Akan kai wani mataki duk irin kulawar uwa ko kuma kulawar uba ya zamto yaransu ko yarinyarta ta fanɗare.
Ka ga yaro ya jefa kansa cikin wannan hatsarin rayuwa, yaro ya rinƙa shaye-shaye sakamakon abokai da ya gamu da su.
Ga matakan da ake bi In Sha Allah zai daina:
1. Matakin farko raba shi da abokan hurɗarsa a sama masa wajen sana’a.
2. Mataki na biyu shi ne ana ɗaukan ayoyin sakina na Al ƙur’ani gaba ɗaya da kuma ayatus Sam, a karanta su a tofa a ruwan sama ko na rijiya, sannan a samu za’afaran da ganyen magarya da muski ɗan kaɗan sai a ba shi ya rinƙa sha da safe da kuma dare.
Sannan za a iya ɗaukan dukkan nau’in kayan mayen da yake sha a haɗa su guri guda; anemo garin kustul hindi cokali uku da kuma man zaitun da man habba da kuma man kwakwa da na tafarnuwa da na’a na’a a haɗa su guri guda da kayan shaye shaye sannan a rufe a bar su su kwana.
In gari ya waye a girgizasu sosai, sai a tace sannan a ba shi kafin ya ci abinci. Ana so da ya sha ya yi amai. Wannan haɗin ana so a rinƙa ba shi duk bayan sati uku ko kuma wata ɗaya. Sannan a haɗa da wannan ruwan da aka yi tofin ayoyin a ciki. Insha Allah duk abinda yake sha zai fita daga ransa ya dawo cikakken mutum.
Minhaj 274
Ayatus Sakina: Minhaj 255
Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Haddar Karatu danna nan.
Domin karanta cikakken bayani a kan Karatun Manzon Allah danna nan
Edita@rumasau-kallamu










