko zabiyi da kuma zabiya. Kuma ana yin wasan Baura da kiɗan Baura, a wannan lokaci ma ana rera waƙoƙi sababbi da zimmar sadar da su.

    – Wasan kokawa

    – Wasan dambe

    – Wasan Sharu: wanda ake yi a lokacin da Hausawa suka shaƙu da Fulani

    – Da sauran wasanni.

    Wurin wasannin al’adun Hausawa, wuri ne ma wanda ake sadar da waƙoƙin baka na Hausa.

    vii) Wuraren Tarukan Makarantu:

    A lokacin da Hausawa suka sadu da Turawa, musamman a zamanin mulkin mallaka; Turawa suka ƙagi makarantu ga Hausawa tun daga zamanin karatun manya har zuwa karatun yara; an kakkafa wa Hausawa makarantu na boko daban-daban.

    To a yanzu a waɗannan makarantu tun daga na boko da kuma na islamiyoyi da a masallatan addinin Musulunci; duka ana yin taruka mabambanta kamar:

    – Tarukan fitar ɗalibai.
    – Taruka na aikin makarantu, kamar tarukan gama makaranta wato Convocation a Jami’a.
    – Taruka na maulidi, kamar Maulidin Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) da na Shaihunai da na Mujahidai da na sauransu.
    – Tarukan ga-Fili-ga-mai-doki.
    – Taruka na Musamman.
    – Da sauransu.

    viii) Wurare na Musamman

    Akwai kuma wasu wurare da ake shirya taruka na musamman domin kawai a rera waƙoƙi sababbi; a sadar da su ga mutanen da aka yi wa su da sauran jama’a na musamman. A ire-iren wurare da muhallai na musamman waɗanda ake nema domin a sadar da waƙoƙi sababbi sukan ƙunshi;

    – Wuri wanda aka zagaye shi, kuma aka yi masa shuke-skuke na ciyayi da wasu hakukuwa masu ƙayatarwa; musamman masu ƙara ganin ido ko warware kwarkwatar ido;

    – Wuri da aka tanada a matsayi na Gadina;

    – Wurin da aka tanada a matsayi na utel-utel ko ɗakin taro na musamman a manyan garuruwa da birane;

    – Wurin da aka keɓe domin shaƙatawa, ko na masaukan baƙi;

    – da sauransu da yawa.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yin Waƙar Baka ko Sarrafa Waƙar Baka danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Aiwatarwa Da Sadarwa A Waƙoƙin Baka Na Hausa wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Saƙo Maƙoƙo

    Saƙo Maƙoƙo

    Sallama farko na miƙo
    Ɗan ƙasa ne ko kwa baƙo
    Wanda ke sama to ya sauƙo
    Ya ji saƙon umma kuma ya karɓa.

    Magana zan yo a kanta
    Tsohuwar nan ta wahalta
    Ni fa tinda na zo cikinta
    Na fahimci akwai abin da bai ba.

    Nai mafarki ne da umma
    Ta faɗan magana da dama
    Dan akwai maganar da ai ma
    Ba buƙatar bayyana ta nan ba.

    Wata ƙila wanin ku zai ce
    Wacce umma hala mutum ce
    Ko kwa aljan to wace ce
    Ɗan uwa ƙasarmu nai nufi ba.

    Ƙorafinta da tai na farko
    Kan ɗiyanta na farko-farko
    Sai ta yo ƙasa can ta sakko
    Sai ta yo maganar da zan faɗi ba.

    Tunda nai aure na farko
    Ga sadaki har da baiko
    Har na haifi wasunku aiko
    Aka auran wanda ban nufi ba.

    Ku kuke nemo mazajen
    Da kuke so sai ku auren
    Sai su zo ƙarshe su cucen
    Su sakeni su bar ni da ciki ba.

    Kansu sau ni su illata ni
    Kalli duk sun raunata ni
    Ga jikina ya yi rauni
    Ni fa ko, ba zan ƙi in mace ba.

    Da abin a iya garen ne
    Kan tsaya to da sumul ne
    To fa kuma duk a jone
    Kuke kan wahalar da ke zuwa ba.

    Sai nace mata ya uwarmu
    Yanzu menene kalamu
    Wa kike so ne ki samu
    Ki yi wuff da abinki ne nufi ba.

    A a na ga kuna ta naci
    Za ku je tonan muruci
    So kuke ku daɗe ni ƙunci
    Ni da ku ai duk muna ta karɓa.

    Nifa dimukradiyar ce
    Bam biɗa in dai wannan ce
    Tinda an yi gwaji shiru ce
    Babu canji ko da na sile ba.

    Abba Marke ka cewa sauran
    Su ji tsoran rabbu sarkin
    Da ya yi ni ya yi ku haƙƙun
    Su fitar ni hannun birirrika ba.

    Don karanta Duka A Murɗe danna nan

    Edita; Rumasa’u M. kallamu

     

  • Waƙar Neman Zaman Lafiya

    Waƙar Neman Zaman Lafiya

    Mawaƙi: Jamilu Alhassan
    Amshi: Zaman lafiya muke so,
    Allah daɗo ƙasata Rabba.

    Bisimilla Sarkin baiwa, Baiwarka ta ishe kowa,

    Bara nake kai nawa, Baiwar Ka yo ƙarawa,

    Bari nai nasiha babba.

    Ƙaro salati Jallah, Gare sa Manzon Allah,
    Ƙaunarsa ɗan Abdullah, Silar barin yin kwalla,
    Faɗar Ma’aikin Rabba.

    Waƙa nake ƙullawa, Zaman salam roƙowa,
    Allah Ka zam ƙarowa, Ƙasarmu Naija tawa,
    Mu daina yin tababa.

    Ku tabbata dangina, Kwai batu ruhina,
    Ku zo ku ji ikhwana, Ku daina yaƙar juna,
    Kuu san hakan ba riba ba.

    Zaman lumana duba, Yana da rana babba,
    Rashin sa ba riba ba, Mu daina yin wata gaba,
    In ji Shi Sarki Rabba.

    Ku tsaya ku ji wani zance, Mu riƙe shi sai mu yi dace,
    Fitina tana nan kwance, La’ana ta gun Mahalicce,
    Ga masu ta da ta duba.

    Aya cikin Anfali, Ashirin biyar ɗan kalli,
    Halin masifa kalli, Ba ta barin mai hali,
    Yaro fa har ma babba.

    Zama idan ai ba fis, Da ka ji an ce zan ƙis!
    Tamkar baru an ce is! Kowa yana yin tinƙis,
    Ba mu so ganin wannan ba.

    Wa’atasimu faɗar Mahalicci, Bihablillahi har da maƙoci,
    Jami’an, babu mai yin ƙunci, Idan mun farraƙe zai ɗaci,
    Rayunmu ban ƙarya ba.

    Idan ka ɗauki Afirka, Akwai ƙasashe leƙa,
    Waɗanda akke yaƙa, Wasunsu na yin kuka,
    Ba su samu zaman aunu ba.

    Burundi in ka dubi, Ruwanda har ma Libi,
    Ka tabbata sun ƙi bi, Kundi na mulki kitabi,
    Ba su daina yin yaƙi ba.

    Laberiya Somali, A nayinti-wan ɗan kalli,
    Sun ƙaurace nasu mahalli, Waɗansu an bar kwalli,
    Domin ba su ma zauna ba.

    Itofiya ita wannan, Iritiriya shi ke nan,
    Nayinti-et su biyun nan, Sun yaƙi juna rannan,
    Ba suy yi adalci ba.

    Sierra Leone har Sudan, Mutum fa wane metan,
    Gidansu sun bar wannan, Zaman rashin fis ke nan,
    Ya sa ba sa zauna ba.

    Idan ka zo nan Naija, Farin ido sai yai ja,
    Kano fa babbar haja, Na Marwa ne kuma yaj ja,
    Amman fa bai kyauta ba.

    Muhammadu na Marwa, Gyauronsa na can Yarwa,
    Ƙala-ƙato ban mantawa, Fitinar da sun shukawa,
    Da yawa akai binnewa, Ka ji halin ‘yan zamba.

    Zangon katab, wayyo ni! Hausa Birom kaico ni!
    Tivi-Jukun can ƙarni, Da yawansu ai sun rauni,
    Wasu ma ba su ko shura ba.

    Idan ka zo nan Yarwa, Boko haram kwai tsiwa,
    A Bama ban mantawa, Wasunmu na a kushewa,
    Abin fa bai kyawu ba.

    A Mubi har ma Gombe, Ba yau ba har ma gobe,
    Addu’arsu hannu tuɓe, Tamkar kwari ba kube,
    Salam salam, ya Rabba.

    Zaman salam kwai auki, Ya zarce ma ɗan sarki,
    Kowa yana nasa aiki, Ticas muna yin maki,
    Ba mu zam muna ganda ba.

    A Yobe nan ce jahata, Abin fa ya so ƙazanta,
    Gwamnanmu ai ya kyauta, Ya ce a bar yin wauta,
    Bai bar mu muna ihu ba.

    A 1st Disemba fotin, A YSU can hostel ɗin,
    Aka zo da kutse domin, A kashe ake yin yaƙin,
    A Monde ba zan manta ba.

    Salmanu sannan Sulfa, Sun zo suna sassarfa,
    Sawunsu sam ba safa, Sauran suna shan suffer,
    Subhana Sarki Rabba.

    Ciza nake tun ɗazu, A Yobe ai dai yanzu,
    Zama na lau ya wanzu, Mun roƙi Sarki Azizu,
    Bai ƙi ya yo amsa ba.

    A yanzu zan yo busa, Na ba ku labarinsa,
    Zaman lumana kansa, Ya zarce daɗin masa,
    Ta Bauchi ban ƙarya ba.

    Ga shawara zan bai wa, Gwamnanmu har ma kowa,
    Ga wanda ke son yalwa, Gun zaman lumana aiwa
    Mu kama Allah Rabba.

    Ina ƙiranmu jumulla, Mai ɗan kwali ko mai hula,
    Rawani da mai jan akala, mu kama Allah walla,
    Mafuta ba za mu rasa ba.

    Shi dai fa rai kwai tsada, Sojojinmu har ‘yan sanda,
    Sun ce sun ji sun kuma yarda, Su nasu ran sun sai da,
    Don kare ƙasata babba.

    A bar batun ɓangaranci, A bai wa kowa ‘yanci,
    Musulum, Kirista maƙoci, Mu mutunta juna.

    Domin karanta cikakken Yabo Daga Waƙar Maryam Fantimoti danna nan.

    Domin karanta cikakken Yabo A Waƙoƙin Baka danna nan.

    Don karanta cikakken Dangantakar Harshe da Waƙa danna nan.