Category: ILIMIN TARIHI

  • Tarihin Alaramma Gambon Takai

    Tarihin Alaramma Gambon Takai

    An haifi Malam Zakariya ɗan Adamu a garin Takai a shekarar 1928. Ɗan baiwa kuma ma’abocin himma da ƙanƙan-da-kai.

    Malam Gambon Takai ya sha banban da sauran makaranta ta fuskar shuhura wajen buɗewa almajirai sirrin Alƙur’ani. Wannan ya sa dattijan malamai zuwa gari ya gari don su yi kwalli da shi. Wannan har yasa wasu na cewa Malam Gambon Takai ya yi gamo da aljannu ne a inda suka buɗe idonsa da sirrukan Alƙur’ani.

    Abokan ƙuruciya lokacin neman karatun Malam Gambo kuwa ba su gushe ba suna bibiyarsa, har sai da wata rana bayan ya yi tafiya suka bincike lakkarsa ko za su ga wani nau’i na Alƙur’ani ko wani kundi na sirrukan Alƙur’ani da ya ke anfani da shi. Ubangiji Maɗaukaki Ya yi masa baiwar murya, koda yana karatu a hankali to kuwa wanda ke nesa zai jiyo muryarsa.

    Da yawa yakan naƙaltawa makaranta sirrukan rubuta Alƙur’ani da haddace shi. Ya isheka misali ga tumbatsarsa wajen warware luggogin Alƙur’ani abin da muka gutsurowa mai karatu mai suna Logar Gambon takai a Babi na Uku, Sashe na Biyu cikin wannan littafin da ke maganan kan dabarun rubutun AIƙur’ani wurin ma’abota tsangaya.

    Hatta malamai masu karatu kan zo tsangayarsa don kallon darasu; wanda ake farawa tun Asuba har sai an yi Azhar sannan a karya a koma.

    Wani abu mai ban sha’awa game da rayuwar Malam Gambon Takai shi ne; himmarsa wajen dogaro da kai da yin kasuwanci. An ce a lokacin da ya ke fita rani da almajirai kamar 50 zuwa 70 zuwa garuruwan Gaya da Kibiya; ba a rasa raguna da tumaki a daure saboda kiwo.

    A duk lokacin da matsuwa ta kama wani almajiri, to kuwa Alaramma ne zai ba shi rance. Bayan girma ya kama shi kuwa, ya kasance yana aikawa da gyaɗa da ƙuli-ƙuli Ikko don a yi masa kasuwanci.

    Mafi yawan tafiye-tafiyen neman karatunsa sun kasance ne a tsakanin Kano da Haɗeja. An ce bai taɓa zuwa Maiduguri ba in ba da niyyar ziyara ba.

    Ya kasance yana naƙalta wa almajiransa sirrin karatu ta hanyar:-

    – Yin tilawar izu ashirin kullum
    – Yin taƙarar izu ashirin kullum
    – Biya allo sau ɗari kafin a yi sabon rubutu
    – Yin rubutu kaɗan, kada ya wuce rubu’i
    – Kada Almajiri ya tashi in ana darasu har sai an gama gaba ɗaya

    Malam Gambon Takai ya rasu a shekarar 1998 ya bar ‘ya’ya shida:-

    – Malam Musa Gambon Takai
    – Malam Lawal Gambon Takai
    – Malam Sani Gambon Takai
    – Malam Saminu Gambon Takai
    – Malam Salisu Gambo Takai

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Alaramma Malam Salihu Ɗangalinja danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Fa’idojin Wadatar Zuci danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Mahiru Sharif Bala

    Tarihin Mahiru Sharif Bala

    An haifi Gwani Sharif Bala ɗan Sharif Musɗafa ɗan Sharif Muhammad a shekarar 1345; wadda ta yi dai-dai da shekarar 1934 a Unguwar Gabari cikin garin Kano.

    Mahiru Sharif Bala ya taso a gidan ilimi da wadata da karamci a inda ya yi karatu a wurin mahaifinsa tare da ɗan uwansa Sharif Ahmad. Mahiru Sharif Bala ya rubuta Alƙur’ani sau uku tun yana ɗan shekara goma sha takwas; kuma a dai-dai wan nan lokaci ne aka yi masa auren fari. Mahiru Sharif Bala ya kutsa fannonin ilmi inda ya karanci tafsiri da Hadisi da Fiƙhu a Unguwar Makwarari.

    Wani abin mamaki game da rayuwar Mahiru Sharif Bala ya yin neman Alƙur’ani shi ne: bai taɓa zuwa ko’ina ba kamar yadda abin yake wajen mafi yawan makaranta. Babbar baiwar da Mahiru Sharif ya shahara da ita baya ga ƙarfin tilawar Alƙur’ani, shi ne gwanintar rubutunmu na Magribi.

    Kwanciyar baƙaƙen AIƙur’ani irinsu “Kaulasan” da Lam’ara da tsaiwar Bayala shaida ce ga ficen da Mahiru Sharif Bala ya yi a wannan fage. Saboda irin baiwar rubutunsa da irin karɓuwar da yake da ita tsakanin makaranta Alƙur’ani ba a ƙasar Kano ba kawai; har ma da wasu sassa na Afrika ta Yamma; ta sa Mahiru Sharif Bala ya juyi littattafai a sassan ilman Musulunci da hannunsa irinsu:-

    – Asshifa
    – Dala’ilul Khairati
    – Ishriniyya
    – Alburda
    – Hamziyya
    – Risatul Anwar
    – Igasatul ibad
    – Risala
    – Iziyya da sauransu

    Babu shakka wannan ya sauƙaƙawa makaranta tsangaya waɗanda ba su saba da rubutun sharƙiyya ba, damar kutsawa fannoni ilmi.

    A taƙaice za mu iya cewa hannun Mahiru Sharif Bala da tasirinsa a tsarin tsangaya ya zama “hantsi leƙa gidan kowa”; domin kuwa ya ratsa kowane loko da saƙo na makaranta.

    Ma’ana dai, in almajiri bai je gabansa ya yi karatu ba to kuwa ya kwaikwayi irin salon rubutun hannunsa; tun daga kan Juzi’i biyar ko goma har zuwa ashirin.

    Yaɗuwar da Alƙur’anin Mahiru Sharif Bala ya yi ya zarta yaɗuwar mafi yawan Alƙur’anan da aka rubuta da hannu; domin kuwa ya rubuta Alƙur’ani hamsin da hannunsa. An buga bakwai daga cikinsu, kuma an ɗabba’a su fiye da sau dubu ɗari biyu: waɗanda duk sun yi fice da fitar da harji da meram da falalar kowace sura.

    Game da taimakon yin magani da ayoyin Alƙur’ani kuwa, Mahiiru Sharif Bala ya rubuta Alƙur’ani don sha fiye da sau ɗari; Suratul Yusuf sau dubu ɗaya, Bisimilla da Wallahu ya ‘asimuka da Sanuƙ’ri’uka sama da miliyan guda.

    Farin jinin rubutunsa da baiwar da Ubangiji yai masa ta sa an buga:-

    i- Asshifar da ya rubuta da hannunsa sama da dubu talatin
    ii- Dala ilul khairati sama da dubu ɗari
    iii- Ishiriniya sama da dubu ɗari biyar
    iv- Alƙur’ani ɗan izu ashirin sama da dubu ɗari biyar
    v- Alƙur’ani ɗan izu goma sama da miliyan biyu
    vi- Alƙur ‘ani ɗan izu biyar sama da miliyan biyu
    vii- Ƙawa’idi sama da miliyan biyu
    viii- Ashmawi sama da dubu ɗari biyar
    ix- Risala sama da dubu goma
    x- Iziyya sama da dubu goma
    xi- Alburda sama da dubu goma
    xii- Ira’atul biladi sama da dubu goma.

    Har zuwa yanzu, Mahiru Sharif Bala bai gushe ba yana ba da karatu da ilimi a shahararriyar makarantarsa; tare da mataimaka sama da talatin da almajirai yara da manya, maza da mata sama da dubu biyar. Ubangiji Maɗaukaki Ya ƙara masa lafiya ya kuma sanya masa kyawawan ayyukansa a mizani.

    Tsokaci

    Akwai wasu malamai na Alƙur’ani fitattu a Kano da yawa – da ya kamata na gutsurawa mai karatu wani abu daga tarihin rayuwarsu, amma hakan ba ta samu ba.

    Cikinsu akwai Malam Na Mai Ganji da Malam Giwar Takwasa da Malam Husaini Ɗangurai da Malam Ɗangidimoni; da Malam Ɗayyabu Mai Saje da Malam Yahaya Malammadori da Gwani Tata Bunkure da Malam Ɗan Ringim; da Malam Mai Hafizai da ma waɗanda ban ambata ba.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wasu Daga Malamai a Katsina danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Taƙaitaccen Tarihin Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Rahamar Ubangiji Ga Bayinsa

    Rahamar Ubangiji Ga Bayinsa

    Yayin da Allah ubangiji ya halicci mutum ya yi nufin alheri da rabautar duniya da ni’imar lahira da aljanna gareshi amma wannan duk ba ya samuwa sai idan mutum ya yi amfani da hankalinsa da kuma abin da ya dace da ruhinsa da jikinsa, wannan kuwa yana buƙatar abin da zai ɗauke waɗannan buƙatu waɗanda ba wanda zai iya samar da dukkan wannan sai mahaliccin mutum ɗin da ya san shi, kuma ya san buƙatunsa.

    Tun da Allah yana son rabauta ne ga mutum shi ya sa ya halicce shi, don haka ne sai ya samar masa da hanya kamila da zai bi domin samun rabauta ta hanyar wasu amintattun bayi nasa da suke ma’asumai daga dukkan kuskure da mantuwa kuma tsarkaka daga dukkan aibobi da zunubai waɗannan su ne annabawa da manzanni.

    Don haka ne: Annabi shi mutum ne da Allah ya yi masa wahayi ya zaɓe shi a cikin mutane kuma sun kasu gida biyu: Annabi ɗan saƙo shi ne wanda aka aiko domin ya tseratar da mutane daga duhu zuwa haske daga ɓarna zuwa gaskiya daga camfi zuwa gaskiya daga jahilci zuwa ilmi. Annabi ba ɗan saƙo ba: shi ne wanda aka yi masa wahayi zuwa ga kansa kuma ba a umarce shi ya isar da saƙon ga mutane ba.

    Yahudawa suna bin Annabi Musa (a.s) kiristoci kuma Annabi Isa (a.s) musulmi kuma Annabi Muhammad (s.a.w) da sauran annabawa duka. Sai dai musulunci ya shafe sauran addinai da suka rigaya, bai halatta ba ma’abotansu su wanzu a kansu, dole ne a kan kowa ne mutum ya bi koyarwar musulunci. Ubangiji yana cewa: “wanda ya yi riƙo da wani addini ba musulunci ba to ba za a karɓa daga gareshi ba, kuma shi a lahira yana daga cikin masu hasara”.

    Don haka yahudanci da kiristanci ɓarna ne da aka shafe su, amma musulunci mai wanzuwa ne har zuwa ranar kiyama. Annabi Muhammad (s.a.w) shi ne ƙarshen annabawa kuma addininsa shi ne musulunci mai shafe duk wani addini kuma shari’arsa za ta wanzu har zuwa ranar ƙiyama kuma ita kaɗai ce shari’ar da za ta azurta mutum da tabbatar masa da burinsa da amincinsa har zuwa ƙarshen rayuwa duniya da lahira.

    Kamar yadda shi kaɗai ne mutum abin koyi ga dukkan duniya baki ɗaya, dukkan mutanen duniya idan suna son alheri ga kawukansu to dole ne su bi tafarkinsa su yi koyi da kyawawan halayensa (s.a.w) da kuma sanin sashen tarihinsa da ba makawa mu kawo wasu daga siffofinsa (s.a.w): Shi ne Muhammad ɗan Abdullah (s.a.w) kuma mahaifiyarsa ita ce Aminatu ‘yar Wahab.

    An haife shi a Makka ranar Litinin goma sha-biyu ga watan Rabi’ul awwal a shekarar giwa, a zamanin sarki mai adalci Kisra. (wato idan an kwatanta shi da ire-Irensa a cikin sarakunan wannan zamani). An aiko Annabi Muhammad (s.a.w) da saƙo yana ɗan shekara 40 yayin da Jibrilu (a.s) ya sauka gareshi daga wurin Allah (S.A.W) yana kogon Hira wanda yake dutse ne a Makka ya ce masa ka karanta kuma ya saukar masa da ayoyi biyar na surar Alaƙi.

    Sai ya zo ya tsaya a kan dutsen Safa a masallaci mai alfarma na Makka a lokcin akwai jama’a masu yawa a wurin da ake taruwa ya isar da saƙon Allah na shiryar da mutane zuwa ga imani da shi yana cewa da su: “Ku ce babu abin bauta da gaskiya sai Allah kwa rabauta”. A lokacin tunda mutanen Makka mushirikai ne, kuma suna ganin maslaharsu ita ce shirka kuma suna tsoron maslaharsu sai suka riƙa yi masa isgili suna yi masa dariya suna cutar da shi.

    Kuma duk sa’adda ya dage wajen shiryar da su sai su dage wajen cutar da shi har ya ce: “Ba a cutar da wani Annabi ba kamar yadda aka cutar da ni”. Yayin da takurawar mushirikai ta yi yawa sai ya yi hijira zuwa Madina wannan kuwa ita ce hijirar farko a tarihin Musulmi, yayin da suka yi yawa sai ƙarfinsu ya daɗu kuma suka samu koyarwa daga Manzon Allah da shari’arsa mai sauƙi mai hikima, da kuma misali na kyawawan halaye da mutumtaka da wayewa da cigaba a Madina har suka fi dukkan duniya da addini na sama da waɗanda ba na sama ba.

    Kuma an samu yaƙoƙi masu yawa a Madina kuma dukkaninsu sun zama domin kare kai ne daga maƙiya mushirikai da yahudawa da kiristoci da suke kai hari kan musulmi, kuma Annabi a kowane lokaci yana zaɓar ɓangaren sulhu da zaman lafiya ne da rangwame, don haka ne ma adadin waɗanda ake kashewa daga ɓangarorin biyu ba su da yawa a dukkan yaƙoƙinsa tamanin da wani abu, wato; waɗanda aka kashe na musulmi da kafirai duka ba su kai sama da dubu ɗaya da ɗari huɗu ba.

    Tun lokacin da aka aiko Annabi da saƙo har ya tafi daga duniya wahayi yana sauka gareshi kuma Jibrilu (a.s) shi ne ake aiko masa daga wajen Ubangiji (S.A.W) a hankali a hankali har littafin Kur’ani ya cika a cikin shekaru ashirin da uku. Manzo (s.a.w) ya kasance yana tsara wa musulmi duniyarsu da addininsu, yana sanar da su littafi da hikima kuma yana yi musu bayanin dokokin ibada da biyayya da mu’amala da zamantakewa da siyasa da tattalin arziki da sauransu.

    Sai Allah ya saukar da ayar: “A yau ne na kammala muku addininku, na cika ni’imata gareku kuma na yardar muku da musulunci shi ne addini”. A taƙaice, ya tattara dukkan wata ɗabi’a mai kyau da girma da ɗaukaka da kuma ilimi da adalci da taƙawa da kuma iya tafiyar da al’amuran duniya da na lahira, waɗanda babu wani mahaluki da yake da irinsu.

    Wannan shi ne annabin musulmi kuma wannan shi ne addinin musulunci, kuma addininsa shi ne mafificin addinai, littafinsa shi ne mafifcin littattafai domin shi: “Barna ba ta iya zo masa ta gabansa da ta bayansa, abin saukarwa ne daga mai hikima abin yabo”. Muhimmancin samuwar wannan annabi mai daraja wanda ya kasance hanyar shiriya ga dukkan talikai da suke bayan kasa.

