Category: Waƙa

  • Masu Rera Waƙa

    Masu Rera Waƙa

    Masu rera waƙar, su ne asalin mawaƙan, wato waɗanda suke zama su tsara waƙar ta hanyar amfani da basirarsu.

    Waɗannan su ne rukuni na farko, kuma su ne tushe; domin dalilinsu ne aka samar da dukkanin wani nau’in kayan kiɗa da tanadar dukkanin abin da zai kai ga rera waƙar; har ta kai ga yaɗuwa a tsakanin jama’a.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gudumawar Adabin Baka Wajen Haɓaka Tattalin Arziki; Keɓantaccen Nazari Kan Waƙar Baka Ta Situdiyo wanda Ibrahim Baba (Nayaya) ya wallafa shi.

    Domin karanta cikakken bayani akan Takardun da Ake Saya Domin Rubuta waƙar danna nan

  • Keɓantaccen Nazari Kan Waƙar Baka Ta Situdiyo

    Keɓantaccen Nazari Kan Waƙar Baka Ta Situdiyo

    Abin Da Bincike Ya Gano Game Da Gudumawar Adabin Baka Wajen Haɓaka Tattalin Arziki: Keɓantaccen Nazari Kan Waƙar Baka Ta Situdiyo

    Dukkanin wani bincike da za a gudanar ko aka gudanar; za a iske akwai irin nasarar da aka ci a sakamakon yin sa; wanda hakan ya sanya aka gano wasu muhimman abubuwa.

    A wannan nazari kan waƙar baka, an gano wasu muhimman abubuwa da suke da amfani ga rayuwar al’ummar Hausa da ma ƙasa baki ɗaya.

    Cikin abubuwan da binciken ya gano akwai:

    i. Yadda aka sami bibiyar sawu ta fuskar sana’a a tsarin waƙa, daga waƙar baka ta gargajiya zuwa waƙoƙin baka na Situdiyo. Wato sai ya zama kamar abin da Bahaushe ke cewa, “Sawun da na gaba ya taka, na baya ma kan takawa” amma fa ta fuskar sana’a.

    ii. Yadda aka fahimci mamayar mutane a cikin sana’ar waƙoƙin Situdiyo.

    iii. Yadda aka ga tattalin arziki na bunƙasa a dalilin waƙoƙin Situdiyo.

    iv. An fahimce yadda gungun jama’a ke cin abinci a dalilin waƙoƙin Situdiyo na Hausa.

    v. An gano yadda waƙa ta zama wata babbar sana’a a Ƙasar Hausa tun daga jiya har zuwa yau.

    vi. Binciken ya binciko irin nau’o’in mutanen da suke jinginuwa da wannan sana’a ta waƙa a matsayin hanyar samun abin masarufin rayuwa.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gudumawar Adabin Baka Wajen Haɓaka Tattalin Arziki: Keɓantaccen Nazari Kan Waƙar Baka Ta Situdiyo wanda Ibrahin Baba (Nayaya) ya wallafa shi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yabon Gusau A Waƙoƙin Baka danna nan

  • Fitattun Iyayen Gida Na Ɗanƙwairo A Kiɗan Fada

    Fitattun Iyayen Gida Na Ɗanƙwairo A Kiɗan Fada

    Bisa dukkan hasashe, ubangida a wajen Makaɗi yakan zama mutum wanda ya nuna damuwa a harkoki da al’amurran makaɗi; wataƙila kuma makaɗin nan ya fi daidaita tunaninsa da zubin waƙoƙin da yake yi masa.

    Ubangida yakan zama murabbi ta fuskar kyautata ayyukan makaɗa don su zama na ƙwarai.

    Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo tun a farko-farkon tsundumarsa a cikin waƙoƙin baka, Allahu ya hore masa irin waɗannan dattawan iyayengida.

