Tag: yadda ake

  • Tarihin Malam Attahiru Shehu Na Liman (Limamin Masallacin Shehu)

    Tarihin Malam Attahiru Shehu Na Liman (Limamin Masallacin Shehu)

    An haifi Malam Attahiru a farko-farkon sarautar sarkin musulmi Abubakar na uku. Malam Attahiru ya taso cikin tarbiyyar addini wurin mahaifinsa.

    Kasancewar gidansu gida ne na ilmi da yaɗa shi, ya sa shi gadar wannnan sana’a ta koyar da Alƙur’ani da ilmi. Duk da cewa a halin yanzu Malam Attahiru shi ne Limamin Masallacin Shehu da ke Sakkwato, duk da haka makarantarsa ba ta gushe ba ta na yaɗa addini a cikin garin Sakkwato tare da taimakon ‘yan uwansa musamman ma Malam Abubukar da Malam Ibrahim da Malam AbdurRahman da Malam Ahmad Zaruƙu.

    Malam Attahiru Na Liman tsatson Alƙali Abubakar Ladan Rame ne, wanda ɗan Gwaggon Shehu Usmanu Ɗan Fodiyo ne. Wannan zuriya mai albarka ta cigaba da jiɓintar koyar da addini da alƙalanci har zuwa kan Malam Attahiru Shehu Na Liman (Limamin Masallacin Shehu da ke Sakkwato na yanzu).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Malam Buhari Siriddawa (Sarkin Malaman Sakkwato) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Adalci, Tausayawa Mabiya Da Illolin Gallaza Musu danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙur’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Nason Al’adun Yarabawa A Kan Wanzancin Hausawa

    Nason Al’adun Yarabawa A Kan Wanzancin Hausawa

    A wurin Yarabawa ayyuka makamantan na wanzanci Hausawa akwai mutane daban-daban waɗanda suke aiwatar da su a tsakanin mutanen wannan al’umma. Misali ‘bonjamo ko oloola’, suna ne wanda suke kiran dukkan mutumin da yake yin wasu ayyuka irin su tsagar gado da yin kaciya da makamantansu.

    Haka kuma suna kiran wanda yake yin aski kawai da sunan ‘fari – fari’ ko ‘akola’. A saboda haka akwai wasu al’adun Yarabawa waɗanda suka yi naso cikin al’adun wanzanci na Hausawa.

    Cire Belun-wuya

    A al’adar Yarabawa ba su damu da cire wa jariran da aka haifa masu belun-wuya ba, don irin wannan aiki ba ya cikin al’adunsu. Har ma idan an sami wata matsala makamanciyar wannan, sai su ba wanda yake fuskantar matsalar maganin gargajiya ya sha ko ya shafa a wurin da lalurin yake (YASASHL, 6/2/2006).

    Irin wannan al’amari ya yi tasiri sosai a wurin wasu Hausawa waɗanda suka daɗe a ƙasashen Yarabawa, domin kuwa akwai waɗanda ba a cire wa jariran da aka haifa masu belun-wuya da belun-mata musamman a wannan zamani.

    Wannan tasiri ya biyo wasu Hausawa waɗanda suka baro ƙasar Yarabawa suka koma garuruwansu na asali a ƙasar Hausa, don kuwa a nan ma ko da an yi masu haihuwa ba sa kiran wanzami domin ya cire wa jariransu belun-wuya ko belun-mata (UƊ da MBT da MAHD da MAA da MAMI da HZO da MASO da MAIA da HR, 7 da 8 da 9 da 10/2/2006).

    Wannan al’ada ta Yarabawa ta yi naso a kan wanzanci ne saboda ire-iren waɗanda suka yi koyi da ita ba sa bari wanzamai su je gidajensu don yin ayyukan wanzanci. Wannan al’amari ya shafi yadda ake gudanar da wannan sana’a yadda wasu wanzamai suke rasa ayyukan yi.

    Nason Al’adun Yarabawa Kan Askin Jarirai na Suna

    A al’adar Yarabawa ba dole ne a yi wa jaririn da aka haifa aski ba, idan ma ta kama a yi, ba dole ne a yi shi a lokacin da aka haifi jaririn ba. A wurinsu ana yin aski ne a lokacin da ake da sha’awar yin sa ko kuwa a lokacin da suma ta yi yawa, kuma ba dole ne a yi askin ƙwaryar molo ba kamar yadda al’ummar Hausawa suke yi (MGAA, 30/9/2004).

    Irin wannan al’ada ta Yarabawa ta yi naso a kan wasu Hausawa waɗanda suke zaune a ƙasashen Yarabawa, don kuwa a wannan zamani akwai wasu Hausawa waɗanda suke zaune a jihohin Lagos da Oyo da Ondo da Ekiti da Oshun da Ogun waɗanda ba sa yi wa jariran da aka haifa masu askin suna.

    A maimakon haka, sai dai su sanya almakashi su daddatse sumar a lokacin da ta yi tsawo (YASASHL, 6/2//2006 da UƊSA da MBT da MAHD da MAA da MAMI da HZHO da MAS da MAIA da HR, 7 da 8 da 9 /10/2006) .

    Magungunan da Wanzamai Suka Samu Daga Yarabawa

    Wanzamai sun sami magunguna wurin Yarabawa. Daga cikinsu akwai na maganin ciwon ela. Ciwon ela yana kama yara ƙanana ne da jarirai waɗanda ba a yaye ba. Yanayin wannan ciwon shi ne, za a ga tsakanin cinyoyin yara sun sale sun yi jawur.

    Idan kuma mace ce har cikin farjinta da gefensa duk sai ya sale ya yi jawur. Wurin da ciwon yake zai ta yi wa yaran ciwo da ƙaiƙayi wanda yake tilastawa yaran su soshe wurin, a wasu lokuta a lokacin da yaran suke susar wurin sai ya riƙa fitar da jini.

    Maganin ela wanda Hausawa suka samu daga wurin Yarabawa shi ne, sai a sami sabulun salo a riƙa wanke wurin da ciwon yake, daga nan sai a sami attarugu ƙwaya ɗaya a wanke bakin yaron da yake da matsalar. Bayan nan kuma sai a sami sauyoyin bini-da-zugu da ganyensa a dafa su da ruwa, idan ya huce sai a sanya yaron a cikin ruwan ya ɗauki wani lokaci a ciki.

    A lokacin da aka fito da yaron daga cikin ruwan, sai a sami ƙyalle mai kyau a shafe ruwan da yake wurin ciwon, daga nan sai a sami man ja a riƙa shafawa a wurin. Za a yi ta yin haka kullum har lokacin da yaron ya warke (YASASHL, 6/2/2006).

    Karanta Shigowar Yarabawa Ƙasar Hausa

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Addu’ar Wanda Ya Ji Wani Ciwo A Jikinsa

    Addu’ar Wanda Ya Ji Wani Ciwo A Jikinsa

    Annabi, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce: ‘Ka sanya hannunka a wajen da yake maka ciwo a jikinka, ka ce:

    بِسْمِ اللهِ

    ثلاثاً

    Bismillah. Da sunan Allah (nake neman waraka). (sau uku)

    Sannan ka ce:

    أعُوْذُ بِاللهِ وَقُدْرَتِهِ مِنْ شَرِّ مَا أَجِدُ وأَحَاذِر

    (سبع مرات)

    A’uzu billahi wa ƙudratihi min sharri ma ajidu wa uhadir

    Ina neman tsari da Allah da kuma Ikonsa daga sharrin abin da nake ji (na ciwo) kuma nake jin tsoransa (sau bakwai)

    Karanta Addu’ar Tafiya (Wadda Matafiyi Yake Yi)

    Edita@rumasau-kallamu

  • Addu’ar Tafiya (Wadda Matafiyi Yake Yi)

    Addu’ar Tafiya (Wadda Matafiyi Yake Yi)

    الله أكبر، الله أكبر، اللهُ أَكْبَرُ سُبْحَانَ الذي سَحْرَ لَنَا هَذَا وَمَا كُنَّا لَهُ مُقْرِنِينَ وَإِنَّا إِلَى رَبَّنَا لَمُنْقَلِبُونَ ، اللهُمَّ إنا نسألُكَ فِي سَفَرنَا هَذَا الْبِرَّ والتّقْوَى ، وَمِنَ الْعَمَلِ مَا تَرْضَى ، اللهُمَّ هَون عَلَيْنَا سَفَرَنَا هَذَا وَاطوِ عَنَّا بُعْدَهُ ، اللهُمَّ أَنتَ الصَّاحِبُ في السَّفَرِ، وَالْخَلِيفَةُ في الأَهْلِ، اللهُم إِنِّي أَعُوْذُ بِكَ مِنْ وَعْنَاءِ السَّفَرِ ، وَكابَةِ الْمَنْظَرِ وَسُوءِ الْمُنقَلبِ فِي الْمَالِ وَالأَهْلِ.

    Allahu akbar, Allahu akbar, Allahu akbar, subhanallazi sakkara lana haza wama kunna lahu muƙrineen wa ina ila rabbina lamun ƙalibun allahumma ina nas’aluka fi safarina haza al-birra wattaƙwa, wa minal amali ma tarda, Allahuma hauni alaina safarana haza wadwi anna bu’udahu, Allahuma anta sahibu fil safari wal kalifatu fil ahli allahuma inni a’uzubika min wana’i safari wa kabatil wanzari wa su’il mun ƙalibi fil mali wal ahli

    Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma. Tsarki ya tabbata ga (Ubangiji) Wanda ya hore mana wannan (abin hawa); ba mu kasance masu ikon sarrafa shi ba. Haƙiƙa mu masu komawa ne zuwa ga Ubangijinmu. Ya Allah! Muna roƙon Ka nagarta da tsoron Allah a cikin wannan tafiya ta mu, da kuma aiki wanda Kake yarda da shi. Ya Allah! Ka sauƙaƙe mana wannan tafiya ta mu, kuma ka naɗe mana nisanta. Ya Allah! Kai ne Ma’abocinmu a cikin wannan tafiya, kuma Halifanmu a cikin iyalanmu. Ya Allah! Ina neman tsari da Kai daga wahalar tafiya, da abin gani mai sanya ɓacin rai, da kuma komawa mummuna ga iyali da dukiya.

    Domin karanta Yadda Ake Addu’ar Hawa Abin Hawa danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Shigowar Yarabawa Ƙasar Hausa

    Shigowar Yarabawa Ƙasar Hausa

    Yarabawa suna ne wanda Hausawa suke kiran mutanen da suke kudu-maso-yamma da ƙasar Hausa a tsohuwar Daular Oyo da Ijebu Ode da Ogbomosho da Egba da Ekiti da Ibadan da Ilori da sauran wurare da suke kusa da waɗannan ƙasashe.

    A halin yanzu mafi yawa daga cikin al’ummar Yarabawa suna zaune a kudu maso yammacin Nijeriya a jihohin Lagos da Oyo da Oshun da Ondo da Ogun da Ekiti da kuma a kudu maso yammacin jihar Kwara. Ana kuma samun su a ƙasashen Jamhuriyar Benin da Togo da Cote D’iɓoire da Saliyo.

    Akwai daɗaɗɗiyar dangantaka tsakanin Yarabawa da mutanen ƙasar Hausa, wadda tun farko ta kasuwanci ce. An sami bayanan da suka nuna akwai dangantakar kasuwanci a tsakanin Yarabawa da mutanen ƙasar Hausa a cikin ƙarni na goma sha takwas. A wannan lokaci ne wasu ‘yan kasuwa daga Ogbomosho suka shigo Kano kuma suka zauna a cikin birni.

    Wannan dangantaka ta ƙara ƙulluwa ta hanyar kasuwancin da aka riƙa yi a tsakanin mutanen ƙasar Hausa da na ƙasashen kudu waɗanda suke bin hanyar da ta bi Zariya zuwa ƙasar Nufe ta zarce zuwa ƙasashen Yarabawa. An sami ire-iren waɗannan Yarabawa a ƙasar Katsina da Zariya (Adeleye: 1975:592).

    Da yawa daga cikin Yarabawan da suke zaune cikin ƙasar Hausa a yanzu sun shigo ne a cikin ƙarni na ashirin a sakamakon kafuwar mulkin mallaka. A Kano an sami al’ummomin Yarabawa masu yawan gaske waɗanda suka shigo a farkon ƙarni na ashirin, kuma suna daga cikin mutanen farko waɗanda aka kafa unguwar Sabon Garin Kano da su.

    Sun shigo Kano da Zariya don yin aikin ginin hanyar jirgin ƙasa wadda aka kawo Kano, ko kuwa don yin aiki a tashar jirgin ƙasa, ko don yi wa Turawan Mulkin Mallaka aikace – aikace, ko kuwa don yin aiki a kamfanonin da Turawa suka kafa a waɗannan wurare. Wasu Yarabawan kuwa sun shigo ne don yin aikace-aikacen addini na Musulunci ko na Kirista.

    A sakamakon jin daɗin zama da suka yi a wasu garuruwan ƙasar Hausa musamman a Kano da Zariya da Katsina da Gusau da Sakkwato, sai wasu Yarabawan da suka shigo a matsayin ma’aikata bayan sun ajiye aiki suka yanke shawarar ci gaba da zama a waɗannan garuruwa. Wannan kuwa ya faru ne sakamakon jin daɗin zama da al’ummomin waɗannan wurare da suke zaune da kuma samun damar yin kasuwanci ba tare da fuskantar wata matsala ba.

    Misali, Alhaji Abdul’aziz Kehinde wanda yana ɗaya daga cikin al’ummar Yarabawa da suka fara shigowa Kano a cikin shekarar 1911, ya zo a matsayin ma’aikaci a tashar jirgin ƙasa. A shekarar 1925, sai ya ajiye aiki ya shiga harkar kasuwanci a nan Kano. Akwai ire-irensa masu yawa cikin garuruwa da ƙauyukan ƙasar Hausa, waɗanda bayan sun ajiye aiki, sai suka ci gaba da zama a wuraren da suke cikin ƙasar Hausa (Baƙo: 1990:104).

    Bunƙasar kasuwancin gyaɗa a cikin shekarar 1920 ya ƙara taimakawa wajen shigowar Yarabawa cikin ƙasar Hausa musamman a ƙasar Kano. Mafi yawanci daga cikin waɗannan Yarabawa suna yin kasuwancin gyaɗa ko tuƙa matocin da ake ɗauko gyaɗa daga ƙauyuka zuwa Kano. Haka kuma kafa kasuwar Sabon Gari a Kano cikin shekarar 1918 ya ƙara taimakawa wajen shigowar Yarabawa a garin Kano.

    Fitattu daga cikin Yarabawa ‘yan kasuwa waɗanda suka shigo Kano a farkon ƙarni na ashirin sun haɗa da Alhaji Muhammadu Salihu Olowo wanda ya zo daga Ilesha a cikin shekarar 1903. Da farko ya fara zama a unguwar Ayagi daga baya sai ya koma Sabon Gari cikin shekarar 1916. Yana daga cikin waɗanda suka taimaka aka gina masallacin Yarabawa na Sanmori – ad – deen a cikin shekarar 1925.

    Akwai kuma Alhaji Sani Giwa wanda ya zo Kano daga Abeokuta a cikin shekarar 1920. A duk faɗin Sabon Gari da kewaye Yarabawa da waɗanda ba Yarabawa ba suna ganin mutuncinsa saboda dattakonsa da karimcinsa da riƙe alƙawarinsa. Wannan ne ya sa shi zama Sarkin Yarabawa na farko a ƙasar Kano.

