Ga ta nan, ga ta nanku.
An yi wasu kishiyoyi biyu masu zaman lafiya a tsakaninsu a wani gari. Ba su taɓa ɓata wa juna rai ba. Suna nan, sai wata rana ɗaya daga cikinsu ta kwanta jinya. To da ma kowaccensu tana da ’ya mace, ’ya’yan kuma sun yi kama da juna ainun, yadda ba kowa ne zai iya bambance su ba, tamkar dai ’yan biyu.
Da mai jinyar nan ta ga alamun ciwon nata ba na tashi ba ne, sai ta kira kishiyarta, ta ba ta amanar ’yarta. Kishiyar ta karɓa, kuma ta yi alƙawari za ta kula da duka yaran biyu kamar ita ta haife su. Da mai jinyar ta rasu, sai kishiyar ta ci gaba da kula da yaran har suka girma, suka zama ’yan mata.
To amma saboda tsabar so da adalci da take yi wa ’yar kishiyarta, sai ya zamanto ba ta iya gane ’yarta daga cikinsu, domin kamanninsu ɗaya. Sai wata tsohuwa ta ziyarce su da ta lura da yanayin matar ta hanyar adalcin da take nunawa a tsakanin yaran, sai ta rinƙa yi mata faɗa a kan yaya za ta riƙi ɗan wani kamar nata.
Sannu a hankali, har dai ta fara karkata ga zancen tsohuwa, to amma sai tace ba za ta iya gane ɗiyarta daga cikin yaran ba. Sai tsohuwar nanta ba ta shawara da cewa in sun je ɗaukar ruwa kafin su dawo, ta dafa dambu, ta ajiye a bakin randa, in sun dawo suna jin yunwa za su fara ci.
To sai ta bari sai sun fara cin dambun sai ta daka musu tsawa, tana cewa: “Kun san yadda yake ne, ba ku tambaya kafin ku fara ci? ”Tsohuwa ta ce mata ta lura da kyau, domin wadda ta fara cire hannunta daga akushin dambun to ita ce ’yar kishiyarta. Wadda taƙi cire hannunta, kuma ta ce suna jin yunwa ne, to ita ce ’yar cikinta.
Sai kuwa matar nan ta yi hakan. Bayan yaran sun dawo daga ɗaukar ruwa sai suka hangi dambu a bakin randa, suka nufi bakin randa da gudu, suka fara cin dambu. Nan take sai ta daka musu tsawa, tana cewa: “Kun san yadda dambun yake ne, ba ku tambaya ba kafin ku fara ci? ”Nan da nan suka razana, sai ’yar kishiyarta ta cire hannunta daga cikin akushin dambu, ita kuma ’yarta ta cikinta, ta dubi uwarta ce: “Haba mama, muna jin yunwa ne fa.
”Daga nan sai ta kama ’yarta ta kai daki, kuma ta kama’yar kishiyarta ta yi mata tsaga a fuska. Daga nan fa sai ta fara gana wa ’yar kishiyar nan tata azaba iriiri, har ya kai ga in za su ci abinci, sai ta ƙi zuba wa ’yar kishiyarta nata abincin a akushi, sai ta zuba mata a ƙasa. Amma kuma maimakon ’yar kishiyar nan ta rame ko ta damu, sai ƙiba kurum take yi.
Daga nan sai ta daina ba ta abincin sam-sam, har ma dai takore ta daga gidan, wai ta je can kabarin uwarta ta karbi abinci. Da yarinya ta ji haka, sai ta yi ta kuka, ta kama hanya ta tafi bakin kabarin uwarta tana kuka. Ana haka, ana haka, wata rana da ta je kabarin uwar tana kuka, sai uwar ta fito ta rarrashe ta, ta ba ta abinci, ta ci ta ƙoshi.
Haka dai, kullum sai ta je bakin kabarin uwarta, ta fito ta ba ta abinci. Nan da nan ta sake yin ƙiba, ta yi kuma kyau, ta goge, abin gwanin ban sha’awa. Ita kuwa mai uwa a murhun, sai ramewa take yi. Uwarta ta rasa abin da za ta yi. Wata rana sai wasu samari suka je tambayar uwar cewa ɗaya daga cikinsu yana son ya shiga neman auren marainiyar.
Maimakon ta yi abin da samarin suka nema, sai ta ce sai dai su auri ’yarta. Su kuma suka ce waccan mai tsaga a fuska suke so. Amma sai ta hana su, ta mare su, ta gaya musu kada su sake zuwa gidan neman aure in ba ’yarta suke so ba. Da marainiyar nan ta ga haka, sai ta gudu, ta shiga uwa duniya. Tana cikin tafiya a dokar daji, sai ta ga shinkafa da nama.
