Addu’a Ga Yaran Da Ba Sa Ji

0
26

Yaron da ake gani ya ɗauko hanyar lalacewa ba ya jin magana; ba a sa shi ya yi kuma ba a sa shi ya bari, to ga wata tajriba da ya kamata uwa ta yi wa yaranta.

Ranar Juma’a rana ce mai tsada. Shi ne lokacin sallar la’asar, duk addu’ar da kika yi a lokacin tana da tasiri ga wanda aka yi wa. A wata ruyuwar ma an ce Annabi Yaƙuba (Alaihis Salam) ya yi wa ‘ya’yansa addu’ar neman gafarar kuskuren da suka aikatawa ɗan uwansu Yusuf bayan Allah ya bayyanar da shi, don haka lokaci ne mai daraja.

Ana son bayan kin yi sallar la’asar ki sami ruwan zamzam ko kuma na rijiya ko kuma wanda kika yi alwala kika rage.

Bayan kin idar da sallarki cikin addu’arki sai ki karanta wannan addu’ar kamar haka;

“Ya maliku yaumud din, iyyaka na’abudu wa iyyaka nasta’in, ihdina siraɗal mustaƙim, siraɗal ladhina an amta alaihim, gairil magdubi alaihim waladdaaliin”

Sai ki roƙi Allah ya tsare miki yaranki ko yarinyarki tare da kiran sunanta ko sunanshi. Ki yi shi adadi mai yawa kya iya yin ɗari 100, kina karantawa kina tofawa cikin ruwan. In kin gama sai ki ƙara tahiya ita ma ƙafa ɗari 100 ki tofa cikin ruwan. Akan so kullum ki yi wannan har sai wata Juma’ar ta zagayo, kina yi kina tara ruwa. In kin gama sai ki rinƙa ba shi ruwan yana sha da safe kafin ya ci abinci haka da daddare kafin ya kwanta bacci. Inkuma ya yi kangarewar da ba zai sha ba, sai ki sarrafa masa a cikin abinci ya ci ya sha. Za ki ga mamaki yadda yaronki zai koma In Sha Allah.

Domin karanta cikakken bayani akan Matakan Da Za A Bi Domin Hana Yara Shaye-shaye danna nan.

Don karanta Hukunce-hukuncen Ƙananan Yara danna nan 

 

 

Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu

labarin da ya wuceYadda Ake Addu’ar Biyan Bashi
Labarin na GabaAbubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Ciwon Sanyi