    Muhimmai daga cikinsu sun haɗa da:

    a) Abubakar na Birnin Ƙaya a Gundumar Maradun
    b) ‘Yandoton Tsahe, Alhaji Aliyu II (1960-1991)
    c) Sardaunan Sakkwato, Firimiyar Jihar Arewa, Alhaji Sir Ahmadu Bello Sakkwato (1962-1966)
    d) Sarkin Maradun Alhaji Abubakar (1939-1964)
    e) Sarkin Maradun Muhammadu Tambari (1964-1981)

    f) Sarkin Maradun Ibrahim II, Maigandi (1981-2003)
    g) Sarkin Daura, Alhaji Muhammadu Bashar (1966-2007)
    h) Sarkin Sudan, Alhaji Shehu Malami Wurno
    i) Sarkin Das, Alhaji Bilyaminu Usman
    j) Da sauransu

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ƙungiyar Makaɗa Musa Ɗanƙwairo Ta Kiɗa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Waƙa A Matsayin Sana’a danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Sauya Akalar Kiɗan Gado Zuwa Na Fada Da Na Game-Gari

    Sauya Akalar Kiɗan Gado Zuwa Na Fada Da Na Game-Gari

    Makaɗa Musa Ɗanƙwairo Maradun tun yana cikin aiwatar da kiɗa na Gayauna; wato tun kafin a naɗa shi Sarautar Sarkin Kiɗan Sarkin Maradun yake shigowa da wasu halaye masu jan hankali; da buɗa ido a yanayin kiɗan da ya taras iyaye da kakanni suna yi a gidansu.

    Domin haka tun a aiwatar da waƙoƙin baka na Gayauna Musa Ɗanƙwairo yake shiryawa da sadar da:

    i) Waƙoƙin Noma

    A waƙoƙin noma, Makaɗa Musa Ɗanƙwairo, ya yi farin jini sosai, jama’a sun so waƙoƙinsa, musamman waƙoƙi na noma; waƙoƙi ne da suke ƙunshe da lugga da zaɓaɓɓun kalmomi. Ga kuma zayyana faruwar abubuwa da adonta harshen waƙa tun ma ba a turken yabo; da ɗiya na zambo da ba’a da sauransu ba. Sannan ga Ɗanƙwairo da murya mai zaƙi da kaurara zance kuma mai jan hankali mai sauraro.

    ii) Waƙoƙin Fada

    Waƙoƙin fada, waƙoƙi ne waɗanda Ɗanƙwairo ya yi wa ‘ya’yan Sarakuna da Sarakuna kansu da Hakimai; da Dagatai da masu riƙe da muƙaman Sarauta da sauran masu jinin Sarauta da makamantansu.

    iii) Sarkin Kiɗa

    Makaɗa Abdu Kurna Maradun (1899-1962) yayan Ɗanƙwairo, ya lura da irin tumbatsa cikin ƙwarewar da Alhaji Musa Ɗanƙwairo ya samu a kiɗan noma da na fada (Sarauta); inda kuma ya dinga kai gayaunan kiɗa, ya sutta kuma ya jima.

    Abdu Kurna ya dinga jan kunnuwan Musa Ɗanƙwairo, yana yi masa kandarki, har dai wata rana ya gaya wa ubangidansa, Sarkin Ƙayan Maradun da bakin waƙa yana shaida masa:

    Jagora: Sarkin Ƙaya wa Ƙwairo faɗa,
    ‘Y/Amshi: Bai barin halinai,
    Jagora: Daga zuwa Maƙera, ni maikiɗi,
    : Ban ji labarinai ba,
    : Sai can zuwa Ɗanmanau,
    : Na Ruwan Kiɗi sa sirdi,
    ‘Y/Amshi: Hau ko kana gane shi,
    : Na Ruwan kiɗi hau doki,
    : Tahi ko kana iske mai,
    : Shi yay yi damben girma,
    : Jikan Hassan ɗan Iro,
    : Sarkin Ƙaya mai gayya,
    : Na Magaji ba tagewa.