Sai shinkafa ta yi wa budurwar nan magana, ta ce idan tana jin yunwa ta zauna ta ci. Amma sai yarinya ta ce ta ƙoshi, kuma ta ci gaba da tafiya. Can kuma sai ta ga naman kaza, sai naman ya yi mata tayi, amma sai ta ƙi ci, ta ci gaba da tafiya. Haka ta rinƙa haɗuwa da kayan daɗi iri-iri, amma ta ƙi amsa tayinsu, ta haƙura da yunwar da take ji, ga baƙin cikin da ke damunta.
Tana cikin tafiya sai ta ga hadari ya haɗu, ita kuma babu inda za ta fake. Ta duba nan, ta duba can, sai ta hangi wata ’yar bukka, nan take ta nufe ta a guje, ta buɗe ta shiga. Bayan ta zauna sai ta ga wani babban kumurci a gefenta. Sai macijin nan ya sulalo ya nufo wurinta, amma ba ta ji tsoro ba sai kallon sa take yi.
Da ya ji bayaninta, sai ya tambaye ta tana iya gane garin, sai tace ta sani. Ba tare da ɓata wani lokaci ba, sai ya ce ta shirya su je su kai musu ziyara. Jin haka ya sa ta shiga murna da shirye-shiryen tafiya. Ta tanadi kayan sutura da sauran kayan masarufi. Da ranar da suka sa ta zo, sai Sarki ya sa aka haɗa su da dawakai da ’yan rakiya masu yawa, sai ka ce ita ce matar Sarki, suka kama hanya.
Da suka isa garin, sai ita da mijinta da ’yan rakiyarsu suka nufi gidan iyayenta, suka shiga gidan, mutanen gari kuma suna ta mamakin yadda wannan yarinyar da aka ba wuya a baya ta koma. Da ’yar’uwarta ta gan ta sai ta rungume ta, amma da kishiyar uwarta ta fito sai ta ce ba ita ce ta ɓata ba, to amma saboda tsagun fuska da ta yi mata, sai ta gane ta.
Nan take suka rungume juna cikin murna. Bayan amarya ta huta sai suka fara hira, ta kwashe labari tun daga barinta gida har zuwa lokacin da ta auri ɗan Sarki. Data gama ganin dangi, sai ita da mijinta suka yi musu sallama, suka kama hanya tare da ’yan rakiyarsu, sai garin mijin.
Bayan tafiyarta sai kishiyar uwarta ta ce lallai ita ma ’yarta ta je ta auro ɗan Sarki. A kan dole yarinya ta amsa. Da ta kama hanyar tafiyar neman ɗan Sarkin da za ta aura, kamar dai yadda ’yar’uwarta ta yi, tana shiga daji sai ta ga shinkafa da nama. Tun kafin ma a yi mata magana sai ta tsuguna ta fara ci. Sai shinkafa ta ce da ita: “‘Yan mata zo ki ci shinkafa.
”Da budurwa ta ji haka sai ta dubi shinkafa ta mayar mata da jawabi: “Da ma ko ba ki yi magana ba, ai ina jin yunwa.” Sai ta ci gaba da cin shinkafa har ta ƙoshi. Daga nan sai ta kama hanyar ta fara tafiya. Ba ta yi nisa ba kuma sai ta haɗu da naman kaza. Nan ma ta zauna ta ci har ta ɗebi cinya da fukafukai da ƙirjin kaza a hannunta, ta yi guzuri. Ta sa kai ta fara ci gaba da tafiya tana lasar baki.
Ba jimawa sai hadari ya taso, ta rasa yadda za ta yi. Gashi ba gari kusa a baya, kuma ba ta san inda ta dosa ba. Can sai ta hangi wata ’yar bukka, ta ruga a guje ta shiga, sai ta ga wani shirgegen maciji. Tana ganin macijin nan sai ta ƙwala ihu, tana neman hanyar gudu. Sai ɗan yaro ya ɓullo ɗauke da abinci, ya ce ta ba macijin abinci.
Sai ta ce: “Tabɗi! Ta yaya ina jin yunwa in ga abinci in ba wani maciji?” Sai ta kama cin abinci, ta yi watsi da maciji. Jim kaɗan sai macijin ya fara rikiɗa. Tana ganin haka sai ta faɗi sumammiya, watau ba ta ga ɗan Sarki ba, balle ta san kamanninsa. Bayan ta farka sai ta gan ta a gidan wasu masu sarauta, amma talakawane da wani ɗan yaro ya zo ya gaya mata cewa za a zo a yi mata kitso, amma idan makitsiyar ta ba ta abin ƙwalama kada ta ci.
Tana cikin haka da macijin nan, sai wani ƙaramin yaro yaɓbullo ɗauke da kayan abinci, ya gaya mata ta ba macijin nan abinci. Nan da nan ta ba shi ruwa ya sha, kuma ta ba shi abinci ya ci. Da ya ƙoshi sai ya rufe baki. Bayan ta kammala ciyar da macijin nan da shayar da shi ruwa, sai yaron ya tambaye ta ko ita ma za ta ci abincin ne.
Sai tace ta ƙoshi. Sai macijin nan ya sake yin ƙoƙarin razana ta, amma sai tace ita komai ya ga dama ya yi mata, domin ba ta da wurin zuwa, kuma ta riga ta sadaukar da rayuwarta. Da jin haka, sai macijin ya shiga rikiɗa, yana zama namun daji daban-daban, amma duk da haka ba ta razana ba. Maimakon haka ma, sai ta gyara zama tana kallon ikon Allah, har dai macijn nan ya rikiɗa, ya koma yaro matashi kyakkyawa.
Yarinyar ba ta sani ba, ashe macijin nan ɗan Sarki ne yake neman aure, amma sai ya bi wannan hanya don ya sami mace mai hankali, mai amana. Nan da nan ya sa aka ɗauke ta a kan doki, akakai ta gidan Sarki, aka ɗaura mata aure da shi, aka sha biki. Bayan an gama biki sai aka tura yaro ya gaya wa amarya za a zo a yi mata kitso, to amma matar da za ta yi mata kitson mayya ce, kuma za ta zo da kayan ciye-ciye a hannunta, idan ta ba ta kada ta ci.
Yaron ya ce mata ta riƙe duk abin da za ta ba ta a hannunta, ko sau nawa ta ba ta kuwa kada ta sa a baki. Yaro ya ƙara bayyana mata cewa, bayan wannan mayya ta gama kitso za tayar da matsefata a gidan, amma kada ta gaya mata, ta kyale ta ta tafi. Bayan ta tafi kuma za ta dawo ta tambayi matsefatar, to sai ta miƙa mata haɗe da kayan ciye-ciyen da ta ba ta.
Amaryar ta amince. Da makitsiya ta zo gidan, sai aka ce ta je ta yi wa amarya kitso. Da ta fara kitso sai ta miƙa wa amarya kayan ƙwalama, wai ta ɗan lashe bakinta da shi, sai amarya ta karɓa kamar za ta ci, amma sai ta riƙe a hannunta. Jim kaɗan kuma sai
ta sake miƙa mata wani abincin, sai amarya ta karɓa ta haɗa su a hannunta. Haka dai har sai da suka gama kitso, makitsiyar ta tashi za ta tafi, sai ta yar da matsefin da ke hannunta a tsakar ɗakin amarya, amma amarya ta ƙi gaya mata.
Makitsiya ta kaɗa kai ta yi tafiyarta. Bayan wasu ’yan sa’o’i da tafiyarta sai ta dawo, wai ta manta matsefinta a gidan, sai amaryata ɗauko mata, ta haɗa mata da kyautar da ta ba ta ta kayanƙkwalama a lokacin da take yi mata kitso. Da mayyar nan ta ga an dawo mata da tarkacenta, sai kawai ta fara zage-zage, ta kama hanya a fusace ta fita abinta. Amarya da mijinta ɗan Sarki suka ci gaba da zamansu cikin jin daɗi.
Wata rana sai amarya ta kwanta a ɗaki ita kaɗai tana ta rusar kuka. Da mijinta ya shigo sai ya tambaye ta abin da ya faru, sai tace tana tunanin gidansu ne da mahaifinta da kuma kishiyar mahaifiyarta wadda ta riƙe ta. Ta kwashe labarinta gaba ɗaya ta gaya masa. Tana jin wannan ƙa’ida sai ta ce: “Tabdi! Ai ni in har na ga abin daɗi ba zan ƙyale shi ba sai na ci.
…..”Da makitsiya ta zo ta fara kitso sai ta miƙa wa yarinyar abin ƙwalama, sai ta karɓa ta kai baki ta cinye. Da ta sake miƙa mata na biyu sai ta sake lanƙwamewa. Bayan sun gama kitso sai makitsiyarta yar da matsefinta, sai ta ce da ita: “Ai kin manta matsefinki.” Sai ta juya ta karɓa, ta tafi tana dariya. Bayan wasu ’yan kwanaki sai yarinyar nan, abin tsautsayi ta kamu da cuta, wadda ta zama ajalinta aka binne ta, ba tare da ta auri ɗan sarkin ba. Kurunkus.
Abubuwan Da Labarin Yake Koyarwa
- Munafunci dodo ne, yakan ci mai shi.
- Mai rabon ganin baɗi ko ana ha maza ha mata sai ya gani.
- Hassada ga mai rabo taki ce.
- Mahakurci mawadaci.
Wannan tatsuniya an ciro ta ne daga littafin TASKAR TATSUNIYOYI wanda Bukar Usman OON ya wallafa.
Karanta Tatsuniyar Ƙawancen Kyanwa Da Bera
Edita@rumasau-kallamu








