Jihar Kano jiha ce dake a Ƙasar Nijeriya. Tana da yawan fili kimanin kilomita murabba’i 20,131 da yawan jama’a milyan sha ɗaya da dubu hamsin da takwas da dari uku (jimillar shekara 2011).
Babban birnin tarayyar jihar ita ce Kano. Abdullahi Umar Ganduje shi ne gwamnan jihar tun zaben shekara ta 2015 har zuwa yau. Mataimakin gwamnan shi ne Nasiru Gawuna. Dattijan jihar sun haɗar; Aminu Kano, Maitama Sule, Sani Abacha, Murtala Mohammed, Sanusi Lamido Sanusi, Ibrahim Shekarau, Isyaka Rabi’u, Aliko Dangote, Rabiu Musa Kwankwaso, Barau I Jibrin da Kabiru Ibrahim Gaya.