Waiwaye A Kan Al’adun Gargajiya

0
84

Masana irin su Ibrahim (1982) da Bunza (2006) sun gabatar da bayanai dangane da asali da ma’anar kalmar al’ada. Don haka a taƙaice kalmar al’ada tana nufin dukkanin rayuwar ɗan Adam tun daga haihuwarsa har zuwa kabarinsa.

Dangane da wannan fasali da ake magana a kai, al’adun gargajiya na nufin tsarin rayuwar Hausawa wadda ta shafi abinci da sutura da muhalli da zamantakewa da shugabanci da bukukuwa da wasanni da makamantansu.

Ma’anar Wasa

Sa’id, B. (2006) sun bayyana ma’anar wasa da cewa, “abu ne da akan yi don raha ko nishaɗi, ko motsa jiki.” A wata ma’anar kuwa Ɗangambo (2008) ya bayyana kalmar wasa da cewa, “shi ne motsa jiki don samun walwala.” Duba ga waɗannan bayanai da ma’anoni da suka gabata, za a iya cewa wasa shi ne sanya walwala da nishaɗi tare da nuna farin ciki, wanda a wasu lokutan har da motsa jiki.

Wasannin Gargajiya A Ƙasar Gaya

Al’umma kan tafiyar da rayuwarsu, da al’adunsu cikin gwagwarmaya don cimma wasu buƙatu na rayuwa. Wannan yakan jawo wa al’ummar ingantaccen tarihi mai cikakken asali da abubuwan alfahari. Haka kuma al’adun kan samar da annashuwa ba ya ga ilimantarwa.

A ƙasar Gaya akwai wasannin gargajiya waɗanda al’ummar suke gudanar da su, wasu daga cikin wasannin sun haɗa da: wasan Mage da wasan Ƙunshi da wasan Jemau da wasan Taushen fage da wasan Dagajirau (saran-kai) da sauran wasanni waɗanda sun sha bamban da al’ummar ƙasar Hausa.

Wanann bayanin an ciro shi ne daga maƙala mai taken Nazarin Wasan Ƙunshi Jiya Da Yau A Ƙasar Gaya wadda Magaji Ahmad Gaya Ph.D Sashen koyar da Hausa Jami’ar Northwest, Kano ya wallafa.

Emai: magaya@nwu.edu.ng

08066009039

Danna nan don karanta Nason Al’adun Baƙi Maƙwabta Na Kusa A Wanzancin Hausawa

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceYadda Wasu Kayan Da Hausawa Ke amfani Da Su Ga Doki Suke
Labarin na GabaSamuwar Rubutun Ajami
Dr. Magaji Ahmad Gaya
Dr. Magaji Ahmad Gaya shahararren malami ne a fannin harshen Hausa. Ya yi digiri na uku (PhD) a ɓangaren nazarin al’adu a jami’ar Umaru Musa “Yar Adua da ke Katsina. Haka kuma ya yi aikin koyarwa a wasu makarantun firamare da sakandare da kuma Kwalejin Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kumbotso. A halin yanzu yana koyarwa a Jami’ar Northwest, Kano Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya.