An haifi Alaramma Malam Abubakar Yunusa a shekarar 1920 a garin Tsakuwawa a ƙaramar Hukumar Miga da ke cikin Jihar Jigawa. Ana yi masa laƙabi da Gwani Daudu saboda sarautar kakanninsa ta Galadiman garinsu.
Alaramma Malam Abubakar ya shahara da baiwar karatu na yankan shakku. Saboda irin kaifin ƙwaƙwalwar da Ubangiji Maɗaukaki Ya ba shi, an ce Gwani Daudu ba ya manta duk abin da ya yi ido biyu da shi tun daga ƙuruciyarsa. Zarton malami, ma’abocin karamci da son almajirai. Gwani Daudu ya yi fice cikin dattijawan alarammomi da wayewa a zamanance da kuma kutsuwa fannonin ilmi Fiƙhu da Tafsir da Lugga da Nahwu.
Gwani ya fita neman karatu bayan ya zama matashi mai kimanin shekaru goma sha biyar kuma bai koma gida ba sai da ya samu Alƙur’ani kuma ya rubuta shi. Ya yi tafiye-tafiyen neman karatu cikin Birniwa da Kirikasamma da Gayan. Gwani Daudu ya kafa tsangayun AIƙur’ani a birane daban-daban kamar garuruwan Mai Tafari da Kirikasamma da Kuka Uku.
Don haka ne ma a halin yanzu ake kiran wata kasaitacciyar makaranta a garin Damaturu da tsangayar Gwani Daudu.
Bayan Gwani Daudu ya dawo birnin Kano kuwa ya zauna a wurare daban-daban da suka haɗa da Durumin Zungura da Kankarofi cikin ƙaramar Hukumar Birni. Daga bisani kuma ya koma Unguwar Gwale.
Gwani Daudu ya shahara da kyakkyawar maƙwabtaka da saraki da sauran al’umma. Saboda haka ne ma Sarkin Kano Ado Bayero ya ba shi filin da ya faɗaɗa tsangayarsa da ke Unguwar Gwale.
Malaman Gwani Daudu sun haɗa da:-
- Malam Mai Ɗanbahar Mai Tafari
- Malam Iliya Gayan
- Gwani Ɗankwandarai
Gwani Daudu ya rasu a ranar 22 Sha’aban 1421, dai-dai da 17 ga Nuwambu 2000. Ya rasu ya bar ‘ya’ya da almajirai masu yawa:-
‘Ya’ya:
- Malam Muhammad Abubakar
- Malam Ahmad Abubakar
- Malam Susi Abubakar
- Malam Tamimuddari
- Malam Adisaru
- Malam Arisu
Manyan Almajiransa sun haɗa da:-
- Malam Ali Basukkwace
- Malam Umar Panshekara
- Malam Ahmad Ɗantsadawa
- Alh. Hamza Yusuf
- Malam Garba Na’ibi
- Malam Muhammad Ɗan Meram
Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Alaramma Malam Isa ƊanƘauranmata Bin Umar danna nan.
Domin karanta cikakken bayani a kan Misalan Waƙafi Ababen Koyi A Tarihin Musulunci danna nan.
Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.