Juyin -Juya Hali A Rubuce-rubucen Littattafan Adabi

0
153

Duk da cewa maza su suka. fara rubuce tun 1933 Mukhtar (2004). Amma wacce ta fara Rubuta ƙagaggen Labari na Hausa ita ce Hafsatu Abdulwaheed, Abdalla Uba Adamu (2024). Mace ta farko ‘Yar Arewa da fara rubuce-rubuce a Hausa da Fulatanci ita ce Dadasare Abdullahi Uwargidan Dr. R M. East takan taimaka wa Maigidanta Jaumisare (R.M. East) da labaran da akan saka a Jaridar Gaskiya Ta fi Kwabo da kuma tace labaran. Dadasare (2019)

Waɗannan su ne wasu daga cikin talife-talifen wannan marubuciya wacce babu shakka ta yi namijin ƙoƙari a wannan nau’i na Adabin na tailfin Hausa da Fultanci. Bayan sai ita Zuwaira Isa wacce ta rubuta ƙagaggen littafi a 1972 sannan tana ‘yar makaranta a Rikkos can jos amma ba a buga ba sai daga baya, mai suna Ɗaki Ba Ya Tashi Jinka Ya Zauna.

Ya iso kasuwar ta Kano tun 1992, to sai bayan shekaru uku ne wato a 1995 littafin Bilkisu ya fara bayyana kamar yadda aka gani a jerin littattafan nata, a sama. Ita kuma Bilkisu it ace ta fara rubuta littafai masu na Hausa, kimanin guda ashirin cikin shekaru uku zuwa huɗu.

Littattafan zuwaira Isa Danlami Jos sun haɗa har da:

  • Zuwaira Isa daki Ya Tashi Jinka Ta Zauna (1992) Gaskiya corporation Ltd.Zaria.
  • Zuwaira Isa Labarin So (1995) littafi na 1-3 City Publishers Jakara, Kano.
  • Zuwaira Isa Sants in Soyayya (1996) littafi na 1-3 city Business Centre Daneji, Kano.
  • Zuwaira Isa  kissar Mata (1996) City Publishers Goron Dutse Road Jakara,Kano.
  • Zuwaira Isa  Wahala Siraxin Masoya (1997) Sauqi Bookshop and Publishing Company Sabon Gari,Kano.
  • Zuwaira Isa  ‘Ya’ya Mata (1999) littafi na 1-3 M Square Telecomm,Zoo Road, Kano.

Sauran littattafan wannan marubuciya da muka ji labarinsu amma ba su zo hannuna ba har lokacin da zan buga wannan littafi sun haɗa har da:-

  • Zuwaira Isa  A Lallaɓa Auren Zamani
  • Zuwaira Isa  Mowar Mata
  • Zuwaira Isa  Ƙwarya Ta Bi Ƙwarya
  • Zuwaira Isa  Kara Da Kiyashi
  • Zuwaira Isa  A Ci Duniya Da Tsinke
  • Zuwaira Isa  Duniya Labari, Ciwon ƙauna, ƙishirwar Bege (d.s.)

Bayan waɗannan, mata marubuta, daga cikin maza kuma waɗanda suka fi fice kamar yadda wallafe-wallafe ya nuna akwai Nazir Adam Salih da kuma Ado Ahmad Gidan Dabino. Wasu daga cikin littattafan Nazir Adam Salih sun haɗa da:-

  • Nazir Adam Salih  Me Ya Fi Kuxi? Kamnas Publishers, Kano.
  • Nazir Adam Salih  Kibiyar Ajali littafi na 1-2 (1996) City Business Centre Daneji, Kano.
  • Nazir Adam Salih  Naira Da Kwabo littafi na 1-2 (1998) Jet Age Publishers Kano.
  • Nazir Adam Salih Birnin Sarauniya (1998) Qamnas Publishers Kano.
  • Nazir Adam Salih Ta Leƙo Ta Koma (b. kw.) Qamnas Publishers Kano.
  • Nazir Adam Salih Mutuwar Kasko (1999) Layeet Printers Kano.
  • Nazir Adam Salih  Aljani Ya Taka Wuta (2000) Jet Age Printers Kano.
  • Nazir Adam Salih A Ci Bulus (b. kw.)
  • Nazir Adam Salih  Kudi Da Maciji (b. kw.)
  • Nazir Adam Salih  Damisar Takarda (2000) Jet age Printers Kano.

Amma shi Ado Ahmed Gidan Dabino shi ma ya taka muhimmiyar rawa a cikin wannan nau’in adabi inda littattafansa suka fito kamar haka:-

  • In Da So Da Ƙauna (1991) Gidan Dabino Ado Ahmed  Publishers, Kano.
  • Masoyin Zamani I (1993) Gidan Dabino Publishers, Kano.
  • Wani Hanin Ga Allah (1994) Gidan Dabino Publishers, Kano.
  • Kaico! (1996) Gidan Dabino Publishers, Kano.
  • Duniya Sai Sannu (1997) Gidan Dabino Publishers, Kano. Mukhtar (2004)

Adabin Kasuwar Kano

To amma a cikin shekarar 1984 wata al’adar rubuce-rubuce ta ƙagaggun littattafai ta kunno kai wadda aka sa wa suna Adabin Kasuwar Kano, a Turance “Kano Market Literature”. An sami wani jigo na soyayya inda ya yi tasiri sosai da sosai a cikin wannan adabin. Daga cikin waɗanda suka share fage akwai irin su littafin;

  • Rabin Raina littafi na ɗaya(1984) na Talatu Wada Ahmed
  • Soyayya Gamon Jini (1986) na Ibrahim Hamza Abdullahi
  • In Da Rai (1987) na Idris Imam
  • Budurwar Zuciya (1987) na Balaraba Ramat Yakubu
  • Kogin Soyayya (1988) na A.M. Zahraddeen
  •  Idan So Cuta Ne (1989) na Yusuf M. Adamu.

