Shi da yara suka zauna suka gama shan ruwan sanna ya sa Afaf ta kwashe kwanukan, nan suka zauna suka cigaba da kallo suna wasannisu. Har lokacin kwanciyar bacci babu wanda ya ba shi matsala a yaran. Ya tasa su a gaba ya raka su ɗakinsu domin su yi shirin bacci; yana shiga ɗakin zarni ya doki hancinsa.
Ya dubi Afaf yace ‘Ba na ga Ummi ta fitar da katifun nan ba? Me yasa suke zarni?’ ‘Ta fitar Abba, sai da yamma sannan ta shigo da su gaba ɗaya. Ban sani ba ko katifar Habib ce ba ta bushe ba don ba mu san an yi fitsari ba sai wajen la’asar sanna ya gaya mata Shukra ta yi masa fitsari bayan asuba da ka kwantar da ita.
Shi ne aka shanya, to ina jin ita ce ba ta gama bushewa ba.’ Ya ƙarewa ɗakin kallo, ko shimfiɗa ba a yi ba a kan gadon don haka ya sa Afaf ta yi musu shimfiɗa yayin da shi kuma ya wuce da su banɗaki don su yi brush. Nan da nan kowa ya shirya bayan sun fito sun kwanta ya cewa Afaf ‘Wai sai yaushe katifun nan za su daina zarni ne?’
‘Ni ma ban sani ba Abba, kuma fa idan ba ka saka su sun yi fitsari da daddare ba haka gobe ma za su sake yin fitsarin nan fa. Dama Anti ce kullum take tashinsu, Nasreen sau ɗaya ita kuma Shukra sau biyu shi yasa basa yi a kwancen. ‘To ƙarfe nawa take tashinsu?’
‘Wallahi Abba ni ma ban sani ba, kawai dai tana tashinsu.’ Ya amsa sannan ya fito ya dawo parlor ya zauna; to shi yanzu ya za a yi ya san ƙarfe nawa zai saka su wani fitsari, ga shi kuma ga dukkan alamu idan ya bar su suka cigaba da fitsarin nan a kwance to lallai gidan zai daina zaunuwa.
To amma ƙarfe nawa zai saka su? Wataƙila sai dai kawai idan ya tashi kwanciya bacci ya saka su shikenan. Nan ya zauna a parlor ɗin ya cigaba da kallonsa yana chatting, har ya sami Khadeejan ma online suka ɗan yi hira.
Ba su fi awa ɗaya da kwanciya ba ya jiyo kukan Shukra daga ɗakin, da sauri ya dire wayar da take hannunsa ya nufi ɗakin. Tana zaune a kan gadon tana ta faman kuka har da hawaye. Ya ƙarasa ya zauna a kusa da ita yana cewa ‘Menene Shukra?’ ‘Kashi zan yi.’
‘To ai ba sai kin yi kuka ba Shukra, sauko mu je na saka ki a toilet.’ Ya sauke ta daga kan gadon ya ja hannunta suka wuce banɗaki, suna shiga ya cire mata wando ya fara ƙoƙarin ɗora ta a kan toilet ta dafe duwawu tana juyi tana cewa ‘Ina fo na Abba a shi zan yi.
’Cikin muryar lallashi yace ‘To ai ba a ganshi ba ki yi haƙuri ki hau toilet. ‘Mu je ka duba banɗakin Anti fo ɗina yana nan Abba a shi zan yi kashin.’ Ya ɗauke ta gaba ɗaya ya ɗora a kan toilet yana cewa ‘To ki gama kashin kada ya fito in ya so idan kika gama sai mu je mu dubo fo ɗin.’
Kafin ya rufe bakinsa ta zame ta sauka daga kan toilet ɗin, tana kuka. Ta cigaba da bubbuga ɗuwawunta tana shirin ficewa daga banɗakin tana cewa ‘Fo na yana banɗakin Anti bari na ɗauko a shi zan yi kashin.’ Cike da tsananin mamaki da takaici yake kallonta, ga dukkan alamu kashin ya matse ta amma ita ba ta da niyyar zama a toilet ɗin nan so take dole sai ya ɗauko mata fo; fo ɗin da ya riga ya jefar ba tare da kowa ya sani ba.
