An karɓo daga Abu Sa’id Ibnul Mu’alla (Radiyallahu anhu) yace; Na kasance ina salla a masallaci sai Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya kira ni.
Sai ban amsa ba, sannan sai ne je wajensa na ce salla neke yi. Sai ya ce; “Shin Allah bai ce: ” Ku amsawa Allah da Manzonsa ba idan suka kira ku? Sai ya ce; zan sanar da kai surar da ta fi kowace sura girma a cikin Alƙur’ani kafin ka fita daga masallaci”.
“Sai ya riƙe hannuna, da muka kusa fita sai na ce; “Ka ce za ka sanar da ni surar da tafi kowace sura girma a cikin Alƙur’ani, sai ya ce; “Ita ce Alhamdu lillahhi rabbil alamin; Ita ce (Mai ayoyin) bakwai da maimaitawa kuma ita ce Alƙur’ani, mai girma da aka ba ni” (Bukahri: 4202).
Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Suratul Baƙara danna nan.
Domin karanta cikakken bayani akan Falalar Ziyarar Mara Lafiya danna nan.
Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.