Fassara Huɗuba Daga Masallaci Mai Alfarma 24th January 2025

0
35

Sheikh Dr Saleh Bin Abdullahi Bin Humaid

Mai Fassara:
Dr Abdullahi Yunusa Machina

Shugaban Shashi
Dr Abdurrahman Muhammad Sani Yakubu

Huɗubar Masallaci Mai Alfarma
Sheikh Bandar Abdul-Aziz Balila 23/07/1446H

HUƊUBA TA FARKO
Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, mafakar waɗanda ke cikin tsoro da ƙa-ƙa-ni-ka-yi, Mai ba da kariya ga masu neman mafaka. Ina yaba Masa, kuma ina gode Masa, tsarki ya tabba a gare Shi, Mai taimakon mabuƙata, Mai rarrashin waɗanda suka karaya, kuma Mai karbar tuban masu tuba.

Ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, Ubangijin masu rauni, mai taimakon waɗanda aka zalunta, kuma Mai karɓar addu’ar waɗanda suke cikin tsanani. Kuma ina shaidawa lallai Shugabanmu kuma Annabinmu Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa, jagoran masu hasken fuska, Mai shiryar da dukkan halittu, tsira da aminci da albarkar Allah su tabbata a gare shi, da Alayensa tsarkaka nagartattu, da Sahabbansa masu ɗa’a da albarka, da Tabi’ai, da waɗanda suka bi bayansu da kyautatawa har zuwa ranar ƙiyama.

Bayan haka:
Ya ku mutane!
Ina yi mana wasiyya da tsoron Allah, saboda haka, ku ji tsoron Allah, Allah Ya rahamce ku, ku yi riƙo da igiyarSa, kuma ku nemi mafaka a wajenSa, sai burukanku su cika, kuma ku ji daɗin haɗuwa da Shi, lallai duk wanda ya kira Shi kuma ya roƙe Shi, to, ba zai taɓe ba, kuma duk wanda ya ƙasƙantar da kansa gare Shi kuma ya yi fatan haɗuwa da shi, to, ba zai yi nadama ba, ta yaya hakan ba zai kasance ba, alhali Shi ne Mai cewa: (Shin wanene zai amsa wa wanda ya shiga cikin halin ƙa-ƙa-ni-ka-yi yayin da ya kira Shi?).

Sannan ku sani, Allah Ya yi muku rahama, cewa lallai duniya tana gudana ne bisa ƙaddarawarSa da hukuncinSa, kuma gudanar da al’amuran halittu tana kasancewa ne bisa nufinSa da yardarSa, kuma zukatan mutane suna tsakanin yatsun Ubangijimmu Mai rahama, yana jujjuya su yadda ya so a cikin ƙasa da sama, don haka, ku kyautata zato ga Ubangijinku, kuma ku yi fatan samun alheri daga Mahaliccinku, domin lallai wanda ya kyautata zato ga Allah, to, zai isar masa, kuma Zai jiɓinci lamuransa, kuma Ya ba shi abin da yake fata da buri.

Allah Ya ce a cikin Hadisi Ƙudusi: “Ni ina daidai da zaton bawana gare Ni, kuma Ina tare da shi idan ya ambace Ni, idan ya ambace Ni a asirce, sai na ambace shi a asirce, idan kuma ya ambace Ni a cikin dandazon jama’a, sai In ambace shi a cikin dandazon da ya fi wancan alheri, idan kuma ya kusance Ni da ɗani ɗaya, sai In kusance shi da zira’i, idan kuma ya kusance Ni da zira’i, sai in kusance shi da gaba guda, idan kuma ya zo gare Ni yana tafiya, Zan zo masa da gaggawa. (Bukhari da Muslim suka rawaito)

Ya ku bayin Allah!
Kyautata zato ga Allah ibada ce daga cikin manyan ibadu, kuma aiki ne daga cikin mafi girman ayyukan neman kusanci ga Allah, wanda yake nuni a kan cikar imani, da kyawun zuciya, da yarda da abin da Allah Mai rahama Ya ƙaddara.

An rawaito daga Abdullahi ɗan Mas’ud Allah Ya ƙara masa yarda, ya ce: “Ina rantsuwa da wanda babu abin bauta bisa cancanta koma bayansa, ba a ba wa wani bawa mumini wani abu da ya kai kyautata zato ga Allah Maɗaukakin Sarki alheri ba, ina kuma rantsuwa da wanda babu abin bauta bisa cancanta koma bayansa, bawa ba zai kyautata zato ga Allah Maɗaukakin Sarki ba, face sai Allah Ya ba shi abin da ya zata, hakan ya kasance ne saboda alheri a hannunSa yake”. Ibnu Abid-dunya ne ya rawaito.

