Tarihin Shehun Malami Muhammad Rabi’u Ɗan Tinki (1897-1959)

0
30

Malam Rabi’u ɗan Yunusa ɗan Alhasan ɗan Baru. An haife shi a garin Tinki a cikin ƙaramar hukumar Bici da ke Jihar Kano cikin shekarar 1897.

Malam Rabi’u ya taso ciki ƙuruciya manisanciyar wargi da wasanni irin na matasa. Ya yi karatu a gaban mahaifinsa. Muhammad Rabi’u Ɗan Tinki ya kasance mutum ne mai yawan haƙuri da kawaici da yawan sabo da jama’a. Ya haddace Alkur’ani tun yana ɗan shekara goma sha huɗu. Sannan ya fara karatun littatafai irin su Ahalari da lziyya.

Daga nan ya nemi izinin muhaifinsa ya bi wani baƙon mashahurin malami da ake kira Malam Kunta. Bayan ya zauna tsawon lokaci a wurinsa, sai ya nemi izini zuwa wajen Mahiru Kalla mutumin Damagaram cikin Jamhuriyar Nijar.

Ya zauna a wajensa tsahon lokaci har ya sauke litlatafai da yawa a fannin ilimin ƙira’a da Tawhid da litlafai irinsu Nuniyar Sakawiy da Hidayatussibiyan da Tuhfatul adfal da Mukaddimat Jazary, da Shadibiyya da Lamiyyatul Kira ‘at.

Shaihun malamin bai gushe ba yana kutsawa cikin fagagen ilmai da gogayya da malamai har sai da ya dangana da garin Maiduguri ya yi karatu a wurin Mahiru Ahmad. Daga nan ya dawo Kano ya sauka Haɗejiya ya kara dukuta a gaban Malam Is’hak daga bisani ya dawo Kano ya cigaba da koyarwa.

A lokacin da Malam Ɗantinki ya samu labarin Mahiru Hamid, sai ya nemi izinin ya zama almajirinsa. A nan ma ya karanta littafai da dama musamman fannin dabti wanda shi ma ɓangare ne na ilimin Rasmu da ilimin wasullan Alkur’ani.

Abokan karatun Shehi Rabi’u wurin Gwani Hamid sun haɗa da Malam Ɗan Gunduwawa da Malam Aliyu Mai Kwaro da Malam Ɗan Karofin Yashi da Malam Yunus Ɗan Gumel da Malam Ɗan Kanuri da Malam Isah Ɗan Kwandarai da Malam Sabo Ƙofar Wambai da Malam Umar Ɗan Mai-Rigar-Fatu.

A halin yanzu tsangayarsa ta cigaba da bunƙasa kuma ta yi rassa a hannun ɗan sa Halifa Sheikh Is’haka Rabi’u.

Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Gwani Saleh Danzargu danna nan.

Domin karanta cikakken bayani a kan Taƙaitaccen Tarihin Samuwar Waƙoƙin Baka a Ƙasar Hausa danna nan.

Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

labarin da ya wuceYadda Falalar Karatun Al-Ƙur’ani Ya Ke
Labarin na GabaTattali da Kulawar Ɗanƙwairo da Majiɓintansa