Matakan Farfaɗo Da Tsangayun Alƙur’ani Da Raya Su

Tsangayun Alƙur'ani

Written by

in

Zai yi kyau kowace jiha ta bi hanyoyi don cimma wannan buri bisa shawartar masana da kuma jami’anta. Kaɗan daga waɗannan matakai sun haɗa da:-

  • Kafa ma’aikata ko hukumar ilmin Tsangayun Alƙur’ani.
  • Ƙididdigar yawan tsangayu da yawan malamansu da almajiransu don sanin girma ko faɗin nauyin da ke wuyan kowacce jiha, kamar dai yadda kowace gwamnati ta san yawan malamanta da ɗalibanta a kowace makaranta ta boko
  • Wayar da kan ma’abota tsangayu da kula da kyakkyawar dangantaka da su don samun jituwa da fahimtar juna mai ɗorewa ta hanyar tarukan ƙarawa juna sani da shirye-shirye a gidajen rediyo da talabijin.
  • Nusar da al’uma muhimmancin tsangayu da makaranta Alƙur’ani don ƙara samun gata daga Al’uma ta kafafen watsa labarai.
  • Gina tsangayu da gyara waɗanda suka lalace da samar da rumfunan darasu.

Shiri na musamman kan:-

  • Bunƙasa noman tsangayu ta hanyar raba taki da iri da kuma shawarwari daga ƙwararru.
  •  Bunƙasa sana’o’i don dogaro da kai musamman ga matasan alarammomi da ke yankan farce ko dako da sauransu.
  • Samar da ƙananan masana’antu mallakin tsangayu da jari kamar injinan niƙa da yin sabulu da na haɗa abincin kaji da makamantansu.
  • Yankawa makaranta ko mahaddata albashi ko alawus a matsayin su na malamai a tsangayunsu. Wasu a sanya su a rajistar jihohi, wasu kuma su kasance daga aljihun ƙananan hukumominsu.
  • Sauƙaƙawa makaranta masu sha’awar zurfafa iliminsu damar cigaba da ilmi a cibiyoyin ilmin da suka dace cikin jihohinsu.

Domin karanta cikakken bayani a kan Samar Da Tsangayun Gwaji Na Gwamnati danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Jerin Gwamnonin Kano Daga (1967 zuwa yau) danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

Comments

Leave a Reply