    (Musa Ɗanƙwairo, Waƙar Shi yay yi dambe girma & Gusau, 1988: sh. 224).

    iv) Waƙoƙi Game -Gari

    Kurwar Musa Ɗanƙwairo ta waƙar baka ba ta keɓe shi ya tsaya a rera waƙoƙin noma ko na fada ba. Musa Ɗanƙwairo ya kawo wani yanayin sussuka da daddare; yayin da ya shigo da aiwatarwa da rera waƙoƙin da a yau nake kira da waƙoƙi Game-Gari (Gusau, 2008a, sh. 161-162).

    Waƙoƙi Game-Gari kuwa sun ƙunshi waƙoƙin Malamai da Alƙalai da Lauyoyi da Attajirai; da sauran ‘Yan Kasuwa da Ma’aikata da ‘Yansiyasa da siyasar kanta da Sojoji da Jarumai da Dakaru da sauran Mayaƙa; da Mafarauta da Maharba da masu sana’o’i da Samari da ‘Yanmata da Dabbobi da Tsuntsaye da Ƙwari da Gulabe da Dazuzzuka da sauran madangantan waɗannan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Fitattun Iyayengida Na Ɗanƙwairo a Kiɗan Fada danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Musa Ɗanƙwairo A Koyo Da Biyayyar Waƙa

    Musa Ɗanƙwairo A Koyo Da Biyayyar Waƙa

    Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun ya tashi, ya girma a gidansu; ya tarar da ana harka ta kiɗa da waƙa. Magabatansa tun daga Kaka Maiganga da mahaifinsa dukkansu makaɗa ne na noma; da yaƙi da kuma Sarauta da suka aiwatar da kiɗa da farar ganga da kuma gangar kotso.

    A bisa ɗabi’a ta gadon gida, mutum zai koyi abin da ya tarar ana gudanarwa a gidansu. Hausawa sukan ce, gadon gida alala ga rago, a yayin da Musa Ɗanqwairo ya fara tasawa, sai ya karkata wajen koyon abubuwa na hukunce-hukuncen addinin Musulunci da kuma hidimomin kiɗa da waƙa waɗanda suka shafi wasu harkoi na zamantakewar Hausawa.

    Musa Ɗanƙwairo ya fara biyayya ta sanin makamar waƙar baka tun a wajen mahaifinsa, Makaɗa Usman Ɗankwanagga24. A wajen mahaifin nasa ya koyi kaɗa kanzagi da karɓin waƙa da jajircewa a karin waƙa da samar da rauji na waƙa (Gusau, 2019: sh. 10-11).

    Haka kuma Musa Ɗanƙwairo ya daɗa gwangwajewa a zuba ɗiya na waƙar baka a biyayyar da ya yi a yayin Halifantakar da ya yi wa wansa Abdu Kurna. Domin himmar Musa Ɗanƙwairo da ƙwazonsa da basirarsa, wansa Sarkin Kiɗan Sarkin Maradun Abdu Kurna, ya naɗa shi ya zama Daudun Kiɗa kuma Ɗangaladimansa.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Musa Ɗanƙwairo a Gayaunar Waƙa danna nan.

    Don karanta cikakken bayani a kan Waƙar Shawara Ga Mai Bilicin danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Musa Ɗanƙwairo A Gayaunar Waƙa

    Musa Ɗanƙwairo A Gayaunar Waƙa

    Makaɗa Abdu Kurna yana daga cikin makaɗa na ƙungiya; waɗanda suka yarje wa wasu mataimakansu su dinga zuwa taɓe na yin waƙa; wato gayaunar kiɗa.

    A lokacin da Sarkin Kiɗa Abdu Kurna ya lura wazirinsa Musa Ɗanƙwairo ya laƙanci waƙar baka; sai ya ba shi faraga ya dinga fita da abokansa yawon rera waƙoƙi lokaci bayan lokaci wato sa’i da wata bukata.