    Haka kuma akwai Mr.D.O.Sanya Olu wanda shi ma ya shiga Kano ne cikin shekarar 1920, kuma shi ne mutum na farko wanda ya fara kafa Otel a Sabon Garin Kano a shekarar 1939. Da farko sunan Otel ɗin Colonial Hotel, amma da aka sami ‘yancin kai, sai ya canja masa suna zuwa Paradise Hotel (Baƙo, 1990:) Waɗannan misalai ne kawai aka kawo don akwai ire-irensu masu yawa da suke zaune a cikin garin Kano da kewayenta.

    A garin Gusau ma akwai Yarabawa masu yawan gaske waɗanda suka shigo don yin harkar kasuwanci da sauran hulɗoɗi. An bayyana cewa tun kafin ƙarni na goma sha tara akwai Yarabawa waɗanda suke kasuwancin goro a ƙasar Hausa. A cikin ƙarni na ashirin musamman a cikin shekarar 1920 ne ake tsammanin Yarabawa masu yawa sun fara shigowa garin Gusau.

    A lokacin wasu sun shigo domin yin kasuwanci, wasu kuma sun shigo domin yin aikace-aikace a kamfanoni da ma’aikatun da Turawa suka kafa irinsu tashar jirgin ƙasa da dai sauran wurare.Yarabawan da suka shigo garin Gusau suna gudanar da kasuwanci iri daban-daban, misali matansu suna sayar da man ja da sabulun salo da man shafawa irin wanda suke yi, ana kiran sa da suna “Mai Zubi”.

    Su kuma mazan suna sana’o’i irin su gyaran kekuna da ɗinkin keke da ginin bulon siminti da yin aski da dai sauransu. Haka kuma wasun su sai suka shiga harkar sufuri. An bayyana cewa an ƙirƙiro yin hayar mota tasi a garin Gusau cikin shekarar 1969, kuma Yarabawa mazauna garin Gusau ne suka fara yin wannan sana’a. Daga cikin su akwai Alhaji Abdulatif S.Adegoke da Alhaji Afolabi da Mr.Ganiyu Raji (Usman, 2000:205, 206).

    A sakamakon daɗaɗɗar dangantaka tsakanin Yarabawan da suka shigo Gusau da Hausawan Gusau, wasu Yarabawan sun yi auratayya da mutanen da suka tarar wanda yin haka ya haifar da musayar al’adu. A halin yanzu Yarabawan da suke zaune a garin Gusau suna zaune a unguwannin Sabon Garin Gusau da Canteen da Tudun Wada da GRA da Sabon Fegi da Birnin Ruwa da Bakin Kasuwa da sauran wurare a cikin garin Gusau da kewaye (Usman, 2000:205).

    Kamar yadda Yarabawa suka shigo ƙasar Hausa, an sami Hausawa masu yawa waɗanda suka yi ƙaura daga ƙasar Hausa suka shiga ƙasar Yarabawa, kuma sun yi fiye da shekaru ɗari a wannan ƙasa.Ire-iren waɗannan Hausawa suna zaune a unguwannin Alaba da Agege da Obalande da Hausa Line a Lagos da kuma a Sabo Ibadan da Sasa a Ibadan da kuma a Shagamu da Ilori da dai sauran wurare a ƙasar Yarabawa.

    Daga cikin ire-iren waɗannan Hausawa mazauna ƙasar Yarabawa akwai Sarkin Hausawa Dogara wanda ya bayyana min ta hannun Sakatarensa cewa an haife shi a Lagos, mahaifinsa ma a Lagos aka haife shi. A halin yanzu yana daga cikin fitattun mutane masu faɗa-a-ji a jihar Lagos, don kuwa daga cikin matansa akwai wadda ‘ya ce ga Oba na Lagos.

    Bayansa akwai Sarkin Hausawa Alhaji Kabiru Garba wanda tsohon Hafsan Soja ne wanda ya yi ritaya, kuma yana zaune a Arewa House Ebute-Metta Lagos. A Ibadan akwai Sarkin Sasa Alhaji Haruna Mai Yasin wanda shi asalinsa mutumin Zakka ta ƙaramar hukumar Safana a jihar Katsina ne. A yanzu yana ɗaya daga fitattun mutane masu faɗa-a-ji a jihar Oyo.

    Don karanta Shigowar Nufawa Ƙasar Hausa danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Yadda Hukuncin Tusar Gaba Yake A Fiƙihu

    Yadda Hukuncin Tusar Gaba Yake A Fiƙihu

    Tusar gaba (fitar iska daga gaban mace ) a fiƙhu na karya alwala.

    A cikin koyarwar musulunci, Annabi ﷺ ya bayyana cewa abubuwan da ke karya alwala sun haɗa da fitar da iska daga baya ko daga gaba, ko da kuwa iska ce kawai ba tare da najasa ta fita ba. Wannan ya shafi maza da mata.
    Dalili:
    • Hadisin Annabi ﷺ da ke cewa: “Allah ba ya karɓar salla ba tare da tsarki ba, kuma ba ya karɓar sadaƙa daga satar abu” (Muslim ne ya ruwaito).
    • Ulama sun bayyana cewa “tsarki” a nan yana nufin alwala, kuma duk abin da ya fito daga gaba ko baya yana karya ta.

    Saboda haka:

    Idan aka fitar iska daga gaba, dole a sake alwala kafin yin salla ko wata ibada da ke buƙatar alwala.
    To, ga cikakken bayani a kan abubuwan da ke karya alwala da kuma waɗanda malamai suka yi rikici a kansu, bisa ga mazhabobi.

    Abubuwan da malamai suka yi ittifaki suna karya alwala

    Waɗannan dukkanin malamai huɗu (Hanafi, Maliki, Shafi’i, Hanbali) sun yarda suna karya alwala:
    1.Fitar da kowane irin abu daga al’aura (gaba ko baya)
    •Fitsari
    •Bahaya
    •Fitar maniyyi, maziyyi, wadiyyi
    •Iska daga baya ko gaba (tusar baya ko tusar gaba).
    2.Fitar da jini mai yawa daga al’aura
    3.Suma ko shiɗewa gaba ɗaya
    •Idan mutum ya rasa hankalinsa saboda bacci mai nauyi, maye, magani, ko ciwo.
    4.Shafar al’aura da hannu kai tsaye (a mazhabar Shafi’i da Hanbali)
    •Amma Hannafi da Maliki suna da wasu sharuɗa kafin ya karya alwala.
    Edita@rumasau-kallamu
  • Yadda Ake Addu’ar Hawa Abin Hawa

    Yadda Ake Addu’ar Hawa Abin Hawa

    بِسْمِ اللهِ وَالْحَمْدُ لِلَّهِ سُبْحَانَ الَّذِي سَحْرَ لَنَا هَذَا وَمَا كُنَّا لَهُ مُقْرِنِينَ وَإِنَّا إِلَى رَبِّنَا لَمُنْقَلِبُونَ، الْحَمْدُ لِلّهِ، الْحَمْدُ لِلَّهِ، الْحَمْدُ لِلّهِ، اللهُ أَكْبَرُ، اللهُ أَكْبَرُ، اللهُ أَكْبَرُ سُبْحَانَكَ اللَّهُمَّ إِنِّي ظَلَمْتُ نَفْسِي فَاغْفِرْ لِي فَإِنَّهُ لاَ يَغْفِرُ الذُّنُوبَ إِلا أَنتَ.

    Bismillahi wal hamdulillahi subhanallazi sakkara lana haza wa ma kunna lahu muƙrineen wa inna ila rabbina lamunƙalibuun ,alhamdulillah alhamdulillah alhamdulillah Allahu akbar Allahu akbar Allahu akbar subhanakalla-humma inni zalamtu nafsi fagfirli fa innahu la yagfiruz-zunuba illa anta.

    Da Sunan Allah. Dukkan yabo ya tabbata ga Allah. Tsarki ya tabbata ga (Ubangiji) Wanda ya hore mana wannan (abin hawa); ba mu kasance masu ikon sarrafa shi ba. Hakika mu masu komawa ne zuwa ga Ubangijinmu. Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, dukkan yabo ya tabbata ga Allah, dukkan yabo ya tabbata ga Allah. Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma, Allah ne Mafi girma. Tsarki ya tabbata gare Ka, ya Allah! Haƙiƙa ni na zalunci kaina, Ka gafarta mini, domin babu wanda yake gafarta zunubai sai Kai.

    Karanta Addu’ar Da Ake Yi Idan Za a Yanka Dabba Ko Soke Ta

    Edita@rumasau-kallamu

  • Bet9ja Cacar Zamani

    Bet9ja Cacar Zamani

    Wata nau’i ce ta caca da ake yin ta ta yanar gizo, mutum za ya yi rijista da bet9ja, ya buɗe account, ya sa kuɗi gwargwadon yadda zai shiga, sa’annan sai ya canka tsakanin ‘yan wasa da za su buga ƙwallo, ya ayyana cewa wane cikin minti kaza misali za ya sa ƙwallo kaza a raga, ko kuma wane zai jefa ƙwallo kaza, ko club kaza shi ke da galaba ko nasara.

    Idan zaɓinsa ya tabbata zai iya cin dubu 100 a Naira 200 da ya shiga, wannan kuwa ita ce haƙiƙanin caca da Allah (SWT) ya haramta, wadda ta ƙunshi abubuwa kamar haka:

    1- Garari, rashin tabbas, ko ya ya ƙanƙantar kuɗin da za a ka sa.
    2- Cin dukiyar mutane ba tare da wata wahala, ka sa 200 ka kwashe dubu 100, a banza.
    3- Haifar da gaba da ƙiyayya da hana salla da ambaton Allah (SWT), kamar yadda Allah (SWT) ya bayyana.

    A yau matasa ganin wannan banzar ta sa suka yawaita cikinta, tunaninsu ya kau daga hanin Allah (SWT) ga caca, a halin shiga cikinta zai janyo wa ma’abocinta matsaloli da dama kamar:

    1- Saɓa wa hani na Allah (SWT), domin Allah ya yi umarni da a nesanci caca.
    2- Birgima da cuɗanya cikin datti da ƙazanta ta Shaiɗan, bal Allah (SWT) ya ce: “Datti ne daga aikin Shaiɗan”.
    3- Rashin rabautuwa duniya da lahira, domin Allah (SWT) ya ce: “Ku nesance su domin ku samu rabauta”.
    4- Za ya samu matsala ta adawa da ƙiyayya da yan’uwansa.
    5- Za ya samu matsala ta ƙaranta yin salla da zikiri ko ma ya daina
    6- Kamar yadda ma’abocin sa zai:
    a- Sangarce a harkar neman halaliya da lalaci saboda ya ga banza.
    b- Zai haifar masa da damuwa da jinyar gangar jiki dss.

    Allah ya tsare mu.

    As-Sheikh Dr. Isa Garba Nayaya
    11/12/2020

    Karanta Shigowar Nufawa Ƙasar Hausa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Rahoton WikiHausa Na Ƙarshen Shekarar 2024

    Rahoton WikiHausa Na Ƙarshen Shekarar 2024

    A shekarar da muka yi ban kwana da ita manhajar wikiHausa ta samu nasarori da dama waɗanda suka taimaka wajen yaɗuwarta a duniya baki ɗaya. Daga cikin nasarorin da ta samu kuwa akwai yaye ɗalibai sama da ɗari a fannin koyon sarrafa na’ura mai ƙwaƙwalwa cikin harshen Hausa.

    Baya ga haka, WikiHausa ta samu nasarar samun ƙarin mabiya a shufukanta na sa-da zumunta, inda ta samu dubunnan mabiya daga ƙasashe daban-daban kama daga ƙasashen Afirka da ma sauran ƙasashen duniya irin su Portugal, India, Malaysia, Brazil, Amerika da wasu da dama.

    Haka kuma, WikiHausa ta samu babbar nasarar ƙulla yarjejeniya da manya-manyan ƙungiyoyi, waɗanda suka haɗa da ƙungiyoyi masu zaman kansu wato NGO’s (misali; less Privileged And Almajiri Initiative da vertical farms da Nasiha foundation da kuma jami’ar Ahmadu Bello Da ke Zari (ABU)) da ƙungiyoyin marubuta da mawaƙa (misali; AWAN) da ƙungiyoyin Malamai da ɗalibai da dai sauransu. 

    Wani ƙarin tagomashi shi ne, a ranar 19 ga watan Oktobar shekarar da muka yi ban-kwana da ita ne aka ƙaddamar da manhajar ta WikiHausa a gidan Malam Aminu Kano da ke Gwammaja wato Mambayya House. Inda taron ya samu halarta manyan mutane daga ciki da wajen jihar Kano. Manyan malamai da daktoci da farfesoshi sun gabatar da tattaunawa ta musamman don ilmantar da mutane da kuma nuna musu muhimmancin harshen Hausa.

    Haka zalika WikiHausa ta samu nasarar samun ɗalibai masu bautar ƙasa, waɗanda za su shafe tsawon watanni goma sha ɗaya suna aiki tare. A dai cikin shekarar da muka yi bankwana da ita ne WikiHausa ta samu takardar shaidar ɗaukar nauyi daga jami’ar tarayya da ke Dutse wato FUD. An gabatar da taron ne a ranar 10 ga watan Oktoba 2024 a jihar Jigawa. 

    Baya ga haka a cikin shekarar an samu nasarar kafa gidauniyar WikiHausa, wato WikiHausa Foundation inda gidauniyar ta koyar da manoman ƙaramar hukumar Gwarzo dabarun zamani na noma. 

    Sannan kuma an gudanar da taron wayar da kai ga masu fama lalurar gyambon ciki (Ulcer) da ciwon suga(diabetes) akan hanyoyin yin azumi cikin sauƙi, wanda taron ya gabata a watan Mayun shekarar ta 2024 a masallacin Alfurƙan da kuma Makarantar Kiwon lafiya wato school of Hygiene da ke Kano. An kuma kafa WikiHausa Institution da V.R inventa, sai kuma alaƙa ta musamman da muka samu da Vision Resonance.  

    Kaɗan kenan daga cikin nasarorin da WikiHausa ta samu a shekarar 2024, kuma muna fata shekara mai kamawa ta 2025 ta zo mana da ɗimbin nasarorin da suka fi na wannan shekarar.  WikiHausa sai sambarka!!!     

    Karanta Waƙar Bikin Ƙaddamar Da Manhajar WikiHausa

    Edita@rumasau-kallamu

  • Shigowar Nufawa Ƙasar Hausa

    Shigowar Nufawa Ƙasar Hausa

    Nufawa su ne mutanen da suke zaune a farfajiyar da ta haɗa kogin Kwara da kogin Kaduna. Da farko fatauci da noma da kamun kifi su ne manyan sana’o’insu na gargajiya. An bayyana cewa wurin da suka fara kafa cibiyar gudanar da mulkinsu na a Muregi wadda take a gefen mahaɗar kogin Kwara da kogin Kaduna.

    Da farko tsarin tafiyar da shugabancinsu tsari ne wanda yake ba kowane ƙauye damar tafiyar da mulkinsu na cin-gashin kansa. Wannan ne ya sa suke zaune a cikin rukuni-rukuni. Daga cikin waɗannan rukunoni babba daga cikin su wanda yake shugabancinsu shi ne rukunin “Beni-Nufe”.

