Yadda Falalar Suratul Falaƙi Da Nasi Take

0
136

An karɓo daga Uƙubatu ɗan Amir (Radiyallahu Anhu) yace; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) yace; “Ba ka ga waɗansu ayoyin da aka saukar da su jiya da daddare ba, ba a taɓa ganin irinsu ba”. Su ne ƙul’a’ uzu bi rabbi falaƙi” da ƙul’a’uzu birabbinnasi” (Muslim 814).

Faɗakarwa

Ina nasiha da ba da shawara ga ‘yan uwa musulmi da mu kula sosai da Alƙur’ani ta wajen haddace shi; da yawan karanta shi, da koƙarin fahimtar ma’anonisa da kuma yin aiki da shi; domin samun tsira da arziki da wadata a duniya da lahira.

Allah ka sa mu dace, Allah ka sanya mu zama ahalinka a halin Alƙur’ani. Amin.

Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Zikiri Ya Ke danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Zikiri danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

labarin da ya wuceZikiri Yayin Shiga Gida
Labarin na GabaTarihin Kafuwar Ƙasar Saudi Arabia