Addu’a Idan Mutum Yana Cikin Damuwa

0
32

Wannan addu’ar mutum yakan yi ta idan ya shiga cikin damuwa ko ya shiga cikin wani hali, ko tashin hankali; ya rasa yadda zai yi sai ya lazimci karanta wanan addu’ar. Allah zai fidda shi daga cikin wannan tashin hankalin da damuwa.

An ruwaito daga Imam Ali Hassan Shazah, yana koyawa almajirinsa wannan addu’ar. Ga ta kamar haka;

“Ya wasi’u ya Aleem, ya zal fadlul azeem, wa in tamsasni bi durrin fala kashifa lahu illa anta, wa’in turidni bi khairin fala raadda bi fadlik, tusibu man tasha’u min ibadak wa antal gafurur rahim”

Akan so duk lokacin da ka yi salla ko ka yi wani aikin alkhairi ka karanta wannan addu’ar, Ubangiji Allah zai yaye maka damuwarka In Sha Allah. Ansamo wannan addu’ar daga littafin MAFATIHUL FARAJ shafi na 110. Domin karanta cikakken bayani akan Addu’ar Kyautata Tsakanin Ka Da Ubangiji Da Neman Gafara dannna koren rubutu. Don karanta Addu’a Gatan Mumini danna koren rubutu. Edita; Rumasa’u Muhammad Kallamu
labarin da ya wuceMa’anar Damokuraɗiyya
Labarin na GabaAbubuwan Da Ya Kamata Ka Sani Akan Android