Wasu Alamomin Da Ake Iya Gane Mai Shan Kayan Maye

0
8

khairatu.shehu

Akwai wasu alamomi da ake iya gane masu shan ƙwayoyi. Wasu daga cikinsu sun haɗa da:

  • Yawan tara kwalaben maganin mura da tari ko sirinji
  • Allura ko kuma yankakkun takardu
  • Yawan kunna turaren (ƙamshi) wuta a cikin ɗakin matasa
  • Ƙin shiga cikin mutane, musamman a gida
  • Yawan ƙamshin turare iri daban-daban don kawar da warin da yake tare da su
  • Rashin ƙoƙari a makaranta (amma wata sa’a kuma an ce wai ƙoƙari suke sa wa)
  • Yawan ladabi da gaishe da mutane (wanda ba a saba gani a da ba, ko kuma ana yi amma lokaci ɗaya a ga abin ya ƙaru)
  • Lokaci ɗaya yarinya ta sauya ƙawaye, ba ta kuma damu da ƙawayenta na da ba, sannan yanayin harkokinta su sauya
  • Rashin dawowa gida da wuri da daddare (don shaye- shayen miyagun ƙwayoyin an fi yin su daga yamma zuwa dare)
  • Sauyin halaye da ɗabi’un yarinya waɗanda ba a saba da ganin ta tana yi ba
  • Yawan sa baƙin tabarau
  • Yawan son tafiya wajen biki, a je kuma a daɗe ba a dawo ba
  • Sauyawar yanayin bakin matashiya, a dinga ganin ta tana nuna wani launi daban a leɓe ko kan harshe
  • Sauyawar ƙwayar ido ta koma ja, idon yana iya ɗaukar fiye awa biyar bai koma daidai yadda yake kafin a sha ƙwayar ba, ko kuma idon ya dinga rawa, kamar ƙwalla ko kuma ana rufe shi ana buɗewa
  • Karkatar da kai ko kaɗa kai, musamman ga masu shan hodar Iblis (cocaine)
  • Lokacin da ake magana da matashi ko matashiya a ji suna sambatu marasa kan gado
  • Yawan yin tamɓele a maganganunsu
  • Zazzare idanuwa haka kawai, wanda suke kira ‘cin magani’
  • Yawan fushi ko ɗacin rai
  • Neman faɗa babu dalili
  • Yawan barci.

Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Mata Da Shaye-shayen Kayan Maye: Ina Mafita? Wanda Ado Ahmad Gidan Dabino MON ya wallafa.

Danna nan don karanta Matsalolin Da ‘Yan Maye Suke Cin Karo Da Su

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceMatsalolin Da ‘Yan Maye Suke Cin Karo Da Su
Labarin na GabaIna Mafita?
Ado Ahmad Gidan Dabino
Shahararren marubucin littattafan Hausa ne a Najeriya, sannan mai shiryawa da bayar da umarni sannan ɗan wasa ne a shirin finafinan Hausa kuma ɗan jarida. Tare da shi aka kafa wasu ƙungoyoyi na marubuta da masu shirya finafinai. Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta karrama shi da lambar yabo ta ƙasa mai taken, Member of the Order of the Niger (MON) bisa hidimta wa jama'a da yake yi a cikin ayyukansa.