Ƙara Yawaita Ibadu Da Alhairi A Goman Ƙarshe Na Ramadan

0
815

An karɓo daga A’isha (Radiyallahu anha) ta ce: Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam) ya kansance yana ƙoƙari a goman ƙarshe, fiye da yadda yake yi a sauran lokutan “Muslim 1175).

An karɓo daga gare ta A’isha (Radiyallahu anha) ta ce: Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam) Ya kasance idan goman ƙarshe ta kama, yana raya dare yana tashin iyalansa, yana zage damtse yana ƙaurace musu”. (Bukhari 2024, Muslim 1174).

Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar I’itikafi danna nan.

Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi domin karanta cikakken littafin danna nan.

labarin da ya wuceFalalar I’itikafi
Labarin na GabaFalalar Yin Umara A Watan Ramadan