An karɓo daga jabir (Radiyallahu anhu) ya ce: Haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam) ya ce: A”Duk buƙatar da aka sha ruwan zamzam saboda ita, Allah zai biya wannan buƙatar”. (Sahihin hadisi ne duba sahihul jami’i 5502).
Abdullahi Ibn Abbas (Radiyallahu anhu) ya kasance idan zai sha ruwan zamzam yana karanta wannan addu’ar; Allahum inni as’aluka ilman nafi’an wa riziƙan wasi’an, wa shifa’an min kulli da’in”. Hakim ne ya ruwaito.
Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Salla A Masallacin Haramin Makka Da Madina danna nan.
Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Raya Daren Lailatul Ƙadari danna nan.
Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.
Edita; RMK