Falalar La Ilaha Illallahu

0
14

An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) ya ce: “Wanda zai fi kowa azurta da samun ceto na ranar ƙiyama, shi ne wanda ya faɗi “La ilaha illallahu” dan Allah (Bukhari: 99).

An karɓo daga Abu Hurairah (Radiyallahu Anhu) Haƙiƙa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce: “wanda ya ce:

“La’ilaha illalahu wahdahu laa sharika lahu lahul mulku wa lahul hamdu wa huwa ala kulli shai’ in ƙadirun” sau ɗari (100) a yini guda.

Za a ba shi ladan ‘yanta bayi goma, za a rubuta masa lada ɗari, za a shafe masa zunubai ɗari, zai sami kariya daga shaiɗan a wannan yini har yamma, kuma babu wanda zai zo da wani abu da ya fi abinda ya zo da shi sai dai wanda ya aikata fiye da wannann. Kuma wanda ya ce:

“Subhanallahi wa bi hamidihi” sau ɗari a yini guda.

Za a zubar da zunubansa ko da yawansu ya kai kumfar teku. (Bukhari 3293, Muslim 2691)

Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Tasbihi Ya Ke danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Sallatut Tasbihi danna nan.

Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi domin karanta cikakken littafin danna nan.

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceFalalar Istigfari
Labarin na GabaFalalar Tasbihi