    Don karanta Gudunmawar Iyaye Wajen Gina Al’umma danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tarihin Malam Mahmud Manzo Arzai

    Tarihin Malam Mahmud Manzo Arzai

    An haifi Malam Mahmud ɗan Muhammad ɗan Mahmud dan Muhammad a Damagaran cikin Jamhuriyar Nijar. Malam Mahmud ya zo Kano a lokacin girma ya fara kama shi. Malam Mahmud ya taso a hannun mahaifinsa a inda ya karanci Alƙurani.

    Ya shahara da sada zumunci da yawan kyautatawa ga baƙo da ɗan gari. Malam Mahmud ya yi tafiye-tafiye na neman Alƙur’ani izuwa alƙaryu masu nisa irinsu Inkibalwa da tsangayar Kolorum. Don haka ma ya sadu da manyan malamai irinsu Gwani Ahmad da Malam Yahaya da Alaramma Malam Yusuf wanda ake yi wa laƙabi da Malamin Mali da gwani Mahmud halifan Gwani Dipchan (shugaban makaratan Ƙasar Hausa) inda ya naƙalci ilmin Alƙur’ani da Rasmu da Tajwidi.

    Malam bai gushe ba yana kutsawa cikin neman Alƙur’ani da fannoninsa, har sai da ya sauka birnin Kano. A lokacin da ya iso kuwa almajirai suka riƙa dandazo don su sha daga tafkin ilminsa. Abu ne mai wahala ƙwarai da gaske ƙididdige yawan almajiran Malam Mahmud Manzo Arzai.

    Kaɗan daga cikinsu sun haɗa da Malam Muhamud Danja Zuwo, da Malam Lawan Saleh da Malam Gali Adhama.

    Wannan makaranta ta Malam Manzo ba ta gushe ba tana wanzuwa a hannun zuriyarsa cikc da ɗaruruwan almajirai, lokacin da Malam Manzo ya rasu babban ɗansa Malam Muhummad Mahmud wanda aka fi sani Malam Usman shi ya jagorance ta tare da taimakon ‘yan uwansa Malam Muktari Manzo mai koyar da ilimin Tajwidi da Malam Laminu shi ne mai darasu sai Malam Mustafa da Malam Abba da Malam Sunusi da Malam Ibrahim.

    Tsokaci

    Makarantar Malam Manzo Arzai ta shahara da ladabtar da kangarrarun yara ta hanyar addu’o’i da yi musu tarbiyya da karatun Alƙur’ani da lazimta musu addinin. A inda ake sanya su a mari. Mutane kan taso gari da gari don kawo ‘ya’yansu. Da yawa wannan tsari na tarbiyyantarwa ya kan taimaka wajen gyara tarbiyyar kangagararru har sai ka ga sun wayi garisun kintsu.

    Wasu ma sun zama malamai, albarkacin addu’o’i da lazimta musu Sallah akan lokaci da sauransu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Tarihin Sheikh Muhammad Barnoma danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Takaiceccen Tarihin Rayuwar Dr. Yahaya Tanko danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Tarihin Sheikh Muhammad Barnoma

    Tarihin Sheikh Muhammad Barnoma

    An haifi Malam Muhammad Barnoma ɗan Gwani Muktari a garin Misau. An ce bayan mahaifinsa Gwani Muktari ya yi hijira daga Barno shi ne ya kafa Masarautar Misau bisa tsantsar Shari’ar Musulunci a wancan lokacin.

    Malam Muhammad Barnoma ya taso a garin Misau cikin kulawar mahaifinsa, kuma ya yi karatun Alƙur’ani da sauran fannoni wurinsa. Mahaifinsa Gwani Muktari ya fita da shi daga ƙasa Misau har suka sauka a garin Kila cikin ƙasar Bauchi. Daga nan ne ya dawo Kano ya sauka wurin Mashahurin malamin ilmi Malam Mahmud Salga.

    A lokacin kuwa da Sarkin Gumel Nakuta ya nemi Malam Salga ya tura masa wani daga almajiransa don ya karantar da su AIƙur’ani da ilmi, sai ya umarci Malam Muhammad Barnoma da ya wakilce shi. Malam Barnoma ya kafa makaranta a Gumel ya kuma yaɗa ilmi har tsawon shekaru 60. Malam Barnoma ya haifi manyan ‘ya’yansa a Gumel. Da ga bisani ya dawo Kano ya cigaba da ba da karatu har ya rasu.

    Bayan rasuwar Sheikh Barnoma, ɗansa Malam Usman Barnoma ya cigaba da jagorantar wannan gida da makaranta.

    An haifi Malam Usman a garin Aikawa da ke Gumel a shekarar 1943. Ya haddace Alƙur’ani yana ɗan shekara goma sha huɗu, Malam Usman Barnoma ya yi karatu wurin Malam Sani Lukoro a Unguwar Gyaranya da ke Kanon Dabo.

    Malam Usman ya shahara da kyawawan halaye da yawan karamci, ga shi kuma ma’abocin bincike da nazari cikin littafan Musulunci. Saboda irin himmarsa an ce yana karanta izu arba’in a kowace rana. Manyan malamansa sun haɗa da Shehu Atiku da Malam AbdulMajid Salga da Malam Sani Mahmud. Manyan almajiransa kuwa sun haɗa da.

