Iyalin Musa Ɗanƙwairo

0
30

Iyali suturar mutum, iyali suturar gida. A bisa yanayin zamantakewar bil Adama da aljannu, cikar ɗa, mutum namiji ko ‘ya, mutum mace ita ce yadda Allah ya hore musu, ya ba su dama, suka assasa zuriya ta kankin kansu.

Ta haka za su sami nutsuwa, da samun ayyukan yi a duniyarsu da lahirarsu, musamman ma idan suka yi aiki da hukunce-hukuncen addini da matakan zamantakewar rayuwa bisa kyakkyawan zaɓi da dacewa. Haka kuma aure yana a kan gaba wajen tsayar da usra ko iyali da za su iya zama ƙwarara, ina ma a ce an bi sharuɗɗa da kyawawan dangogi na yin sa.

Alhaji Musa Ɗanƙwairo wanda aka fi sani kuma ake kira da Maradun, ya sami jagoranci na iyaye wajen yin matar farko 21. A yayin zaman Ɗanƙwairo a doron rayuwar duniya bayan matarsa ta fari, ya auri mata da yawa kuma wasu daga cikinsu ne suka haifa masa ‘ya’ya har goma sha bakwai (17).

Matan Aure na Musa Ɗanƙwairo

Mata waɗanda Alhaji Musa Ɗanƙwairo ya aure a rayuwarsa ta duniya su ne:

i) Hauwa Taladan
ii) Hajiya Hadiza (Ikka/Tashikka)
iii) Amina
iv) Tumba
v) Rabi (‘Yar Zuma)
vi) Maryam (Amarya)
vii) Hauwa
viii) Maimuna

‘Ya’yan Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maza da Mata

Ga tsarin sunayen ‘ya’yan Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun ta bin ɗakunan iyayensu mata da suka haɗa da:

i) Ɗakin Hauwa (Taladan)

ii) Ɗakin Hajiya Ikka (Tashikka)
a) Muhammadu Ɗanmakaɗa, Dauda na ɗaya (1)
b) Alhaji Garba, Zwacin Kiɗi, Marafa, Daudu (2)
c) Audu Adodo, Wakilin Kiɗa
d) Zulaihat
e) Habiba

iii) Ɗakin Amina
f) Ummaru Ka-ji-Dama (Makaɗin Noma)
g) Amina (Kassu): Tana aure a Maradun

iv) Ɗakin Tumba
h) Sanin Ɗanƙwairo, Zakin Murya

v) Ɗakin Maryam (Amarya)
i) Sa’adatu
j) Muhammadu Balarabe
k) Umaru

vi) Ɗakin Rabi’a (‘Yarzuma)
l) A’ishatu (Indo)
m) Malam Musa Tunau (Malamin Makarantar Allo)

vii) Ɗakin Hauwa
n) Abubakar, Ciroman Kiɗa
o) Amina, Ige
p) Ibrahim Ɗan’auta22

viii) Ɗakin Maimuna
Ba ta Haihu ba.

Bishiyar Iyalin Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun

Kaka Maiganga
Usman Ɗankwanagga = Yarnunu
Musa Ɗanƙwairo23 Amina Binta (Maryam)

= Hauwa = Haj. Hadiza =Amina = Tumba = Maryam =Rabi = Hauwa =Maimuna
(Taladan) (Ikka Tashikka) (Amarya) (‘Yar Zuma)
Malam Musa Ba ta
Tunau haihu ba
Umaru Amina (Kassu)
(Ka-Ji-Dama) Tana Aure Sa’adatu Muh Umaru
a Maradun (‘Yabbata) Balarabe
Muhammadu Sani (Zaƙin Murya)
Ciroma Amina Ibrahim Ɗan’auta
Abubakar (Ige) (Harkokin
Magaji na (2) Kasuwanci)
Muhammadu Garban Audu Zainabu Habiba
(Ɗanmakaɗa) Ɗanƙwairo (Adodo)
Magaji na (1)

= Salame = Baraka
Muhammadu Muh Tamaikiɗi
Ɗanjimma Basiru
Magaji na (3)

Domin karanta cikakken bayani a kan Kiɗa da Waƙoƙin Makaɗa Musa Ɗanƙwairo danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Ma’anar Kiɗa da Makaɗi danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

labarin da ya wuceZubar Da Miyau Ga Mai Juna Biyu
Labarin na GabaCututtukan Haƙori
Prof. Sa’idu Muhammad Gusau
FARFESA SA'IDU MUHAMMAD GUSAU, An haife shi a Gusau jihar Sakkwato, (Maris 24, 1952). Ya yi karatun firamare na Islamiyya daga 1965-1969, ya je kwalejin sarkin Musulmi Abubakar daga Junairu 1970 zuwa Yuni 1973. Ya yi Diploma, Digiri Na farko (B.A), na biyu (M.A) da Digiri na uku (Ph.D) duk a jami'ar Bayero, Kano.