Kuma shi ne ƙudurce abin da ya dace da Allah Maɗaukakin Sarki na ma’anonin kyawu da buwaya, a sunayenSa da SiffofinSa, da maganganunSa da ayyukanSa masu daraja, tare da cikar iko a cikin abinda ya gabata da wanda zai zo nan gaba, da abin da yake ginuwa a kan haka na tasiri da ɗabi’u kyawawa.

Shi Allah Maɗaukakin Sarki Shi ne Mai rahama, Mai jinƙai, Mai karamci, Mai yawan baiwa, Mai tausayi Mai yawan kyauta, Mai tausasawa, Mai yawan tagomashi, Mai tsananin ƙarfi Mai cikakken iko, Mabuwayi Mai girma, Mai amsa addu’ar masu tsananin buƙata, Ubangijin uwayengiji, Mai gudanar da gizagizai, Mahaliccin halittunSa daga turɓaya, rayayye da ba ya mutuwa, tsayayye da ba ya bacci.

Shi ne Makusanci tare da ɗaukakarSa, Maɗaukaki tare da kusancinSa, Masanin abin da Ya rubuta kuma Ya gudanar da shi, halin halittunsa da ke ƙasa ko sama ba ya ɓuya a gare Shi, Mai hikima a ayyukanSa, Mai tausayin bayinSa, Mai taimakon wanda ya nemi kariyarSa da jiɓintarSa.

Zuwa ga wanda jinya ta kwantar da shi kuma ta wahalar da shi, ta danƙwafar da shi a kan gadajen asibitoci, har suka zama su ne gidansa da makwancinsa, ga addu’ar Annabi Dawuda lokacin da jinya ta tsananta gare shi, lokacin da ta rinjaye shi ta ramar da shi, sai ya risina ga Allah Maɗaukakin Sarki ya kira Shi, yana mai bayyana buƙatarsa zuwa ga Ubangijinsa Majiɓincinsa:

((Kuma ka tuna) Ayyuba lokacin da ya roƙi Ubangijinsa (yana cewa): “Lallai cuta ta same ni, kuma Kai ne Mafi jinƙan masu jinƙai” () Sai Muka amsa masa (roƙonsa) sannan Muka yaye cutar da take tare da shi, Muka kuma ba shi (madadin) iyalansa (da ya rasa) da kuma kwatankwacinsu tare da su don jinƙai daga gare Mu da kuma wa’azi ga masu bauta (ga Allah)).

Zuwa ga wanda aka haramta masa mai ɗebe kewa daga ƙawa ta rayuwa, wanda aka sanya masa kewa saboda kaɗaici, da shagaltuwar kowane ma’abocin iyali da duniyarsa, a ina ka bar addu’ar Annabi Zakariyya tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yayin da ya risina wa Majiɓincinsa Allah, ya roƙe Shi a boye, ya nemi agajinSa kuma ya yi fatan samun rahamarSa, da wata addu’a da duk wani ma’abocin rayuwa zai raurawa da ita, kuma idanuwa su kwaranyo da hawaye saboda ita:

((Ka tuna) kuma Zakariya’u lokacin da ya roƙi Ubangijinsa (cewa): “Ya Ubangijina, kada Ka bar ni ni kaɗai (ba magaji), Kai ne kuwa Fiyayyen magada”. () Sai Muka amsa masa Muka ba shi Yahya, Muka kuma gyara masa (mahaifar) matarsa. Lallai su sun kasance suna gaggawa wajen yin alheri, suna kuma roƙonmu suna masu kwaɗayin (rahamarmu) kuma masu tsoron (azabarmu), sun kuma zamanto masu ƙasƙantar da kai gare Mu).

Haka kuma zuwa ga wanda bashi ya durƙusar da shi kuma ya gajiyar da shi, samunsa ya yi ƙaranci, matsalolin rayuwa suka yi masa dabaibayi suka taɗe ƙafafuwansa a hanyar neman abinci, ina ka bar karamcin Mai karamci! da arziƙin Mai yawan azurtawa da kyautar Mai yawan kyauta! Wanda Yake cewa a cikin Littafinsa: (kuma idan bayina sun tambaye ka game da Ni, To Ni kusa nake da su, ina amsa kiran mai kira idan ya kira Ni; to, su amsa Min nawa kiran, kuma su yi imani da Ni, don su shiryu) kuma Shi ne Mai cewa: (Sai na ce: “ku nemi gafarar Ubangijinku, lallai Shi Ya kasance Mai Yawan gafara ne() Zai saukar muku da ruwan sama mai yawa() kuma Ya daɗe ku da dukiyoyi da ƴaƴaye Ya kuma sanya muku gonaki Ya gudanar muku da ƙoramu).

Zuwa ga wanda ya shiga cikin tsanani, abokan gaba suka haɗe masa, duniya ta yi masa ƙunci, ku ɗaga hannu, ku yi ƙanƙan da kanku, ku roƙi Allah kuna masu yaƙini da cewa Zai amsa muku, domin Allah Maɗaukakin Sarki yana ganin bigirenku, Ya san cututtukanku kuma Yana ganin hawayenku Yana jin kokenku, Shi ne kuma Mai ikon cin galaba a kan abokan gabarku, idan Allah Mai girma da ɗaukaka Ya yi nufin wani abu, sai Ya samar masa da sanadi.

Don haka sai ku kyautata zato ga Ubangijinku, ku yi riƙo da LittafinSa da kuma Sunnar Annabinku tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, saboda a nan ne nasara da tabbatuwa suke, kuma dai da su ne ake samun kuɓuta ta gaskiya (Har yayin da Manzanni suka ɗebe ƙauna da imanin mutanensu, su kuma kafiran suka yi zaton an faɗa musu ƙarya ne game da zuwan azabar Allah, sai taimakonmu ya zo musu, sai Muka tserar da wanda Muka ga dama; ba kuwa za a kawar da azabarmu daga mutane masu laifi ba).

Ya ku bayani Allah! Ahir ɗinku da ɗebe ƙauna da kuma fitar da rai daga rahamar Allah, domin su ne hanyar kafirci da ɓata, kamar yadda Ma’abocin girma da buyawa Ya ce: (Kada ku ɗebe ƙauna daga rahamar Allah, lallai ba mai ɗebe ƙauna daga rahamar Allah sai mutane kafirai).

Kuma Ya ce: (Ba wanda zai ɗebe ƙauna daga rahamar Ubangijinsa sai ɓatattun mutane), domin lallai ɗebe ƙauna daga rahamar Allah yana daga cikin munana zato ga Allah, Allah Ya ce: (Kuma idan Muka yi wa mutum ni’ima sai ya bijire ya kuma juya kwuiɓinsa; idan kuwa sharri ne ya same shi sai ya zama mai yawan yanke ƙauna).

Kuma ku kiyayi masu sa yanke ƙauna, masu kashe gwuiwa, masu sa cire rai daga rahamar Allah: Ka ce wa wanda ya cika zuciyarsa da munanan zace-zace, wanda yake ƙuntata mana duniya cewa: sirrin rabauta shi ne: Kyautata tsammaninka ga wanda ya halicci rayuwa ya kuma raba arziki.

Imam ibnul Ƙayyim Allah ya yi masa rahama ya ce: Duk lokacin da bawa ya kasance mai kyautata tsammani ga Allah, mai kyautata fata gare Shi, mai dogoro na gaskiya da Shi, to, lallai Allah ba Zai tozartar da fatansa ba har abada, domin Shi Allah Tsarki ya tabbata a gare Shi baya tozarta fatan mai fata, Baya kuma lalata aikin mai aiki.

Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina neman gafarar Allah gare mu da sauran Musulmi daga kowane laifi, saboda haka ku nemi gafararSa, lalle Shi ne Mai yawan gafara Mai yawan jinƙai.

HUDUBA TA BIYU

Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, kamar yadda ya dace da cikarSa da wadatarSa, kuma ina gode Masa godiya da za ta yi daidai da kyautarSa da baiwarSa. Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya a ƙasa da sama, kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammad BawanSa ne kuma MazonSa, ya kai maƙura cikin kamala ta bil’adama, tsira da amici da albarkar Allah su tabbata a gare shi, da Alayensa, da Sahabbansa, da waɗanda suka bi tafarkinsu da hanyarsu.

Sa’annan, ku sani, ya ku bayin Allah! Lallai a cikin wuraren da kyautata wa Allah zato yake ƙarfafa, kuma ake rinjayar da fatanSa akan tsoronSa da fargabarSa, idan mutuwa ta zo wa bawa, ya yi dab da rabuwa da duniya, saboda lallai shi Mumini duk yadda ya kai da sakaci, duk yadda ya kusanci saɓo da munanan ayyuka, manya da ƙanana, ya sani cewa lallai Allah Mai ji ne Mai gani ga bayinSa, kuma Mai cikakkiyar masaniya ne game da rauninsu, Kuma Shi Mai tausayin su ne da suturta su.

An karɓo daga Jabir bin Abdullahi Al’ansari Allah Ya ƙara musu yarda, ya ce: “Na ji Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi kafin ya rasu da kwana uku yana cewa: (Kada ɗayanku ya kuskura mutuwa ta riske shi face yana kyautata wa Allah Maɗaukakin Sarki zato). Muslim ne ya ruwaito shi.

Malamai Allah Ya yi musu rahama sun ce: “Wannan jan kunne ne game da yanke tsammani, da kuma kwaɗaitarwa a kan kyakkyawan fata a yayin cikawa, wato shi ne ya sa rai cewa lallai Allah Zai ji tausayin sa, kuma Ya yafe masa”. Sannan ku yi yi salati da sallama ga mafi alherin halittun Allah, Muhammad bin Abdillah, domin haƙiƙa Ubangijinku Ya umurce ku da haka, Allah Maɗaukakin Sarki Ya ce: (Lallai Allah da Mala’ikunsa suna salati ga Annabi, Ya ku waɗanda kuka yi imani ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa).
Ya Allah Ka yi daɗin tsira da aminci da albarka ga BawanKa kuma ManzonKa Annabinmu Muhammadu.

Ya Allah Ka ƙara yarda da Halifofi guda huɗu, Jagorori nagartattu, Abubakar da Umar da Usman da Ali, da sauran Sahabbai goma da aka yi wa bushara da Aljanna, da waɗanda suka yi mubaya’a ƙarƙashin bishiya, da sauran Sahabbai baki ɗaya, da Tabi’ai, da waɗanda suka biyo su da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

Ya Allah Ka ɗaukaka Musulunci da Musulmi, Ka kiyaye shingen Addini, Ka taimaki bayinKa masu Tauhudi, Ya Mai tsananin ƙarfi. Ya Allah, Ka kawar da damuwar masu damuwa daga cikin Musulmi, Ka yaye ƙunci ga waɗanda ke cikin tsanani, Ka biya bashin masu bashi, Ka warkar da marasa lafiya daga cikin Musulmi.

Ya Allah, Ka ba mu tsaro a ƙasashenmu, Ka gyara shugabanninmu da majiɓinta al’amuranmu, Ka ƙarfafi shugabanmu, majiɓincin al’amuranmu, Hadimin Masallatai biyu masu alfarma, Ya Allah! Ka tsawaita rayuwarsa cikin lafiya da kwanciyar hankali, da ni’ima mai yawa.

Ya Allah, Ka datar da shi tare da Yarimansa amintacce, akan dukkan abin da zai kawo gyara ga ƙasa da al’umma, da kuma ɗaukaka ga Musulunci da Musulmai, Ya Ubangijin talikai.
Ya Allah, Ka zama mai ƙarfafa da ba da nasara da taimako ga ‘yan’uwanmu masu Rauni.
Ya Allah, Ka taimake su a Falasɗinu da duk inda suke, Ya Ubangijin talikai. Ya Allah, Ka kare sojojinmu masu tsaron iyakoki da fagagemmu.

Ya Allah, Ka kiyaye su da idanunka waɗanda ba sa barci, Ka ƙarfafe su da ƙarfi daga gareKa wanda ba ya gushewa, Ya Ubangijin talikai. Ya Allah, Ka sanya mu cikin waɗanda za a tsawaita rayuwarsu, kuma ayyukansu su yi kyau, cikin lafiya da Imani da alheri da kyautatawa. Ya Allah, Ka sanya mafi kyawun ayyukanmu su kasance na ƙarshe, mafi alherin lokutan rayuwarmu su kasance ƙarshensu, kuma mafi kyawun ranakummu ranar da za mu haɗu da Kai, kuma Ka karɓi rayukanmu alhalin Kana yarda da mu, ba Ka fushi da mu, Ya Ubangijin talikai.

Ya Allah, Ka sanya zukatanmu su ratayu da yardarKa, Ka raya su da tsoronKa da kiyaye dokokinKa, Ka sanya mu cikin masu kyautata zato gare Ka a duniya da Ranar haɗuwa da kai, Ya Mafi tausayin masu tausayi. Ya Ubangijinmu, Ka ba mu kyakkyawa a duniya, kuma Ka bamu kyakkyawa a lahira, Ka tsare mu daga azabar wuta. Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin buwaya daga abin da suke siffantawa, aminci ya tabbata ga Manzanni, godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai.

Don karanta Tsarabar Makon Sabbai 2025 danna nan

Edita; Rumasa’u M. Kallamu

labarin da ya wuceWayewa Da Cigaba A Mesopotamia
Labarin na GabaTarbiyyar Yara