Category: Addu’o’i

Mun samar da wannan ɓangaren ne, domin samar da Addu’o’i na addinin musulunci a harshen Hausa kuma a sauƙaƙe. Za ku iya kai wa gare su ta hanyar amfani da kwamfutoci ko wayoyin hannu cikin sauƙi.

WikiHausa ta kowa ce. Kowa zai iya taimakawa da ilimi ko gyara.

Bugu da ƙari, kowa na iya amfani da wannan kafa domin koyo ko koyarwa.

  • Addu’ar Da Ake Ma Wanda Ya Sanya Sabuwar Tufa

    Addu’ar Da Ake Ma Wanda Ya Sanya Sabuwar Tufa

    “Tublii wa yukhliful laahu ta’ala”.

    {Allah ya sa ka mayar da ita tsumma, kuma Allah Maɗaukaki ya mayar maka da wata (tufar}.

    “Ilbis jadiidan wa ish hamiidan wa mut shahidan”.

    {Allah ya sa} ka sanya sabo, kuma ka rayu kana abin yabo; kuma ka mutu kana shahidi (wanda aka kashe a tafarkin Allah).

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Addu’ar Shiga Da Fita Daga Banɗaki danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Za Ka Mayar Da Gidanka Masarautarka danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Yadda Ake Addu’ar Tafiya Zuwa Masallaci

    Yadda Ake Addu’ar Tafiya Zuwa Masallaci

    “Allahumma ja’al ,fii ƙalbii nuuran, wafii lisaanii nuuran, wafii sam’ii nuuran, wafii basarii nuuran, wamin fauƙii nuuran, wamin tahtii nuuran, wa’an yamiinii nuuran, wa’an shamaali nuura, wamin amaamii nuuran, wamin kalfii nuuran, waj’al fii nafsii nuuran, wa a’azim lii nuuran, wa azzim lii nuuran, waj’al lii nuuran, waj’alnii nuuran, Allahumma A’aɗinii nuuran, waj’al fii asabii nuuran, wafii lahmii nuuran, wafii basharii nuuran, Allaahumma ja’al lii nuuran fii ƙabarii, wa nuuran fii izaamii, wa zidnii nuuran, wa zidnii nuurann fii izaamii, wa zidnii nuuran, wa zidnii nuuran, wa hab lii nuuran”.

    {Ya Allah ka sanya haske a cikin zuciya ta, da haske a kan harshena, da haske a ji na; da haske a gani na, da haske a ɓirɓishi na, da haske a ƙarƙashi na, da haske a baya na; ka sanya haske a cikin rai na, ka girmama haske gare ni, ka sanya ni (na zama) haske; ka sanya haske a cikin jijiyoyi na, da haske a cikin nama na, da haske a cikin jini na; da haske a cikin gashi na, da haske a cikin fata ta. Ya Allah ka sanya mini haske a cikin ƙabari na, da haske a cikin ƙasusuwa na; ka ƙara mini haske, ka ƙara mini haske, ka ƙara mini haske, ka ba ni haske a kan haske}.

    Domin karanta cikakken bayani akan Addu’ar Shiga Masallaci danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Addu’ar Ismullahil A’azim danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Addu’ar Shiga Masallaci

    Addu’ar Shiga Masallaci

    “A’uzu bil-laahi aziimi, wabi wajhihil kariimi, wa sulɗaanihil ƙadiimi, minas-shaiɗaanir rajiimi. Bismil-laahi, was-salaatu was-salaamu alaa Rasuulil-laahi, Allaahummaftahlii abwaaba rahmatika”.

    {Ina neman tsarin Allah Mai girma, da na Fuskarsa mai Alfarma, da na Mulkinsa daɗaɗɗe, daga shaiɗan tsinanne. Da sunan Allah, tsira da aminci su tabbata ga Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasallam). Ya Allah! Ka buɗe mini ƙofofin rahamarka}.

    Domin karanta cikakken bayani akan Addu’ar Fita Daga Masallaci danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Nafilolin Sallah danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Addu’ar Fita Daga Masallaci

    Addu’ar Fita Daga Masallaci

    “Bismil-laahi was-salaatu was-salaamu alaa Rasuulil-laahi (Sallallahu Alaihi Wasallam), Allaahumma inni as’aluka min fadhlika, Allaahumma’asimnii minas-shaiɗaanir rajiimi”.

    {Da sunan Allah, tsira da aminci su tabbata ga Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam). Ya Allah! Ina roƙonka daga falalarka. Ya Allah! Ka kare ni daga shaiɗan tsinanne}.

    Domin karanta cikakken bayani akan Addu’o’in Kiran Sallah danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Addu’a Idan Mutum Ya Yi Fushi danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Addu’ar Da Ake Yi Bayan An Binne Mamaci

    Addu’ar Da Ake Yi Bayan An Binne Mamaci

    Annabi, (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya kasance idan aka gama binne mamaci, sai ya ce; “Ku nema wa ɗan uwanku gafara, kuma ku roƙa masa tabbatuwa; domin yanzu ne ake yi masa tambayar ƙabari”.

    “Allaahummagfir lahu, Allahumma sabbit’hu”.

    {Ya Allah! Ka gafarta masa. Ya Allah! Ka ba shi tabbata}.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Addu’ar Ziyarar Maƙabarta danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Mene Ne Amfanin Zumunci? danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita; Rumasa’u M. Kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Ziyarar Maƙabarta

    Yadda Ake Addu’ar Ziyarar Maƙabarta

    “Assalaamu alaikum ahlad diyyaari minal mu’uminniina wal muslimiina wa innaa in sha’allaahu bikum laa hiƙuuna. (Yarhamul laahul mustaƙdimiina minnaa wal musta’akhiriina) as’alul laaha lanaa wa lakumul aafiyata”.

    {Aminci ya tabbata a gare ku, ya ku ma’abota waɗannan gidaje daga muminai da musulmi, kuma mu ɗin Allah ya so masu riskuwa ne da ku. Kuma Allah ya ji ƙan waɗanda suka yi saura. Ina roƙon Allah aminci daga bala’i, gare mu da gare ku}.

    Domin karanta cikakken bayani akan Addu’ar Da Ake Yi Bayan An Binne Mamaci danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Haƙƙin Wanda Mutuwa Ta Raba Shi Da Abokin Zamansa Daga Cikin Ma’aurata danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita; RMK

  • Addu’ar Tashi Daga Majalisi

    Addu’ar Tashi Daga Majalisi

    Addu’ar Tashi Daga Majalisi (Domin Neman Yafewa Ga Abin Da Ya Gudana A Cikin Majalisin).

    A’isha, Allah ya yarda da ita, ta ce: Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam), bai taɓa zama a wani majalisi ba, ko ya karanta Alƙur’ani, ko ya yi wata sallah face ya cika da waɗannan kalmomi:

    “Subhaanakal laahumma wa bi hamdika ashhadu an laa ilaaha illaa anta astagfiruka wa atuubu ilaika”.

    {Tsarki ya tabbata gare ka, ya Allah, da yabo gare ka. Ina shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai kai; ina neman gafararka, kuma ina tuba zuwa gare ka}.

    Sai A’isha ta ce:- “Ya Manzon Allah! Na lura cewa ba ka taɓa zama a wani majalisi ba, ka yi karatun Alƙur’ani, ko ka yi sallah face ka faɗi waɗannan kalmomi. Sai ya ce: “Ƙwarai. Duk wanda ya faɗi wani alheri sai waɗannan kalmomi su zama kamar hatimi ne ga alherin da ya aikata, wanda kuma ya faɗi sharri, sai su zama kaffara ne gare shi”.

    Domin karanta cikakken bayani akan Addu’a A Lokacin Da Mutum Zai Haw Abin Hawa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Ladubban Addu’a A Musulunci danna nan.

    Edita; RMK

  • Addu’a Idan Mutum Zai Yi Tafiya

    Addu’a Idan Mutum Zai Yi Tafiya

    “Allaahu akbar, Allaahu akbar, Allaahu akbar, subhaanal lazii sakkara lanaa hazaa wama kunnaa lahu muƙriniina wa innaa ilaa rabbinaa lamunƙalibuuna, Allaahumma innaa nas’aluka fii safarinaa hazaa birra wat taƙ’waa, waminal amali maa tardhaa, Allaahumma antas saahibu fis safari, wal khaliifati fil ahli, Allaahumma innii a’uzu bika min wa’asaa’is safari, wa ka’aabatil manzari wa suu’il munƙalabi fil maali wal ahli”.

    {Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma. Tsarki ya tabbata ga (Ubangiji) wanda ya hore mana wannan (abin hawa); ba mu kasance masu ikon sarrafa shi ba. Haƙiƙa mu masu komawa ne zuwa ga Ubangijinmu. Ya Allah! Muna roƙon ka nagarta da tsoron Allah a cikin wannan tafiya ta mu, da kuma aiki wanda kake yarda da shi. Ya Allah! Ka sauƙaƙe mana wannan tafiya ta mu, kuma ka naɗe mana nisanta. Ya Allah! Kai ne Ma’abocinmu a cikin wannan tafiya, kuma Halifanmu a cikin iyalanmu. Ya Allah! Ina neman tsari da kai daga wahalar tafiya, da abin gani mai sanya ɓacin rai, da kuma komawa mummuna ga iyali da dukiya}.

    Idan ya dawo daga tafiyar tasa, sai ya faɗi wannan addu’a kuma ya ƙara da cewa:

    “Aayibuuna taa’ibuuna aabiduuna li Rabbinaa haamiduuna”.

    {Mu masu komowa ne, masu tuba, masu bauta, kuma masu godiya ne ga Ubangijinmu}.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Addu’ar Shiga Wata Karkara Ko Wani Gari danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Sallar Kisfewar Rana Da Wata (Zazzaɓin Rana Da Wata) danna nan.

    Edita; RMK

  • Yadda Ake Addu’ar Shiga Wata Karkara Ko Wani Gari

    Yadda Ake Addu’ar Shiga Wata Karkara Ko Wani Gari

    “Allaahumma Rabbas samaawaatis sab’i wamaa izlalna, wa Rabbal shayaaɗiini wamaa aƙlal na, Rabbas shayaaɗiini wamaa adhlalna, wa Rabbar riyaahi wamaa zaraina, as’aluka khaira hazihil ƙaryati wa khaira ahlihaa wa khaira maa fiihaa, wa a’uza bika min sharrihaa wa sharri ahlihaa wa sharri maa fiihaa”.

    {Ya Allah! Ubangijin sammai bakwai da abin da suka rufe; kuma Ubangijin ƙassai bakwai da abin da suke ɗauke da shi; kuma Ubangijin shaiɗanu da waɗanda suka ɓatar; sannan Ubangijin iska da abin da ta yayyaɗa! Ina roƙon ka alherin wannan alƙarya; da alherin mutane da ke cikinta, da alherin abin da ke cikinta. Kuma ina neman tsari da kai daga sharrinta; da sharrin mutanenta; da sharrin abin da ke cikinta}.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Addu’ar Shiga Kasuwa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Mutane Biyar Da Suka Yi kama Da Manzon Allah (S.A.W) danna nan.

    Edita; RMK

  • Addu’ar Komowa Daga Tafiya

    Addu’ar Komowa Daga Tafiya

    Abdullahi ibn Umar, Allah ya yarda da shi, ya ce; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya kasance idan ya kama hanyar dawowa daga tafiya wani yaƙi; ko aikin hajji ko umara, idan ya hau tudu sai ya yi kabbara sau uku; sannan ya ce:

    “Laa ilaaha illallaahu wahdahu laa shariika lahu, lahul mulku walahul hamdu, wahuwa alaa kulli shai’in ƙadiirun, aayibuuna taa’ibbuna, aabiduuna li rabbinaa haamiduuna, sadaƙal laahu wa’adahu, wa nasara abdahu wa hazamal ahzaaba wahdahu”.

    {Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kaɗai; babu abokin tarayya a gare shi. Mulki nasa ne (shi kaɗai); kuma shi mai iko ne a kan komai. Mu masu komawa ne, masu tuba, kuma masu godiya ne ga Ubangijinmu. Allah Ya gaskata alƙawarinsa, Ya taimaki bawansa, Ya ruguza rundunonin kafirai shi kaɗai}.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yin Kabbara Da Tasbihi Yayin Da Ake Tafiya danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani akan Yadda Ake Tafiya Sujudah danna nan.

    Edita; RMK