Lailatul Ƙadri

0
66

SALMANU FARISS ADAMU

Wasu kwanaki ne masu ɗimbin falala, waɗanda suka fi watanni dubu, sannan kuma ba a samunsu, sai a cikin watan Ramadan, a kwanakin goma ƙarshensa.

حدثنى زياد عن مالك عن يزيد بن عبدالله بن الهاد عن محمد بن إبراهيم إبن الحارث التيمى عن أبى سلمة  بن عبدالرحمن عن أبى سعيد الخدرى أنه قال :كان رسول الله صلى الله عليه وسلم يعتكف العشرالوسط من رمضان فاعتكف عاما , حتى إذا كان ليلة إحدى وعشرين وهى اليلة التى يخرج فيها من صبحها من اعتكافه قال : من اعتكف معي فليعتكف العشر الأوخر, وقد رأيت هذه اليلة أنسيتها , وقد رأيتنى أسجد من صبحها فى ماء وطين فالتمسوهافى العشر الأخر والتمسوهافى كل وتر ,قال أبو سعيد فأمطرت السماء تلك اليلة وكان المسجدعلى عريش فوكف المسجد قال أبو سعيد :فأبصرت عيناي رسول الله صلى الله عليه وسلم إنصرف و على جبهته وأنفه أثر الماء والطين , من صبح ليلة إحدى وعشرين .

An ruwaito daga Ziyadi daga Malik daga Yazidu bin Abdulllah bin Hadi daga Muhammad bin Ibrahim bin Haris Al-tamimi daga Abu-Salma bin Abdullahman daga Abu-Sa’idul Kudri, haƙiƙa shi ne yace, Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam) ya kasance yana Ittakafi a goman tsakiyar watan Ramadan, sai ya yi Ittikafi a wannan shekarar, har sai da ya kasance daren ashirin da ɗaya (ta same shi a cikin masallaci) ita ce da ya fita safiyarta, wanda zai yi Ittikafi a cikinta yace “Duk wanda zai yi Ittikafi tare da ni, to a daren goma ƙarshen (Ramadan), haƙiƙa ya ga a cikin wannan daran, sannan sai ya manta da ita, haƙiƙa na ganni ina sujjada a cikin safiyarta, akwai ruwa da taɓo, sannan (sai annabi yace) ku neme ta a cikin kwanaki goman ƙarshen (Ramadan ), sannan (ya ƙara cewa) ku neme ta a cikin kowacce rana (na ranar).

Saboda haka wannan hadisin ya yi magana a kan abubuwa guda biyu Ittikafi da lailatul ƙadri, Ibin Abdulbari yace wannan hadisi shi ne ya inaganta a wannan babi, saboda annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) ya kasance yana Ittakafi a kwanakin goman tsakiyar watan Ramadan.

Haka kuma  imamu Hafiz Ibin Hajar yace, shi ne da yi wa wawin damma da kuma sin sakina (ɗauri ko mara wasali), sannan kuma Ibin Abdulbarri yace wannan ruwarta (ta Manzon Allah) yana Ittikafi  har sai da ya kasance a daren ashirin da ɗaya, ita ce daren da ya fice a cikin ta da safiyarta, domin yin Ittikafi’’.

Wannan ruwayar tana ɗaya daga cikin ruwayar Yahaya da Abubakar da shafi`i, amma a cikin ruwayar kala biyu ce da ta Ibin wahabi da Ibin Ƙasim, waɗanda suka fitar da ita (annabi yana Ittikafi), amma kuma ba su ambaci safiyar ba.

Amma kuma shi Ibin Hazim ya faɗa misalin wannan ruwayar, inda yake cewa a cikin huɗubar  daren ashirin da ɗaya,  annabi ya shiga Ittikafi, ita ce daren ashirin da biyu, saboda abin da aka faɗa a ƙarshen wannan hadisi.

Sai ya buɗe idonsa, sai ga  annabi (Sallallahu alaihi wasalla) a gefensa a ranar, sannan kuma sai ga alamar ruwa da taɓo a cikin safiyar daren ashirin da ɗaya.

Abin nufi a nan shi ne, mutum ya shiga Ittikafi kafin daren ashirin da ɗaya (lailatul ƙadri), sannan sai ya manta da ita, sai yace “annabi ya ga mala’ika da haske da idonsa”, sannan kuma ya gani  a farkon wannan daren ya ga kaza da kaza a cikin daren, ya ga masallaci, mai girma kuma ga haske, sannan kuma a saman masallaci, ruwa yana zuba, saboda haka alamomin da ake iya gane daren lailati ƙadri ne.

Misali kamar su gushewar rana, zubar ruwan sama, washewar sararin samaniya, gari ya yi tsit, rashin jin sautin karnuka ko dabbobi, da sauransu. Sannan kuma ana iya samu daren lailatul ƙadri a ranar daren ashirin da ɗaya ko da uku ko da biyar ko da bakwai, ko da tara waɗannan su ne ranakun da ake iya samun lailatul ƙadri.

Amma Abi-Sa’id yace, sama ta kece da ruwa a wannan daren, sannan masallacin ya kasance tamkar ginshiƙi, sai masallacin ya tsaya, sannan kuma  Abi-Sa’id yace sai annabi (Sallallahu alaihi wasalla) ya buɗe idanunsa, sai ya juya sai ga goshinsa da hancinsa akwai alamar ruwa da taɓo a daren Asubahin da ya shiga na watan Ramadan.

An ruwato daga Ziyadu daga Malik daga Abudullah bin Dinari daga Abdullah bin Umar (yace) haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalla) yace’’ ku binciki (ku kirdado) daren lailatul ƙadri a cikin bakwai ɗin ƙarshe.

Abin nufi a nan shi ne a kwanaki ashirin da bakwai ɗin ƙarshen.

حدثنى زياد عن مالك عن هشام بن عروة عن أبيه : أن   رسول الله صلى الله وسلم قال “تحروا ليلة القدر فى العشر الأخرين من رمضان .

An ruwaito daga Ziyaddu daga Malik daga Hishamu “ku binciki daren Lailatul ƙadri a cikin (kwanaki) ashirin ɗin ƙarshen watan Ramadan.

حدثنى زياد عن مالك عن أبى النضر مولى عمر بن عبيدالله : أن عدالله إبن أنيس الجهني قال لرسول الله صلى الله عليه وسلم : يا رسول الله , إنى رجل شاسع الدارفمرنى ليلة أنزل لها , فقال رسول الله صلى الله عليه وسلم ” أنزل ليلة ثلاث وعشرين من رمضان ”

An ruwaito daga Ziyadu daga Malik daga Abi-nadhir mai yi wa Umar bin Ubaidullah hidima (yace), haƙiƙa Abdullah bin Unaisu Aljuhaniyyu yace da Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam), ya manzon Allah ni mutum ne mai rusasshen gida, ka umarce ni da daren da aka saukar da ita (Lailatul ƙadri), sai Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalla) yace da shi “An saukar da daren (Lailatul ƙadri), ashirin da uku a cikin watan Ramadan”.

Amma Ibin Abdulbarri yace wannan ruwayar yankakkiya ce, saboda Abi-nadhir bai riski Abdullah bin Unaisu ba, sannan kuma bai gan shi ba, amma haƙiƙa Imam Muslim ya sadar da wannan hadisin ta hanyar Dhahaku bin Usman daga Abidi daga Busra bin Sa’id daga Abdullah bin Unaisu da lafazin Hadisin Abi-Sa’id daga Daud ya sadar da shi ta hanyar Ibin Ishak daga Muhammad bin Ibrahim Attamimu daga Umrata bin Abdullah bin Unaisu daga mahaifansa kamar yadda wannan hadisin na Muwaɗɗa Malik ya nuna haka.

An ruwaito daga Ziyadu daga Malik daga Humidu Aɗɗawilu daga Anas bin Malik, tabbas ne yace, Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalla) ya fita tare da mu a cikin watan Ramadan, sai yace “ni na ga mutane biyu suna jayayya, sai suka dakata, (sai yace da su) ku neme ta a cikin (ashirin da) tara ko bakwai ko biyar’’.

حدثنى زياد عن مالك أنه بلغه : أن سعيد بن المسيب كان يقول : من شهد العشاء من ليلة القدر , فقد أخذ بحظه منها.

An ruwaito daga Ziyadu daga Malik (yace) haƙiƙa shin labari ya same shi lalle Sa’id bin Musayyibin ya kasance yana cewa, duk wanda ya shaida (ya yi sallah) Isha’i a cikin Lailatul ƙadri (Ai a cikin ranakun da ake sa ran ganinsu), haƙiƙa ya riski daren lailatul ƙadri.

Haka kuma Ibin Abdulbarri yace, wannan ba zai iya kasancewa ba, sai kawai ra’ayi ne, sannan ba zai riƙi komai ba, sai  dai neman dacewar Allah (Subhanahu wata’ala) a cikin wannan ranar.

Saboda haka malamai sun ƙarawa junansu sani a kan daren Lailatul ƙadri, saɓanin mai yawa, daga cikin su akwai maganar baban malamin nan Al-araki, saboda ita (Lailatul ƙadari) ba ta yi dai-dai da sauran shekaru ba ko ranaku.

Ma’ana ganin wannan daren sau ɗaya ya taɓa faruwa a zamanin Manzon Allaah (Sallallahu alaihi wasalla), sannan kuma an faɗa a wata maganar, wannan daren yana kewayawa ne a kowace shekara, a wata faɗar kuma an ce Lailatul ƙadri tana cikin rabin watan Sha’aban, sannan kuma wasu sun ce, A a an keɓance ta ne a cikin watan Ramadan.

Sannan za a iya samunta a cikin kowanne dare (Ramadan), Bugu da ƙari kuma Sheikh Sabkiyu ya yarinjar da shi, amma malam Sarkhisu ya faɗa a cikin sharhin ‘’ Hidayatu’’. Maganar Abi-Hanifa yace za mu same ta (daren Lailatul ƙadri) an ciro ta ne a cikin dukkanin Ramadan, haka nan ma abokinsa ya faɗi haka sauransu.

Haka ma an ruwaito daga Ibin Abi-Asim daga Anas yace, babu wanda ya sani daga cikin mu (ranar ganin Lailatul ƙadri), sai wani malami daga cikinsu yace, A a, Lailatul ƙadri, tana cikin rabin watan Ramadan, sai kuma wani mutum yace, A a tana cikin daren goman sha shida ne, na Ramadan.

Sai kuma wani yace, A a tana cikin daren goman sha bakwai, sannan sai wani yace, A a tana cikin daren goma sha takwas, sai kuma wani ya ƙara cewa, A a tana cikin daren goma sha tara ne, sai kuma wani ya sake cewa, A a tana cikin daren ashirin ga watan Ramadan,

Haka kuma sai wani yace, A a ita Lailatul ƙadri abar so ce, sannan kuma tana cikin goman tsakiyar watan ramadan, sai kuma wani yace A a ita kuma abin so ce, sannan tana cikin goman ƙarshe.

Sai kuma wani yace, A a, Lailatul ƙadri tana cikin daren ashirin da biyu na watan Ramadan har zuwa daren talatin ga watan Ramadan, sannan kuma wasu suka ce Lailatul ƙadri, tana cikin goman tsakiyar watan Ramadan, wasu kuma suka ce tana cikin goman ƙarshen.

Amma a cikin mazahabar Imam shafi’i jamhurum Sahabbai (mutanan mu) suka ce, haƙiƙa ita Lailatul ƙadri tana goman ƙarshe watan Ramadan, sannan kuma abar so ce a kan mu, sai dai ita abar ayyanawa ce a kan wannan al-amari, sannan kuma wannan daren na Lailatul ƙadri ba za ta gushe ba, har zuwa ranar lahira, kowanne ranaku goman ƙarshe (na wata) abar ɗaukakawa ce.

Daga ƙarshe kuma,mazahabar imam shafi’i sun rinjayar da daren ashirin da ɗaya shi ne daren Lailatul ƙadri, sannan kuma dukkanin mazahaban nan guda huɗu sun yi bayani a kan kwanakin sa ran ganin Lailatul ƙadri.

A takaice, alamomin daren lailatul ƙadri suna da yawa, amma dai idan ana cikin tsananin zafi ko sanyi, to a ranar daren za a samu sauƙi, idan kuma garin akwai duhu, to za a samu haske a garin da sauransu.

Domin karanta Falalar Gaggauta Shan Ruwa danna nan 

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceAddu’ar Gama Alwala
Labarin na GabaRubutacciyar Fassarar Huɗubar Idin Ƙaramar Sallah (Eid Kabir) Daga Masallaci mai Alfarma