Ya kai hannu ya damƙota tana shirin ficewa daga banɗakin, ya mayar da ita kan toilet ɗin ya zaunar da ita yana cewa ‘Anti ta kulle ɗakinta ta tafi da mukullinta sai ta dawo za ta buɗe mana, ki yi kashin a nan.’ Ta sake direwa ta sauka daga kan toilet ɗin tana buga ɗuwawu har da juyi saboda yanda kashin ya matse ta tana cewa ‘Ka zo na nuna maka Abba ba ta rufe ba, a buɗe ɗakin yake ɗazu ma na shiga.’
Kafin ya yi wani abu kashin ya ƙwace mata, ɗan kaɗan ya faɗo ya zame daga ɗuwawunta ya ɓata tsawon ƙafarta sanna ya dire a ƙasan toilet ɗin. Ya yi wuf ya ɗauketa ya daka mata tsawa yana cewa ‘Ki zauna a nan ki yi kashin nace, kalli yanda kika ɓata jikinki kika ɓata toilet ɗin da kashi.’
Ta sake fashewa da kuka tana yi tana shessheƙa, takaici ya sa ko magana ba zai iya yi mata ba don haka ya ƙyale ta kawai yana tsaye tana rungume da ƙafarsa yana jira ta gama. Ko minti ɗaya ba ta yi ba tace masa ta gama kashin, ya leƙa toilet ɗin shi bai ga komai ba. Yace ‘Idan fa kika yi min kashi a wando zane ki zan yi Shukra gara ki gama kashin nan a nan.’
‘Na gama. Ya ɗauketa cak ya ajiye ta a wajen wanka, ya ɗauki sprayer ɗin yin tsarki ya fesa mata ruwan da ƙarfi ta yanda ruwan ya wanke kashin jikinta, sannan ya saɓi sabulu ya wanke mata da hannunsa. Ya ɗauke ta ya fitar da ita ya shirya ta ya kwantar da ita sannan ya koma banɗakin; ya tsaya daga bakin kofa ya ƙarewa banɗakin kallo.
Ga guntun kashin da ta jefar a ƙasa sannan gashi duk ta shafe na jikinta a jikin toilet ɗin banɗakin har ya fara wari. Ya yi tsaki ya juya ya fice, jimawa kaɗan ya dawo ɗauke da tissue paper, ya warware kusan rabinta sannan ya yi amfani da ita ya ɗauke guntun kashin jefe a toilet ɗin. Sannan ya sake warwarowa ya goge toilet ɗin ya yi flushin sannan ya fito ya dawo parlor ya zauna cike da takaici da gajiya.
A nan a parlor ɗin bacci ya kwashe shi, wataƙila saboda tsabar gajiya domin bacci ya yi masa nauyi sosai. Maganar Shukra ce ta farkar da shi wadda ta je tashinsa tana sanar da shi za ta sha shayi. Ya tashi zaune yana mittsike ido, ya lalubi waya ya duba lokaci; ƙarfe ukun dare saura.
Haka ya tashi ya haɗo mata shayin ya zo ya ba ta ta shanye sannan ya ja hannunta suka koma ɗakin. A nan ya tarar ita da Nasreen duk sun riga sun yi fitsarinsu a kwance; ya canzawa Shukra kaya ya lallaɓa ya kwantar da ita a gefen da bai jiƙe ba kusa da Afaf. Ya ɗan tsaya ya ƙarewa ɗakin kallo, sai kuma ya juya ya fice.
Gaba ɗaya kansa ya kulle; wai dama haka yaran nan suke ko kuwa don sun ga mahaifiyarsu ba ta nan ne kuma Khadeeja ba ta nan suka saka shi a gaba suka hana shi sakat, domin wasu abubuwan da suke yi ma kamar da gayya musamman Shukra.
Har zai zauna a parlor ɗin kuma ya tuna sai ya dafa abinda zai yi sahur don haka y wuce kitchen, ya janyo indomie ya ɗebo park uku sannan ya nemi tukunya ya ɗora; Afaf da Habib sun yi ta fushi a kan jiya bai tashe su sahur ba don haka yau idan ya gama dafa abincin sai ya tashe su.
Nan da nan ya dafa idomie ya zubawa kowa a plate ya ɗora a dining table sannan ya haɗawa kansa shayi. Bayan ya gama ya wuce ɗakinsu, ya kunna fitila sannan ya ƙarasa ya tashi Afaf, ta zauna a kan gadon tana mittsike ido sanna ya wuce ciki ya tashi Habib. Yana juyawa ya buɗe ido yace ‘Abba asuba ta yi ne?’
‘No da saura, sahur za mu yi tukunna ga indomie can na dafa.’ Ya ba shi amsa. Ya gyara kwanciya yana janyo abun rufarsa yana cewa ‘Ni ba zan yi azumi ba Abba, sai gobe.’ Ya rufe ido ya cigaba da baccinsa ba tare da ya sake bi ta kan Abban nasa ba. Afaf wadda take zaune a bakin gadonsu ta juyo tace ‘Abba wai sahur za mu yi.’
‘Eh.’ ‘To Abba ai jiya ne ya kamata mu yi azumi kuma ba ka tashe mu ba, ni ma dai gaskiya yau ba zan yi azumin ba sai gobe. Dama haka muke yi da Anti; mu yi ɗaya mu sha ɗaya.’ Ta faɗa cikin halin ko in kula. Ba ta ma tsaya ta saurari amsar shi ba ta koma ta kwanta ta rufe ido.
Nan ya tsaya yana kallonsu cike da mamaki; wai su yaran nan me yake damunsu ne? yanzu za su ce za su yi abu kafin wani lokaci sun canza ra’ayi. Gaskiya ya jinjinawa mata, ai idan ba mace ba babu wanda zai iya raino; jiya fa Afaf fushi ta yi da shi saboda bai tashe ta ba amma yau kuma ita yake tashi tana ce masa wai yau bai kamata ta yi azumi ba.
Yana fitowa daga ɗakin ya haɗa indomie ɗin ya juye a tukunyar ya rufe ya ajiye musu a kan idan gari ya waye sa ci abincin safe, sannan ya dawo ya ƙarasa sahur ɗinsa.
Kamar yanda suka saba yau ɗin ma da tun asuba suka tashe shi a kan yunwa suke ji, haka ya shiga kitchen Afaf ta taimaka masa ya haɗawa kowa cereal domin duk sun ce ba za su ci indomie ba don ta yi sanyi kuma ba sa son ɗumame, da ya takura musu ma sai Nasree cewa ta yi ‘Abba kai fa idan ka dafa indomie ba ta daɗi, ka bari idan Anti ta dawo ta koya maka.’
Don haka kawai sai ya mayar da indomie ɗin ya rufe. Tun wajen goma na safe yake sa ran shigowar Ummi don ya riga ya gaya mata yau ma ta zo, sai dai ga mamakinsa har wajen sha ɗaya saura ba ta shigo ba; gashi har na fara yi masa ƙorafin yunwa kuma ana ba shi warning ba za a ci indomie ba sai da taliya ko macaroni.
Yana shirin fita ya je gidan su Ummin aka buga gate; ƙanwarta ce wadda suke kira Nana, wadda ba ta fi shekaru bakwai ba. Bayan ta gaishe shi tace ‘baba yace na gaya maka Ummi ba za ta sami zuwa wajen su Afaf ba yau don ta tashi da mura me zafi tana kwance, yace sai dai ko zuwa gobe idan ta sami sauƙi za ta shigo.’
Jiki a sanyaye ya amsa ‘To, kice ina mata sannu kuma ki ce ina gaida Baban. ’Ya rufe kofar ya koma cikin gidan gwiwarsa a sanyaye; ya zai yi da yaran ga gidan kace-kaca musamman kitchen ɗin, ko ina kwanuka. Tukunna ma; mura fa aka ce Ummi take yi. Inna lillahi wa inna ialaihi raji’un! Allah ya sa yarinyar nan ba Covid-19 ta kwaso ba garin yawon tsiya, don tabbas idan ta kwaso to ta shafawa yaransa.
‘Subhanallah!’ ya faɗa a fili yana daf da ƙarasawa cikin gidan. Bayan ya shiga gidan ya yi musu bayanin Ummi ba ta da lafiya. Yana ji yana gani haka ya haƙura Afaf ta dafa musu jallof macaroni, bayan sun gama ci kuma ta kwaso wanke-wanke ta fice da shi waje ta wanko; duk da ƙoƙarinsa na hana ta amma haka ta dage ta wankesu.
Sannan ta umarci Halifa da ya share cikin gidan wanda shi ma nan da nan ya yi, suka dawo suka zauna. Wunin ranar haka ya yi shi yana gyangyaɗi domin ko ya rufe ido da niyyar bacci haka wani zai rugo kai ƙara har Afaf ɗin ma, ko kuma a zo a ce masa ana buƙatar wabi abu; ita kam Shukra haka kawai ma da ta ga ya shiga ɗaki binsa take yi, idan kuam a parlor ne da ya rufe ido za ta kirawo sunanshi tace ya buɗe ido ta nuna masa wani abu.
Haka har aka kusan magriba sannan ya samu da taimakon Afaf ya soya musu dankalin bature kuma ya dafa musu indomie ta ɗan yi daɗi. Wuni yaran suka yi suna ciye-ciye amma ko da ka sha ruwa ma saka shi suka yi a gaba ana cin abinci suna masa surutu da rigingimu kala-kala; shi dai zai iya cewa ba a hayyacinsa ya ci abincin nan ba. Haka ya dinga ci yana ƙwarewa.
Ya cika bakinsa da dankali Shukra ta miƙe ta jefar da dankalin da yake hannunta tana dafe ɗuwawu tana cewa ‘Kashi Abba.’Ji ya yi wani malolo ya tokare masa maƙogoro; wai ita Shukra ba ta tashi kashi ne sai mutum yana tsaka da wata sabga? Lallai yanzu ya tabbatar Khadeeja tana da ƙoƙari don kusan tunda aka fara azumin nan sai ana tsaka da cin abinci sannan Shukra take cewa za ta yi kashi kuma ta tashi ta sakata; idan ma ta yi jinkiri shi ne yake nuna damuwarsa.
Ya dubi Afaf wadda ya kula kamar ta ɓata rai ne yace ‘Yaya Afaf ki saka ƙanwarki a toilet ta yi kashi.’ Ta tashi a fusace ba tare da ta amsa ba ta dire kofin shayin da take sha a ƙasa, tana ɗaga kafa ta yi fatali da kofin shayin ya zube ya fallatsa ya ɓata Habib wanda yake kusa da ita. Ya miƙe a fusace yana nunata ‘Dalla malama ji yanda za ki ƙona ni da shayi saboda kashin wata.’
Ita ɗin ma a fusace tace ‘To ka matsa mana, ko ba ka gani ne?’ Abbansu ya buɗe baki zai yi magana Shukra tace ‘Kashi Abba.’ Ya tuna yanda suka yi cikin dare ya tabbatar bai shirya wanke kashi a parlor ba don haka ya miƙe ya wuce su ya ja Shukra ya nufi banɗaki da ita. Sai da ta gama kashin ya wanke mata ya fito sannan ya saka su a gaba ya yi musu faɗa, ya sa Afaf ta gyara inda ta ɓarar da shayi.
Ya kurɓi shayinsa da ya bari ya ji ya yi sanyi, haka dai ya haƙura ya shanye ya ɗan ƙara cin abincin. Haka ya haƙura ya nemi waje ya zauna yana tunani don zai iya cewa ba ƙoshi ya yi ba ya dai haƙura da abincin ne kawai, haka ya dinga bin su da kallo suna ta wasanninsu har loakcin kwanciyar bacci.
A cikin wannan halin Mustapha ya ƙarasa kwanaki biyu shi da yaran a jigace, ga shi duk wanda ya yi atishawa ko tari a cikin yaran sai ya firgita saboda gani yake kamar corona ce ta kwantar da Ummi kuma su ma sun shafa a wajenta.
Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Bakwai
Edita@rumasau-kallamu