    Makaɗa Musa Ɗanƙwairo ya yi waƙoƙin noma da yawa lokacin gayauna. Daga nan ne Abdu Kurna ya ba shi izini ya dinga haɗawa da waƙoƙin masu Sarauta, musamman ma ‘ya’yan Sarakuna.

    Waƙar Gayauna ta Sarauta wadda Musa Ɗanƙwairo ya fara shiryawa da aiwatarwa da rerawa da sadarwa; ita ce wadda ya yi wa Abubakar ɗan Sarkin Noma Usman na Birnin Ƙaya.

    Ga wasu ɗiya na waƙar:

    G/Waƙa: Ɗan Sarki a gode maka,
    : Jikan Dodo Ɗangwamma.
    Jagora: Ya tafi daji ba shi komawa,
    : Kullum daƙe duƙe sai duƙe,
    ‘Y/Amshi: Gyado mai ƙoƙarin gabce,
    : Ɗan Sarki a gode maka,
    : Jikan Dodo Ɗangwamma.
    Jagora: Mijin Ɗiya jikan Nomau,
    : Gwarzon Ango karsanin Ali,
    : Gungaman Iro ɗan Jatau,
    : Kullum daga duqe sai duqe,
    ‘Y/Amshi: Gyado mai ƙoƙarin gabce,
    : Ɗan Sarki a gode maka,
    : Jikan Dodo Ɗangwamma.
    (Waƙar Musa Ɗanƙwairo 30 ta Abubakar Birnin Ƙaya)

    Domin karanta cikakken bayani akan Sauya Akalar Kiɗan Gado Zuwa Na Fada Da Na Game-Gari danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Gudumawar Waƙoƙin Baka na Situdiyo Wajen Haɓaka Tattalin Arziki danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shine daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Kiɗa Da Waƙoƙin Makaɗa Musa Ɗanƙwairo

    Kiɗa Da Waƙoƙin Makaɗa Musa Ɗanƙwairo

    Kiɗa da waƙa ta baka wani fage ne wanda yawancin makaɗa masu tunani da ƙwaƙwalwa da fasahar shirya kalmomi; musamman ta fuskar zaɓensu da baiwa ta hangen nesa da furuci mai cusa tarbiyya ta ruhi da ta gangar jiki suke aiwatarwa ga al’ummominsu.

    Wasu ladubban waƙoƙin baka sun haɗa da bayanai na tarbiyyatarwa da faɗakarwa da jan hankali; zuwa ga kyawawan ayyuka da halaye na gari, musamman waɗanda al’umma da addinin al’umma suke aiki da su.

    Domin haka, waƙar baka ta ƙunshi wasu matakai da sigogi na aiwatarwa wato shiryawa da ƙullawa; da kuma rerawa tare da sadar da ita ga al’umma. Kuma waɗannan su ne suke ɗaukar hankalin al’umma wajen sauraron waƙoƙin baka da aiki da su.

    Makaɗin baka yakan zama tilas ya san waɗannan ladubban waƙar baka; waɗanda Allahu yake yi masa ilhama da su ta hanyoyin koyo da biyayya ko jibilliyya ko bisa wata buƙata ta rayuwa.

    Domin karanta cikakken bayani akan Musa Ɗanƙwairo a Koyo da Biyayyar Waƙa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Mawaƙan Da Ake Yi Wa Kiɗan Fiyano danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Wasu Waƙoƙin Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau

    Wasu Waƙoƙin Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau

    2.1 Sanƙiran Aliyu Gadanga (Ibrahim Imo) :
    ‘Ali Ɗan’agunda Jikan Jama’a.’
    Kirarin Sanƙira na Aliyu Gadanga da na S.M. Gusau :

    2.2 Aliyu Gadanga Gusau :

    ‘Sai na zo mu Taya shi Murna,
    Mu zo mu ga Farfesa Sa’idu.’ 

    2.3 Babangida Kakadawa Gusau 

    ‘Farfesa Sa’idu Muhammad.’
    Waƙar Babangida Kakadawa ta ‘Baban ɗan Ƙasa na
    Ƙasar nan’ 
    ‘Furofesa ne Sa’id’
    Waƙar Babangida Kakadawa ta ‘Furofesa ne Sa’id’

    2.4 Aminu Ladan Abubakar, Alan Waƙa, Baharun Waƙa :

    ‘Ga ka Farfesa ga ka Katibi kan Adabi,
    Sannu Farfesa Sa’idu ɗan Muhammad na Gusau.’ 
    ‘Ga ka Farfesa ga ka Katibi kan Adabi,
    Sannu Farfesa Sa’idu ɗan Muhammad na Gusau.’ 
    ‘Gangaran ka fi Gwani Shehu Adibi na Gusau,
    Mashahurin Malami Sa’idu Muhammad na Gusau.’ 
    ‘Shehin Adabi da Al’ada,
    Sa’idu Gusau Furofesa Mafakar Mazaje.’ 

    2.5 Sarfilu Umar Zarewa Ɗanbaiwa, Maiwaƙa 

    ‘Sannu Furofesa Gusau,
    Sa’idu Muhammad na Gusau,
    Ko an ja Maka za a sau,
    Maka a Fannin Ilimi.’ 

    2.6 Ibrahim Bello, Billy’O 
    ‘Furofesa Gusau Gaisuwa Muka zo,
    Za mui maka.’ 

    2.7 Maryam Fantimoti, Sarauniyar Waƙa ta Sarkin Kano :

    ‘Furofesa Sa’id Muhammad na Gusau,
    A gai da Babban Malami a Harshen Hausa
    Ɗan Ƙwarai.’

    2.8 Muftahu Umar Muhammad Maiwaƙa, Kano 

    ‘Da Madubin Adabi Sannu Turka ta ilimi,
    Yau Furofesa Sa’idu Muhammad na Gusau Muke
    Waƙewa.’ 
    ‘Prof. Gusau Madalla Shehu Sa’idu ɗan Babba,
    Ga Gwani Adibin Shehi ɗan Muhammadu Ɗankullum.’ 

    2.9 Shehu Ajilo Ɗanguzuri, Kaduna

    ‘Baba Furofesa nau,
    Sa’idu Mamman Gusau.’ 
    ‘Sa’idu Muhammad,
    Na gode Sa’idu Furofesan Hausa.’ 

    2.10 Abdul Jos Maiwaƙa na Sarkin Waƙa Naziru 

    ‘Farfesa Baba Sa’idu Muhammad Gusau sha Kallo,
    Sashen Hausa na Jami’ar Bayero,
    Ƙumdum Kamarka ba a yo ba.’ 

    2.11 Abba Abdulƙadir Shu’aibu (Abban Baba)

    ‘Sannu Jarumi Furofesa Sa’idu Muhammad Gusau,
    A gai da Katibi jan Zaki Baba Tushen Hausa’ 

    2.12 Rubutawa: Sulaiman Ahmad Usman (Baba Sule) :

    Rauji da Rerawa: Sarfilu Umar Zarewa Ɗanbaiwa Maiwaƙa,
    G/Waƙa: ‘Babban Gijin Jami’ar Bayero,
    Farfesa Sa’idu mai Gaskiya’ 

    2.13 Alhaji Imamu Muhammad Sanusi, Ɗanƙwairon Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmuminu Kabir Usman

    ‘Furofeso Sa’idu Gusau,
    Ɗan Muhammadu ka Buwai Arna’ 
    ‘In ga ɗan Muhammadu Ɗankullum,
    Sa’idu Furofesa ne kai’ 
    ‘Furofesa Sa’idu Gusau ɗan Muhammadu,
    Ka buwai Arna’ 

    2.14 Rubutawa: Fatima Uba Adamu 

    Rauji da Rerawa: Sarfilu Umar Zarewa Ɗanbaiwa
    G/Waƙa: ‘Baba Sa’idu Gusau Furofesa,
    Mai Zurfin Ilimin Sanin Harshen Hausa,
    Babban Furofesa’ 

    Domin karanta cikakken bayani a kan Waƙoƙin Fada Da Wasu Waƙoƙi Game-Gari danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Gudumawar Waƙoƙin Baka na Situdiyo Wajen Haɓaka Tattalin Arziki danna

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Diwanin Waƙoƙin Baka Juzu’i Na Biyar (Matanonin Wasu Zaɓaɓɓun Waƙoƙin Makaɗan Baka); wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Rataye na 3: Waƙar Shan Ƙwaya ta Alhaji Dr Adamu Ɗanmaraya, Jos

    Rataye na 3: Waƙar Shan Ƙwaya ta Alhaji Dr Adamu Ɗanmaraya, Jos

    To kar a sha ƙwaya,

    Ƙwaya ko ba ta da kya,

    Jama’a ku saurara.

    To kar a sha ƙwaya,

    Ƙwaya ko ba ta da kya,

    Dubban mutanen gida,

    Daji suna zance,

    “Ƙwaya ko ba ta da kyau”,

    To kar a sha ƙwaya,

    To kar a sha ƙwaya,

     

    Kakanka ba ya sha,

    Babanka ba ya sha,

    Me ya kai ka shan ƙwaya?

    To kar a sha ƙwaya,

    Ƙwaya ko ba ta da kyau,

    Matarka ba ta sha,

    Mamarka ba ta sha,

    ‘Ya’yanka ba ya sha,

    Me ya kai ka shan ƙwaya?,

    To kar a sha ƙwaya,

     

    Ƙwaya fa ba ta da kyau,

    Ta kan sa a lalace,

    Ƙwaya fa ba ta da kyau,

    Ta kan sa a lalace,

    Ƙwaya ku saurara,

    Ƙwaya ku bar sha dai,

    Ƙwaya fa ba ta da kyau,

    Don Allah ku saurara,

    To kar a sha ƙwaya,

    To kar a sha ƙwaya,

    Kwaya fa ba ta da kyau,
    Jama’a ku saurara,

     

    Ƙwaya ku bar….

    To tun ba na sha,

    Wani nawa ba ya sha

    To kar a sha ƙwaya,

    Ƙwaya fa ba ta da kyau,

    Jama’a ku saurara,

    Kakanku ba ya sha,

    Kakarka ba ta sha,

    Me ya sa ka sha ƙwaya?

    Ƙwaya!

    Ƙwaya!

    Na tsine ‘yan ƙwaya,

    Na la’anci ‘yan ƙwaya,

    Ƙwaya fa ba ta da kyau,

    Jama’a a saurara

    Na la’anci ‘yan ƙwaya,

    Na tsine ‘yan ƙwaya,

    Jama’a a bar sha dai,

    Wallai ba ta da kyau,

    Wallahi ba ta da kyau.

     

    Don karanta Waƙar Hana Shan Ƙwaya da Sauran Kayan Maye danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Mata Da Shaye-shayen Kayan Maye: Ina Mafita? Wanda Ado Ahmad Gidan Dabino MON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Rataye na 2: Waƙar Hana Shan Ƙwaya da Sauran Kayan Maye Ta Marigayi Abdullahi Sani Makarantar Lungu

    Rataye na 2: Waƙar Hana Shan Ƙwaya da Sauran Kayan Maye Ta Marigayi Abdullahi Sani Makarantar Lungu

    Kuma babu ƙarfi wajen mai shan ta ni na faɗi,

    Domin jininsa takan tsotse ya bar tafiya.

    Bacci kwa in har ya kwanta sai ya kai mako,

    Ba wanda zai ce da kai ya gan shi ya juya.

     

    Aiki fa ja a gaban mu a taimaka jama’a,

    Don alhaki ne wuyan kowanmu kar mu ƙiya

    Gyaran ƙasa dole sai an kau da shashanci,

    Sannan fa duk ci gaban jama’a ya zam tafiya

     

    A ɗau matakin da za a ga babu kwaya sam,

    Domin mu tsere ta kaicon rayuwar duniya.

    A hukunta mai sha da mai saida ta kar a raba,                                                              Laifinsu ya yi kama da fashi a Nijeriya.

     

    Burinmu ya bar cika in har ba mi azama,

    Mun kau da ƙwaya ba ƙarshe za mu sha kunya.

    Wannan masifar fa ba birni kawai ta tsaya,

    Har ƙauyuka ta gama duk ‘yan uwa ku jiya.

     

    A wajen manoma akan ce wai da sun sha ta,

    Wai sai su kwana suna aiki fa ba gajiya.

    In masu neman karatu sunka je gunsu,

    Wai sai su ce maganin niyya fa kar ku ƙiya.

     

    In ban da ƙarya ina wani maganin niyya,

    Da za ya sanya ƙwaƙwalwa har ta zama tawaya

    In na tuno lamarin kan ba ni mamaki,

    Hanyar da za a bi gyaran nan ya zam tafiya.

     

    Ƙwaya takan ɓata dukkan rayuwar jama’a,

    In har aka yi sakaci ba a tashi an aniya.

    In har ana so ƙasa ta zamo cikin tsari,

    Sai an kawar da abin maye da sa tawaya.

     

    Wasu sanya ƙwaya suke randa ta kan hanya,

    Jama’a ku gane da makircinsu kar ku biya.

    Duk ci gabanmu suke nema ya salwanta,

    Don tun da farko fa su ba su samu tarbiyya.

     

    Kuma har da mata a wannan kar ku ce ƙari,

    Da masu aiki da kwaya babu wai ku jiya.

    A gidan biki ko ko suna sai a same ta,

    A cikin ruwa ko kunun zaƙi da za a biya.

     

    Wallahi duk wanda ya ba ɗan uwansa guba,

    Ya sani haƙiƙa Ta’ala zai yi sakayya.

    Duk mai nufin cutatar da waninsa ya wahala,

    Shi zai ga cuta a kansa fa babu wai ku jiya

     

    Duk ɗan ƙasa nagari burinsa ai kirki,

    Ba za ya so ‘yan uwansa cikin rashin shiriya.

    A kiyayi ƙwaya da ganye kar a raɓe su,

    In dai da son a ji daɗin rayuwar duniya.

     

    In anka ce hankali kuma ya gushe babu,

    Ai rayuwa ba ta amfani a nan ku jiya.

    Komai muƙamin mutum wa za ya raɓe shi?

    Domin kwa ya cusa kansa a surƙuƙi da ƙaya.

     

    Na bayyana muku kwayar nan fa cuta ce,

    Domin takan hana barci har ido ya tsaya.

    In babu barci ko tilas hankali ya gushe,

    Domin ƙwaƙwalwar mutum ta ɓaci ta tawaya.

     

    Daga nan mutum sai ya hau yawon da ba gaira,

    Bare dalilin da za a ji tausayi a biya.

    Sai zantuka marasa kai babu gindinsu,

    Ƙwaya fa ta fara narkewa a nan ku jiya.

     

    Kuma sai ya zauna ba zai wanka bare wanki,

    Suma da annakiya sun san gurin ɓuya.

    Sai tsince-tsince a bola ko cikin kwatami,

    Tsumma a gunsa kwa ya wuce ai ta jayayya.

     

    Ai ba batun wani jin daɗi a kan wannan,

    Sai jefa kai a tsiya da barin abin kunya.

    Wa zai ga wannan ya nuna har yana sha’awa?

    Sai dai a nemi tsari da halin maƙi shirya.

     

    Domin karanta Rataye Na 1: Waƙar ‘Yar Maye Ta Ahmad Tijjani Gandu danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Mata Da Shaye-shayen Kayan Maye: Ina Mafita? Wanda Ado Ahmad Gidan Dabino MON ya wallafa.

    Edita@rumasau-kallamu