    – Dr. Muhammad Nuruddeen Musa
    – Dr. Abdullahi Saleh Pakistan
    – Malam Mahmud Barnoma
    – Malam Hamza Abdullahi

    Makarantarsa ta shahara da shigar da tsarin zamani cikin karantarwarta musamman ma sanya kayan makaranta da azuzuwa da sauransu.

    Domin karanta cikakken bayani akan Tarihin Alaramma Malam Aliyu Ɗan Kadawa (1868- 1998) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Tarihin Fati Nijar danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Isra’i Da Mi’iraji

    Isra’i Da Mi’iraji

    Ranar 27 ga watan Rajab

    Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) ya hau kan shimfiɗar “Rafarahu”, domin ganawa da Allah (Subhanallahu wata’ala).

    Ranar ce, annabi Muhammad ya haɗu da;

    1. Annabi Adamu (A.S) a sama ta ɗaya.

    2. Annabi Isa (A.S) da Annabi Yahya (A.S) a sama ta biyu .

    3. Annabi Yusuf (A.S) a sama ta uku.

    4. Annabi Idris (A.S) a sama ta huɗu

    5. Annabi Haruna (A.S) ta biyar.

    6. Annabi Musa (A.S) a sama ta shida

    7. Annabi Ibrahim (A.S) a sama ta bakwai , yana kishingiɗe da ma’ul ma’amur.

    Sannan kuma mala’iku miliyan tara ne (9,000,000) suka karɓi Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) a ranar da ya yi Isra’i da Mi’iraji. Guda miliyan bakwai (7,000,000) suna yi masa lale, guda miliyan biyu kuma suna feshin turare mai ɗan karan ƙamshi.

    Don karanta Munasabar Isara’i Da Mi’iraji danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Wayewa Da Cigaba A Mesopotamia

    Wayewa Da Cigaba A Mesopotamia

    Greeks (Girkawa) su ne suka sawa ƙasar da take tsakanin kogunan biyu Tigris da Euphrates suna Mesopotamia. Wannan koguna sun kwaranyo daga duwatsu a ƙasar Turkey. Sun rabu gida biyu daga asalinsu sannan suka yi tafiyar mil 400 suka shiga Persian Gulf.

    Ƙasar Mesopotamia yanzu ita ce gabas ɗin Iraq. Wannan ƙasa ta Mesopotamia ana ce mata (Fertile Crescent) ta ƙunshi kudu maso gabacin Anatolia, da Syria da Iraq. Wanda suka fara kawo ci gaba ko wayewa a wannan wuri ko ƙasa su ne Sumerians. Mutanen da suka yi mulki a wannan ƙasa ta Mesopotamia tun daga farkon wayewa Clement (1936: 67) ya kasa su kashi shida:

    1. Sumerians wanda su asalinsu Caucasians ne da ƙasar Asiya, sun shigo ta Arewacin Mesopotamia sun yi mulki sama da shekara 6000 da suka wuce wato daga 4000 BC zuwa 2750 BC.
    2. Semites: Akkadian da Babylonian daga Arewacin Mesopotamia sun yi mulki daga 2750 BC zuwa 900 BC an kori Akkadiyawa, sannan daga bisani Babyloniyawa suka zo bayan wani lokaci. Sarakunansu da suka yi fice su ne Sargon I da kuma Hammurabi.
    3.  Assyrians su ma semite ne sun yi mulki daga 900 BC zuwa 612 BC su ma daga Arewacin ƙasar suka fito. Shahararrun sarakunansu su ne Sargon II da Sennacherib da kuma Assurbanipal 
    4. Chaldeans su ma Semite sun zo daga kudancin ƙasar sun yi mulki daga 612 BC zuwa 538 BC wanda ya fi shahara a cikinsu shi ne Nebuchadnezzar.
    5. Persians sun zo daga gabas su Ayrans (Indo-Europeans) sun yi mulki daga 538 BC zuwa 331 BC.
    6. Alexander mutumin Grika ƙasar Mecedonia ya zo ya cinye ƙasar da  yaƙi ya kafa daularsa (Empire) daga 331 BC 323 BC. Daga baya kuma Rumawa sun mallaki ƙasar kafin zuwan Musulunci.

    Sumerians su ne suka fara zuwa wannan ƙasa daga gabashin Asiya (Caucasians) shekaru 7000 da suka shige. Sun zauna a wannan tabkin kuma a hankali suka mulki maƙwabatansu kuma su ma asalinsu ɗaya na harshen Semitic. Kamar shekara 5000 da suka shige sai suka fara karɓe ƙasashen maƙwabtansu kuma suka wayar musu da kansu.

    Sumerians su ne mutanen farko da suka fara gina manyan garuruwa, babban birninsu yana da mutane 100,000 a wancan lokacin. Dalilin haka ne yasa ake cewa su ne suka fara wayewar kafa garuruwa (wato urban Civilization). Sumerians sun kafa Uruk wanda shi ne babban birni na farko a tarihin duniya sun kuma kafa Lagash da Ur (Adler p. 15).

    Sumerians sun shahara a tarihi saboda abubuwan da suka ƙirƙira. Su ne suka fara ƙirƙiro rubutu na ƙwarai (sophisticated). Su ne suka ƙirƙiro ƙasaitaccen gini na farko, wanda aka yi amfani da linta da ginshiƙai yadda iska ba za ta faɗar da shi ba kuma har yanzu ana amfani da dabararsu.

    Su ne ake zaton sun ƙirƙiro taya mai juyawa (wheel). Su ne kuma suka ƙirƙiro (gravity flow irrigation). Su ne suka fara yin tsarin makaranta a tarihin ɗan Adam, haka kuma su ne suka ƙirƙiro gasasshen tubali na gini (Adler p. 15). Sun ƙware a ƙirar kayan ƙarafa (bronze), da tukwane masu juyawa, da kekuna masu tayar ƙarfe da kwale-kwale da sassaƙa da manyan gininnika da kuma abinda ya fi kowane mahimanci –plow.

    An samu waɗannan bayanai a cikin dubunnan kayayakin da suka zana a wurare daban-daban. Sumerians sun shahara a harkar saƙa da rini kuma suna yin kaya na ƙasaita shuwagabaninsu na sa wannan kayayyaki masu kyau da burgewa. Wannan sana’oin sun haɓaka kasuwanci a garuruwan Mesopotamia da kuma cinikayya tsakanin su da sauran ƙasashe. Ana kai kayansu ƙasashe daban-daban. Kuma saboda wannan arziƙi da ƙasar take da shi shi ne yasa ake yin gagarumin biki na ƙasaita wanda ya sa ƙasar ta shahara (McNeill).

    Shekaru kamar 4200 da suka shige, wani mahari, kuma ɗan Semitic, Sargon (the Great) ya shigo ya cinye ƙasar Mesopotamia ya kafa mulkinsa da daularsa a garin Akkad kusa da garin Baghdad (ta wannan zamanin). Kafin zuwan Sumerians a garuruwansu suke babu sarki ɗaya da yake mulkar su,  shi ne ya haɗa ƙasar ƙarƙashin jagoranci ɗaya.

    Daular Akkadiyawa ba ta kai shekara 200 ba amma duk da haka sun yadda da wayewar kai irin na ƙasar Sumeria a gabas ta tsakiya. Kuma mulkinsu ya haɗa gabas ta tsakiya da kuma Misira. Bayan wannan daular ta Akkad aka samu daular Babylon daga nan kuma aka sami daular Assyria.

    Abinda yasa cewa aka yi Daular Akkad “Empire” ta farko saboda su ne suka fara mulkar  mutane daban a wata ƙasar. Mulkinsu ya faɗaɗa a doran ƙasa daga arewancin Iraqi zuwa kudancin ƙasar. Ita ce “Empire” ta doran ƙasa ta farko a tarihin duniya. Bayansu an samu “Empires” iri-iri a tarihin duniya (Howe 2002).

    Domin karanta Wayewar Farko danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Wayewar Kan Ɗan Adam 3

    Wayewar Kan Ɗan Adam 3

    Catal Huyuk

    Catal Huyuk (Hill at Fork in the Road) wannan wurin yana ƙasar Turkey inda aka sani da Anatolia (Ancient-ta daɗeɗɗen lokacin) a kusa da shahararen garin Konya. A shekarar 1961 aka fara tono wannan mazauni na mutane wanda ya fi shekara 9500. Wannan wuri yana tsakanin tsaunuka (hills) biyu kuma abubuwan da aka tono sun nuna cewa mutane sun fara zama a babban gari kafin a wannan ƙasa Mesopotamia.

    Saboda haka wataƙil idan bincike ya tabbata nan gaba wannan ƙasar ita ce za ta zama tushen Wayewar Kan Dan Adam. An tono gidaje 160 kuma ana zaton mazauna garin sun kai mutum 2,500. Gidajen ana shigarsu ne da tsani ta sama, idan an shiga sai a ɗauke, kuma babu tituna ko hanyoyi a tsakanin gidajen. An sami zane da fenti kalolin ja da baƙi da fari.

    Masana suna zaton mazauna wannan wuri mafarauta da manoma ne saboda kayayyakin da aka samu kuma ƙasar wurin na da albarka saboda tana kusa da tabkin Carsamba. An sami sassaƙen abin bauta mai kan namiji da mace wanda yasa wasu suke zaton daidaiton maza da mata a wannan babban mazaunin mutane. Kuma kusa da wannan wurin an tono abubuwa a Nevalli Cori da Gobekli Tepe wanda ana ganin cewa mazaunin Neolithic ne shekara kamar 10000 zuwa 11500.

    An kuma samu abubuwa da suka nuna harkar noma da kiwo. A Gobekli Tepe a dutsen Taurus an tono wurin bauta (cult sanctuary) kuma babban wuri wanda a ƙalla ana zaton mutum 500 suka yi aikinsa sun buƙaci kayan aiki masu da kuma tsarin gudanawar (logistics). A wani gari Hacilar kusa da Catal Huyuk an sami wata tukunya da aka yi ta kamar kan ɗan Adam wadda ta fi shekara 7500 (Hattstein 2009: 12-15). 

    Mesopotamia

    Wayewar kan ɗan Adam ta fara ne daga lokacin da ya fara noma a ƙalla shekara 10000 a kusa da kogin Nile ta ƙasar Misira (Egypt) (Guest 1979: 5). Amma wasu masana tarihi irin su McNeil (1967: 11) suna da ra’ayin cewa a Mesopotamia aka fara noma tsakanin shekaru 10000 da kuma 8500 da suka shige.

    A wannan lokacin mazauna Mesopotamia ana kiransu Sumerians sun fito daga Arewa kuma su “Caucasians” ne ba “Semites” ba ne wanda suka zo daga baya daga ƙasar Larabawa kuma suka mallaki ƙasar (Clement 1936: 71). Sumerians sun fara sarrafa muhallinsu da noma da kuma kiwo. Sun zo wannan wuri daga wasu ƙasashen saboda ni’imar wurin kuma kafin su fara noma su ma kiwo da kuma tara abubuwan tsirrai suke yi sannan kan su waye suka fara kafa ƙauyuka (Haughen 2009: 45).

    Sun fara noman alkama da barley. Dabbobin su kuma su ne tumakai da awaki. Noman da suka fara shi ne ake kira da “slash and burn agriculture” wato idan ni’imar wuri ta ƙare sai su bar wurin su matsa gaba zuwa wasu shekaru kafin su dawo wurin. 

    Wannan irin noma ya faru ne a wuraren da suke da ruwan sama. Wuraren da babu ruwan sama kuma mutanen sun dogara da ruwan kogunan Euphrates da Tigris. Saboda haka suka ƙirƙiro dabarun ɗauko ruwa daga koguna zuwa gonaki a bakin kogunan. Wannan babban aiki ne mai buƙatar dubunnan mutane da kuma ƙwarewa da tsarin zamantakewa saboda abin ya fi ƙarfin ɗaiɗaikun magidanta.

    Kafin wannan tsari magidanta suna noma kawai na abincin da zai ishe su kowa yana zaman kansa, sai dai kawai abubuwan da suka shafi biki da kuma tarukan addini. Amma noma a bakin koguna yasa tsarin zamantakewa ya canja. Ma’aikata sun ƙaru kuma dole aka samar da yanayin gudanar da aikin da samun masu ƙwarewa a harkar tafiyar da mutane (managerial elite).

    Babu wanda yasan lokacin da aka fara samun ƙwararru amma dai ana zaton cewa lokacin da mutane suka fara yaƙar juna daga nan wasu suka fara nuna ƙarfinsu da ƙwarewarsu. Sannan kuma wanda suke da ilmin addini na wancan lokacin su ma suka fara bayyana kuma an hankali addinin mutanen Mesopotamia ya fara ƙarfi da ire-iren ibadunsu. Masu kula da sha’anin suka sa mutane suka fara yi wa abubuwan bautarsu hidima  (McNeil 1967: 13). 

    An samu bayani irin na zane yadda rayuwa ta kasance a wani gari mai suna Lagash. Wannan gari an raba shi gida uku (ko ɓangarori uku) daidai da harajin da magidanta suke biya ga abin bautarsu a wannan lokaci. Masana tarihi sun yi bayani cewa harajin da mutanen garin ke biya ya fi ƙarfin kuɗin da suke samu daga amfanin noman damina.

    Saboda haka dole su yi wani aikin ƙarfi a cikin shekarar don su biya harajin da shuwagabanin addininsu suka ɗora musu. Wannan yasa an ƙirƙiro noman rani (irrigation) mutane suna yin aiki a wuraren noman ana biyansu daga harajin da suka biya na kayan noman damina. Wasu kuma suna yin wasu ayyukan da shuwagabanin addinin suka sa su.

    Wannan ayyuka da aka ƙirƙiro sun sa mutane sun bambanta a ƙwarewa iri-iri, kuma aka fara sana’oi kamar ƙirar gwal, sarrafa katako, ɗinki, zanen gidaje, kaɗe-kaɗe, waƙa da sauran abubuwan nishaɗi don farantawa abubuwan bauta.

    Waɗannan ma’ikata ba sa yin noma saboda haka sun sami lokaci na ƙwarewa akan ayyukansu don ba su raba hankalinsu. Wannan yasa wayewar kai ta bayana a wannan garuruwa da suka kafu a tabkin Tigris da Eupharates 5000 zuwa 6000 lokacin da aka fara rubuta abubuwan da suke faruwa a wannan ƙasar ta Mesopotamia. 

    Danna nan don karanta Wayewar Kan Ɗan Adam 2

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Wayewar Kan Ɗan Adam 2

    Wayewar Kan Ɗan Adam 2

    Wasu masana sun ba da sharaɗai na wayewar kai. Sharuɗan sun haɗa da rubutu, a bisa wannan sharaɗi babu wayewar kai ga mutanen da ba su da rubutu. Wasu kuma sun ƙara da sharaɗin ƙira (technology), a wannan ra’ayin babu wayewar kai ga wanda ba sa gini, ko da dutse ko da ɓangori (brick) (Robert).

    Wasu masana irin su Vico sun samu wayewar da ba a rubuta ta ba saboda ya fito da tsari nazarin da zai sa a fahimci irin wannan wayewar (Hughes-Warrington 2015: 324). Sarrafa ƙarfe yana daga cikin alamar wayewar Ɗan Adam saboda cigaban da ya kawo a harkar rayuwa. Ɗan Adam ya fara sarrafa copper ya haɗa ta da lead da tin ta ba shi bronze wanda ya fi ƙarfi (Adler 1996: 10).  