    Akwai rukunonin ƙauyuka goma sha biyu waɗanda suka haɗu suka yi ƙasar Nufe, su ne kamar haka; Lafiya da Bida da Doko da Eso da Nufeko da Eda da Towagi da Yesa da Gaba da Panjuru. Daga baya sun haɗu a ƙarƙashin shugabancin ƙananan sarakunan “Beni-Nufe” (Bello, 1999:27).

    Dangane da shigowar Nufawa ƙasar Hausa yana da matuƙar wuya a ce ga lokacin da suka fara shigowa wannan ƙasa. Abin da aka sani shi ne, akwai daɗaɗɗiyar dangantakar al’adu da addini da kasuwanci a tsakanin Nufawa da mutanen ƙasar Hausa. Ta hanyar wannan dangantaka ‘yan kasuwa daga ƙasar Nufe suna safarar kayayyaki daga ƙasarsu da kuma waɗanda suka sawo daga kasuwannin ƙasashe maƙwabtansu don su sayar a kasuwannin ƙasar Hausa.

    Ire-iren waɗannan kayayyaki sun haɗa da kayan farin ƙarfe irin su ludduna da ‘yan hannu na mata da likkafun siradan dawaki da dai sauransu. Ta hanyar wannan kasuwanci wasu ‘yan kasuwa Nufawa suka kafa unguwar Ayagi a cikin Birnin Kano (Baƙo, 1990:72).

    Haka kuma an sami wasu ‘yan kasuwa Nufawa waɗanda suke fatauci a tsakanin ƙasar Hausa da ƙasar Nufe cikin ƙarni na goma sha bakwai da na sha takwas suna safarar kayayyaki irin su riguna girken Nufe da bindigogi da bayi da babanni da dai sauransu. Ire-iren waɗannan fatake wasunsu sun zauna a ƙasar Hausa zama na dindindin (Adeleye, 1975:592).

    Bayan waɗanda suka shigo ƙasar Hausa don yin kasuwanci, wasu Nufawan sun shigo ƙasar Hausa don neman ilimin addinin Musulunci. Wannan ya faru ne sakamakon karɓar addinin Musulunci da mafi yawancin Nufawa suka yi.

    An sami shigowar Nufawa da yawan gaske cikin garuruwan ƙasar Hausa musamman a cikin ƙarni na goma sha tara bayan jihadin Shehu Ɗanfodiyo. Sun shigo cikin wasu garuruwan ƙasar Hausa musamman Sakkwato wadda ita ce cibiyar Daular Sakkwato don neman ilimin addinin Musulunci (Bello, 1999:29).

    Sakamakon kafuwar mulkin mallaka a ƙasar Hausa a cikin ƙarni na ashirin an sami ƙarin shigowar Nufawa a wannan ƙasa. Sun shigo ne don neman ilimin zamani wanda Turawa suka kawo. Dangane da haka ne wasunsu sun shigo garuruwa irin su Sakkwato da Zariya da Katsina da Kano, don a wancan lokacin a waɗannan garuruwa ne aka fara kafa makarantun koyar da ilimin zamani a duk faɗin arewacin Nijeriya.

    Ana ɗaukar ɗalibai daga ko’ina cikin wannan yanki har daga ƙasar Nufe. Misali, a cikin shekarar 1935 daga cikin ɗaliban da aka ɗauka a Kwalejin Katsina akwai Nufawa cikinsu (Indabawa, 1997:200).

    A cikin wannan ƙarni dai an sami ƙarin shigowar wasu Nufawa a sassa daban-daban na ƙasar Hausa don neman aiki a ma’aikatun da Turawan Mulkin Mallaka suka kafa a wasu garuruwan da suke cikin ƙasar Hausa. An sami Nufawa waɗanda suka yi aiki a matsayin leburori da masinjoji da dai sauran ayyuka.

    Ga waɗanda suka sami damar yin karatun zamani an ɗauke su a matsayin akawu-akawu don su yi aiki a tashoshin jiragen ƙasa da dai sauran ayyuka. An kuma ƙara samun shigowar Nufawa cikin ƙasar Hausa bayan samun mulkin kai. Sun shigo don yin aikace – aikace a hukumomi da ma’aikatu da kamfanonin Gwamnatin Jihar Arewa.

    A Sakkwato ma akwai ire-iren waɗannan Nufawa kamar Malam Abdullahi Ndagi da Malam Mohammed Bello da Alhaji Abdullahi Jimada da dai sauransu. A Sakkwato Nufawa sun kafa ƙungiyar taimakon-kai-da-kai don haɗa kan dukkan Nufawan da suke zaune a Sakkwato da kewaye a unguwannin Anguwar Nufawa da Pategi da Kurmin Nufawa da Tako da dai sauransu (Bello: 1999:36, 48,50).

    Kasancewar mafi yawancin Nufawan da suka shigo ƙasar Hausa mabiya addinin Musulunci ne ya sa suka sami karɓuwa wurin al’ummar Hausawa. Wannan ya taimaka an sami musayar al’adu da auratayya a tsakaninsu.

    Kamar yadda Nufawa suka shigo ƙasar Hausa, an sami wasu Hausawa da suka yi ƙaura daga ƙasar Hausa suka koma ƙasar Nufe. Ire – iren waɗannan Hausawa sun je wannan ƙasa ne don yin kasuwanci da wasu hulɗoɗi.

    A sakamakon haka ne a yanzu akwai Hausawa masu yawa waɗanda suke zaune a garuruwa da ƙauyukan ƙasar Nufe, waɗanda suka haɗa da Bida da Katcha da Lafai da Agaye (Hira da GHM, a garin Bida, a ranar 18/8/2004). Ire-iren waɗannan Hausawa sun zama ‘yan ƙasa kuma suna magana da harshen Nufanci kamar yadda suke magana da harshen Hausa, kuma al’adunsu da na Nufawa na yi wa juna shigar giza-gizai.

    Nason Al’adun Nufawa Kan Hausawa

    Ayyuka irin na wanzancin Hausawa waɗanda Nufawa suke yi ba su da yawa kamar yadda aka same su a wurin al’ummomin Fulani da Barebari da Buzaye. Wannan dalili ne ya sa nason da aka samu na al’adun Nufawa cikin wanzancin Hausawa ba su da yawa ƙwarai. Amma kuma duk da haka akwai wasu fannoni na wannan sana’a waɗanda suka samo asali daga al’adun Nufawa.

    Cire Belun-wuya

    A al’adar Nufawa ba su damu da cire belun-wuya ba, maimakon cirewa suna ba da magani ne. Wannan al’ada ta yi naso a kan wasu Hausawa waɗanda suke zaune a ƙasar Nufe, don kuwa akwai waɗanda idan aka haifa masu jariri, maimakon wanzami ya cire belun, sai dai ya ba da magani wanda za a riƙa ba jaririn ya riƙa sha ko kuwa a ɗaura masa wani karhu a wuya (Hira da AGHM da AMB, Jihar Neja da AYAUB, Jihar Neja da HMA da YDG da AM da AD a ranakun 18 da 19 da 20 ga watan Agusta 2008).

    Wannan al’amari ya yi tasiri a kan wanzancin Hausawa saboda wasu wanzamai waɗanda suke yin ayyuka a ire-iren waɗannan gidaje suna rasa ayyuka. Wanda a dalilin haka abubuwan suke shigowa a wurinsu za su ragu.

    Askin Jarirai na Suna da Lokacin Yin sa

    Wani ɓangare wanda al’adun Nufawa suka yi naso a cikin wanzancin Hausawa shi ne ta fuskar askin jarirai na suna. A al’adar Nufawa ba dole ne a yi wa jariri aski a ranar suna ba, ana iya yin wannan aski a kowace rana kafin a yi suna ko bayan an yi suna. Wasu ma ba sa yi wa jariran da aka haifa maza ko mata askin ƙwaryar molo, a maimakonsa a lokacin da ta yi tsawo sosai, sai dai a daddatse ta da almakashi.

    Irin wannan al’ada ta yi tasiri sosai a kan wasu Hausawa waɗanda suke zaune a ƙasar Nufawa da ma wasu da suke zaune a wasu sassa na ƙasar Hausa, don kuwa a wannan zamani akwai wasu Hausawa waɗanda a lokacin da aka yi masu haihuwa, idan aka kwana biyu ko uku da haihuwar, sai su sanya wanzami ya yi wa abin da aka haifa namiji ko mace aski ba sa jira sai ranar suna.

    Wasu kuma ba sa yin askin sai bayan kwana ɗaya ko wuce haka da yin suna. Yin haka ya saɓa al’adar yin askin jariri a ƙasar Hausa (ADS da MMSAB da MLTG da HIAY da MHYB, a ranakun 18 da 19 da 20/8/2008).

    Nason Al’adun Nufawa ta Fuskar Ladar Aikin Wanzanci

    A al’adar Nufawa idan aka yi wani aiki wanda ya danganci aski ko kaciya ko ba da maganin gargajiya, waɗanda aka yi wa aikin ne suke biya, ba kamar a al’adar Hausawa ba, wadda idan aka yi haihuwa ko kaciya ‘yan’uwa da abokan arziki ne suke tattara kuɗi su biya wanzamin. Haka kuma hatsi ne kawai suke bayarwa, ba a sanya kayan yaji irin su barkono da kanwa da citta da makamantansu.

    Irin wannan al’ada ta yi naso a kan wasu Hausawa waɗanda suke zaune a ƙasar Nufawa domin kuwa a wannan zamani duk wanda matarsa ta haihu, shi ke biyan wanzamin da ya yi aski da sauran al’adun wanzanci, saɓanin yadda ake yi a ƙasar Hausa inda ‘yan’uwa da abokan arziki suke tattara kuɗi domin biyan wanzamin.

    Haka kuma tsaba kaɗai ake ba wanzami, ba a haɗawa da kayan yaji kamar yadda aka saba yi a ƙasar Hausa. Wannan al’amari ya yi tasiri a kan wanzanci saboda an sami akasi ta fannin abubuwan da ake biyan wanzami waɗanda suka saɓa da ire-iren waɗanda ake bayarwa a al’adar Hausawa (ADS da MMSA da MLT da HIAY da MHYB, 18 da 19 da 20/8/2008).

    Karanta Shigowar Buzaye Ƙasar Hausa

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu