Tag: bahaushe

  • Addinin Bahaushe

    Addinin Bahaushe

    Kafin zuwan addinin Musulunci yammacin Afrika,  Bahaushe na addinin gargajiya, wasu na bautar iskokai,  wasu mutum-mutumin itace, ko dodo, ko rana, ko ruwa  da dabbobi (Malumfashi, 2008 & Adamu, 1997). Amma  a yau, yawancin Hausawa Musulmai ne, a kan sami  tsirarun Kiristoti da masu addinin gargajiya (NNPC,  2007).

    Domin karanta cikekken littafin Danna nan 
  • Tsarin Zamantakewar Bahaushe

    Tsarin Zamantakewar Bahaushe

    Tun asali, Bahaushe, ba mutum ba ne mai zama kara  zube ba, al’ummar Hausawa na qaru ne ta hanyar aure,  bayan yarjejjeniya tsakanin iyayen miji da na mata.

    Kafin zuwan addinin Musulunci Bahaushe ba shi da  iyakar adadin mata da zai aura, hasali ma, ana tinqaho da  yawan ‘ya’ya da mutum ke da su. 

    1. Aure  

    Aure shi ne qulla yarjejjeniya don halartawa mace da  namiji su zauna a matsayin mata da miji, su kuma haifi  ‘ya’ya da xaukar xawainiyyarsu (Alhassan, 1980 &  Encarta, 2009). 

    Neman Aure  

    A da a qasar Hausa, iyaye suke zavawa ‘ya’yansu wanda  za su aura, ba a barin yaro ya je a nemo mata da kansa,  har ana faxin, ‚ta yaro kyau take, ba ta qarko‛. Ta  vangaren iyayen mace kuma, ba sa amincewa wanda ba  shi da sana’a ‘ya, su ma sun fi karkata su ba wa wanda  ba za ta sha wahala ba a hannunsa ba. A da, a kan iya yi  wa yarinya miji tun kafin a haife ta, ko tun tana jaririya,  ko tun tana yarinya ko kwaila. Iyaye kan iya haxa aure  da wanda suke son haxa zumunci cikin dangi, ko  jagororin yanki, ko abokan iyaye. 

    Domin Karanta Bayani akan Zuwan Ilimi Qasar Hausa Danna nan 

    A wani lokacin kuma, idan saurayi ya ga budurwa, zai  faxawa abokinsa ko mahaifiyyar ko kawunsa don su sanar da mahaifinsa ko wakilinsa domin nema masa izinin tsayuwa da yarinya sannan a qulla soyayya, domin  a al’adar Bahaushe, har a Musulunci ba a yarda a keve  ko cakuxuwa tsakanin mace da namiji ba.

    Shi ya a bisa  al’ada, bayan samun amincewa daga iyayen yarinya,  saurayi ne zai riqa zuwa gidan su yarinya domin hira, da  yammaci ko da daddare, a cikin zauren gida, ko qofar  gida, ko gindin bishiya ta kusa da gida, domin ana sa  musu ido7. A wajen zance galibi ana tattauna al’amuan  yau da kullum, da nufin fahimtar juna.  

    Bayan samun fahimtar juna tsakanin namiji da mace,  dangin namiji za su aika dattawa da goro (wani lokacin  da kuxi) domin kai wa gaisuwa. A nan, dangin maza za  su nemi auren yarinya, su kuma dangin mata za su  amince, ko su qi amincewa, ko su amince da sa  sharruxxa. 

    Domin Karanta Ma’anar Bahaushe Danna nan 

    Bayan gaisuwar dattajai, akwai gaisuwar abokan saurayi,  shi ma za a je da goro, domin a gaisa da gidan su  budurwa tare da shi mai neman auren (amma shi ba ya  magana, saboda kunya irin ta Bahaushe).  

    Na-Gani-Ina-Son  

    Na-gani-ina-son kaya ne da manemin aure ke haxawa ya  kai gidan su budurwa. Kafin shigowar Larabawa da  Turawa qasar Hausa, Bahaushe na haxa kayan noma (abin da ake girbe na abinci) a matsayin kayan na-gani ina-so. Zuwan Larabawa da sabbin tufafi, kayan qawa da  kwalliya sai ya koma kayan lefe a cikin kwalla, jaka, har  zuwan akwati, za a haxa tufafin sawa, da kayan  kwalliya, da goro da kuxi, dattijai (maza ko mata) ne shi  ma suke kaiwa gidan su amarya. Bisa al’ada, za a rinqa  yawo da wannan kaya, gidajen dangi domin a sa albarka. 

