Yabo Daga Waƙar Aminu Alan Waƙa

0
389

Aminuddeen Ladan Abubakar (Alan Waƙa) ya yi wa Farfesa Gusau waƙoƙin yabo da dama; amma a wannan takarda an ɗauki waƙa ɗaya mai taken “Ga ka Farfesa” ; wadda a cikinta aka zaƙulo yabon da ya yi masa. 

Ga wasu ɗiya da Alan waƙa ya yi yabo a cikin su:

G/Waƙa: Ga ka Farfesa,
Ga ka Farfesa ga ka katibi kan adabi,
Sannu Farfesa Sa’idu ɗan Muhammadu na Gusau.
Jagora: Yau akala na karkata na tunkari Gusau,
Zan yabon masani mutafannunin nan na Gusau,
Wanda yai harsasai kala-kala yam maye sau,
A fagen ilmi yau da gobe ya zamma da sau.
Jagora: Adabin Hausa na yabon ka Farfesa Gusau,
Manazarta ma ka yi tubali sun ɗara sau,
Littafan tarke da dabarbarun Hausa ka sau,
Har da talifin tarke na siya da dama a Gusau.
Jagora: Alan waƙa ke yabon ka don ka ɗara sau.

Sanannen makaɗi ne a ƙasar Hausa wanda ya yi waƙoƙi da dama a ɓangarori da dama, cikin su har da waƙoƙin yabon Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau.

An haifi Aminu Ala a ranar 11 ga watan Fabrairu, 1973 a unguwar Yakasai ta Kano. Ya yi haddar Alqur’ani da karatun littattafai; sannan ya yi karatun boko inda ya kai matsayin Difloma. Yanzu haka yana zaune a Birnin Kano, yana tare da iyalansa, sannan yana da muƙaman sarautu a wasu ƙasashen Hausa kamar: Ƙaraye, Bichi, Dutse da Gobir. (Gusau, 2016:229 – 234).

Taƙaitaccen Tarihin Aminuddeen Ladan Abubakar (Alan Waƙa)

Wannan suna an samar da shi ne ta hanyar haɗa farkon sunayensa, wato Aminuddeen Ladan Abubakar, sai aka sanya masa mahaɗin ‘n’, sannan aka yi ƙari da kalmar ‘Waƙa’ a gaba.

Ya yi wannan waƙa rerawa ta farko a yammacin ranar Laraba 10 ga Maris, 2021, wadda ta dace da ranar bikin auren Hindatu Sa’idu Muhammad Gusau.

A fagen waƙa kai rubutuka sun fice sau,
Haka labaran ƙage kai nazar sun fice sau,
Binciken Ala da yawan su taskarka Gusau.

Idan aka lura da waɗannan baituka da suka gabata, za a ga tsantsar yabo ta fuska guda; amma sai aka rarraba shi zuwa wasu rassa amma duk a ɓangaren ilmi.

Makaɗin, ya yi ƙoƙarin yabon Farfesa ta fuskar yalwatar iliminsa, inda ya zamana ilimin ba a ɓangare guda ba, wato fanni ne da dama. A kalmar ‘Mutafannun’ wadda ya yi amfani da ita wajen nuna Farfesa Gusau yana da ilimi a vangarori biyu ko uku, wato Hausa da Turanci da kuma Larabci. Har wa yau, a wajen yin yabo ga yalwar ilmin nasa, sai ya yabi yadda ya kasance ya yi tarke a ayyukan marubuta littattafan Hausa na ƙagaggun labarai, haka zalika a fagen waƙa ma ya yi irin wannan tarke da rubuce-rubuce da dama.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Yabo Gonar Makaɗi: Nazarin Yabon Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau A Cikin Wasu Waƙoƙin Baka Na Situdiyo wanda Ibrahin Baba (Nayaya) ya wallafa shi.

Domin karanta cikakken bayani a kan Yabo Daga Waƙar Maryam Fantimoti danna nan

Domin karanta cikakken bayani a kan Muhallan Da Ake Waƙoƙin Fiyano Na Hausa danna nan

labarin da ya wuceMa’anar Yabo
Labarin na GabaWaƙa A Matsayin Sana’a