Ɗagowa Daga Ruku’u: Bayan kowacce gaɓa ta koma mazauninta; ya tsaya daram kar ya mayar da hannuwansa kan ƙirjinsa, wato; (Qabdu) su ne kaɗai zai bar su a sake kamar yadda mafi yawan malamai suka ce.
Sannan sai ya yi kabbara, ya tafi sujuda; zai tafi sujuda ne da hannuwansa a wajan wasu malamai; ko da gwuiwar kafafunsa, a wajan wasu malamai ana so ya saɓawa yadda raƙumi ke faɗuwa idan zai kwanta.
Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Tafiya Sujudah danna nan.
Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Yin Sallar Istihara danna nan.