Waƙa Ta 2 Ga Farfesa Mu’azu Sa’adu Muhammad Kudan

0
12

Daga Salmanu Faris Kudan, Shugaban Ƙungiyar Marubutan Arewa ta Ƙasa Nijeriya

1.

A yau mun taru cikin alkunya,

Domin girmama gwarzonmu mai dubayya,

Haske ya sake yalwata cikin Hausaniya,

Da samun Farfesa Mu’azu a mai kyan halayya.

2.

Ka jima kana hura wutar hikima,

Kana tsarkake harshenmu ba taƙama,

A makarantu sun ɗauki darusa ba gardama,

Sun zame wa ɗalibai hasken tafarki mai tsunduma.

3.

Mu’azu Sa’adu, ginshiƙin Hausar mu ta dauri,

Ka ɗaukaka harshen da kakanni suka bari.

A yau an saka maka rawanin girma tuturi,

Ka zama damina mai sanyaya shuka ba fari.

4.

Salmanu Faris Kudan na taya ka murna,

Da wannan matsayi mai jan hankalina,

A madadin marubutan Arewan zaurena,

Muna yi maka fatan ƙarin nasarori da zayyana.

5.

Girmanka ya zama abin jingina ba wariya,

Ƙwararrun marubuta suna sanya ka a zuciya.

Ka zama tubalin da ya ƙara ɗaure ginin Hausaniya,

Harshen da ke ɗaukaka Arewa da Nijeriya.

6.

Muna yi maka addu’ar fatan alheri,

Rayuwa mai cike da ƙarin annuri.

Allah Ya saka maka cikin mafi alheri,

Ya ƙara nisan kwana bisa tsari.

Karanta Waƙar Murnar Zama Farfesa Ga Mu’azu Sa’adu Muhammad

Edita@rumasau-kallamu

labarin da ya wuceWaƙar Murnar Zama Farfesa Ga Mu’azu Sa’adu Muhammad
Labarin na GabaWaƙa Mai Taken Jakadan Allah