    Saboda rashin manyan gine-gine masu inganci shi ne yasa suke ganin babu wayewar kai a gururuwan masu bauta gargajiya (pagan) na Arewacin Nijeriya, inda suke gine-gine na ƙasa da kuma yayi, idan aka kwatanta su da ƙasar Masar. Gini ana yinsa don ya daɗe, kamar na ƙasar Masar ba don ɗan lokaci kaɗan ba, kamar na wannan mutanen Arewacin Najeriya.

    Wasu masana suna ganin cewa wayewar kai na tabbata ne idan mutane suka yi yawa kuma kowa yana da sana’a ko aiki da kuma ƙwarewa a kai: wasu suna gini, wasu na ƙira, wasu yin tukwane da sauransu kuma sun dogara da wasu su yi aikin samu abinci wato manoma da masunta da kuma mikiyaya.

    Duk da wannan sharaɗai babu itifaƙi akan ma’anar wayewar kai saboda ana samun abinda ake ganin wayewar kai ne amma bai cika wannan sharaɗai ba. Saboda haka wasu masana sun faɗa cewa abinda ya dace shi ne a ce wayewar kai na tabbata idan aka samu wasu daga cikin wannan sharuɗan (Roberts 1980: 10).

    Wayewar Kai abu ne mai sarƙaƙiya a tafarkin wayewa mutane suna haɗa abubuwa da yawa na rayuwa da suka shafi aiki ko ɗabi’a. Saboda wayewa tana ƙaruwa da ƙarin ilmi da kuma fahimtar rayuwa. A kullum mutane ƙaruwa suke da ilmi da kuma fasaha wannan shi ne wayewa ba a kasance a wuri ɗaya ba.

    Misali yanzu ilmin fasaha da ƙira ya sa mutane suna bincike a sararin samaniya kuma har wata ma sun je. Fasaha tana bambanta tsakanin wanda suka waye da kuma wanda ba su waye ba (Roberts 1980: 10).

    Wasu daga cikin masana tarihi da ‘yan jarida na turai suna ganin cewa babu wata wayewa idan ba ta turai ba ce. Duk abinda ya faru kafin turai ta mallaki duniya ba waye ba ne a wurinsa. Wanda ya ƙarfafa wannan ra’ayi shi ne Kenneth Clark a fim ɗinsa na talabijin da aka nuna a BBC mai suna “Civilization A Personal View”.

    A wannan fim ya kore duk wani wayewar kai na ko ina sai dai na turai ta yamma har na Byzantine Ravenna, Celtic Hebrides, Viking Norway da kuma mulkin Charlemagne. A fahimtarsa tun daga faɗuwar Rome har zuwa tashin turai ta yamma babu wayewa. A fahimtarsa babu wayewa kafin zuwa addinin Krista kuma babu wayewa a gabas ɗin duniya (Ferguson 2011: 1-2). 

    Masu nazarin Civilization na ƙasashen turai sun bambanta shi da Culture (al’adu) a ra’ayinsu Culture ta al’ummar da ba su waye ba ce (primitive) shi kuma Civilization na wanda su ka waye ne.

    Don karanta Wayewar Ɗan Kan Adam 1 danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Auren Annabi SAW Da Nana Saudat

    Auren Annabi SAW Da Nana Saudat

    An ɗaura auren annabi (Sallallahu alaihi wasallam) da Sayyada Saudat ‘yar Zam’ata Baƙuraishiya, sannan sunan mahaifiyarta shi ne Al-shamus ‘yar Ƙais daga ƙabilar Banu Najar.

    Bayan rasuwar Sayyada Khadija da wata ɗaya cikin watan da Sayyada Khadija ta rasu, bayan rasuwar mijinta ɗan Baffanta Assakaranu Bin Amru, haƙiƙa ta yi imani da Allah (SWT) da manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam),  Sannan ta saɓawa ‘yan uwanta da ɗan Baffanta (na bautan gumaka).

    Haka kuma ta yi hijira tare da mijinta zuwa Habasha a karo na biyu (2), akan hanyarsu ta dawowa mijinta ya rasu Assakaranu Bin Amru Bin Abdulsham. Sannan bayan rasuwarsa Sayyada Saudat ta dawo daga Habasha, sannan kuma iyayenta duk babu musulmi a ciki, sai wata sahabiya ana kiranta Khaulatu Bin Hakim, sai ta zo ta samu annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam), a lokacin ana cikin ƙuncin raɗaɗin rasuwar Sayyada Khadija.

    Sai ta zo ta sami annabi  (Sallallahu alaihi wasallam) tace da shi akwai wata mace mijinta ya rasu kuma ta yi Imani da kai, amma ‘yan uwanta kafirai ne, idan ta koma gida za su iya wulaƙanta, ko za ka iya aurenta ne? Sai annabi ya tura wannan sahabiya Khaulatu `yar Hakim ta nema masa auranta.

    Sai ko ita Saudatu `yar Zam’atu amince, aka ɗaura aurensu ta zama ita ce matar annabi (Sallallahu alaihi wasallam) ta biyu bayan Khadija Bin Khuwailid. Sannan Saudat ta rasu a watan Satumba ko Oktoba a shekara ta 674 miladiyya. Daga ƙarshe Saudat tana da ɗa guda ɗaya wanda ta haife shi a gurin mijinta na farko, sunan ɗan shi ne Abdurrahman Bin Sakran, an kashe shi a yaƙin Jalula a shekara ta 637.

    Don karanta Auren Annabi SAW Da Nana Khadija danna nan

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu