Shugaban Istigfari

0
399

An karɓo daga Shaddad Ɗan Aus (Radiyallahu Anhu) daga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: shugaban Istigfari shi ne ka ce :

Allahumma anta Rabbi, laa ilaha illa anta, khalaƙatani, wa ana abduka; wa ana ala ahdika, wawa’adika mastaɗ’atu, abu’u laka, bini’imatika alayya; wa abu’u laka, bi zanbi fagfir lii, fa innahu laa yagfiruz zunuba illa anta”

Ya ce: wanda ya faɗi wannan da safe yana mai cikakken imani sai ya mutu a wannan yinin kafin yamma; to shi ɗan Aljanna ne, idan da daddare ne yana mai cikakken imani, sai ya mutum kafin safiya; to shi ɗan Aljanna ne” (Bukhari 6306).

An karɓo daga Abu Huraira (Radiyallahu Anhu) ya ce; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce; “Haƙiƙa ni kaina ina yin istigfari ina tuba fiye da sau saba’in a yini ɗaya”. (Bukhari 6307, 3259).

Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Salati Ga Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) Ya Ke danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Salati Ga Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) Bayan Tahiyya danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

labarin da ya wuceRamuwar Azumin Ramadan
Labarin na GabaYadda Falalar Zikirin Tashi Daga Majalisa Yake