(Duba muƙalar Yusuf M. Adamu 1996).

Bayan wannan an sami mace a karon farko wacce ta yi fice a cikin rubutun adabi na Hausa inda ta rubuta ƙagaggun littattafai a ƙalla sama da guda ashirin (20) a cikin shekaru huɗu rak. Wannan kuwa ita ce uwargida Bilkisu Salisu Ahmed Funtuwa, wadda kafin ta yi aure ake kira Bilkisu Ibrahim. Nabature Funtuwa.

Ita dai wannan marubuciya ta yi fice a kan waɗannan rubuce-rubuce ba ma kawai tsakanin mata ba, hatta cikin mazan ma na wannan nau’in adabin babu wanda ya kamo ta. Binciken da muka yi, ya nuna cewa. Makaranta littattafan wannan nau’in adabin har bincikawa sukan yi ko sabon littafinta ya fito su yi maza su karanta don kada wani ya ba su labarinsa. Kaɗan daga cikin irin waɗannan rubuce-rubuce nata sun haɗa har da:-

  • Bilkisu S.A.F Allura Cikin Ruwa, (1995) Gidan Dabino Publishers Kano, Nijeriya.
  • Bilkisu S.A.F Sirrin Ɓoye littafi na 1-2 (1996) City Publishers Jakara Kano, Nigeria
  • Bilkisu S.A.F Wa Ya San Gobe littafi na 1-3 (1996) City Pulishers Jakara Kano, Nijeriya.
  • Bilkisu S.A.F Ƙarya Fure Take, littafi na 1-2 (1996) Nabila Surayya Bookshop.
  • Bilkisu S.A.F Gaskiya Na Mafaɗinta littafi na 1-2 (1997) Printed
  • Bilkisu S.A.F Kyan Ɗan Maciji littafi na 1-2 (1997) Printed
  • Bilkisu S.A.F In Da kwaɗayi littafi na 1-2 (1998).
  • Bilkisu S.A.F Ki Yarda Da Ni (b. kw) littafi na 1-2
  • Bilkisu S.A.F Sa’adatu Sa’ar Mata (b. kw)
  • Bilkisu S.A.F Maryamu (1999) littafi na 1-2
  • Bilkisu S.A.F Mugun Zama (1999) littafi na 1-2 Anti Bilki Bookshop Kano
  • Bilkisu S.A.F Kowa Ya Raina Tsaiwar Wata (1999) littafi nal-2 Anti Bilki Bookshop Kano.

Kammalawa

A taƙaice, takardar wata tafarki ce a fagen adabin Hausa, musamman ta fuskar rubuce-rubucen da suka shafi tarbiyya da gyaran halaye. Saboda haka Littattafan ƙagaggun Labari ba wai labaran soyayya kawai suke ba, har ila yau suna nuna irin rawar da adabi ke takawa wajen sauya tunani da ɗabi’a.

A matsayin shawara, akwai buƙatar a ci gaba da nazarin irin waɗannan marubuta domin fahimtar tasirin rubuce-rubucen Hausa wajen gina tarbiyyar matasa da inganta al’ummar Hausawa gaba ɗaya. Duk waɗannan suna jan kunne ne da a tarbiyyantar da mutune su yi aiki da tarbiyya a cikin mu’amalarsu da mutane.

Ana cusa tarbiyya wajen horar da mutane ko ilimantar da su, ko ta hanyar rubutu, domin a gano kaifin hankalin mai karatu idan da buƙatar gyara a gyara maka ko a cusa musu labarai na ban tausayi ko na jin ƙai ko ta hanyar yi musu tarbiyyar ta ta hanyar gargajiya misali Karin Magana da Tatsuniya ko kuma ta hanyar gaya musu wani labari mai daɗi na baka ko a rubutaccen ƙagaggen labari wanda kuma shi ne muka yi magana kai.

Wanann bayanin an ciro shi ne daga muƙalar da aka gabatar a taron makon Hausa wanda ya gabata a Ranar 24 ga wata Oktoba 2025 a Jami’ar Ilimi ta tarayya da ke Bichi.

Danna nan don karanta Samuwar Rubutun Ajami

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceMijin Marigayiya Babi Na Ƙarshe
Labarin na GabaKa Ɗauka Ka Sani
wikiHausa
wikiHausa kundin ilimi (insakulofidiya) ce da ke ilimantar da jama'a yara da manya da maza da mata wajen samun ilimi a saukake, cikin harshen Hausa.