    Ba al’adar Bahaushe ba ce budurwa ta bi saurayi xakinsa, ko fita yawon  shaqatawa, ko hira a cikin mota, waxannan duk kwaikwayo daga wasu  qabilu, da kuma bayan zuwan Turawa.

    Wani lokacin, a kan haxa kayan na-gani-ina-so da kayan  yankan rana domin a yanke ranar bikin aure. Dangin mace  za su sa ranar da suka shirya domin a zo a karvi auren  mace. Idan gidan maza ba su shirya ba za su nemi a xaga  musu. Daga nan akwai ‘yan kyaututtuka zance don qara  danqon soyayya da saurayi ke ba wa budurwa. 

    Domin Karanta Al’adar Bahaushe Danna nan 

    Bikin Aure  

    Kafin kwana xaya da xaurin aure, Bahaushe yana da  al’adar sakin lalle. Babanai mata ke sawa mace lalle a  gidansu, haka shi ma namiji za a sa masa lalle a daren  jajiberan xin xaurin aure. 

    A washegarin xaurin aure, maza za su taru, dangin maza su  kawo sadaki, su nemi a ba su auren mace, cikin siga, a raba  goro, a yi addu’a, a watse. Kafin zuwan addinin Musulunci,  Bahaushe na bayar da kayan noma, ko dabba a matsayin  sadaki. Da yammancin xaurin aure kuma, akwai al’adar  chuxa (wankan ango ga namiji8), washegari da rana, gidan  maza da mata, suna yini, za a dafa abinci a ci, da daddare  kuma a kai amarya gidanta ‘yan mata na tafiya suna waqe  da tafi.

    A da, ana kai amarya a kan doki, ko amalanke, har  zamanin ababen hawa na zamani (mota). Iyayenta za su  siya mata gado da katifa, da kwanuka, da turmi da tavarya,  da tukunyar girki. Za a je xakin amarya a yi mata jeren  kwanuka, da kateb, da kujeru. 

    A wajen xaukar amarya, akwai kuxin uwar-xaki, da kuxin  qawayen amarya da na buxar baki/kai da abokan ango ko  ango ke bayarwa. Bayan an kai amarya, akwai kayan gara da gidan mace ke kaiwa gidan maza, kayan toye-toye ne,  da kayan abinci, da mai, da gishiri, wasu kuma har da  babbar riga wa ango don qarfafa zumunci. 

    Domin Karanta wane ne bahaushe Danna Nan

    Kamar a Haxejia, a yammacin chuxa, ango zai sa babbar riga, ya fito  tsakar gida, babanai da ‘yan uwansa mata, da makwafta su zo suna ta saka  masa kuxi a aljihu.

    Daga cikin al’adun da Bahaushe ya aro a bikin aure, akwai,  ashobe (anko) daga Yarbawa, sannan an xauko wasu al’adu  masu nashe kuxi a wajen biki, partyn Arabian night, Indian  Night, da picnic da party dinner inda za a je ango da  amarya, a xauko DJ da MC, a yi raye-raye a wani  kevantaccen wuri (xakin taro ko otel).  

    Bayan kawo amarya, gidan su amarya kan aiko da kayan  gara, kayan ne na toye-toye, da kayan abinci da mai.  Wani lokacin ana kawo ango har bayan suna ma don  qarfafa zumunci. 

    1. Rainon Ciki, Haihuwa da Suna  

    Yahaya (2001) Idan mace ta xau ciki, Bahaushe na ba wa mai ciki kulawa ta musamman wajen samar ma ta da  abin ci mai kyau, da xauko mata ‘yar aiki. 

    Bayan mace ta haihu da kwana huxu, za a kai kayan  xauri. A kwana na biyar za a dama kunu (na kanwa ko  na tsamiya) a rarrabawa makwafta, ‘yan uwa da abokan  arziki. A rana ta bakwai (bayan sati ya zagayo) kuma za  a tara mutane, a raxawa yaro suna, a raba goro, a yanka  rago, wanzami kuma ya yi wa yaro aski, ya cire masa  ‘yar wuya. A al’adar Bahaushe, ana wankan jego da  tafasassan ruwan zafi, da ganyen darbejiya ko ganyen  sabara har na tsawon kwana arba’in, safe da maraice. 

    1. Tarbiyyar Yara da Xabi’un Bahaushe  

    Bahaushe na shayar da jajiri na shekara biyu, bayan nan  a yaye shi, a kais hi gidan kakanninsa, domin ya mance  da nono. Bahaushe na tarbiyantar da ‘ya’yansa qanana  da tatsuniyoyi, musamman da daddare a gidajen tsofi. Bayan shekaru 5 zuwa 6, a yi wa yaro shayi (kaciya), a  shekera ta bakwai kuma, kais hi wajen koyon sana’a.

    Bahaushe na yi wa yaro horo da faxa, duka, ko harara a  lokacin da yaro zai yi kwaxayi ko qiriniya a wani waje,  surutu a lokacin cin abinci. Xan Bahaushe kan tsugunna  domin nuna ladabi ga babba a lokacin gaisuwa, ko idan  yana masa magana. 

    A da a qasar Hausa, makwafcinka na da iko a kan  ‘ya’yanka, wajen bayar da tarbiyya, ko faxa idan yay i  rashin ji. Wani lokacin makwafci kan iya haxa ‘ya’yan  makwafta don shayi, ko faxa, ko wakilci wajen neman  aure, ko sulhu. 

    Bahaushe na haxa auratayya domin qarfafa zumunci. A  zumuncin unguwa kuwa, kowa zai fito da abinci a zauna  a majalissa. Bahaushe na da kishin makwafcinsa, ‘yan  unguwarsa, ‘yan garinsu, da mai jin harshensa9. BAHAUSHE yana da xabi’u da turbar rayuwa kusa da ta Musulunci, yana da kunya, kawaici, karamci, amana,  ladabi da biyayya, tausayi, zumunci da taimakekkeniya  (Abdullahi, 2008) .

    Domin karanta cikekken littafin Danna nan 

     

  • Adabin Bahaushe

    Adabin Bahaushe

    Adabi kalmar Larabci ce da ke nufin al’ada. Al’ada ta  qunshi dukkan abubuwan da al’aumma ke yi waxanda  suka haxa da ilimi, imani, fasaha, qere-qere, tarbiyya da  sauran halayyen xan Adam (Talyor, 1871). Aristotle  (384 – 322BC) al’ada madubin rayuwa ce. 

    Ubali (2021) Bahaushe na da al’adu ta jiyau da ganau.  Jiyau ita ce al’adar da take cikin tunani, ko ake ji da  kunne, kamar zumunci, kunya, faxa, kishi da sauransu.  Ganau kuma ita al’adar da ake iya gani da ido, ko yi  aikace da gavvan jiki, kamar tufafi, sa’ana, haihuwa da  sauransu. 

    Domin Karanta Ma’anar Bahaushe Danna nan 

    Amma a nan, adabi ana nufi fasahar qirqira ta harshe  cikin tsarin labari, waqe ko kwaikwayon rayuwar zahiri  domin koyar da al’umma tsarin rayuwa mai kyau. Kafin  zuwan rubutu suna adana adabinsu da baka, wannan dalili ya sa tarihi da adabin Bahaushe da yawa suka  salwanta. Kafin zuwan rubutu qasar Hausa, Bahaushe na  amfani da harshe wajen sadar da baka/ka (orature a  Turance, oral + literature = ora(l litera)ture). Wasu  kuma suna amfani da duma, fatun dabbobi, ko dutse, ko wata masaida a jikin mutum. 

    Amfanin adabin baka ga al’ummar Hausawa a wancan  lokaci ana jiyar da yara tarihi, bada tarbiyya cikin  labarun tatsuniyoyi, tarihi, tarihihi, hikaya, al’amara,  karin magana, salon magana, take da qirari, zaurance,  don yaxa martabar Hausa da xabi’unsu, ko wasa  kwakwalwa da gagara gwari (tongue twister), nishaxi,  gina tunani da falsafar rayuwar Hausawa duk da harshen  Hausa (Xangambo, 2008). 

    Domin Karanta Al’adar Bahaushe Danna nan 

    Ta vangare waqa da kixa Bahaushe yana, mawaqa da  makaxan fada (mis., Xankwairo), makaxan sana’a,  makaxan jama’a (misali, Mamman Shata da Haruna Uji),  makaxan maza (mis. Gambo Fagada), makaxan mata  (mis. Barmana Coge da Mai Amada).

    A wajen kixa  Bahaushe na amfani da goge, kalangu, gurmi, kuntigi,  garaya, tafi, qaho, jauje, gula, ganga, duman girke,  kotso, tambari, kwarya, akayau da kayan bushe-bushe  irin su algaita, qaho, kakaki, farai da sauransu (Gusau,  2008). Bahaushe yana da sauran waqoqi da yake a  lokacin aikin gona, aikin gayya, yaqi, ko yara a wajen  wasa, kamar ‘yargalala ta mata da sauransu.  BAHAUSHE na amfani da kixi da waqa, ko waqe domin zuga, jinjina, qara qaimi, zambo, faxakarwa, ko  isar da wani saqo.  

    Domin Karanta wane ne bahaushe Danna Nan

    Bahaushe yana wasan kwaiwayo na gauta da ake a fadar  sarakuna, yana kwaikwayon hawan dokin kara, da tashe  bayan zuwan addinin Musulunci don nishaxi da  faxakarwa.

    Domin karanta cikekken littafin Danna nan 
  • Harshen Bahaushe (Harshen Hausa)

    Harshen Bahaushe (Harshen Hausa)

    Ta dangin harsunan, harshen Hausa xaya ne daga cikin  harsunan ‘Afro-Asiatic’ mai dangi da Larabawa,  Kivxanci, Yahudanci, Habashanci, Somali da sauransu  (Encarta, 2009). 

    A duniyar yau ana qiyasta adadin masu magana da  harshen Hausa sun kai 150,000,000. Harshen Hausa na  da matsayin na 11 a cikin harsuna 65,000 da ake magana  da su a faxin duniya (Limanci, 2019). Hausa ce yare na  25 a harshen da masu ji na asali. Akwai kuma sama da  mutum 30,000,000 da suke jin Hausa a matsayin harshen  a biyu (Enthologue, 2022).  

    Domin Karanta wane ne bahaushe Danna Nan

    Bayan nan, Bahaushe ya ci gaba zama a yankunan  Arewacin Nijiyeriya, Kudanci Nijar, ya kuma yi tafiye tafiye zuwa nahiyar Turawa, Asiya (qasashen Labarawa  da gabashin duniya, qasar Sin da sauransu) ta dalilin  aiki, kasuwanci ko neman ilimi. A yau Hausa ta zama  yaren duniya, ana amfani da ita a manyan gidajen jaridun  radiyo na Amurka (VOA), Birtaniyya (BBC), Jamani  (DW), Chaina (CRI) da sauran manyan qasashe. Tana  daga cikin harsunan da ake fassara huxubar ranar Arfa a  Saudiyya. Tana kuma cikin harsunan fasahar zamani, da  harsunan manhajojin fassara na zamani (misali, Google  Translator).  

    Harshen Hausa yana kusa da harsunan Ron, Bole, Zaar,  Bura, Kamwe, Bata, Angas, Bade, Warji, Buduma,  Musgu, Gidar, Tumak, Nancere, Kera, Dangaleat,  Mukulu, Sokoro, Ngizim, Kare-kare da Kanakuru. 

    Harshen Hausa na qaruwa da qara faxaxa a yankunan  Nijeriya, har tana qoqarin nashe wasu harsunan Nijeriya  da suka haxa da; Yankam, Pyem, Fillanci, Biram,  Gunganci, Fakkanci, Dokkanci, Banganci, Kamuka,  Acipanci, Shanga, Kyanganci, Katab, Kagoro, Tara,  Gure, Kurama, Ninzo, Kadara, Kanin, Badanci, Ngizim,  Bolewa, Tera, Tangale (Sarki, 2005, Bello, 2018,  Sama’ila, 2016 da Buba, 2002).

    Domin Karanta Al’adar Bahaushe Danna nan 

    1. Kare-karen Harshen Hausa  

    Karin harshen (dialect) nufin ma’anin magana a cikin  harshe xaya, da ake samun bambance-bambacen wajen  furuci (accent), ko ginin jimlar, ko zavar kalmomi  tsakanin yanki ko al’umma (sociolect), ko qabila  (ethnolects), ko gida/muhalli (ecolect), ko xaixaikun  mutane (idiolect) (Rotimi et al, 2014) 

    Qaura da Hausawa ke yi zuwa wasu yankuna ta dalilin  kasuwanci, neman ilimi, auratayya, ko cakuxuwa da  wasu qabilu na daga cikin dalilan da ke sabbaba karin  harshen wata al’ummar Hausa ya bambanta da wata  al’umma. 

    A vangaren amfani da yaren Hausa, Bahaushe yana da  kare-karen harshe (dialects) na rukuni da yanki. Karin  harshen rukunin mutane na da dangantaka da jinsi,  shekaru, mulki ko sana’a. Misali, akwai kalmomi ko  yanayin amfani da harshe da malamai ke da shi da ya  bamban da na ‘yan kasuwa, haka a tsakanin maza da  mata, yara da manya. 

    A karin yanki akwai Hausa Bakwai, da Banza Bakwai. A  Karin harshen Hausa-Bakwai, akwai ‘karin gabas’ akwai  ‘karin yamma’, an samu waxannan kare-kare ta dalilin  kafa garuruwan Hausa da jikokin Bayajidda suka yi a  900s (Liman, 1974). 

    A karin gabasanci akwai: Kananci, Zazzaganci,  Bausanci, Gudanranci, Damagaranci, Haxejiyanci. A  Karin yammaci akwai: Dauranci, Sakkwatanci,  Gobiranci da sauransu. 

    Kananci, Sakkwantanci, Dauranci, Haxejiyanci,  Zazzaganci da Bausanci na daga cikin manyan kare karen Hausa saboda yawan al’umma da ke amfani da karin a yankunan Hausawa (ie. Kano, Sakkwato, Daura,  Haxejiya, Zazzau, Katsina da Bauchi). Sauran akwai  Canganci (Gaya), Gobiranci (Gobir), Agadasanci da  Damagaranci (daga qasar Nijar). 

    Misalin, Bahaushen Haxejiya da kudanci qasar Kano  sukan furta harafin /hy/ a madadin /sha/, mis. hyayi a  matsayin shayi. Ko, a karin gabas suna amfani da /r/,  yamma kuma /l/ a kalmomi, harshe/halshe, harbi/halbi,  farke/falke da sauransu. Ko canja wasu haruffa misali,  fira/hira, Audu/Abdu (Noun, ). 

    Domin Karanta Ma’anar Bahaushe Danna nan 

    A wani karin kuma ana a qarin ‘ya’ a bayan lamiri a  Sakkwatanci, ‘ni’ (Kananci), ‘niya’ (Sakkwatanci),  kai/kaiya, ke/keya, mu/muya da sauransu. A wajen nuni,  wannan (Kananci), wanga/wagga (Sakkwatanci). 

    Wani lokacin kuma, akwai bambancin zaven kalmomi  na yanki, misali: hanya/turba, makani/gwaza,  gishiri/manda, barci/kwana, abinci/cimaka, fitsari/sayi,  gafiya/bargu, wuni/yini/uni, ‘ya/xiya da sauransu. 

    Bahaushe da yake zaune a wani yanki mai cakuxe da  wasu qabilu mazauna Suleja, Jos, Yawuri (yankunan  Banza Bakwai) da sauransu, sukan canja lamirin mace  zuwa na namiji misali: matata/matana, motata/motana,  rigata/rigana da sauransu. 

    1. Baqin Kalmomi Cikin Harshen Hausa  

    Ta vangaren amfani da kalmomi, Yaren Hausa ya samu  cakuxuwa da kalmomi Larabci (saboda zuwan addinin  Musulunci), da na Turanci (a zuwa Turawan Mulkin  Mallaka), sai jefi-jefin kalmomi daga harsunan da  yarukan makwafta Yarbawa, Inyamurai, Fulani, Bare 

    Bari, Kanuri da sauransu a sunayen abinci da sutura.

    Addinin Musulunci ya yi wa harshen Bahaushe tasiri  sosai, domin Bahaushe na amfani da kalmomin Larabci  wajen magana (Ibrahim, 1982), har ta kai ga wasu  kalmomi Hausan na qoqarin vacewa da maye gurbinsu  da na Larabci; misali: arziki (wadata), mai koyo (xalibi),  raino (tarbiyya). A vangaren Turanci kuma, Bahaushe ya  ari kalmomin Turanci na baqin abubuwa, gwamnati,  ofisi, birki, mota, da sauransu.  

    Akan samu auren harshen (code mixing) tsakanin  harshen Hausa da Turanci (Engausa/Ingausa) wajen  magana. Kalmar Ingausa, (Ing = English, ausa = Hausa).  Ingausa shi ne yin amfani da kalmomin, ko yankin  jumlar Hausa da Turanci a lokacin guda wajen magana. 

    Akwai ‘code mixing’, haxa kalmomi Hausa da Turanci. Akwai kuma ‘code switching’, idan mutum na magana  da Hausa, sai ya juye a koma yi da Turanci. 

    Domin karanta cikekken littafin Danna nan 
  • Ma’anar Bahaushe

    Ma’anar Bahaushe

    Kalmar Bahaushe tana da ma’ana ta fuskokin harshe,  al’ada ko gado, siyasa, addini, wurin zama (muhalli) ko  xabi’ar mutum. 

    Ta fuskar harshe, shi ne wanda harshensa na farko (L1)  Hausa ne, kuma ba ya jin kowanne harshe sai Hausa, ita  ce harshensa na mu’amalar yau da gobe (Bunza, 1990). 

    Ta fuskar gado, shi ne wanda iyayensa da kakaninsa  Hausawa ne, koda shi ba ya jin Hausa (Bunza, 1990). 

    Ta fuskar siyasa, Bahaushe shi ne wanda ya zauna ko  aka haife shi a qasar Hausa na sama da shekara ashirin,  koda iyayensa da kakaninsa ba Hausawa ne. Wannan  jimawar za ta ba shi damar amfani da harshen, da xabi’a  irin ta Bahaushe. Ta wannan fuskar, sauran qabilu ma na  iya zama Hausawa (Manby, 2016). 

    Domin Karanta wane ne bahaushe Danna Nan

    Ta fuskar addini, wasu na ganin wanda ba ya addinin  Hausawa, ba Bahaushe ba ne, shi ya sa Hausawa kan  cewa ‘yan uwansu da ba su karvi addinin Musulunci ba  da suna: Maguzawa (jam’i), Bamaguje (namiji),  Bamagujiya (mace) (Bunza, 1990). 

    Ta fuskar muhalli (wurin zama), Bahaushe shi ne wanda  yake zaune a qasar Hausa (Bunza, 1990 da Adamu 1978) Smith (1970) duk mutumin da yake rayuwa a qasar  Hausa daga a qarni na 15th a lokacin garuruwan Hausa  sun kafu shi ne Bahaushe, sannan harshen Hausa ne  babbar alamar da za a iya gane Bahaushe da shi. 

    Ta fuskar xabi’a, Bahaushe shi ne wanda ya tasirantu da  al’adun Hausawa suka yi tasiri a rayuwarsa ta yau da  kullum, koda ba Bahaushe ba ne (Bunza, 1990 da  Adamu 1978). 

    Wasu kuma na kallo Bahaushe da fuska uku, Have,  Hausa-Fulani (Kaxo) da Banza. Havawa su ne asalin  Hausawa waxanda suka haxa da qabilun Gobirawa,  Kabawa, Rumawa, Adarawa da Maouri sune masu mulki qasar Hausa kafin zuwan Jihadin Fulani da Shehu  Usman Xanfodiyo (Omniglot, 2015)  

    Hausa-Fulani, asali mutanen kudancin Nijeriya ne suka  qirqiro kalmar, don dunqule al’ummar Hausawa da  Fulani saboda alaqar kut-da-kut tsakanin Bahaushe da  Fillace. Fulani na zaune a qasar Hausa ta dalilin  auratayya, kiwo, kasuwanci ko neman ilimi tun kafuwar  Daular Sokoto. Waxannan Fulanin suna jin harshen  Hausa sosai, kuma sun xabi’antu da xabi’ar Bahaushe,  daga cikin qabilun Fulani akwai; Jovawa, DambazawaMudubawa, Mallawa da Sulluvawa da suke da asali daga  Futa Toor, ko Fouta Djallon ko Wolof (yanki da ke  tsakanin Senegal da Mauritania a yau).

    Domin Karanta Al’adar Bahaushe Danna nan 

    Su kuma Banza  jikokin Karaf-da-Gari ne mazauna garuruwan da jikokin  Bayajidda suka kafa. Su Hausawa ne da suka haxu da  wasu qabilun mazauna Illorin (tare da Yarbawa),  Gwarawa, Ajawa, gere, Bankal da wasu. Sune idan suka  yi magana da karin harshensu ake ce musu ‘gwarawa’,  ko ‘bagwari’.  

    A yau, abu ne mai wuya a samu asalin Bahaushe, saboda  autayayya tsakanin wasu qabilu, hakan na nufin sauyin  halitta, yanayi da kama, Bahaushe ya yi auratayya da Fulani, Nupe, Kanuri, Shuwa, da sauran qabilun  Kudancin Nijeriya. Bahaushe a yau, haxuwar qabilu ce  daban-daban, da ke rayuwa Arewacin Nijeriya,  Kudancin Nijar, da sauran sassan duniya (Malumfashi,  2018). 

    Domin karanta cikekken littafin Danna nan 
  • Asali Da Muhallin Bahaushe

    Asali Da Muhallin Bahaushe

    Bahaushe shi ne mutumin qabilar Hausawa masu magana da harshen Hausa. Hausa harshe ce da take cikin rukunin harsunan yankin tafkin Chadi (Chadic) masu rassa daga ‘Afroasiatic’ da suka haxa da Larabci, Yahudanci da Buzanci, Habashanci, Somali da Kanuri (Encarta, 2009 & Greenberg, 1963).

    A halitta Bahaushe baqar fata ne, da yake zaune a yankin Sahara, shi ya sa ake qiran yankin da Bilal Sudan (qasar baqaqen fata, ko Negro a Turance). Sai dai ana samu farare a cikin Hausawa jefi-jefi saboda auratayya tsakanin wasu qabilun Fulani, Shuwa da Auzunawa waxanda suke farare a halitta (Malumfashi, 2018).

    Domin Karanta wane ne bahaushe Danna Nan

    Qasar Hausa, ita ce muhalli da Hausa ke rayuwa. Saboda da qaura, ba za a iya iyakance qasar Hausa ba a yanzu (Alhassan, 1982). Yankin da Bahaushe ke rayuwa na asali, shi ne yankin da ke tsakanin layi na 15N zuwa na 18N (Arewa da Ikwaita), da kuma tsakanin layi na 8E da na 12E gabas da ayin Girinwic. Wannan yankin na tsakanin Asodu ta qasar Agadas ta Nijar, kudu da qasar Sudan daga Arewa. Daga gabas yankin ya yi iyaka da tsohuwar Daular Borno, yamma da tafkin Chadi, daga yamma qasar Benin da gavar kogin Kwara, daga kudu kuma qasar Gwari (Kwalli, 1996 & Adamu, 1997).

    Sanin haqiqanin asalin Bahaushe yana da givi sosai, saboda abin da aka fi labartawa na tarihin Bahaushe ‘tarihihi’2ya fi ‘tarihi’ yawa a ciki, kasancewar an sami lokaci mai tsayi, ba tare da sahihin tarihin a rubuce ba, saidai labarin baka na kunne-ya-girmi-kaka. Bahaushe mutum ne, mai tsatso tun daga kakanmu Annabi Adamu السالم عليه. Asalin Bahaushe a Afrika ya fara tun shekaru 30,000 zuwa 2 Tarihihi shi ne tarihi yake a jirkice, gurvatacce da har ba a iya gaskiya daqare-qare a cikinsa (Yahaya da wasu, 1992).

    60,000 baya da wasu mutane suka yada zango a Nahiyar Afrika daga cikin qabilun Ham ta Kibxawa, Sudaniyawa da Babas (Malumfashi, 2018).
    Dr. Yusuf Maitama (1929 – 2017) ya ce, ‚asalin Bahaushe mutumin qasar Habasha ne (Ethiopia, Afrika ta Arewa maso gabas). Daga kalmar Habasha, aka samu ‘Habsha’ zuwa ‘Hausa’.‛ Asalin mutanen Habasha su kuma, sun taso ne daga Asiya, daga cikin qabilun Labarawa da Kivxawa. Bahaushe ya taso daga Habasha ya nufo Afrika ta yamma.

    Domin Karanta Al’adar Bahaushe Danna nan 

    Bahaushe ya fara kafa gari daga yada zango domin kiwo, farauta, fatauci, zuwa gina gidajen noma, har ya fara samar da qauyuka, da unguwanni, zuwa birane, har aka kafa masarautu da faxaxa qasa (Gusau, 2008).

    A wata ruwayar, a qarnin baya an yi wasu yankuna cikin daular Songhai ta Mali da ake qira da Guber ko Gobir3da Ausa. Wasu na ganin, ta iyu daga kalmar Ausa aka sami (H)ausa (Malumfashi, 2018).

    Domin karanta cikekken littafin Danna nan 
  • Wane Ne Bahaushe?

    Wane Ne Bahaushe?

    Idan muka juya kan sanin wane ne Bahaushe kuwa? A iya cewa mafi yawancin mazauna Ƙasar Hausa su ne al’ummar Hausawa.

    Amma akwai wasu ƙabilu waɗanda suka yi kaka-gida a wannan Ƙasa ta Hausa; har hakan ya sanya suka koma Hausawa a harshe da al’adu da kuma adabi.

    Waɗannan ƙabilu kuwa sun haɗa da Fulani, Buzaye, Barebari, Nufawa, Yarbawa da sauransu. Amma Ibrahim (1981:1) ya bayyana cewa Hausawa su ne mutanen dake zaune a Ƙasar Hausa tuntuni, kuma suna magana da harshen Hausa a matsayin harshen uwa.

    A ra’ayin Adamu (1983:3) kuwa, na ganin Hausawa sun haɗa da mutanen nan waɗanda saboda ƙaura da magabantansu suka yi daga Ƙasar Hausa; zuwa wasu sassa dake maƙwabtaka ta kusa ko ta nesa da Ƙasar Hausa; koda kuwa ba sa magana da harshen Hausa ko yin al’adun Hausawa, sun ɗauka su Hausawa ne.

    Misali, Abakwariga dake zaune a Jihar Taraba ta Nijeriya da kuma wasu dake ikirarin cewa su Hausawa ne; waɗanda ke zaune a ƙasashen Cote de Voire da Burkina Faso da Mali.

    Magaji (1986:3), ya nuna Hausawa dai su ne mutane waɗanda harshensu shi ne Hausa. Haka kuma dukkanin al’adunsu da ta’adunsu na Hausa.

    Haka kuma addinin Musulunci ya yi cikakken tasiri a kansu.

    A ra’ayin Sallau (2000:71) kuwa, na ganin waɗanda saboda ƙaura da magabatansu suka yi zuwa Ƙasar Hausa sun manta da harshensu da adabinsu da al’adunsu na asali sun ɗauki na Hausawa. A taƙaice sun koma Hausawa a harshe da adabi da al’ada. Misalin ire-iren waɗannan mutane sun haɗa da Barebari, Kambarin Barebari, Barebarin Katsina da Buzaye da wasu Fulani.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Nazarin Matsalolin Aure a Ƙasar Hausa Daga Mahangar Zabiya Lawisa da Fatima Jalo wanda Ibrahim Baba (Ibrahim Garba Nayaya (Baban Fauzan) ya wallafa shi.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ma’anar Aure A Ƙasar Hausa danna nan

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ladubban Addu’a A Musulunci danna nan

  • AL’ADAR BAHAUSHE

    AL’ADAR BAHAUSHE

    Abin kunya ne budurwa ta je gidan su saurayinta a ƙasar Hausa

    Da a al’adar Bahaushe, ba yadda za a yi budurwa ta bi saurayi gidan su ko ta je wajensa, saboda kunya da kamun kai irin na Bahaushe.

    Amma yanzu don rashin kamun kai da rashin sanin ƙimar kai, sai ta karaɗe dangin su kaf kafin a yi auren.

    Don haka, ba mai mararin ganin ta, yayin da aka yi auren, don duk sun gama ganinta, don haka ba za ta yi irin farin jinin da amarya ke yi ba.

    kuma yanzu iyaye mata su ke ba wa ‘ya’yansu lasisin yin haka, domin su ma irin waɗannan iyayen akwai alamun rashin kamun kai a tare da su.

    Shi ma kuma saurayin sai ya yi ta kwasarta, yana yawo da ita, wai shi ga mai budurwa.

    Hakan ne yake jawo shi ɗin ma, karan kansa saurayin ba zai damu da ita ba, bayan an yi auren.

    Shi ne bayan auren lokaci kaɗan, sai a ga an fara samun matsaloli, ta yau daban ta gobe daban, tunda dama mahaifiyarta ba ta ba ta tarbiyya mai kyau ba.

    A ƙarshe ya kamata mu koma kan al’adar mu ta asali, iyaye su nuna wa ‘ya’yansu cewa ba burgewa ba ce bin saurayi zuwa wani waje, ko da kuwa gidansu ne, ta haka ne za mu kare ‘ya’yanmu daga faɗawa cikin rayuwa mara kyau da gurɓatattun halaye.

    Domin karanta tarihin Hausawa da al’adunsu danna nan