Malam Sani Hafizi Katsina
An haifi Malam Sani a shekara ta 1916. Ya fara karatun Alƙur’ani tun yana yaro ƙarami. An kai shi gabas (Maiduguri) don ya sami ƙwaƙƙwarar tilawa. Ya zauna a Nguru a inda ya haddace Alƙur’ani sannan ya tafi katagum yankin Guddiri daga bisani kuma ya isa Maiduguri. Ya zauna wurin Malam Ɗan kutama a Bazamfareri a inda ya Gyara tilawarsa.
Malam Sani ya koma Katsina a shekarar 1994, wato shekarar guda Bayan rasuwar sarkin Katsina Muhammad Dikko. Malam Hafizu ya kafa tsangayarsa kusa da babban Masallacin juma’a da ke Katsina.
Malam Salisu Gidan Liman Kurfi
Malam Salisu ya shaharar da karatun Alƙur’ani a garin kurfi. Makarantarsa na karɓar baƙuncin ɗaruruwan almajirai a inda suke hadda ce Alƙr’ani. Mafi shahara daga ɗalibanta su ne Liman Ɗayyabu da Malam Daudu.
Domin karanta cikakken bayani a kan Wasu Daga Fitattun Malaman Alƙur’ani A kurfi danna nan.
Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Buɗe Karatun Alƙur’ani Da Bismillah A Cikin Sallah danna nan.
Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.
Edita@rumasau-kallamu