Yabo Daga Waƙar Maryam Fantimoti

0
347

Kamar Aminuddeen Ladan Abubakar (Alan Waƙa); Zabiya Maryam Sale Fantimoti ita ma ba a bar ta a baya ba, ta yi waƙoƙin yabo da dama ga mutane mabambanta; cikinsu kuwa har da Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau.

A wannan ɓangare, an ɗauko ɗaya daga cikin waƙoƙin da Maryam Fantimoti ta yi masa, inda aka zaƙulo muhallan da ta yi wannan yabo domin fito da su fili.

G/Waƙa: Furofesa Sa’idu Muhammad na Gusau,
A gaida Babban Malami a harshen Hausa
Ɗan ƙwarai.

Jagora: Akwai adabi gare shi sashi-sashi,
A fannin Hausa sai na ce ga shi,
Idan ya tsaya yana bayani ma’ishi,
Sai in ce

ɗalibai maqoshi.
Sa’idu Muhammad Gusau ɗan gayya ɗan ƙwarai.

Jagora: Nauyin ba ya sa ka ka makara,
Domin ɗalibanka kar sai ta jira,
Ga ka da alƙawar kamar tattabara,
Idan ka faɗa za ka yi shi ka tara,
Za ya zuba ya ba wa kowa ya sha ɗan ƙwarai.

Jagora: Ga ka da halinka mazaje na jiya,
Idan an gano ka za a tuna jiya,
Sannan laffazin da duka za aka biya.

Taƙaitaccen Tarihin Zabiya Maryam Sale Fantimoti

An haife ta a shekarar 1977 a unguwar Gyaɗi-gyaɗi ta Kanon Dabo, sannan ta yi karatu tun daga Islamiyya har zuwa Sakandare.

Game da waƙa kuwa, ta fara tun tana ƙarama, kawo yanzu ta yi waƙoƙi da dama, wanda har ta kai ga duniyar Adabi ta san ta, kuma har ta kai ga zama Sarauniyar Waƙa ta Sarkin Kano (Gusau, 2016:244-245).

Fantimoti shi ne sunan da ake yi mata alkunya da shi.

Jagora: Duk wani ɗalibi ya zauna ya iya,
Du’a’i ne muke wa Baba na Baba ɗan ƙwarai.

Jagora: Ka zama dattijo mai haɗa kowa,
Lallashi gare ka mai tausawa,
Koyarwarka Baba ta isa a yi wa,
Duk wani ɗalibi mu je zakka zuwa,
Hallata zamaninka Ubanmu ɗan ƙwarai.

Yabon Da Zabiya Maryam Fantimoti Ta Yi Wa Farfesa

Zabiya Maryam Fantimoti ta yi yabo ga Farfesa ta hanyar ambatar bayyana faɗin ilminsa, inda ta nuna shi a matsayin ‘masanin sassan adabi’. Shi kuwa adabi, daman ya kasu zuwa gida biyu a jimlace, wato adabin baka da adabin zamani , amma kowane ɓangare yana da nasa rassan.

To a nan, sai Zabiya Fantimoti ta yabe shi ta hanyar nuna cewa yana da ido a kowane ɓangare na adabin. Sannan sai ta ɗora ga cewa, duk yayin da ya tsaya yana bayani kan adabi ga ɗalibai, to fa za su kwankwaɗa daga kogin ilminsa har su ƙoshi.

Sannan a baiti na gaba, sai ta bayyana yabon ta fuskar ƙwazonsa wajen rashin nawa ko kasala, ta yadda a duk lokacin da yake da darasi ga ɗalibai, to fa babu wani abu da zai sanya ya ƙi zuwa, zai bar duk wani uzirinsa ya je ya yi wa ɗalibai darasin. Saboda ƙoƙarin yabonsa ta fuskar cika alƙawari, sai Zabiya ta ambace shi da tattabara.

Domin yabon gaskiyarsa kuwa, Zabiya Fantimoti ta bayyana shi da ‘mazan jiya’. Mazan jiya su ne mutanen da ake bayyana su da cikakkiyar kamala, gaskiya, ƙwazo, himma, riƙon amana, juriya da kuma magana ɗaya, ma’ana idan sun tsaya a kan magana, ba sa sauyawa saboda son zuciya ko wata buƙatarsu ta daban. 

To siffanta mutum da wannan suna na mazan jiya, kai mutum ne maƙurar yabo ga kyawawan siffofi. Sannan sai ta jingina masa kalmar ‘dattijo’ wadda ita ma siffa ce da ake yabo da ita ga nagartaccen mutum mai magana ɗaya, kuma wanda ba ya saɓa alƙawari ko cin amana.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Yabo Gonar Makaɗi; Nazarin Yabon Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau A Cikin Wasu Waƙoƙin Baka Na Situdiyo wanda Ibrahin Baba (Nayaya) wallafa shi.

Domin karanta bayani a kan Yadda Ma’anar Roƙo Take danna nan

labarin da ya wuceYadda Ma’anar Roƙo Take
Labarin na GabaTaƙaitaccen Tarihin Farfesa Sa’idu Muhammad Gusau