Addu’ar Maganin Damuwa Da Baƙin Ciki

0
35

khairatu.shehu

اللّهُمَّ إِنِّي عَبْدُكَ ابْنُ عَبْدِكَ ابْنُ أَمَتِكَ، نَاصِيَتِيبيَدِكَ ، مَاضٍ فِيَّ حُكْمُكَ، عَدْلٌ فِيَّ قَضَاءُكَ أسْأَلُكَ بِكُلِّ اسْمٍ هُوَ لَكَ سَمَّيْتَ بِهِ نَفْسَكَ أَوأَنْزَلْتَهُ فِي كِتَابِكَ ، أَوْ عَلَّمْتَهُ أَحَداً مِنْ خَلْقِكَ أَوْ اسْتَأْثَرْتَ بِهِ فِي عِلْمِ الْغَيْبِ عِنْدَكَ أَنْ تَجْعَلَ
الْقُرْآنَ رَبيعَ قَلْبِي ، وَنُورَ صَدْرِي ، وَحَلاءَحُزْنِي وَذَهَابَ هَمِّيَْ

Allahumma inni abduka inbnu abdika ibnu amatika,nasiyatee biyadika,madin fiyya hukmuka, adlun fiyya ƙada’uka, as’aluka bi kulli ismin huwa laka sammaita bihi nafsaka au anzaltahu fee khitabika, au allamtahu ahadan min khal’ƙika awistaasarta bihi fee ilmil gaibi indaka an taj’alal ƙur’ana rabee’a ƙalbee,wa nura sadree wajala’a huznee wazahaba hammee.

Ya Allah! Ni bawanka ne, kuma ɗan bawanka, kuma ɗan baiwarka. Makwarkwaɗata a Hannunka take, hukuncinka zartacce ne a kai na, kuma ƙaddararka gare ni mai adalci ce. Ina roƙon Ka da kowane Suna naka, Wanda Ka ambaci Kanka da Shi, ko Ka saukar da Shi a cikin Littafinka, ko Ka sanar da Shi ga wani daga cikin halittarka, ko Ka keɓance Kanka da saninsa a cikin ilimin da ke da ke wurin Ka, da Ka sanya Alkur’ani ya zama kaka ga zuciyata, da haske ga ƙirjina, da kwaranyewa ga baƙin cikina, da kuma mai tafiyar da damuwata.

اللّهُم إنِّي أَعُوْذُ بِكَ مِنَ الْهَمِّ وَالْحُزْن، وَالْعَجْز وَالْكَسَلِ وَالْبَحْلِ وَالْجُبْنِ ، وَضَلْعِ الدَّيْنِ وَغَلَبَةِالرِّجَال

Allahumma inni a’uzu bika minal hammi walhuzin, wal’ajzi walkasal walbukli waljubni, wadal’il deeni wagalabatir rijaal.

Ya Allah! Ina neman tsarinka daga damuwa, da baƙin ciki, da gajiyawa, da lalaci, da rowa, da ragwantaka, da nauyin bashi, da rinjayen mazaje.

Karanta Addu’ar Addu’ar Shiga Wata Karkara Ko Wani Gari

Edita@rumasau-kallamu

 

labarin da ya wuceYadda Falalar Suratul Ƙulhuwallahu Ahad Take
Labarin na GabaAddu’ar Wanda Ya Ji Tsoron Zaluncin Wani Mai Iko