Tag: yadda ake

  • Shigowar Buzaye Ƙasar Hausa

    Shigowar Buzaye Ƙasar Hausa

    Buzaye mutane ne waɗanda suke zaune rukuni-rukuni a cikin Hamadar Sahara da kuma a yankin Sahel da yake cikin Afrika ta Yamma.

    Buzaye sun kasu zuwa manyan rukunoni uku kamar haka; akwai na Tassili-ni-Ajjar da na Ahaggar da kuma na Adrar-n-Ifoghas (Labaran, 1975:1). Al’ummar Buzaye suna zaune a bisa tsarin zamantakewar rukunoni. Kowane rukuni yana tafiyar da harkokinsu a ƙarƙashin wasu shugabanni.

    Akwai Amanokal waɗanda su ne dattawa masu bayar da shawara kan dukkan abin da ya shafi al’ummarsu. Imajeghen su ne mayaƙa kuma suna ƙarƙashin ikon Imghad waɗanda su ‘ya’ya aka haife su. Akwai kuma “Ineslemen”waɗanda su suke yin sasanci da alƙalanci da tafiyar da harkokin addinin Musulunci a tsakanin Buzaye.

    Daga nan, sai Enadan watau baƙaƙen maƙera da Ikanawan masu ginin tukwane, daga ƙarshe sai baƙaƙen bayi da ake kira Iklan, idan suka sami ‘yanci ana kiran su da sunan Iderfan. Baƙaƙen Buzaye sun fi jajaye yawa (Hammani, 1975:194).

    Ko da yake mafi yawancin Buzaye makiyaya ne waɗanda suke yawace-yawace domin neman wuraren da za su yi kiwon dabbobinsu, waɗanda suka haɗa da raƙuma da awaki da tumaki da dawaki da jakuna da sauransu, amma wasu daga cikinsu kamar Enadan da Ikanawan da Iklan suna zaune a garuruwa irin su Agades wanda a yanzu shi ne babban birninsu da kuma Arlit da Tchivozum da Iferouom da Ingel da Adeɓbissinat da Tchimia da Tabelot da Aoudaɓas da Elmiki da Egadawel da Dabaga da dai sauransu (Hira da AHSAMA, 20/5/2005).

    Bayan kiwon dabbobi Buzaye suna yin noma da ‘yan aikace- aikacen ƙodago don samun kuɗin ɓatarwa kuma suna yin kasuwanci. Daga cikin abubuwan da suke nomawa akwai dabino da kayan marmari. Akwai tsohuwar dangantaka tsakanin Buzaye da Hausawa wadda ita ce ta taimaka wajen shigowar Buzaye ƙasar Hausa.

    An bayyana cewa sakamakon mamayewar da Larabawa suka yi ko’ina cikin ƙasar Buzaye, an tilasta wa wasu daga cikinsu yin ƙaura suka yiwo kudu har zuwa cikin ƙasar Hausa. Haka kuma shigowar Turawan Faranshi cikin ƙasar Buzaye wadda ta haifar da zanga-zangar da Buzaye suka yi daga shekarar 1916 zuwa 1918 ta ƙara taimakawa wajen yin ƙaurar Buzaye suka yi kudu har zuwa cikin ƙasar Hausa (Labaran, 1975:1).

    Bayan wannan an bayyana cewa dangantakar jini da al’adu da kasuwanci sun ƙara taimakawa wajen shigowar Buzaye ƙasar Hausa. Kafin zuwan Turawan Mulkin Mallaka na Faranshi da na Ingilishi a ƙasashen Sudan ta tsakiya, wasu al’ummomi haɗe suke da juna a ƙarƙashin sarki ɗaya. Zuwan Turawa da kuma ƙirƙiro iyakokin zamani ya raba al’umma ɗaya zuwa ƙasashe biyu.

    A iya ganin haka a tsakanin Maraɗi da Katsina da kuma tsakanin Tchibiri da Zamfara, inda Maraɗi da Tchibiri suka faɗa cikin Jamhuriyar Nijar, Katsina da Zamfara aka bar su cikin Tarayyar Nijeriya. Waɗannan al’ummomi waɗanda suke cikin ƙasar Hausa sun yi iyaka da ƙasashen Buzaye, wannan maƙwabtaka ta ƙara taimakawa wajen yin cuɗanya a tsakaninsu wadda ta haifar da auratayya. Ta haka ne aka sami shigar al’adun Buzaye cikin al’adun Hausawa, haka kuma aka sami shigar al’adun Hausawa cikin na Buzaye.

    Wani al’amari wanda ya ƙara taimakawa wajen shigowar Buzaye ƙasar Hausa shi ne yaƙin jihadin Shehu Usmanu Ɗanfodiyo wanda ya gudana a tsakanin shekarun 1804 zuwa 1809. A wannan yaƙi wasu Buzaye sun taimaka wa rundunar Shehu Ɗanfodiyo, wasu kuma suka taimaka wa sarakunan Gobir. An bayyana cewa Buzaye waɗanda ake kira Kel Geres da Itesan suna zaune a cikin ƙasar Hausa tun lokaci mai tsawo da ya gabata.

    A saboda haka sun ɗauka yawan rundunonin Gobirawa na da ƙarfi sosai wanda za su iya cinye rundunar Shehu Ɗanfodiyo da yaƙi. Wannan ne ya sa suka bayar da goyon bayansu ga Sarakunan Gobir. Amma Buzaye Ineslemen da magoya bayansu sun yi mubayi’a ga rundunar Shehu Ɗanfodiyo, kuma suka shiga aka yaƙi Gobirawa tare da su (Hammani, 1975:197,198).

    A Kano an bayyana cewa Buzaye ne daga Agades suka kafa unguwar Agadasawa a cikin Birnin Kano tun lokaci mai tsawo da ya gabata. An ƙara da bayyana cewa tsakanin shekarar 1916 zuwa 1919 Buzaye kimanin dubu talatin (30,000) suka yi ƙaura daga ƙasarsu suka shigo ƙasar Hausa. Waɗannan Buzaye sun baro ƙasarsu ne suka zauna a garuruwa da ƙauyukan cikin ƙasar Hausa.

    Wannan kuwa ya faru ne sakamakon zanga-zanga da tawayen da suka yi wa Turawan Mulkin Mallaka na Faranshi. Mafi yawa daga cikin ire-iren waɗannan Buzaye sun zaɓi su zauna a garin Kano da ƙauyukan da suke kusa da ita fiye da sauran garuruwan ƙasar Hausa kamar Zariya da Katsina da dai sauransu. Wannan kuwa ya faru ne saboda Kano ta fi sauran waɗannan garuruwa samun wuraren yin aikace-aikacen samun kuɗi, kuma a Kano akwai ‘yan uwa da abokan arziki waɗanda suke zaune a nan shekaru da dama da suka gabata.

    Waɗannan Buzaye suna zaune a wurare daban-daban cikin Birnin Kano musamman wuraren da suke da kamfanoni da gidajen attajirai waɗanda ake ɗaukar su aikin gadi, kuma suna sayar da shayi. Amma aikin gadi shi ne babban aikin da aka san mafi yawancin Buzaye da suka shigo ƙasar Hausa suke yi domin samun kuɗi (Baƙo, 1990: 138,140). Dangane da shigowar Buzaye ƙasar Katsina an sami bayanin da ya nuna sun shigo wannan ƙasa tun fiye da shekaru ɗari biyu da suka wuce. Waɗanda suka shigo suna da yawan gaske kuma a ƙasar Mani suka fara sauka.

    Daga can ne wasu suka ƙara yin kudu waɗanda a yanzu ana samun zuri’arsu a garuruwan da suke kusa da Katsina kamar Kaita da Jibiya da Mashi da Dutsi da Kankiya da Rimi da Charanci da Kusada da Ingawa da Musawa da Safana da Kurfi da Dutsin-ma da Batsari da kuma cikin Birnin Katsina da ƙauyukan da suke ƙarƙashin mulkin waɗannan garuruwa (Hira da MGƊ, a garin Mani, a ranar 14/7/2005).

    Ire – iren waɗannan Buzaye sun kasu zuwa kashi-kashi kamar haka; akwai masu tsagar ɗunkin huɗu da tukarci da makitanawa waɗanda su bayin Buzayen Tassawa ne. Wasu Buzayen sun shigo ƙasar Hausa ne a sakamakon kasuwancin da ya gudana tsakaninsu da mutanen ƙasar Hausa. Bayanai sun nuna tun kafin ƙarni na goma sha tara akwai hulɗar kasuwanci wadda aka gudanar ta hanyoyin kasuwanci waɗanda suka biyo cikin ƙasashen Buzaye.

    Daga nan suka ratsa ta cikin hamadar Sahara zuwa wasu sassan ƙasar Hausa da kewaye. A lokacin da ake gudanar da wannan kasuwanci Buzayen da suke shigowa ƙasar Hausa suna safarar kayayyaki daga ƙasarsu waɗanda suka haɗa da dabbobi da dabino da kanwa da balma da manda da kayan hawan dawaki irin su sirdi da linzami da mashinfiɗan sirdi da kayan ado da dai sauransu. Bayan sun sayar suna sayen kayayyaki daga ƙasar Hausa don kai wa kasuwannin ƙasarsu.

    Ire – iren kayayyakin da suke saye daga kasuwannin ƙasar Hausa sun haɗa da abinci kamar gero da dawa, suna kuma sayen suturu irin waɗanda aka saƙa a ƙasar Hausa da baba da shunin gadi da auduga da dai sauransu.

    Haka su ma Hausawa suna yin safarar kayayyaki daga ƙasar Hausa zuwa ƙasar Buzaye, kuma suna sawo kayayyaki daga wannan ƙasa zuwa ƙasar Hausa. Ta irin wannan kasuwanci ne wasu Buzaye suka yi zamansu a wasu garuruwa na ƙasar Hausa kamar Kano da Katsina da Zamfara da Gobir da kuma ƙauyukan waɗannan garuruwa (Labaran, 1975:11 – 15).

    Dalilin kasuwanci da wasu hulɗoɗi wasu Hausawa sun yi ƙaura daga ƙasar Hausa zuwa ƙasar Buzaye, kuma suna zaune a can shekaru da dama da suka wuce. Tsakanin Buzayen da suka shigo ƙasar Hausa da kuma Hausawan da suka shiga ƙasar Buzaye an sami dangantaka mai inganci wadda ta haifar da musayar al’adu da auratayya a tsakaninsu.

    A nan al’adun Buzaye waɗanda suka shafi aure da haihuwa da mutuwa sun shiga kuma suka yi naso cikin al’adun Hausawa. Haka nan ma irin wannan ta auku ga al’adun Buzaye. Wani babban al’amari da ya faru a sakamakon wannan cuɗanya shi ne, Buzayen da suka shigo ƙasar Hausa shekaru aru-aru da suka wuce, kuma suka yi zamansu cikin ƙasar Hausa sun rikiɗe sun koma Hausawa a harshe da adabi da al’adu, amma wannan al’amari bai shafi Hausawan da suka koma ƙasar Buzaye ba. Don kuwa ba su yada harshensu da adabinsu da al’adunsu ba.

    Nason Al’adun Buzaye A Kan Wanzancin Hausawa

    A wurin Buzaye ana gadon wani ɓangare na sana’ar wanzanci, haka kuma akwai sashen da ba sai an gada ba kowa yana iya yi. Waɗanda suka gaji yin sana’ar wanzanci su ne ake kira da sunan “aghachaou”, kuma su ne suke yin ayyuka irin su cire belun-wuya da kaciya da tsagar gado da ta kwalliya. Amma sauran ayyuka musamman aski kowa yana iya koyo ya riƙa ba dole sai wanda ya gada ba. Dangane da wannan bincike an gano akwai wasu al’adun Buzaye waɗanda suka yi naso cikin wanzancin Hausawa a waɗannan fannoni.

    Cire Belun-wuya

    A al’adar Buzaye a lokacin da aka cire wa jariri ko yaro belun-wuya, sai a jiƙa kanwa da ruwa a ɗiga wa wannan jariri ko yaron ruwan don maganin tsayar da jini da kuma saurin warkewar wurin da aka yi yankan. Haka kuma wanda aka cire wa belun zai sami sauƙin zafi da ciwo a cikin maƙogaronsa inda aka cire belun (AHSAMA, Jamhuriyar Nijar, a ranar 20 ga watan Mayu 2005).

    Wannan al’ada ta yi naso sosai a wurin Hausawa, don kuwa a wannan zamani a mafi yawancin sassan ƙasar Hausa idan aka cire wa jariri ko yaro belun-wuya, sai wanzamin ya umurci iyayen yaron da su jiƙa kanwa da ruwa a ba wannan jariri ko yaron ruwan ya sha domin maganin tsayar da jini da saurin warkewa da kuma sauƙin zafi da tsananin ciwo a cikin maƙogaro kamar yadda Buzaye suke amfani da shi (Hira da MASASKM, a fadar Sarkin Katsinan Maraɗi, Jamhuriyar Nijar, a ranar 2 ga watan Maris, 1998) .

    Aski Da Ladar Da Ake Biya

    A lokacin da aka haifi jariri, a al’adar Buzaye ana iya yi masa aski a kowace rana ake so, ba dole sai an keɓe wata takamaimar rana ba. Mafi yawancin lokaci Buzaye sun fi yi wa jariransu aski kafin ranar suna watau kwana biyu ko uku ko huɗu da haihuwa. Haka kuma a al’adarsu ba wanzaman gado ne suke yin irin wannan aski ba, baƙaƙen maƙera waɗanda su abokan wasan Buzaye ne suke yin irin wannan aski.

    Idan suka gama aski ba a biyan su da wasu kuɗi, suna ɗibar nama ne daga dabbar suna wadda aka yanka, sannan kuma ana ƙara masu da abinci (Hira da AAASA, Jamhuriyar Nijar, a ranar 20 ga watan Mayu, 2005).

    Irin wannan al’ada ta yi naso a cikin wanzancin Hausawa, don kuwa a wannan zamani akwai wasu Hausawa waɗanda ke yi wa jariran da aka haifa aski kwana biyu ko uku ko huɗu da haihuwarsu. Ire-iren waɗanda suke koyi da irin wannan al’ada ba sa bari sai ranar suna su yi wa jariransu aski.Haka kuma wajen biyan ladar askin suna biyan wanzamin da ya yi askin da abinci da naman dabbar suna kamar yadda Buzaye suke yi.

    Wannan al’ada ta yi tasiri a kan wanzanci saboda wanzaman Hausawa da suke yi wa ‘yan’uwansu waɗanda suka yi koyi da wannan al’ada ta saɓa yadda ake yin wannan sana’a a ƙasar Hausa a inda ba a yi wa jariri askin suna sai ranar suna ko bayan an yi suna (Hira da MGƊASASƘ, a fadar Mai Martaba Sarkin Ƙwanni-Birnin Ƙwanni, Jamhuriyar Nijar, a ranar 3 ga watan Maris 1998).

    Nason Al’adun Buzaye A Kan Tsagar Gado

    Akwai wasu Hausawa waɗanda saboda wasu dalilai suke barin tsagarsu ta gado su ɗauki irin ta Buzaye. Misali, a ƙasar Katsina akwai wasu daga cikin mutanen wannan ƙasa waɗanda suka bar yin tsagar gado irin ta Katsinawa watau bille suka ɗauki irin ta Buzaye. Wannan kuwa ya faru ne saboda irin muzantawa da ƙyama da wasu Hausawa suke nuna wa masu irin wannan tsaga ta Katsinanci.

    Saboda hulɗa wadda take tsakanin ire-iren waɗannan Katsinawa da Buzaye, sai suka riƙa kwaikwayon yin tsagarsu a matsayin wadda suka gada. A nan ma wannan al’ada ta Buzaye ta yi naso a kan sana’ar wanzanci saboda wanzaman Hausawa ne suke yi wa waɗannan Hausawa irin tsagar Buzaye, ba wanzaman Buzaye ne suke shigowa ƙasar Hausa don yin ire-iren waɗannan tsaga ta Buzaye.

    Nason Al’adun Buzaye Kan Aski

    Al’ummar Buzaye na yi wa ‘ya’yansu tukku a ƙeya wanda ba sa aske shi sai lokacin da wannan yaro ya yi girma sosai ya isa aure. Irin wannan al’ada ya yi tasiri a kan wasu Hausawa musamman waɗanda suke zaune a ƙasar Buzaye da kuma wasu sassan ƙasar Hausa waɗanda suke maƙwabtaka da ƙasar Buzaye irin su Katsina da Daura da Maraɗi da Ƙwanni da Kano da Zamfara.

    Wannan kuwa ya faru ne saboda a wannan zamani akwai wasu Hausawa waɗanda suke yi wa ‘ya’yansu irin wannan tukku a matsayin na gado (Hira da MGƊASASƘ, a Birnin Ƙwanni da kuma MASASKM, dukkansu a Jamhuriyar Nijar a ranakun 3 da 4 ga watan Maris 1998).

    Nason al’adun Buzaye a irin wannan aski ya fito ne saboda wanzaman Hausawa ne suke yi wa Hausawa waɗanda suka yi kwaikwayon yin irin wannan nau’i na aski ba wanzaman Buzaye ne suke shigowa ƙasar Hausa su yi wa Hausawa ba.

    Karanta Shigowar Barebari Ƙasar Hausa

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Shigowar Barebari Ƙasar Hausa

    Shigowar Barebari Ƙasar Hausa

    Barebari su ne mutanen da suke zaune a Arewa maso gabas da ƙasar Hausa a farfajiyar tabkin Chadi. Su ne suka kafa daular Kanuri ta Kanem Borno a shekaru ɗaruruwa da suka wuce. A bayanan da aka samu an bayyana cewa wannan daula ta fara baɓaka a cikin ƙarni na goma sha ɗaya lokacin mulkin Mai Umme (Hume) 1085 zuwa 1097.

    Ana tunawa da shi a matsayin wanda ya fara karɓar addinin Musulunci daga cikin sarakunan Kanuri. A yanzu babban birnin Barebari shi ne Borno ko Maiduguri. Daga wancan lokaci har zuwa cikin ƙarni na goma sha takwas wannan daula ta sami haɓaka da faɗaɗa a wurare da dama da suke cikin Sudan ta tsakiya. Ta sami damar mamaye al’ummomi masu yawa waɗanda suke iyaka da ita, wannan ne ya tilasta masu biyan kuɗin ƙasa ga sarakunan Barebari.

    Dangane da dangantakar da ta faru a tsakanin Barebari a ɓangare ɗaya da kuma al’ummomin ƙasar Hausa a ɗaya ɓangaren, a iya cewa da farko ta yaƙe-yaƙe ce don mallakar hanyoyin kasuwanci da suka ratsa ta cikin Hamadar Sahara zuwa Afrika ta Arewa. Dangantaka ta biyu ita ce wadda aka samu sakamakon haɓakar addinin Musulunci da ya shigo cikin waɗannan ƙasashe (Adeleye, 1975:557). Haka kuma ana sa ran addinin Musulunci ya shigo cikin ƙasar Hausa ta Borno tun kafin ƙarni na goma sha huɗu (Yahaya, 1988:8).

    Cikakkiyar dangantaka wadda ta ƙara taimakawa wajen shigowar Barebari ƙasar Hausa ta faru ne a ƙarshen ƙarni na goma sha shida. Hakan kuwa ya faru ne a sakamakon haɓaka da Borno ta yi ta fuskar addinin Musulunci, don kuwa a lokacin Borno ta zama cibiyar koyarwa da yaɗa addinin Musulunci wadda babu kamar ta a duk tsakiyar Sudan. Saboda haka ne mutanen ƙasar Hausa ta fuskar addinin Musulunci suka dogara kan malaman da suka fito daga Borno ko waɗanda suka yi karatun addinin Musulunci a ƙasar Borno.

    An sami shahararrun malamai masu yawan gaske waɗanda suka yi ƙaura daga Borno suka shigo ƙasar Hausa. Misali, mahaifan shahararren malamin nan wanda aka haifa a cikin shekarar 1595 mai suna Abu Abdullahi Muhammad b. Masanih b. Muhammad b. Abdullah b. Nuh al-Barnawi al-Katsinawi wanda kuma aka fi sani da suna Wali Ɗanmasani, sun yiwo ƙaura ne daga Borno, shi kuma an haife shi a Katsina. A halin yanzu zuri’ar wannan malami na zaune a unguwar Masanawa ta cikin birnin Katsina.

    Wannan ya bayyana mahaifansa ko kakanninsa suna cikin malaman da suka yiwo ƙaura daga Borno suka shigo Katsina a farkon ƙarni na goma sha shida. Bayan su akwai kuma masanin nan mai suna Muhammad b. Ahmad b. Abi Muhammad al-Tazakhti wanda aka fi sani da sunan Wali Ɗantakum, ya rasu a wajen shekarar 1529. Akwai kuma wani shahararren malami mai suna Makhluf b. Ali b. Salih al-Bilbali wanda ya rasu a cikin shekarar 1532. Waɗannan baƙi har yanzu suna nuna asalinsu Barebari ne don kuwa suna yi wa ‘ya’yansu tsagar fashin goshi irin ta Barebari (Usman, 1972:186,190).

    Dangane da shigowar Barebari Kano, an bayyana cewa, bayan shigowar ɗaiɗaiku tun lokaci mai tsawo da ya gabata, an sami shigowar wasu da yawan gaske a lokuta uku kamar haka:

    • A farkon ƙarni na goma sha biyar a sakamakon rashin zaman lafiya da ya faru a Daular Kanem da ta Borno da kuma buɗe hanyar kasuwanci daga Borno zuwa Kano wadda ta wuce zuwa yankin Gwanja, Barebari masu yawa sun shigo ƙasar Kano.
    • A tsakiya da ƙarshen ƙarni na goma sha takwas an sami shigowar Barebari cikin ƙasar Kano sakamakon fari wanda ya haifar da ƙarancin abinci da aka fuskanta a ƙasar Borno.
    • A sakamakon hare-haren da Rabeh ya riƙa kaiwa cikin Daular Borno a ƙarshen ƙarni na goma sha tara da kuma farkon ƙarni na ashirin ya ƙara taimakawa wajen shigowar Barebari cikin ƙasar Kano.

    Waɗannan Barebari ne suka kafa unguwannin Zangon Barebari da Malangari, haka kuma akwai waɗanda suke zaune a cikin wasu unguwanni kamar Fagge da ‘Yandoya da Gabari dukkan su a cikin Birnin Kano (Baƙo, 1990:72, 98,99).

    An sami bayanin daɗaɗɗiyar dangantaka tsakanin Barebari da mutanen Zariya, domin kuwa an bayyana cewa a cikin ƙarni na goma sha takwas har zuwa lokacin jihadi Daular Borno ta mamaye Zariya. Wannan ne ya sa aka sami zaunannen wakilin Mai na Borno a fadar Sarkin Zazzau wanda yake riƙe da muƙamin “Kachalla”. Wannan dangantaka ta ƙara taimakawa ƙwarai wajen shigowar Barebari ƙasar Zazzau.

    A dalilin haka ne Barebari suka sami sarautar Zazzau, wanda a yanzu daga cikin gidajen sarautar Zazzau akwai gidan Yamusa waɗanda asalinsu Babarbare ne. Ta fuskar addinin Musulunci, Barebari sun yi gagarumin aiki a ƙasar Zazzau da kewayenta, don kuwa daga cikin limaman Zariya, Limamin Kona ana ba da shi daga al’ummar Barebari (Hogben, 1967:118).

    Bayanan da aka samu dangane da ƙaura da shigowar Barebari ƙasashen Hausa na Yamma, wato Zamfara da Gobir, an bayyana cewa an sami shigowar Barebari a waɗannan ƙasashe a lokaci mai tsawo da ya gabata. An ce wasu malamai daga Borno sun shigo ƙasar Zamfara a cikin ƙarni na goma sha bakwai, kuma ana tsammani su ne suka shigar da wasu sarakunan Zamfara cikin addini Musulunci.

    Wasu daga cikin malaman Anka sun bayyana cewa asalinsu daga Borno suke. Waɗannan malamai Barebari suna da babban matsayi a ƙasar Zamfara don kuwa mafi yawanci su ne limamai a Anka (Nadama, 1977:185,186). Ƙaura da shigowar Barebari cikin ƙasar Zamfara ba ga malamai kaɗai ta tsaya ba, a cikin ƙarni na goma sha bakwai an sami wani ɗan sarki da ya yi gudun hijira daga Borno saboda wasu dalilai ya sauka a Fadamar Kanwa.

    Wannan ɗan sarki mai suna Modu Masika ya zo da tawagar dakaru Barebari masu yawan gaske, waɗanda daga cikin su akwai mahaya dawaki ɗari da ‘yan lifidda arba’in. An bayyana cewa waɗannan Barebari sun sauka a wannan wuri lokaci mai tsawo da ya gabata tun kafin zuwan Gobirawa Birnin Alƙalawa (Nadama, 1977:186,187).

    A ƙasar Zamfara akwai Burmawa waɗanda ake sa ran sun fi dukkan mutanen da suke ikirarin asalinsu Barebari ne yawa. Yana da matuƙar wuya a ce a lokacin da suka shigo ƙasar Zamfara daga Borno, amma bayanan da aka samu sun bayyana cewa a lokacin da suka shigo ƙasar Zamfara sun sauka a wuraren da suke kewayen gulbin Sakkwato.

    Shugaban tawagar waɗannan Barebari mai suna Zarra ya sauka a Ƙumcin Gizo, a inda aka ce ya aika wa Galadiman Borno da ya yi masa sarautar Sarkin Burmi. Daga Ƙumcin Gizo wasu suka yi gaba zuwa Jargaɓa, daga ƙarshe suka sauka a Bakura a farkon ƙarni na goma sha takwas. A wannan lokaci ne waɗannan Barebari Burmawa suka kafa wasu garuruwa a ƙasar Zamfara waɗanda suka haɗa da Rara da Riji da ‘Yar Tsakuwa.

    An tabbatar da a cikin ƙarni na goma sha takwas akwai Barebari ‘yan kasuwa da malamai masu yawa a garuruwan ƙasar Zamfara waɗanda suka haɗa da Birnin Zamfara da Kiyawa da Banga Tumfafi da Kamani da kuma ‘Yandoto (Nadama, 1977:191,192).

    Su ma Hausawa saboda kasuwanci da neman ilimin addinin Musulunci sun yi ƙaura daga ƙasar Hausa suka koma ƙasar Borno. Sakamakon shigar Hausawa ƙasar Borno an sami auratayya tsakaninsu da Barebari, amma duk da haka ba a sami abin da ya faru ga Barebarin da suka shigo ƙasar Hausa ba waɗanda suka rikiɗe suka koma Hausawa.

    Hausawan ba su koma Barebari ba, hasali ma dai mafi yawancin Barebari suna magana da harshen Hausa. Abin da ya faru shi ne, Hausawan suna magana da harshen Kanuri kamar yadda suke magana da harshen Hausa, kuma wasu al’adun Barebari sun shiga cikin al’adun Hausawa ta fuskar aure da haihuwa da mutuwa da sauran wasu ma’amalolin rayuwa na yau da kullum.

    Ire-iren waɗannan Hausawa suna zaune a unguwannin Hausari da Bulunkutu da Gwange da London-Ciki da Jajere duk a cikin Birnin Maiduguri da wasu garuruwa a cikin jihar Borno da Yobe. Haka kuma akwai wasu da suke zaune a Damagaram ta cikin Jamhuriyar Nijar (Hira da MSYB, a ranar 26/5/2005).

    Nason Al’adun Barebari a Kan Wanzancin Hausawa

    A wurin Barebari sana’ar wanzanci ta samo asali ne tun lokacin Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi), don kuwa sun bayyana cewa, ita kanta kalmar ‘wanzama’ sunan da suke kiran wanzami da shi, ta samo asali ne daga kalmar Larabci ta ‘hajam’ da ‘hajama’, ma’ana mutumin da yake yin ƙaho, ko ‘bessem kastama’ da harshen Barbarci.

    Sun ƙara da bayyana cewa, wani wanzami ya yi wa Manzon Allah ƙaho, a lokacin da ya fitar da jinin don zubarwa, sai ya ga ƙasa ta buɗe, da kuma ya ɗaga kansa sama, sai ya ga ita ma samaniya ta buɗe.

    Wannan ne ya sa shi tunanin cewa dukkan waɗannan halittu na Ubangiji suna buƙatar a zuba jinin Manzon Allah a cikinsu. Daga nan sai ya yanke hukuncin ya shanye wannan jini. Wannan dalili ne ya sa a yau ake danganta wanzamai da mutane waɗanda suke da jinin Annabi a cikin jikinsu, kuma aka riƙa danganta su da shariftaka (Sheriff, 2000:62).

    A al’adar Barebari ana gadon sana’ar wanzanci, haka kuma a wasu lokuta waɗanda suka yi gado sukan iya koya wa waɗanda ba su gada ba, amma shugaban wanzamai wanda suke kira da sunan ‘Zanna Ɗambusuma’, dole sai wanda ya gaji wannan sana’a ne ake naɗawa kuma Shehun Borno ne yake naɗa shi.

    A yanzu wannan sarauta tana hannun Zanna Ɗambusuma Madu Aji, kuma yana da mataimaka waɗanda kowanen su yana riƙe da irin tasa sarauta waɗanda suka haɗa da ‘grema’ da ‘fuwu’ da ‘kazalla’.

    A al’adar Barebari cikakken wanzami ko ‘wanzama’ ko’diyeji’ shi ne wanda ya koya kuma ya iya ayyuka irin su tsagar gado da cire belun-wuya da kaciya da ƙaho da yin tsagar ciki a ƙarƙashin cibiya da kuma bayar da magungunan gargajiya da sauran ayyuka waɗanda suka danganci kiwon lafiyar mutane (Sheriff, 2000:66). Idan aka nazarci wannan bayani za a fahimci akwai kamanci tsakanin wanzancin Barebari da na Hausawa. Wannan kamanci ya ƙara taimakawa aka sami nason al’adun wanzancin Barebari cikin na Hausawa.

    Wasu al’adun Barebari sun yi tasiri a kan al’adun wanzanci musamman ga Hausawa waɗanda suke zaune a ƙasashen Barebari kamar a Maiduguri da Damagaram da kuma a garuruwan da suke ƙarƙashin ikonsu. Haka kuma akwai wasu Hausawan ƙasar Hausa waɗanda al’adun Barebari suka yi tasiri a cikin rayuwarsu ta fuskar yadda suke tafiyar da al’adun da suka shafi ayyukan wanzanci.

    An sami irin wannan naso ne daga wurin wasu Barebari waɗanda suka shigo ƙasar Hausa daga ƙasar Borno ko dai don yaɗa ilimin addinin Musulunci ko kuwa don yin kasuwanci da wasu ma’amalolin rayuwa. Yanzu za a yi nazarin wasu daga cikin fannonin wanzanci a yi bayanin wuraren da al’adun wanzancin Barebari suka yi tasiri a kan na Hausawa.

    Cire Belun-wuya

    A al’adar Hausawa a lokacin da aka cire wa jariri belun-wuya ana ɗebo sauyar dashi da ta fid-da-tartsa a dafa a ba shi ya sha don maganin zafin da zai biyo baya, kuma wurin da aka yi yankan ya warke da sauri. Sakamakon zamantakewa a tsakanin Hausawa da wasu baƙi an sami wasu magungunan masu sauƙin yi fiye da wanda suke da farko.

    Misali, a al’adar Barebari bayan an cire wa jariri ko yaro belun-wuya, sai a daka ‘ya’yan bagaruwa a jiƙa garin da ruwa a ɗura masa wannan ruwa. Dalilin ba shi wannan ruwan magani shi ne don maganin zafin da zai biyo bayan cire belun kuma ya taimaka wajen tsayar da jini daga wurin da aka cire belun. Haka kuma zai taimaka sosai wajen saurin warkewar wurin da aka yi yankan (Hira da ZƊMA, a ranar 9 ga watan Janairu, 2008 a gidansa da ke a cikin garin Maiduguri).

    Irin wannan al’ada ta yi tasiri a kan wanzancin Hausawa, don kuwa su ma Hausawa musamman waɗanda suke zaune a ƙasar Barebari da kuma wasu sassa na ƙasar Hausa irin su Katsina da Zamfara da Kano da Daura a lokacin da aka cire wa jariransu belun-wuya suna ba su irin wannan magani don koyi da Barebari (Hira da SASN, a ranar 10 ga watan Janairu, 2008 a gidansa da ke a unguwar Bulunkutu cikin garin Maiduguri.

    Tasirin Magungunan Barebari a Kan Wanzanci

    Wani ɓangare na al’adun Barebari wanda ya yi naso a kan wanzancin Hausawa shi ne ta fuskar maganin gargajiya. A wannan ɓangare an bayyana wanzaman Hausawa sun sami magani daga wurin wanzaman Barebari wanda zai taimaka wa wanzami idan yana yin aski wanda ake yi wa askin ba zai ji zafi ko wata takura ba.

    Kamar yadda aka sami bayani an ce wannan magani ya samo asali ne daga wurin wani wanzami Babarbare wanda saboda yadda ya iya aski kuma labarinsa ya kai ko’ina cikin ƙasar Borno.

    Da Shehun Borno ya sami labarin wannan wanzami, sai ya gayyace shi da ya zo don yi masa aski. A lokacin da aka gaya masa, sai ya je wurin mahaifinsa ya sanar da shi. Daga nan ne sai mahaifin wannan wanzami ya shawarce shi da ya samo mullin giginya wanda yake ɗauke da ‘ya’yan giginyar a daka shi cikin turmi a jiƙa cikin ruwa ya riƙa wanke hannuwansa da ruwan maganin.

    Ya bayyana masa cewa yin haka zai taimaka idan yana yi wa mutane aski ba za su ji zafi ko wata takura ba. Da ya bi wannan shawara ta ƙara taimaka masa samun ɗaukaka a wurin Shehun Borno wadda ta kai har aka ba shi sarautar wanzamai watau “Zanna Ɗambusuma”.

    Daga baya, sai sauran wanzamai suka gano wannan asiri su ma suka riƙa yi wanda ya taimaka masu wajen gudanar da wannan sana’a. Sannu a hankali ta hanyar cuɗanya tsakanin wanzaman Hausawa da na Barebari, sai su ma suka sami wannan asiri wanda har a wannan zamani suna amfani da shi (Sheriff, 2000:63).

    Nason Tsagar Gado ta Barebari a Kan Wanzancin Hausawa

    Al’adar da ta danganci tsagar gado irin ta Barebari ta yi tasiri a kan wasu Hausawa. Ta wannan fuska akwai wasu Hausawa musamman a ƙasar Katsina, waɗanda asalin tsagarsu ta gado billen Katsinanci ce. A wannan zamani saboda an ɗauki dukkan mai irin wannan tsaga ta billen Katsina matsayin Bamaguje wanda wasu mutane sukan muzanta, sai wasu masu irin wannan tsaga suka bar yin tsagar gaba ɗaya, amma waɗanda suke sha’awar tsagar, sai suka bar yin irin wannan tsaga suka ɗauki wata tsagar gado suka danganta da zuri’arsu.

    Daga cikin ire-iren waɗannan tsage akwai ta Barebarin Katsina da fashin goshi waɗanda dukkan su asalinsu tsagen gado ne da ake yi wa wasu mutane don su bayyana asalinsu Barebari ne. Wannan al’ada ta yi tasiri cikin al’adun wanzanci saboda wanzamai Hausawa ne suke yin ire-iren waɗannan tsaga, ba wanzaman Barebari ne suke shigowa ƙasar Hausa ba.

    A wannan zamani yana da wuya a ƙasar Katsina a bambance tsakanin waɗannan Barebari da kuma Katsinawa waɗanda suka bar yin tsagarsu ta asali suka ɗauki irin wannan tsaga ta Barebarin Katsina.

    Danna nan don karanta Nason Al’adun Baƙi Maƙwabta Na Kusa A Wanzancin Hausawa

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Tsayar Da Gemu Yake A Al’adar Fulani

    Yadda Tsayar Da Gemu Yake A Al’adar Fulani

    A al’adar Fulani ana tsayar da gemu a lokacin da wanda za a sanya wa gemu ɗansa ko ‘yarsa ta yi aure har ta haihu. Idan kuma ba a haifa masa ɗa ko ‘ya da aka yi wa aure ya haihu ba, sai ya tsayar da gemu a lokacin da ɗa ko ‘yar tsaransa ya haihu. Ana tsayar da gemu a lokacin wani biki na aure ko haihuwa.

    A mafi yawancin lokaci ana tara tsararrakin juna a haɗa su wuri ɗaya don a tsayar masu da gemu. Ana kuma la’akari da waɗanda aka yi wa kaciya a rana ɗaya, sai kuma a sake haɗa su don tsayar masu da gemu a rana ɗaya. Ana tsayar da gemun ne a wurin da ake yin bikin. Tun kafin zuwan ranar ake sanar da ‘yan’uwa da abokan arziki da kuma wanzamin gidan wanda shi ne zai sanya wa wannan mutum ko mutane gemu.

    A ranar da za a sanya gemu bayan dukkan ‘yan’uwa da abokan arziki waɗanda aka gayyata sun taru, sai a kawo ƙwaryar madara a samo ganyen kalgo a naɗa gammo da shi a saka cikin wannan ƙwaryar madara. Daga nan sai wanda za a sanya wa gemu ya fito ya zauna a gaban dattawa. A al’adar Fulani an fi son wanzamin da zai sanya wa wani gemu,ya kasance wanda dukkan mahaifansa watau uwa da uba suke raye.

    Idan kuwa wanzamin da yake yin wanzanci a wannan gida ya rasa ɗaya daga cikin mahaifansa, sai a sami wani daga cikin dangin wanda za a sanya wa gemu kuma wanda dukkan mahaifansa suke a raye ya fara sanya wa wannan mutum gemu. Yadda ake yi shi ne wannan wanda aka wakilta don ya fara sanya gemu zai shafa ruwan madara na cikin ƙwarya da sabulu, daga nan sai ya riƙa shafa bayan askar a wurin gashin haɓar wanda za a sanya wa gemu.

    Daga nan sai ya mayar wa wanzamin da askarsa don ya ci gaba da yin aski da gyaran fuska wanda za a fito da gemu daga nan ya tsaya ba a ƙara aske shi. Idan za a sanya wa Fulani gemu ana aske saje da gashin baki da hana-ƙarya, shi kuma gemun ana kwakkwafe shi sosai ba a barin sa da faɗi sai dai siriri mai tsawo.

    Bayan an gama sanya wa wannan mutum gemu idan akwai wani tsaransa wanda ya isa sanya gemu amma sai ya ƙi sanyawa, a al’adar Fulani sai a sami wani abokin wasansa ko wani dattijo ya mame shi ya ɗauko wannan gammo na ganyen kalgo wanda yake cikin madarar ya shafa masa a gemunsa.

    Da zarar an shafa masa wannan ganye daga nan ya zama dole gare shi ya zauna a sanya masa gemu ko ya shirya ko bai shirya ba. Wannan dalili ne ya sa waɗanda suka san cewa sun isa sanya gemu amma saboda wasu dalilai nasu ba su sanya ba, ko an gayyace su zuwa wurin sanya gemu ba sa zuwa.

    A lokacin da ake sanya gemu ‘yan’uwa da abokan arziki za su riƙa bayar da kari. Daga cikin abubuwan da ake bayarwa akwai kuɗi da dabbobi. Bayan an gama sanya gemun, sai a miƙa wa dattawa ƙwaryar madarar da aka yi amfani da ita wajen sanya gemu. Kowannensu zai sha wannan madara ya kuma shafa wa gemunsa gammon ganyen kalgon da yake cikin madarar.

    Daga nan sai su yi masa huɗuba dangane da abubuwan da suka dace ya riƙa yi da waɗanda ba su dace ya riƙa yi ba. Bayan nan kuma sai dattawan su karkasa kuɗin da aka samu na kari zuwa kashi uku. Kashi na farko a raba wa wanzamin da ya sa gemun da maroƙa, kashi na biyu a ba malamai waɗanda za su yi addu’a, kashi na uku kuma ana sayen goro don a rarraba wa mutanen da suka tattaru a wurin sa gemun. Sauran abubuwan da aka samu kamar dabbobi ana bar wa wanda aka sanya wa gemu, daga nan sai malamai su yi addu’a.

    Waɗannan al’adu na tsayar da gemu a wurin al’ummar Fulani sun yi tasiri a kan yadda wasu Hausawa suke tsayar da gemu. Daga cikin ire-irensu akwai ta lokacin ajiye gemu da kuma wanzamin da zai tsayar da gemu ya kasance wanda dukkan mahaifansa suke raye. Haka kuma akwai wasu Hausawa waɗanda a lokacin da za a gyara masu gemu, sai su sanya a yi shi siriri kamar irin yadda ake yi wa Fulani.

    Askin Jarirai Na Ranar Suna

    Wani ɓangare na wanzanci wanda al’adun Fulani suka yi naso a cikinsa shi ne askinn jarirai na ranar suna. A al’adar Fulani ba a fito da jariri a ranar suna don yi masa aski, wai don tsoron kada mayu su cinye shi. Wannan dalili ya sa Fulani ke kiran wanzami kafin ranar suna ko bayan suna don ya yi aski ba tare wasu mutane sun ga wannan jariri ba. Wannan al’ada ta yi tasiri a wurin wasu Hausawa.

    A yau akwai wasu Hausawa waɗanda suka yi koyi da wannan al’ada ta Fulani waɗanda ba sa fito da jariran da aka haifa masu a ranar suna don yi masu aski. A maimakon haka ana yin askin kafin ko bayan suna, wai don tsoron kar mayu su cinye wannan jariri.

    Nason Al’adun Fulani Dangane da Kaciya

    A wurin yin kaciya ma al’adun Fulani sun yi naso dangane da yadda ake yin ta da kuma wasu al’adu waɗanda suka jiɓance ta. Za a iya ganin haka ta yin la’akari da ranakun da Fulani suka keɓe don yi wa ‘ya’yansu kaciya. Waɗannan ranaku sun haɗa da Juma’a da Lahadi da Talata da Alhamis.

    A al’adar Fulani ba a yi wa yaro kaciya sai shekarunsa na haihuwa sun kai tara zuwa goma sha biyu. A ranar da aka yi wa yaro kaciya da an gama, sai a daka garin gero a dama da nonon shanu a ba yaron da aka yi wa kaciyar ya sha. Haka kuma ana ba dukkan mutanen da suka zo wurin da aka yi kaciyar wannan gari su sha. Shi ma wanzamin da yaransa ana ba su wannan gari su sha. Dalilin shan garin shi ne don a sanyaya zuciyar wannan yaro da aka yi wa kaciya.

    Waɗannan al’adu na Fulani dangane da ranakun da ake yin kaciya akwai wasu Hausawa a sassa daban-daban na ƙasar Hausa musamman waɗanda suke yin hulɗoɗi da Fulani suna yi wa ‘ya’yansu kaciya a waɗannan ranaku. Haka kuma akwai waɗanda saboda koyi da al’adun Fulani ba sa yi wa ‘ya’yansu kaciya, sai a lokacin da shekarunsu na haihuwa suka kai tara ko wuce nan.

    Nason Al’adun Fulani A Kan Tsagar Hausawa

    Tsaga musamman ta gado da ta kwalliya suna daga cikin al’adun Fulani waɗanda suka yi naso cikin wanzancin Hausawa. Ba kamar Hausawa ba waɗanda a mafi yawancin lokaci ‘yan mata ne kawai ake yi wa tsagar kwalliya, su Fulani ana yi wa ‘yan mata da samari, kuma idan za a yi tsagar ba a yin biki kamar yadda ake yi a lokacin da za a yi wa ‘yan matan Hausawa.

    Akwai ire-iren tsagar gado da ta kwalliya na Fulani da dama waɗanda har a wannan zamani ana yi wa ‘yan mata da samarin Fulani ire-irensu,kuma samari da ‘yan matan Hausawa na kwaikwayon yin su. Ire-iren waɗannan tsaga sun haɗa da tsagar gado ta kalangu da fetali da kuma tsagar kwalliya ta ‘yar goshi da kibau da ‘yar baka.

    Tsagar Gado

    A lokacin da Fulani Dallazawa masu jihadi suka ci Katsina da yaƙi suka kafa mulkin Fulani a wannan masarauta, wasu Hausawan ƙasar Katsina sun riƙa kwaikwayon al’adunsu musamman waɗanda suka shafi tsaga. Asalin tsagar gado ta Katsinawa ita ce bille ko tsagar Katsinanci (Sallau, 2000:62, 78).

    Su kuma Fulani Dallazawa tsagarsu ta gado ita ce kalangu (Sallau, 2000:90). Saboda kusanci da waɗannan Fulani, sai wasu Katsinawa waɗanda asalinsu Hausawa ne suka daina yi wa ‘ya’yansu tsagar gado ta billen Katsinanci, sai suka maye gurbinta da tsagar kalangu irin ta Fulani Dallazawa.

    Wannan dalili ne ya sa a yanzu a ƙasar Katsina akwai Katsinawa waɗanda Hausawa ne gaba da baya waɗanda suke yi wa ‘ya’yansu maza da mata tsagar kalangu a matsayin tsagar gado.

    Irin wannan al’amari ya faru ga wasu Hausawan a ƙasar Katsina a lokacin mulkin Fulani Sulluɓawa waɗanda su tsagarsu ta gado ita ce fetali a hannun hagu (Magaji, 2002:23). A nan ma an sami wasu Hausawa waɗanda suka maye gurbin tsagarsu ta gado ta billen Katsinanci zuwa tsagar fetalin hannun hagu irin na Fulani Sulluɓawa. Haka kuma tsagar gadon mahauta ita ce tsagar fetali a hannun dama (Sallau, 2000:77). Su ma a wannan zamani, sai suka bar yin irin wannan tsaga a hannun dama suka mayar da ita a hannun hagu irin ta Fulani Sulluɓawa.

    Dukkan waɗannan nau’o’in tsagar gado na Fulani har a wannan zamani akwai wasu daga cikin mutanen ƙasar Katsina da ke yi wa ‘ya’yansu ire-irensu a matsayin tsagarsu ta gado. Hasali ma akwai waɗanda suke haɗa duka biyun wato tsagar kalangu ta Dallazawa da fetalin hannun hagu ta sulluɓawa.

    Tsagar ‘Yar Goshi

    Irin wannan tsaga ana yin ta a goshi, amma ita ko kusa ba ta yi kama da irin tsagar ‘yar goshi wadda ake yi wa Hausawa ba. Siffar wannan tsaga ta yi kama da kofin da ake sanyawa don cin wata gasa.

    Tsagar Kalangu

    Ita ma tsagar kalangu irin ta Fulani tana da bambanci da irin wadda ake yi wa Hausawa. Tsagar kalangu irin ta Fulani ana yin ta ƙanana kuma sirara ba kamar irin ta Hausawa ba wadda ake yi da girma. ’Yan mata da samarin Fulani ba a yi masu kalangu biyu-biyu kamar yadda ake yi wa ‘yan matan Hausawa, su ɗaya-ɗaya ake yi masu.

    Tsagar Kibau

    Ana yin irin wannan tsaga kamar siffar kibiya, daga nan ne ta sami wannan suna. Ana yin ta ne a fuska bisa kundukuki daidai ƙarƙashin idanu wurin da ake yi wa ‘yan matan Hausawa tsagar kwaluluwa. Asalin wannan tsaga ‘yan mata da samarin Fulani ake wa, sakamakon cuɗanya tsakaninsu da Hausawa ya sa ‘yan matan Hausawa kwaikwayon yin irin wannan tsaga. 

    Tsagar ‘Yar Baka

    Wata tsagar kwalliya wadda ake yi wa ‘yan mata da samarin Fulani wadda kuma ta yi naso cikin al’adun wanzanci da na Hausawa, ita ce tsagar ‘yar baka. Irin wannan tsaga ba ta yi kamanni da irin wadda ake yi wa ‘yan matan Hausawa ba wadda ake yin ta caɓa-caɓa a kumatu. Irin wannan tsaga ana yin gororin tsaga uku-uku ne a kowane kunci kuma kowace ana yin ‘ya’yan tsaga uku-uku ne, amma da na sama da na ƙasa ana yin su a gicciye ne ta tsakiyar ce ake yi a tsaye.

    Ana yin gororin wannan tsaga da ɗan tsawo kuma dukkan su suna ƙarewa a wutsiyar baki. Bayan an yi waɗannan layuka na tsaga ana haɗe su da ƙananan ‘ya’yan tsaga waɗanda su ma ana tsara su uku-uku ana kuma barin ɗan fili a tsakani. Ita ma irin wannan tsaga ‘yan matan Hausawa suna kwaikwayon yin ta.

    Dukkan waɗannan nau’o’i na tsaga waɗanda aka yi bayani a kan su wanzaman Hausawa suna yi wa ‘yan mata da samarin Fulani ire-irensu.Wannan dalili ne ya ƙara jawo hankalin ‘yan matan Hausawa kwaikwayon yin ire-iren su.

    Cire Belun-Wuya

    Wani ɓangare na al’adun Fulani wanda ya yi tasiri a kan wanzanci shi ne wajen cire belun-wuya ko hakin-wuya. A al’adar Fulani a lokacin da aka cire belun-wuya, sai a ɗura wa jaririn da aka cire wa belun nonon shanu mai tsami. Dalilin da ya sa ake ba shi irin wannan nono shi ne don jaririn ya sami sauƙin ciwon da ya biyo bayan cire masa wannan belu. Haka kuma yana taimakawa wajen tsayar da jini daga wannan wuri da aka cire belun kuma wurin zai yi saurin warkewa.

    Wannan al’ada ta Fulani ta yi tasiri sosai wurin wasu Hausawa don kuwa akwai waɗanda a duk lokacin da aka cire wa jaririn da aka haifa belun-wuya, sai su ɗura masa nonon shanu mai tsami kamar yadda Fulani suke yi don yin magungunan da aka yi bayani a kansu.

    Goyon Ciki

    Wani fanni na al’adun Fulani wanda ya yi naso cikin al’adun Hausawa har abin ya shafi sana’ar wanzanci, shi ne goyon ciki. A al’adar Fulani idan mace ta sami cikin fari ba ta haihuwa a ɗakinta. A lokacin da cikin ya kai wata shida, sai a mayar da ita gidan mahaifanta don ta haihu a ɗakin mahaifiyarta. A lokacin da ta haihu haƙƙin mutanen gidan da take aure ne su turo wanzamin gidansu don ya yi wa abin da aka haifa dukkan ayyukan wanzanci.

    Kamar al’adar Hausawa su ma Fulani namiji ne yake da haƙƙin kiran wanzami ba mace ba. Wannan ne ya sa wanzamai zuwa gidajen da ba su ke yin wanzanci ba yin ayyukan wanzanci,don kuwa matar da ta haihu a wannan gida tana aure ne a gidan da suke yin ayyukan wanzanci (Sallau;2000: 9). A nan tasirin al’adun Fulani ya yi naso cikin al’adun Hausawa saboda a al’adar wanzanci wani wanzami ba ya zuwa gidan da wani yake yin aiki ya yi.

    Nason Al’adun Fulani Kan Ladar Aikin Wanzanci

    A lokacin da aka yi wani aikin wanzanci ga al’ummar Fulani wanda aka yi wa ko iyalansa suna bakin ƙoƙarinsu wajen kyautata wa wanzamin da ya yi wannan aiki. Misali, idan aka yi kaciya bayan kuɗi suna kuma ba da zakara ko kaza ko zabo da kuma damen dawa. Haka kuma idan aka yi suna a gidajensu, idan wanzami ya zo kafin ya yi askin jariri na suna ana ba shi abinci mai kyau wanda ya haɗa da dambu da madara a kuma zuba man shanu a ciki.

    Ana kuma dama fura da nonon shanu mai kyau a kawo wa wanzamin ya sha. Bayan kuɗin aski da ƙwaryar aski suna kuma ba wanzamin kan dawo da nono don ya kai wa iyalinsa. Hausawa sun riƙa kwaikwayon yin irin wannan al’ada.

    A lokacin ɗaurin auren budurwa akwai al’adar da Fulani suke kira da sunan walima wadda ake yanka sa ko saniya wanda ake rarraba naman dabbar da aka yanka kashi-kashi a ba kowa nasa rabon. Daga cikin waɗannan kashe-kashe akwai kushekara da ‘ya’yanta waɗanda su ne kason wanzamin da yake yin aikace-aikacen wanzanci a wannan gida.

    Bayan kushekara kuma ana ba shi goro a lokacin da za a ɗaura aure. Dalilin da ya sa ake ba wanzami waɗannan abubuwa shi ne, wai don shi ne ya yi wa wannan budurwa wadda za a yi wa aure gyara a farjinta a lokacin tana jaririya. Saboda haka waɗannan abubuwa suna daga cikin ladar aikin da wanzamin ya yi.

    Dukkan waɗannan al’adu na Fulani da aka kawo a bayani kan su, sun yi naso ne a kan wasu al’adun Hausawa waɗanda suka danganci sana’ar wanzanci da yadda ake yin ta. Haka kuma a mafi yawancin lokaci wanzaman Hausawa ne ke yi wa Fulanin da Hausawa.

    Magungunan da Wanzamai Suka Samo Daga Wurin Fulani

    Wanzamai sun sami magungunan cutar ciwon saɗɗore da kuma ciwon ɗankaɗafi daga wurin Fulani. Shi saɗɗore ciwo ne da yake kama mutum a ƙafa ko a hannu, sai ƙuraje su fito wa mutum caɓa-caɓa a wurin. Wannan ciwo yana da wuyar yin magani, don kuwa sai a yi magani ya warke, bayan wani lokaci kuma sai ya dawo. Maganin wannan ciwo da aka samo a wurin Fulani shi ne, sai a samo ɗan kuka wanda bai ƙosa ba, kuma wanda ya faɗo ƙasa da kansa, watau ba wani ya hau ya ciro shi ba.

    Idan an same shi, sai a ƙona shi, bayan ya huce sai a sami citta mai ‘ya’ya a haɗa su da jar kanwa a daka ya yi gari sosai. Daga nan sai a sami wani ɗan ƙoƙo ko kwano a zuba maganin ciki, a haɗa da man shanu ɗanye a cakuɗe su. A kullum sai a sami ruwa mai ɗumi a riƙa wanke wurin da ciwon yake a riƙa shafa wannan maganin. A duk lokacin da za a shafa maganin, sai an wanke wurin da ciwon yake da ruwan ɗumi. Za a yi ta yin haka har sai wurin ya warke (Hira da AAB, a Daɗin-Kowa Jihar Gombe, a ranar 23/4/2006).

    Karanta Magungunan Gargajiya Na Wanzamai

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Shayar Da Jariri Nonon Uwa Zalla (EXCLUSIVE BREASTFEEDING)

    Shayar Da Jariri Nonon Uwa Zalla (EXCLUSIVE BREASTFEEDING)

    Shayarwa aiki ne da Allah SWT ya tsara halittar jikin mace ta riƙa yinta a duk lokacin da ta haihu, domin samar da ingantaccen abinci ga jariri da kuma nuna masa ƙauna. Kadan daga cikin muhimman abubuwan da ya dace mu sani game da shayarwa su ne:

    1. Amfaninta ga jariri (breastfeeding benefits to the baby):

    Shayarwa tana samar da ingantaccen abinci ga jariri daidai da buƙatar jikinsa, domin yin girma yadda ya kamata. Nonon uwa yana ƙunshe da ƙwayoyin halitta masu bayar da kariya ga jikin jariri (antibodies) don su tsare shi daga cututtuka iri-iri. Sa’annan tana kare jarirai daga hatsarin mutuwa farat ɗaya (Sudden Infant Death Syndrome – SIDS).

    2. Amfaninta ga uwa (breastfeeding benefits to the mother):

    Shayarwa tana taimakon jikin mai-jego wajen saurin murmurewa daga ciwon haihuwa (faster postpartum recovery), ta hanyar sanya mahaifarta ta koma yadda take kafin samun juna biyu. Sa’annan tana matuƙar rage hatsarin kamuwa da cututtukan daji na nono (breast cancer), da mahaifa (uterine cancer), da jakar ƙwan haihuwa (ovarian cancer). Bugu da ƙari, tana ragewa mace hatsarin kamuwa da cutar rashin ƙarfin ƙashi (osteoporosis) wanda yakan iya samunta a lokacin ɗaukewar al’ada (menopause).

    3. Ingantacciyar shayarwa ta hanyar sanya jariri ya kama kan nono sosai (establishing good latch):

    Ya kamata uwa tana rungume jaririnta da kyau kuma ta tabbatar kewayen nan mai launin duhu na kan nono (areola) ya shiga cikin bakin jariri a lokacin shayarwa, ba kan nonon (nipples) kawai ba. Idan baki iya ba, to, ki nemi ‘yan uwanki su koya miki. Hakan zai kare mace daga matsalolin tsagewar kan nono (nipples crack).

    4. Shayarwa a kai-a kai (breastfeeding on demand):

    Jarirai sukan sha nono a kai-a kai, don haka uwa ta tabbatar da cewa tana bai wa jaririnta nono a ƙalla bayan duk awa 2 zuwa 3. Idan yana buƙata ma kafin wannan lokacin, to, ta ba shi. Hakan zai kare ta daga matsalolinmu ciccikowar nono (breast engorgement).

    5. Isasshen ruwan nono (breast milk sufficiency):

    Ruwan nono yana taruwa ne gwargwadon yadda mace take ƙoƙarin shayarwa tare da cin wadatacce kuma ingantaccen abinci. Ma’ana, idan mace tana shayarwa akai-akai, to, ruwan nononta zai yi saurin taruwa. Idan kuma ba ta shayarwa akai-akai, to, za ta fuskanci ƙarancin ruwan nono.

    6. Matsalolin shayarwa (breastfeeding challenges):

    Yawancin mace takan fuskanci matsaloli a lokacin shayarwa, kamar, ciccikowar nono, tsagewar kan nono, ƙarancin ruwan nono, ciwon nono, da sauransu. Idan hakan ya faru, to, a je asibiti domin a yi abinda ya kamata.

    7. Matse ruwan nono (breast milk expression):

    Idan nonon mace yana samar da ruwan nono fiye da buƙatar jaririnta, to, za a iya fuskantar matsalar ciccikowar nono, wanda zai haifar da zazzaɓi. Domin kaucewa hakan, ana iya matsewa a cikin mazubi mai tsabta domin ta bai wa jariri a lokaci na gaba. Ga matan da suke zuwa wurin aiki a ofisoshi kuwa, suna barin jariransu a gida, to, shikenan sai a riƙa bai wa jariran ruwan nonon da suka matse. Ana yin matsewar ne da hannu (hand expression), ko da na’urar matsewa (breast pump), wanda ba duk mata ne suka sanshi ba.

    Daga ƙarshe ya kamata musan cewa shayarwa abu ce ta halitta (natural). Idan mace tana yinta bisa ƙa’ida, to, bai kamata ta ji zafi ba. Idan mace tana Shayarwa kuma tana jin zafi to yana nuna cewa akwai matsala, don haka sai a yi ƙoƙarin gane ta kuma a magance ta.
    Karanta Menene Ƙaiƙayi? (ITCHING)

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tarihin Alaramma Malam Salihu Ɗangalinja

    Tarihin Alaramma Malam Salihu Ɗangalinja

    An haifi Malam Salihu ɗan Dawuda a girin Galinja da ke Kanon Dabo a shekarar 1920 zamanin Sarkin Kano Usman. Mashahurin mahaddaci mai baiwar tilawa da kaifin basira.

    Malam Salihu Ɗangalinja ya yi tafiye-tafiyen neman karatu cikin ƙasar Gumel da Haɗeja; da garuruwa irin su Mainabindi da Kalali da Unguwar Jibrin.

    Bayan Malam Ɗan Galinja ya samu AIƙur’ani, sai kuma ya tsunduma cikin fannonin ilmin Fiƙhu da tajwidi. Ya karanta littafai irinsu Hidayatul Rahman wajen malaminsa Shehu Rabi’u Ɗantinki da Malam Husaini Gwauron Dutse. Saboda irin baiwarsa ta karatu an ce a lokacin ƙuruciyarsa zai yi wuya a lissafa manyan tsangayun da ya je ya sha fari ya tashi; Wannan ya sa sa’o’insa su ka sallama masa.

    Malam Salihu mutum ne mai yawan haƙuri da kawaici da kyautatawa ga almajiransa. Bayan girma ya kama shi sai ya kafa tsangayarsa da ke garin Ƙarfi a inda makaranta ke turuwa don sanin Alƙur’ani daga gare shi. Wadda hakan ya canza yanayin rayuwar mutanen Ƙarfi saboda maƙwabtakar da suka yi da ma’abota Alƙur’ani.

    Malam Salihu Ɗan Galinja ya kasance yana yi wa ‘ya’yansa da almajiransa wasiya da riƙo da Alƙur’ani da kaucewa kwaɗayin duniya.

    Malam Salihu ya rasu a shekarar 1997 ya bar ‘ya’ya da dama, kaɗan daga cikin mazan su ne:-

    • Halifansa Malam Kabir Ɗan Galinja
    • Malam Nafiu Ɗan Galinja
    • Malam Ɗahiru Ɗan Galinja, da ‘ya’ya mata guda tara.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Mahiru Sharif Bala danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Magungunan Gargajiya Na Wanzamai

    Magungunan Gargajiya Na Wanzamai

    Ko da yake masana da manazarta da ɗaliban al’adun Hausawa sun bayyana ma’anar magani da waɗanda ke bayar da shi a ƙasar Hausa, yana da matuƙar muhimmanci a sani, wanzamai suna daga cikin waɗanda ke bayar da shi ga waɗanda suke buƙata (Bunza, 1990:132-134).

    Bayar da magani a wurin wanzamai al’amari ne wanda suka gada daga wurin iyaye da kakanni, kuma sai wanda ya zauna wurin mahaifinsa ko wanda ya koya masa wannan sana’a ne yake sanin ire-iren itatuwan da ake harhaɗawa don yin magani. Akwai hanyoyi da dama waɗanda wanzamai suke bi don gane cututtuka da kuma bayar da maganin kowace irin cuta.

    Hanyoyin da Wanzamai Suke Gane Cututtuka

    Wanzamai suna bin hanyoyi da dama wajen gane irin cutar da ke damun mutum. Waɗannan hanyoyi sun haɗa da duba wurin da cuta take, wato idan aka duba wurin da ciwo yake za a iya fahimtar irin cutar, misali, belun-wuya da cututtukan cikin farji da sauransu.

    Wasu cututtukan kuma ana gane su ta hanyar taɓa wurin da cutar take, misali, ciwon ɓalli-ɓalli da ciwon saifa da sauransu. Haka kuma wanzamai suna gane irin cutar da ke damun mutum ta hanyar bayanin wanda yake da cutar ko wanda yake tare da shi kamar jarirai da yara ƙanana waɗanda ba su iya bayanin abin da ke damun su. Ire-iren waɗannan cututtuka sun haɗa da ciwon zuciya da ciwon sanyin jiki da sauransu.

    Ire-Iren Magungunan da Wanzamai Suke Bayarwa

    Wanzamai suna ba da magunguna iri daban-daban ga jarirai da yara ƙanana don maganin cututtuka irin su ciwon sanyin jiki da saifa da ciwon kai da ciwon ƙazamin goyo da ciwon damsai da ciwon tamalmala da ciwon cibiya. Haka kuma wanzamai na ba mata masu ciki magunguna don renon ciki da kuma waɗanda suka haihu don tanadin abin da aka haifa.

    Bayan waɗannan wanzamai suna ba maza da mata magungunan cututtuka iri daban-daban waɗanda suka haɗa da maganin ciwon zuciya da maganin ciwon haƙori da maganin ciwon kunne da maganin amosanin ƙashi da maganin amosanin ciki da maganin amodari da maganin cututtukan da ake ɗauka ta hanyar saduwa tsakanin maza da mata da maganin ƙarin ƙarfin azzakari da dai sauransu.

    Wannan babi an duba irin yadda aka gudanar da sana’ar wanzanci a jiya dangane da yadda ake yin aski da gyaran fuska da cire belun-wuya da kaciya da ƙaho da wasu ayyuka da ake yi a farjin mata da tsaga wadda ta haɗa da ta gado da ta kwalliya da ta magani da kuma magungunan gargajiya waɗanda wanzamai suke bayarwa.

    Don karanta Yadda Wanzamai Suke Tsaga danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Yadda Wanzamai Suke Tsaga

    Yadda Wanzamai Suke Tsaga

    Tsaga wata alama ce wadda Hausawa da kuma wasu ƙabilu na sassa daban-daban da suke cikin Nahiyar Afrika da wasu sassa na wannan duniya suke yi da aska a fuska ko a wani ɓangare na jiki, don a bambanta wata ƙabila da wata ko mutanen wata Daula da wata ko dangi da dangi ko zuri’a da zuri’a ko don riƙon al’ada ko don magance wata cuta ko kuma don yin kwalliya.

    A al’adar Hausawa tsaga ta kasu zuwa rabo uku kamar haka: Tsagar gado da tsagar magani da tsagar kwalliya. Kowace daga cikin waɗannan kashe-kashe na tsaga tana da dalilan da kan sa a yi ta, kuma kowane kaso ya sake kasuwa zuwa wasu rabe-raben.

    Tsagar Gado

    Tsagar gado ita ce wadda ake yi a fuska don nuna asalin mai ita ko sashin da ya fito. Ita tsagar gado tana bin gadon uba ne ba na uwa ba, watau ana yin tsagar gado ne don nuna asalin wajen uba ba na wajen uwa ba. Tsagar gado ta kasu zuwa kashi uku kamar haka: tsagar gado mai nuna asalin gari ko wurin zama misali, Katsinanci da Dauranci da Kabanci da Ƙwannanci da Gobirci da Zamfaranci da Arauci da sauransu.

    Akwai kuma tsagar gado mai nuna asalin ƙabilar da mutum ya fito misali, barbarci da buzanci da sauransu. Akwai kuma tsagar gado mai nuna ma’abota wata sana’ar gargajiya misali, mahauta da manoma da sauransu. Ana kuma kiran tsagar gado da sunan askar gado. A yanzu za a yi bayani cikakke kan ire-iren tsagar gado.

    Tsagar Gado Mai Nuna Asalin Gari ko Wurin Zama

    Irin wannan tsaga tana nuna asalin gari ko shiyyar da mai ita ya fito a ƙasar Hausa. A da can irin wannan tsaga tana nuna daga Daular da mai ita ya fito, watau ya fito daga ƙasar Katsina ko Daura ko Kabi ko Gobir ko Zamfara da sauransu. A wancan zamanin ta hanyar tsagar gado ne ake yaƙar abokan hamayya. Ana nufin ta hanyar tsagar gado ne idan ana yaƙi tsakanin Daular Katsina da ta Gobir, Katsinawa suke gane Gobirawa, su ma Gobirawa su gane Katsinawa.

    Haka kuma ta hanyar tsagar gado ne ake fahimtar masu irinta zuri’ar wane ne da yake zaune a wuri kaza. Akwai tsaga iri daban-daban a ƙasar Hausa waɗanda suke nuna mazauna wurare ko garuruwa waɗanda suka haɗa da Katsinanci a ƙasar Katsina da Maraɗi ta Jamhuriyyar Nijar, da Dauranci a ƙasar Daura ta Jihar Katsina, da Gobirci a ƙasar Gobir da Zamfaranci a ƙasar Zamfara da Kabanci a ƙasar Birnin Kabi da Arauci na Arawa mazauna Gundumar Dogon-Dutsi da kuma wasu ƙauyukan da suke cikin Gundumar Ƙwanni duk a cikin Jamhuriyyar Nijar da kuma Ƙwannanci a Gundumar Birnin Ƙwanni ta Jamhuriyyar Nijar. Yanzu za a bi ire-iren waɗannan tsaga da aka lissafa a sama domin yin cikakken bayani kan kowace da wurin da ake samun ta.

    Tsagar Katsinanci

    Tsagar Katsinanci tsagar gado ce wadda ake yi wa haɓen ƙasar Ƙatsina na asali ko maguzawan ƙasar Katsina, akan kira irin wannan tsaga da sunan bille ko maguzanci a ƙasar Katsina. Irin wannan tsaga gado biyu ce, gado na farko ana yin su ne a kumatu, gado na biyu bisa fuska. Akwai bambanci tsakanin yawan ‘ya’yan tsagar da ake yi wa saraki da talakawa.

    Ga talakawan ƙasar Katsina ana yin tsaga shida ga kuncin dama, tsaga bakwai a kuncin hagu. Ga ‘ya’yan sarautar haɓen Katsina ana yin tsaga bakwai a kuncin dama, shida a kumcin hagu. Abin nufi anan shi ne, ta hanyar yawan tsaga a kumatu ake bambance wannan saraki ne wannan talaka ne. A halin yanzu ana samun masu irin wannan tsaga a sassan arewaci da tsakiyar Jihar Katsina a ƙananan hukumomin Katsina da Kaita da Jibiya da Mashi da Mani da Dutsi da Ɓatagarawa da Rimi da Kurfi da Dutsin-ma da Safana da Batsari da Ɗan-musa da Charanchi da Ingawa da Kusada.

    Haka kuma ana samun masu irin wannan tsaga a masarautar Maraɗi ta Jamhuriyyar Nijar. Kamar yadda aka bayyana a baya masu irin wannan tsaga su ne haɓen asali na Daular Katsina, kuma su ne sarakunan haɓe na masarautar Katsina. A lokacin da Ummarun Dallaje ya kafa mulkin Fulani Dallazawa a Katsina, sai sarakunan haɓen suka yi ƙaura zuwa Maraɗi wadda da can ƙasar Katsina ce, suka kafa mulkinsu a wurin da sunan masarautar Katsina a Maraɗi.

    Wannan dalili ne ya sa tun daga wancan lokaci har zuwa yanzu ake kiran Sarkin Maraɗi da sunan Sarkin Katsinan Maraɗi. A wannan sabuwar masarauta sun ci gaba da yi wa ‘ya’yansu irin wannan tsaga ta Katsinanci har zuwa wannan lokaci da muke ciki. Bayan ƙasar Katsina da ƙasar Maraɗi ta Jamhuriyyar Nijar duk wurin da aka ga mutum da tsagar Katsinanci to ƙaura ya yi daga waɗannan wuraren zuwa wannan wuri.

     Tsagar Gado Mai Nuna Masu Yin Sana’o’in Gargajiya

    Irin wannan tsaga tana nuna masu irinta suna yin wata sana’a daga cikin sana’o’in gargajiya na Hausawa.Ire-iren wannan tsaga akwai billen hannun dama, wanda yake nuna mai irinta zuri’arsu masu yin sana’ar fawa ne. Akwai kuma tsagar lezumanci wadda take nuna mai irinta masu sana’ar noma ne.

    Tsagar Billen Hannun Dama na Mahauta

    Tsagar Bille a hannun dama tsagar gado ce wadda ake yi wa mahauta a ƙasar Hausa. Ana yin bille ƙarami a ɓangaren fuska na hannun dama gefen karan hanci. Dukkan mai irin wannan tsaga zuri’arsu masu yin sana’ar fawa ne. A yanzu akwai wasu mahauta da kan yi wa ‘ya’yansu tsagar bille a hannun hagu maimakon hannun dama. Tsagar bille a hannun hagu ba ta mahauta ba ce, masu irin wannan bille asalinsu Fulani ne Sulluɓawa waɗanda a yanzu su ne sarakunan Katsina.

    Daga nan ne sai wasu mahauta suka ara suka yafa, suka mayar da shi nasu bayan kuwa ba asalinsu ba ne. Wurin da aka yi bille ne, watau a dama ko a hagu yake bambanta wannan mahauci ne ko kuma Bafulatani Basulluɓe. Irin wannan tsaga ta billen hannun dama ta mahauta ana samun masu irin ta a duk sassan ƙasar Hausa.

    Tsagar Lezumanci Ta Manoma

    Tsagar Lezumanci tsagar gado ce wadda take nuna mai irinta asalinsu manoma ne waɗanda ba su da wata sana’a idan ba noma ba. Tsagar Lezumanci gado biyu ce kuma ta yi kama da tsagar Katsinanci, wurin da suka bambanta shi ne, tsagar Lezumanci ana yin su ne da yawa caɓa-caɓa ba kamar Katsinanci ba da ake yin nan shida nan bakwai. Masu tsagen Lezumanci ana kiransu da sunan Lezumawa.

    Bincike da aka gudanar ya bayyana su Lezumawa asalinsu Zamfarawa ne, sai wani Bazamfare mai suna Jatau ya sayi ɗan uwansa Bazamfare ya sanya shi bauta, sai ya riƙa kiran shi da sunan ‘ZUMU’ watau ɗan’uwa. Sannu-sannu sai aka riƙa kiran sa ‘Lezumu’ watau aka yi ƙarin ɗafa-goshin ‘Le’. Da Jatau ya ga hankalin Lezumu da ƙoƙarinsa sai ya yarda da shi ya kuma ba shi amanar gidansa, sai ya kasance duk harkokin gidan Jatau Lezumu ne yake tafiyar da su.

    Yau da kullum Lezumu yana ta yin bauta a ƙarƙashin ɗan uwansa Jatau har ya gane dukkan asirin Jatau na tsafi. Wannan ne ya ba shi damar yin amfani da wannan asiri ya rinjayi ubangidansa Jatau, ya yi masa juyin mulki, ya amshe gidan sai mai doki ya koma kuturi.

    Daga nan ne aka sami zuri’arsa wadda aka riƙa kira da sunan “Lezumawa” daga sunan Lezumu da mai gidansa Jatau ya riƙa kiran sa. Saboda ƙoƙarin Lezumu da iya tsafin da ya taimaka masa har ya amshe gidan maigidansa ɗan’uwansa Jatau wanda ya yi wa bauta, ya sa ake yi wa zuri’arsa kirari kamar haka:

    “Lezumawan Jatau aska ba ki amana”

    “Lezumawan Jatau taba kashe mai ba ki ruwa”.

    (Hira da ASKS a ranar 3-6-96).

    Ma’anar kirari na farko shi ne, duk irin yadda ka saba da aska idan ka ba ta amana, to wata rana za ta ci amanar mutum domin idan ka yanka ta a jikinka za ta kama, kamar yadda duk da amanar da Jatau ya ba Lezumu, amma da ya gane asirinsa sai ya tumɓuke shi ya amshe gidan.

    Kirari na biyu kuma yana nufin duk wanda ya ba taba ruwa ta sha ta girma idan ya sha ta ba daidai ba, to tana shaƙe shi ya ƙware, ƙarshe ma ta kashe shi kamar yadda Lezumu ya yi wa ɗan’uwansa Jatau wanda ya riƙe shi har ya girma amma ya amshe masa gida.

    Daga lokacin da Lezumu ya amshe gida, sai ya canza tsagarsu daga tsagen Zamfaranci ya zuwa tsagen Lezumanci wanda ya ƙirƙiro wa zuri’arsa, ya kuma mayar da ita tsagarsu ta gado. Irin wannan tsaga ta Lezumanci da Katsinanci a Jihar Katsina ana kiran su da “Hatimin-Noma”. Wannan kuwa ya faru ne saboda shaharar masu irin wannan tsaga a sana’ar noma da kuma ƙwarewarsu wajen yin tsafe-tsafen da suka shafi sana’ar noma.

    A yanzu Lezumawa shahararrun manoma ne kuma matsafa a duk wurin da suke. Ana samun zuri’ar Lezumawa a ƙananan hukumomin Safana da Ɗan-musa da Dutsin-ma da Matazu da Musawa da Batsari da Kankiya da kuma wasu sassan na Jihar Zamfara. A saboda wannan tarihi nasu ya sa a yanzu idan wani biki ya same su sukan gayyaci dukkan danginsu daga ko’ina domin a taru wajen yin bikin (Hira da Sarkin Noma Babban- Kada, Shugaban zuri’ar Lezumawa na Jihar Katsina. A Lezumawar Babban-Kada Safana, a Ranar 11-6-97).

    Tsagar Magani

    Tsagar magani ana yin ta ne domin a fitar da jini daga jikin mutum saboda a sami sauƙi ko a warke daga wani ciwo wanda yake cikin jiki. Ana kuma yin ta don a fitar da mataccen jinin da yake cikin jikin mutum. Wasu Hausawa suna da ra’ayin mataccen jini a cikin jikin mutum kan yi sanadiyyar kamuwa da cututtuka iri daban-daban. Fitar da shi ko rage shi kan sa a sami sauƙi ko a warke daga ciwon. Akwai tsagar magani iri daban-daban da ake yi wa Hausawa, waɗanda suka haɗa da ƙaho da tsagar ɓalli-ɓalli da tsagar fitar- ruwa da tsagar maganin jiri da tsagar maganin kanne da tsagar ciki ga jarirai da tsagar murfi da sauransu.

    Ƙaho

    Ƙaho tsagar magani ce wadda wanzamai kan yi wa mai buƙata. Ana samun ƙaho na sa ko na saniya a gyara shi. Ana kafa ƙahon a bayan mabuƙacin ko a wurin da lalura take. Daga nan sai wanzamin ya yi ta tsotsa ƙahon da yake kafe a wurin da ake buƙatar yin sa. Zai yi ta yin haka har sai ƙahon ya kame sosai sannan ya liƙe ‘yar-ƙofar ƙahon da jijiyar da yake taunawa a cikin bakinsa.

    Yin haka ne zai sa ƙahon ya liƙe wurin da aka kafa shi. Bayan kamar minti goma zuwa sha biyar sai a cire ƙahon saboda a wannan lokacin mataccen jinin ko cutar da ake son fitarwa ta taru daidai wurin da aka kafa ƙahon. Daga nan sai a sanya askar tsaga a tsaga wurin da aka fitar da ƙahon, ana yin tsage daga tara zuwa goma sha biyar. Daga nan sai a sake mayar da ƙahon wurin da aka cire shi.

    Bayan kamar minti goma sha biyar sai a sake cire shi, a wannan lokaci mataccen jini ko cutar ta taru cikin ƙahon, sai a zuba a ramin da aka tona kafin a fara yin ƙahon. Haka za a sake yi kamar sau biyu ko uku, yin haka ya danganta da ƙarfin wanda za a yi wa ƙahon. Daga nan sai a zuba ƙasa a rufe ramin da aka zuba jinin. Shi ke nan an gama ƙaho sai wanda aka yi wa ya saka suturarsa idan ga baya aka yi masa.

    Ana yin ƙaho daga ɗaya zuwa huɗu, amma kafin a kafa wa mutum ƙaho fiye da ɗaya dole sai wanzamin ya tabbatar wannan mutum yana iya ɗaukar fiye da ɗaya. Idan jinin mutum ba shi da yawa, to idan aka yi masa ƙaho fiye da ɗaya ana iya ƙwararsa, maimakon abin ya zama na magani sai ya zama cuta. Wasu wanzamai kan shafa magani a wurin da suka yi ƙaho, wasu kuwa ba sa shafa wani magani matuƙar mataccen jini ya fita buƙata ta biya.

    Yana da muhimmamnci a nan a bayyana ire-iren cututtukan da kan sa a yi ƙaho.Yawan mutuwar jiki da kasala abubuwa ne waɗanda Hausawa suka ɗauka mataccen jini ne yake kawo su. Haka kuma idan mutum ya buge a wani ɓangare na jikinsa har jini ya taru a wurin kuma bai fita ba, ko ya yi targaɗe a wani wuri kuma wurin ya yi kumburi. Bayan an gyara sai a yi masa ƙaho a wurin don a fitar da jinin da ya taru.

    Haka kuma idan murfin ƙahon zuciyar mutum ya faɗa dole sai an yi amfani da ƙaho a jawo shi.Dukkan waɗannan matsalolin rashin lafiya da aka yi bayaninsu, wasu Hausawa sun ɗauka idan aka yi ƙaho za a sami sauƙi ko a warke daga ciwon.

    Tsagar Kwalliya

    Tsagar kwalliya ko jarfa ko shasshawa tana nufin ire-iren tsagen da mata kan sa wanzamai su yi masu a fuska ko a wani ɓangare na jiki domin ado ko kwalliya.Ita tsagar kwalliya an fi yi wa mata ita, domin da wuya a ga namiji ya ba da fuskarsa ko wani ɓangare na jikinsa ga wanzami don a yi masa tsagar kwalliya.

    Ire-iren waɗannan tsage sun haɗa da kalangai da takutuha da kwaluluwa da matakin-soro da ‘yar ƙirji da alluna da me-ka-ce maigida da ‘yarbaka da garɗin-gero da kwanciya-da-masoyi. Akwai kuma tsagen kwalliya waɗanda zamani ya kawo, ire-irensu sun haɗa da alamomin siyasa kamar fartanya mai nuna alamar jam’iyyar N.P.C. da tauraruwa mai nuna alamar jam’iyyar NEPU. Wasu kuma sukan sanya a tsaga masu hoton agogo ko sunan masoyi ga hannuwansu.

    A binciken da aka gudanar a sassan ƙasar Hausa an fahimci mafi yawancin ire-iren waɗannan tsage na kwalliya ana amfani da alamomi iri-ɗaya. Kuma ana kiransu da suna ɗaya, ɗan bambancin da akan samu bai taka kara ya karya ba.

    Lokacin Yin Tsagar Kwalliya

    A al’adance an fi yin tsagar kwalliya da kaka domin kuwa a wannan lokaci an kawar da amfanin gona, kuma sanyi ya fara sauka yadda idan an yi tsagar za ta yi saurin warkewa. Wannan kuma ya faru ne saboda Hausawa suna da ra’ayin a wannan lokaci jiki ya fi saurin tohuwa. A irin wannan lokaci ne wanzamai masu yin tsagar kwalliya ko jarfa suke barin gidajensu domin tafiya yawon jarfa, watau yin tsagar kwalliya a garuruwa da ƙauyukan ƙasar Hausa.

    Wani lokaci kuma da ake yin tsagar kwalliya shi ne watan takutuha. Idan wanzaman jarfa za su sauka a wani gari mafi yawanci sun fi sauka a ranar kasuwar garin don kowa ya san an yi baƙin wanzamai ‘yan jarfa. Kowane daga cikin ‘yan tawagar kan sami gidan da yake da budurwa ya saukar mata. Dukkan yawan kwanakin da za su yi a garin, a gidan da suka sauka ake ba su masauki da abinci har sai sun tashi daga wannan gari.

    A duk wurin da suka je suna tafiya da makaɗa da maroƙa waɗanda suke rera waƙoƙin yabo da na kushe ga ‘yan matan da suka yi masu kyakkyawar sauka da waɗanda ba su yi masu ba. Makaɗan wanzamai ana kiran su da ‘yan kurya ko makaɗan kurya.

    Ire-Iren Tsagar Kwalliya

    A lokacin da za a yi wa budurwa ko yarinya tsagar kwalliya, sai abokiyarta ta ɗauko turmi don wadda za a yi wa tsagar ta zauna ta jingina da wannan turmi. Daga nan sai wannan abiya ta zauna kusa da ita ta dafa kafaɗunta. Ana yin haka ne domin wadda za a yi wa tsagar kar ta nuna kasala. Ita abiyar wadda za a yi wa tsagar ce take gaya wa wanzamin irin tsagar da za a yi wa wannan abiya.

    Wasu kuma samarinsu ne kan zaɓa masu irin tsagar da za a yi masu. Daga nan ne sai wanzamin ya fara tsaga, ana yin tsagar ana kiɗa da waƙa, maroƙa kuma suna shelar a kawo kari. A wannan lokaci ne samari za su yi ta ƙoƙarin gwada bajinta ta hanyar bayar da kari.Su ma ‘yan’uwa da abokan arziki ba a barin su a baya, sai su ma su yi ta ba da nasu karin. Abubuwan da akan bayar na kari sun haɗa da kuɗi da sutura da dabbobi.

    Dukkan abubuwan da aka samu na kari wanzaman ne da makaɗansu da yaransu da maroƙansu suke rarrabawa. Bayan abubuwan da aka samu na kari sai kuma iyayen yarinyar da aka yi wa tsagar su ba da tasu sallamar ga wanzaman.Idan aka sauka gidansu yarinyar da take da dangi da yawa wadda a lokacin da aka fara yi mata tsaga an sami kari sosai, akan ɗauki kwanaki da yawa a wannan gida don ci gaba da yi mata tsaga, kamar misalin kwana biyu zuwa bakwai.

    A mafi yawancin lokaci a saboda kiɗa da waƙa da ake yi a lokacin jarfa waɗanda a cikin waƙar akwai yabo da kuma bayar da ƙarfin gwiwa ga budurwar da ake yi wa tsagar, yakan sa ‘yan mata nuna juriya da daurewa. Wasu kuma gudun kar a yi masu zambo kan sa su daurewa a lokacin da ake yi masu tsaga. Wannan kan sa har a gama yi masu tsagar ba sa nuna wata alama ta kasala ko raggwanci ko su yi kuka. Haka za a yi ta yi daga wannan gida zuwa wancan gidan inda ‘yan mata suke a garin da suka sauka don yi masu tsaga.

    Bayan sun gama a wannan gari sai kuma su ƙara gaba zuwa wani garin.Wanzaman jarfa kan ɗauki lokaci mai tsawo kafin su sake dawowa a garin da suka yi tsaga. A wani lokaci sukan ɗauki misalin shekara biyu zuwa uku ba su dawo a wannan gari ba, sai kuwa idan an bukaci su dawo.Wannan wata alama ce ta nuna kawaici da godiya bisa ga abubuwan da aka yi masu.

    Kalangai

    Kalangai tsaga ce wadda ake yi a fuska daidai saitin kunnuwa. Irin wannan tsaga ƙarama ce marar tsawo ƙwarai, tsawonta bai wuce daidai kunnuwa ba, wasu ana yi masu kalangu ɗaya-ɗaya wasu kuwa ana yi masu kalangai biyu-biyu a kowane ɓangare na fuska, wannan ya danganta da sha’awar wadda za a yi wa tsagar.

    Abin kula a nan shi ne, wasu samari kansa wanzami ya yi masu tsagar kalangu ɗaya-ɗaya a kowace fuska domin sha’awa, ko kuma su ma ‘yan matansu kan bukace su da a yi masu kalangu ɗaya-ɗaya a kowace fuska.

    Akwai kuma waɗanda ake yi wa tsagar kalangu ɗaya-ɗaya a fuska a matsayin tsagar gado. Misali, Fulani Dallazawa zuriyar Malam Ummarun Dallaje (wanda ya yi jihadin jaddada addinin Musulunci a ƙasar Katsina kuma Sarkin Katsina na farko daga zuri’ar Fulani) ana yi wa mazansu da matansu tsagar kalangu ɗaya-ɗaya a fuska a matsayin tsagar gado.

    Tsagar ‘Yar Baka

    Tsagar ‘yar baka tsaga ce ta kwalliya wadda ake yi wa ‘yan mata a kumatu ta haɗe da wutsiyar baki. Wannan tsaga gado ɗaya ce kuma ana yin ta caɓa-caɓa a kumatu. Wasu kan kira irin wannan tsaga da sunan cika baki. Wannan kuwa ya faru ne saboda yadda ake yin ta caɓa-caɓa ga kumatu. An fi yi wa ‘yan mata masu kaurin kumatu irin wannan tsaga don a ƙara rage kaurin kumatun.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

     

     

     

  • Ire-Iren Ayyukan Wanzamai

    Ire-Iren Ayyukan Wanzamai

    Cire Belun-Wuya

    Belun-wuya tsokar nama ce wadda take tsirowa a cikin bakin mutum liƙe da ƙarshen dasashin sama kusa da maƙogaro.Wannan tsokar nama Hausawa sun ɗauka idan ba a cire ta ba, to idan mutum ya girma ciwo na iya kama ta. Idan kuwa ta kamu da ciwo zai sa mutum ya kasa cin abinci ko shan ruwa, ya kuma yawaita yin amai ya kuma rame. Idan kuma wani abu ya taɓa wurin, mutumin zai ji tsananin zafi. Wannan ne ya sa da an haifi jariri sai a kira wanzami domin ya cire ta (Hira da Alhaji Aliyu Sarkin Aski, a Safana, 16-6-96).

    Wasu daga cikin Hausawa ba a cire wa ‘ya’yansu belin wuya, a maimakon cirewa suna amfani da maganin da zai hana su kamuwa da wani ciwo.

    Ire-Iren Ayyukan da Wanzamai Kan yi a Farjin Mata

    Wanzaman gargajiya suna yin wasu ayyuka a cikin farjin mata domin a yi maganin wasu lalurori da sukan iya matsa masu bayan sun yi aure. Wasu daga cikin waɗannan ayyuka ana yin su tun mata suna jarirai, wasu kuma sai sun fara girma ake gane suna fama da lalurar sai a yi masu aikin.

    Akwai kuma waɗanda sai sun yi aure ne za a iya fahimtar suna da lalurin, misali wanzamai suna fahimtar yarinya mai fama da lalurar angurya tun lokacin da aka haife ta sai a cire. Amma lalurar sadadda da mahindi da sarƙa da turu duk sai in yarinya ta girma ne za a iya fahimtar su.

    Domin aiwatar da wannan aikin cikin sauƙi da nasara ba tare da samun sha’awa ba wajen yin waɗannan aikace – aikace wanzaman da suke yin aikin suna shan magani, ko amfani da layu da gurayen da za su kawar masu da sha’awa a lokacin da suke yin waɗannan ayyuka. Misali,a lokacin da za a yi aikin wanzamin da zai yi aikin da wanda zai taimaka masa kan shafa farar ƙasa a dukkan gefen idanunsu, kuma su sanya ta cikin baki suna taunawa suna haɗe ruwan har sai sun gama aikin sannan sai su wanke fuskokinsu da bakunansu.

    Wannan yana taimakawa ƙwarai wajen kawar da sha’awa ga shi wanzamin da mai taimaka masa. Mutane suna yaɗa jita-jita wai idan wanzami ya zo yin ire-iren waɗannan ayyuka idan azzakarinsa ya tashi, to idan ya kwanta ba zai sake tashi ba. To wannan ba gaskiya ba ne, ana amfani da maganin sha’awa domin kar ɓarna ta faru a lokacin da ake yin wannan aikin, saboda wasu mutane ba sa iya riƙe sha’awa su yi haƙuri idan ta kama su.

    Cire Angurya

     Angurya wani tantanin nama ne wanda ake haihuwar mata da shi a cikin farjinsu, wasu kuma sai sun girma yake fito masu. Idan ba a cire shi ba yana iya hana mace saduwa da namiji idan ta girma. Wanzamai suna gane mata masu fama da angurya a lokacin da suka zo cire beli ko hakin-wuya. A nan ne idan budurwa ce sai su binciki farjinta su ga idan tana da angurya sai su cire shi.

    Wasu wanzamai suna amfani da yatsa domin cire angurya. Suna sa babban yatsansu ne su tallabo shi daga tushensa sai su sa ‘yar tsaga su cire shi. Wasu kuma suna amfani da allura da zare domin cire shi. Ana tsiro shi da allurar ne da zaren sai a ɗaga sama a sanya askar aski a yanke shi. Wasu wanzaman kuma suna amfani da hantsaki domin cire shi, ana sanya hantsakin a kamo tushensa sai a sa askar aski a yanke shi.

    Wasu kuma suna amfani da akaifar babban yatsansu su kama shi daga tushensa sai su sa askar aski su yanke shi. Bayan an cire shi sai wanzamin ya tauna ‘ya’yan bagaruwa ya furza a wurin, daga nan kuma sai ya barbaɗa maganin da zai tsayar da jini da wanda zai hana shi sake tuƙowa.

    Gyara Sadadda

    Mace mai lalurar sadadda ana haihuwar ta da wannan lalura, domin ana samun ƙofar farjinta ‘yar ƙarama ce wadda fitsari ne kawai yake iya fita ta wurin, amma can daga cikin farjinta lafiya lau yake. Matsalar a wurin ƙofar farjin take. Wasu kuma ana haihuwarsu lafiya lau, amma saboda rashin tsabta da rashin kula daga wurin iyayensu ko masu riƙonsu sai ƙofar ta sake toshewa.

    Matan da suke da irin wannan matsala idan za su yi fitsari sai ya riƙa fita kamar na namiji. Idan iyayensu suka fahimci haka sai su sanar da wanzamin gidansu domin ya binciki yarinyar don ya gyara ta. Ana yin irin wannan gyara ne ta yadda aka fahimci matsalar.

    Ga waɗanda aka haifa da matsalar, sai an sanya askar aski a ƙara buɗa ƙofar farjin, daga nan sai a barbaɗa maganin da zai tsayar da jini da wanda zai sa wurin ya yi saurin warkewa. Ga kuma waɗanda suka sami matsalar sakamakon rashin kula ko rashin tsabta, ana amfani da hannu ne a sake buɗa ƙofar, daga nan sai wanzamin ya gargaɗi iyayen yarinyar ko masu kula da ita da su riƙa tsabtace farjinta ta hanyar wanke mata a duk lokacin da ta yi fitsari ko ta tashi daga barci.

    Gyara Sarƙa

    Sarƙa lalura ce da ake samu a farjin mace a inda za a tarar leɓatun farjinta sun sarƙe yadda ba za ta iya ganin ƙofar farjinta ba. Irin wannan matsala ba kasafai ake samun ta ba, akan daɗe ba a sami mace mai fama da irin wannan matsala ba. Idan an sami mace da lalurar sarƙa aka kai wa wanzami domin ya gyara yana amfani da hikimar da ya gada kuma ya ƙware a kanta domin gyara ta.

    Ba dukkan wanzamai ne suke iya gyara mace mai matsalar sarƙa ba, ko a cikin wanzaman gado sai waɗanda suka koya wajen tsofaffin wanzamai suke iya gyara mace mai matsalar sarƙa. Wanzamai suna gyara mace mai matsalar sarƙa ta amfani da hannuwansu su raba leɓatun farjin su kawo magani su shafa a wurin yadda kowane zai tsaya a wurin da yake ba tare da ya sake sarƙewa da ɗan uwansa ba. Wanzamin zai yi ta yin haka har sai wurin ya zauna daidai ƙofar farjin ta fito sosai.

    Cire Mahindi

    Mahindi shi ma wata lalura ce wadda ake samu ga farjin mata wadda ta yi kama da angurya amma suna da bambanci. Shi mahindi tsokar nama ce take tsirowa ta toshe ƙofar farjin mace ta hana ta saduwa da namiji. Wajen cire shi ana amfani da askar aski ne ko askar tsaga (‘yartsaga), a sanya akaifa a ɗago shi sama, sai a sanya askar a yanke shi.

    Gyara Turu

    Wata matsalar wadda wanzamai suke gyarawa a farjin mace, ita ce ta turu. Shi turu ana samun matsalar shi ga mata ƙalilan. Matan da suke da wannan ciwo idan suna saduwa da namiji azzakarin ba ya wucewa duka a cikin farjin saboda turun da yake ciki ya tare ƙofar.

    Mata masu irin wannan lalura suna iya ɗaukar ciki, sai dai idan sun zo haihuwa sukan fuskanci matsalar da kan kai ga sai an yi masu yankan gishiri, wanda wani al’amari ne mai haɗari. Ita ma wannan matsalar ba dukkan wanzamai ne suka iya gyara ta ba, sai wanzamai da suka koya ga wanzamai na da can.

    Wanzamai suna gyara turu ta hanyar sanya yatsunsu biyu manuni da na kusa da shi a cikin farjn mace mai wannan matsala, su kama shi da yatsun su buɗe shi yadda ba zai tokare azzakarin namiji a lokacin da ake saduwa da matar ba.

    Kaciya

    Kaciya tana nufin yanke ko cire fatar da ta rufe kan azzakarin mutum. A ƙasar Hausa wanzamai ne suke yin kaciya, kuma mafi yawanci an fi yin kaciya a lokacin sanyi. Dalilin da ya sa aka fi yin kaciya a lokacin sanyi shi ne, a wannan lokaci jikin mutum ya fi saurin tohuwa, don a wannan lokaci ko rauni mutum ya yi zai yi saurin warkewa.

    A lokacin sanyi kuma an kai ga amfanin gona, abinci ya wadata, yaran da aka yi wa kaciya za su sami wadataccen abincin da za su ci, jikinsu ya tohu da sauri su yi saurin warkewa, kuma a wannan lokaci aiki ya yi sauƙi za a sami wanda zai tsaya ya riƙa kula da su.

    A al’adar Hausawa yawanci sai yaro ya kai shekara bakwai abin da ya yi sama da haka nan za a yi masa kaciya. Hausawa ba su faye yi wa yaro kaciya yana da shekara takwas da haihuwa ba. Saboda an camfa wai idan aka yi wa yaro kaciya yana da shekara takwas, to wani bala’i na iya faɗa masa. Wannan ne ya sa idan ba a yi wa yaro kaciya yana da shekara bakwai ba, to ba za a yi masa ba, sai ya kai shekara tara ko goma.

    A da idan za a yi kaciya ana tara yaran unguwa ɗaya a gida ɗaya domin yi masu kaciya, a sanya mutum ɗaya ya tsare su yana kula da su don kar su fama kaciyar. Amma a yanzu wasu suna yin haka, wasu kuwa da sun tashi yi wa ‘ya’yansu kaciya, sai su kira wanzami ya yi kaciyar ba tare da sun gaya wa kowa ba.

    A ranar da za a yi wa yaran kaciya wanzamin da zai yi kaciyar tare da yaransa masu taimaka masa kan yi sammako zuwa gidan da za a yi kaciyar. A al’adar Hausawa an fi son a yi sammako domin a wannan lokaci yaran da za a yi wa kaciyar ba su farka daga barci ba.

    An fi son a yi kaciyar da sun farka sun wanke idanunsu, watau ba su kai ga motsa jikinsu ya tashi ba. Wani dalili da yake sa a yi kaciya tun da sassafe shi ne, a wannan lokaci rana ba ta fito ba bare ta yi zafin da zai sa jinin yaron da za a yi wa kaciyar ya tashi, wanda zai sanya idan an zo yi masa kaciyar ya zubar da jini da yawa.

    Idan za a yi wa yara kaciya ba a gaya masu ranar da za a yi don kar su sami fargaba ko su gudu su ɓuya. Haka kuma a lokacin da za a yi masu kaciya an fi son wani daga cikin ‘yan’uwansu ya riƙe su don kar su yi tsammanin cuta masu za a yi. Ana kuma ba su wani abu mai daɗi kamar alewa da makamantanta wadda za ta ƙara kwantar masu da hankali su ƙara yarda da ba cutar su za a yi ba. A lokacin da za a yi kaciyar ana rufe wa yaron da za a yi wa kaciyar idanu don kar ya ga jini na zuba daga jikinsa hankalinsa ya tashi.

    A lokacin da za a yi wa yaro kaciya idan ya nuna kasala abokan wasansa da kakanninsa kan riƙa yi masa dariya, a wani lokaci sukan tambaye shi, idan ba ya son a yi masa kaciya ya ba da wani abu a ƙyale shi. A irin haka wasu kan ce sun ba dukkan dabbobin da ke gidansu da gidan duka, wasu ma kan ce sun ba da wani daga cikin ‘yan gidansu ko wani daga cikin mahaifansu.

    Idan wanzami ya yi kaciya, bayan kuɗin kari waɗanda ‘yan uwa da abokan arzikin iyayen yaron da aka yi wa kaciya suka bayar, su ma iyayen yaron suna ba wanzamin tasu sallamar. Irin wannan sallama ta haɗa da kuɗi daidai arzikin iyayen yaron, bayan kuɗi ana kuma ba da damen dawa da zakara domin wanzamin ya sami hatsin da za a riƙa yi ma abinci ba tare da ya sha wahalar neman abinci ba.

    Shi kuwa zakara da ake bayarwa ana ba da shi wai ladar jinin da ya fitar a jikin ɗan kaciyar. A da can idan aka yi wa yaro kaciya ya zama dole a ba wanzamin damen dawa da zakara, amma a halin yanzu saboda juyawar zamani wannan al’adar ta fara ƙaura, wurare kaɗan ne ake bayarwa. A maimakon su ana ba da kuɗi gwargwadon arzikin iyayen yaron da aka yi wa kaciyar.

    Bayan waɗannan kuma a da can kayan da suke jikin yaron da za a yi wa kaciya idan an tuɓe su, bayan wanzamin ya gama kaciyar, sai ya ɗauke su ya kai wa ‘ya’yansa.

    Kaciyar sa-Wandonka

    Wannan kaciya ƙarin hikima ce da wanzamai suka samu a gargajiyance, wadda ake yi wa yaro kaciya da an gama ya sanya wandonsa ya yi tafiyarsa ya ci gaba da yin harkokinsa na yau da kullum. A irin wannan kaciya ba a tsare yaro domin yin jinya kamar yadda ake yi kafin zuwan wannan hikima. A taƙaice a iya cewa kaciyar sa-wandonka ci gaba ne wasu wanzamai suka samu a gargajiyance.

    Ita wannan kaciya babu wani bambanci wajen yin ta da irin kaciyar da wanzamai suke yi, wurin da bambancin yake shi ne wajen sanya magani. A wannan kaciya ba a tauna bagaruwa a furza ruwan, a maimakonta ana shafa ruwan magani mai mai, sai kuma a naɗe kaciyar da wani farin ƙyalle kamar yadda ake yi wa kaciyar asibiti.  Wannan farin ƙyalle da ake naɗawa ba zai fita ba sai a lokacin da kaciyar ta warke.

    Karanta Yadda Askin Sarauta Yake

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Askin Sarauta Yake

    Yadda Askin Sarauta Yake

    Askin sarauta na nufin askin da ake yi wa sarakuna ko wasu masu riƙe da sarauta a ƙasar Hausa. Ga al’ada ba kowane wanzami ne yake yi wa sarki aski ba, kowane sarki yana da wanzamin da yake yi masa aski, kuma wannan wanzami shi ne sarkin aska ko magajin askar wannan sarki.

    Kowane sarki akwai ranar da yakan keɓe wadda ake yi masa aski. Mafi yawancin sarakuna an fi yi masu aski a ranar Litinin ko Talata. Dalilin da ya sa ake ware waɗannan ranaku shi ne, shi wanzamin ya san da wannan rana da kuma lokacin da zai riƙa zuwa, to a ranar ba zai yi tafiya zuwa wani wuri ba domin kar ya saɓa. Wasu kuma suna yin aski a waɗannan ranaku ne saboda camfe-camfe.

    Kuma kowane sarki yana da askar da ake yi masa aski wadda ba a yi wa kowa aski da ita sai shi. Sai kuwa idan bayan rasuwarsa a ci gaba da yi wa wanda ya gaje shi aski da ita. Bugu da ƙari, ba a kowane wuri ake yi wa sarki aski ba, sarkin askarsa ko magajin askarsa yake tarar da shi a gidansa ya kai shi bargarsa domin ya yi masa aski. Dalilin da ya sa ake bin waɗannan sharuɗɗa na yi wa sarakuna aski shi ne, domin kariya daga maƙiya kar su harbe su, ko su yi masu wasu surkulle ta hanyar aski da zai yi dalilin su rabu da sarautunsu ko wani sharri ya same su, ko rashin lafiya, ko ma dai su mutu.

    Game da ladar da sarakuna suke biyan wanzamansu bayan sun gama masu aski, ba a lokacin da suka yi askin suke biyansu ba. Su sarakuna a lokacin da suka bukata sukan aika wa sarakunan askarsu da kyauta mai yawa. Ire-iren kyaututtukan da sarakuna kan ba sarakunan askarsu sun haɗa da manyan riguna da kuɗi da abinci (gero da dawa da makamantansu) da dawaki. Haka idan wani biki na aure ko na haihuwa ya sami wanzamin sarkinsa kan taimaka masa sosai.

    Aski da Gyaran Fuska

    Aski na nufin amfani da askar aski mai kaifi domin a aske sumar da ta tsiro a kan mutumin da ya bukaci a yi masa askin.A ƙasar Hausa masu yin sana’ar aski ana kiransu da sunan wanzamai. Gyaran fuska na nufin amfani da irin askar da ake yin aski domin aske gashin da ya tsiro a fuskar mutumin da ya bukaci a yi masa gyaran fuska.A al’adar Hausawa maza ne kawai ake yi wa aski da gyaran fuska.

    Ga kuma wanda ya ajiye gemu sai a gyara gemun ya fito sosai. Gyaran fuska yana da matuƙar muhimmaci ga rayuwar Hausawa, domin kuwa ana kiran wanzamai yin gyara saboda masu gashi da yawa ko ƙasumba su ji daɗi ga fuskarsu. Ga wasu suna nuna, idan gashi ya tsiro masu a fuska yana yi masu ƙaiƙayi sosai har sai in an aske shi sannan za su ji daɗi ga fuskarsu.

    Akwai aski iri daban-daban da ake yi wa Hausawa, kuma kowane daga cikinsu akwai dalilan da kansa a yi shi. Ire-iren waɗannan aski sun haɗa da askin ƙwaryar molo da gyaran fuska da askin sarauta da askin jarirai na suna da askin tuba da zanko da tukkaye da bawale da askin muzantawa da kuma tsayar da gemu.

    Askin Ƙwaryar Molo

    Askin ƙwaryar molo aski ne wanda ake yi wa Hausawa da wasu al’ummomi. A irin wannan aski ana aske dukkan suma ne tas har idan rana ta haskaka kan wanda aka yi wa askin sai mutum ya ga kan yana ƙyalli. Idan za a yi askin ƙwaryar molo da fari ana fara jiƙa sumar da ruwa sai ta jiƙa sosai daga nan sai a bi da sabulu domin ta ƙara laushi.

    Yana da muhimmanci a fahimci cewa, duk sumar da ba ta jiƙa da ruwa sosai ba, idan aka yi saurin shafa sabulu, ba za ta yi laushi kamar wadda ta jiƙa sosai ba. A irin wannan gaggawar ce za a tarar idan ana yi wa mutum aski zai ce da zafi. Idan ta jiƙa sosai aka shafa sabulu ta fi sauri da daɗin aski ga wanda yake yin askin da kuma wanda ake yi wa.

    Bayan suma ta jiƙa, sai a fara aski daga ɓangaren fuska kusa da kunnen dama a nufi wajen ƙeya. Ana bi ana askewa tare da la’akari da bin kwanciyar sumar, wato ana bin yadda sumar ta kwanta ba tare da tarbar kan gashin ba. Idan an aske dukkan gashin da yake baya, sai a juyo tsakiyar kai a nufo wajen goshi domin shi ma a aske shi.

    Bayan duk an aske gashin da yake bisa kai, sai a sake shafa ruwa domin a maimaita askin tare da bin hanyoyin da aka bi lokacin aka fara yin askin.Haka kuma idan babban mutum ne mai gashi a fuska, sai kuma a yi masa gyaran fuska.

    A’al’adar Hausawa askin ƙwaryar molo yana da muhimmanci sosai, domin kuwa al’ada ta mayar da shi dole, har ma Hausawa a da can sun ɗauka dukkan wanda ya bar suma da yawa bisa kansa tamkar mahaukaci ne, mai yin koyi da ɗabi’a marar kyau. Wannan ne ya sa iyaye kan tilastawa ‘ya’yansu yin askin ƙwaryar molo, wasu ‘ya’yan ba cikin suna buƙata ba. Maroƙan Hausawa na gargajiya suna yi wa wanzamai kirari kamar haka:

    “In ba domin ku ba,

    Da mahaukata sun yi yawa”

    Ma’ana, in ba don wanzamai suna yi wa mutane aski ba, da yawan mutane masu gashi duguzun kamar mahaukata sun yi yawa cikin duniya.

    Askin Jarirai na Suna

    Askin jarirai na suna shi ne askin farko da ake yi wa jarirai bayan an haife su, ana yi wa jarirai maza da mata aski. A al’adar Hausawa ana yin wannan aski a ranar da aka raɗa wa jaririn suna. A da can kafin zuwan addini Musulunci a ƙasar Hausa ana yin wannan aski ne a lokacin da dangi na wajen uba da dangi na wajen uwa suka taru domin raɗa wa jariri suna.

    Misali, a al’adar Kaina-Fara Arnan Birci da suke zaune a Ƙauyen Goda ta Birci a Ƙaramar Hukumar Kurfi ta Jihar Katsina, sai jariri ya kwana arba’in da haihuwa sannan za a yi masa aski, kuma a wannan rana ne za a raɗa masa suna. A halin yanzu ana yi wa jarirai askin suna a rana ta bakwai da haihuwa. A wasu ƙauyuka ana yin askin jariri da maraice lokacin da dangi mata na wajen wadda ta haihu da dangin wanda ya haihu duk sun haɗu a wannan lokaci ne wanzami zai yi askin. Dalilin haka kuwa shi ne, don kowa ya ba da tasa gudummuwar wajen yin askin

    Dangane da ladar da ake biyan wanzami idan ya yi askin jariri na suna za mu ga a gargajiyance a ƙasar Hausa kafin samuwar kuɗin zamani ana biya ne da hatsi da dabbobi da kuma tsuntsayen gida irin su kaji. A nan dangin masu haihuwa na maza da na mata duk suna ba da nasu ga wanzamin.

    Bayan an gama aski sai a fitar da kushekara ko karfata daga ragon suna a ba wanzamin. Daga nan kuma sai a ba wanzamin ƙwaryar aski. Dukkan waɗannan kayayyaki da ake ba wanzami, Hausawa sun ɗauka ba su biya shi ladan aikin da ya yi ba, domin in ba shi ba, babu mai iya yin ayyukansa. Wannan dalilin ne ya sa ake haɗa wa wanzami dukkan waɗannan kayayyakin abinci, saboda kar rashin abinci ya sa shi tafiya neman abinci, haka ka iya jawo idan an haihu aka zo neman sa ba za a same shi ba, don ya tafi neman abinci.

    Tukkaye

    Tukkaye ana yin su ne bisa kan yara maza ɗaya-ɗaya. Abin nufi a nan shi ne, su tukkaye ana barin gashi a lokacin da ake aski kaɗan-kaɗan a wasu wurare bisa kan yaron da ake yi wa aski waɗanda a mafi yawancin lokaci ba a aske su sai lokacin da za a yi wa yaro kaciya. Wasu tukkayen kuwa manya ne, waɗanda masu wasan fage suke sanyawa a yi masu domin kwalliya a bisa kawunansu.

    Ire-iren masu wasan fagen da suke yin tukkaye sun haɗa da ‘yan kokowa da ‘yan dambe da ‘yan kwarako da ‘yan dadale da gardawa da sauransu. Su tukkaye da ma can asalinsu na Hausawa ne, sauran baƙi da suka shiga cikin Hausawa su ma sun zo da irin nasu tukkaye, misali, Buzaye da a yanzu sun koma Hausawa, ana yi wa ‘ya’yansu tukkuwa ɗaya a bisa ƙeya, har sai ta kai ga matakin da gashin tukkuwar ya yi tsawo sai a yi masa kitso.

    Shi ma ba za a aske shi ba sai lokacin da za a yi wa yaron kaciya. Wasu kuma daga cikin Hausawa kan yi wa ‘ya’yansu tukkuwa ɗaya bisa tsakiyar kai, wasu kuma a kusa da goshi. Ita wannan tukkuwa ta kusa da goshi an fi yi wa almajirai ita, don har ana kiran wannan tukkuwa “leƙa tukunya”. Dukkan waɗannan tukkaye da aka yi bayani a sama ana aske wa yara su ne lokacin da za a yi wa yaron kaciya.

    Su kuwa waɗannan da suke yin tukkaye domin wasan fage suna yin tukkayen ne a lokacin da za su fara wasan fagen, ba kuma za su aske su ba sai lokacin da suka manyanta suka tuba da yin wasan fage, a lokacin ne za su yi askin tuba.

    Ana yin wasu tukkayen domin a muzanta mutum, watau idan aka kama wani mutum ya yi sata ko wani mummunan laifi wanda ya saɓa wa al’ada, idan ana son muzanta shi a idon jama’a, sai a sanya wanzami ya yi masa tukkaye da yawa a bisa kansa, a shafa masa baƙin tukunya a fuska, sai a sami makaɗi a zagaya da shi cikin kasuwa da wasu wuraren da mutane suke zama, ana yi masa kiɗa yana rawa tare da faɗar irin laifin da ya aikata wanda ya sa aka yi ma sa irin wannan aski.

    Ana kuma yin irin waɗannan tukkaye a lokacin wasan kalankuwa, idan wani ɗan kallo ya yi laifi aka kama shi.Idan aka yi masa tara ba shi da kuɗin biya, sai a kira sarkin askar wasan ya yi masa tukkaye da yawa bisa kai, a kuma shafa masa baƙin-tukunya a fuska. Daga nan sai a sanya shi ya goya wata budurwa a riƙa zagayawa da shi a cikin filin da ake yin wasan kalankuwa. Ana yi masa kiɗa yana rawa da wannan budurwa a goye, har sai ya zagaye ko’ina, sannan ya zo gaban Sarkin Samari ya ajiye budurwar ya yi godiya shi ke nan an sallame shi.

    Haka kuma ana yin tukkaye a lokacin da ake yi wa jariri askin suna, idan iyayen jariri da abokan arziki ba su biya kuɗin ana aski ba, ko kuma ba su ba wa kakanni kuɗin ana aski ba, sai su kakannin su biya kuɗin askin, daga nan sai su riƙa yi wa iyayen jaririn gorin cewa sun sayi jaririn, ya zama ɗansu ke nan, idan ana son a fanshe shi dole a nunka yawan kuɗin da kakanni suka ba da na ana aski a mayar masu.

    Tsayar Da Gemu

    A al’adar Hausawa, mutum ba ya ajiye gemu, sai ya kai wasu shekaru na haihuwa, ko kuma sai ya kai lokacin da al’ada ta ƙayyade mutum ya ajiye gemu. Yawanci lokacin yakan zo idan matar ɗansa ta ko ‘yarsa ta haihu, watau ya ɗauki jika ke nan, ya isa ya ajiye gemu.

    Idan kuwa ba shi da ɗa ko ‘ya wadda ta isa aure har ta haihu, to sai a kwatanta da haihuwar ɗan abokin haihuwarsa ko ‘yarsa. Ba za a sa gemu ba sai a lokacin wani biki na aure ko na suna a gidan. Tun kafin zuwan ranar ake sanar da ‘yan ‘uwa da abokan arziki da wanzamin gidan wanda shi ne zai yi wa wanda za a sanya wa gemu aski da tsayar da shi.

    Karanta Sana’ar Wanzanci A Jiya

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Sana’ar Wanzanci Take A Zamanin Baya

    Yadda Sana’ar Wanzanci Take A Zamanin Baya

    Wannan babi ya duba sana’ar wanzanci a jiya wato yadda aka gudanar da wannan sana’a kafin al’ummar Hausawa su sami shigar al’adun wasu baƙi cikin al’adunsu. A nan an yi bayani a kan matsayin sana’ar wanzanci a al’adar Hausawa da kayan aikin wanzanci da kuma yadda ake gudanar da ayyukan wanzanci waɗanda suka haɗa da aski da gyaran fuska da cire belun-wuya da na mata da kaciya da tsaga da bayar da magungunan gargajiya.

    Matsayin Sana’ar Wanzanci a Al’adar Hausawa

    Kowane irin al’amari wanda ya danganci yadda ɗan Adam yake tafiyar da rayuwarsa ta yau da kullum yana da irin nasa matsayi a idanun masu yin sa da waɗanda ake yi wa. Wannan ne ya sa aka ga ya dace a duba matsayin sana’ar wanzanci a al’adance da irin yadda al’ummar Hausawa suke kallon wannan sana’a da masu yin ta.

    Sana’ar wanzanci tana da babban matsayi a al’adar Hausawa, wannan kuwa ya faru ne saboda ire-iren muhimman ayyukan da wanzamai suke aiwatarwa. Haka kuma al’ummar Hausawa suna girmama wanzamai, wannan ne ya sa Alhaji Sale Gambara a cikin bakandamiyarsa yake cewa, a duk gari akwai manya uku waɗanda su ne kamar haka; shugaban da yake jagorancin mutanen garin, sai limamin garin daga nan sai wanzamin garin.

    Haka kuma a fannonin adabin Hausawa akwai wurare da dama waɗanda aka bayyana muhimmancin wannan sana’a. Misali, a cikin littafin da Alhaji Nuhu Bamalli ya rubuta mai sunan “Mungo Park Mabuɗin Kwara”, wanda aka yi bayani a kan tafiye-tafiyen Mungo Park a sassan Afrika ta Yamma a shafi na 42-43 an yi bayyanin inda wannan matafiyi ya bayyana ya zama wanzami.

    Haka su ma makaɗan ƙasar Hausa suna bayyana muhimmancin wanzami a idon Hausawa. A iya ganin haka a waƙar da Ɗan’anace ya yi wa Shago inda yake cewa:

    “Ɗan Abdu Gazaguru,

    Ai na faɗa maka goga,

    Wanga kashi da kay yi ba dawa ne ba,

    Kar ka kashe Na’ila wanzami na,

    Ai shi ka yo muna gyara,…”

    Kuma kasancewar wanzaman gargajiya masana tsubbace-tsubbace da sihirce-sihirce ne masu ban mamaki da al’ajabi da ban tsoro ya sa al’ummar Hausawa suke ɗaukar su kamar wasu dodanni ko wasu mutane da ake tsoro. Wannan ne ma ya sa ba a yi wa wanzamai gardama ko gatse ko shisshigi dangane da yadda suke aiwatar da ayyukansu, don tsoron kar su yi wa mutum wani abu da zai cuce shi.

    Haka kuma al’ummar Hausawa sun ɗauki wanzamai a matsayin wasu mutane masu bayar da taimako idan wata lalura ta rashin lafiya ko bukatar maganin gargajiya ta taso. A nan ma makaɗan Hausawa sun bayyana irin rawar da wanzamai suke takawa wajen yin ire-iren waɗannan tsatsube-tsatsube.

    Misali, a waƙar da Alhaji Mamman Shata Katsina ya yi wa Ciroman Aski na Jalingo ya bayyana irin yadda wanzamai suke harbin ‘yan uwansu a lokacin da suka zo yin aski sai su riƙa yin kyarmar hannu wadda take yin dalilin a riƙa yankar wanda ake yi wa aski. Ga irin yadda ya bayyana haka cikin wannan waƙa:

    “Ga wani ya zo aski,

    Sun harbai hannu nai na karkarwa,

    Da ya zo gun aski,

    Sai na ga jini na ta zubowa…”

    Haka kuma karin maganar Hausawa ya ƙara fito da matsayin wanzami a idon Hausawa kamar haka:

    Kowa ya ci ladar kuturu, dole ya yi masa aski.

    Kushekarar jaki sai wanzamin kura.

    Wanzami ba ya son jarfa.

    Waɗannan dalilai ne suka sa al’ummar Hausawa suke matuƙar kyautata wa wanzamai da dukkan abin da ya dace na kyautatawa, kuma kowane mutum ya yarda da dukkan ayyukan wanzanci, ana yi masa da dukkan iyalinsa. Idan bukatar aikin wanzami ta kama matuƙar bai zo lokacin da ake buƘatar ya zo ba, ana tarar da shi har gidansa don a gani ko lafiya? Wannan dalili ya sa yin ayyukan wanzanci a wurin Hausawa a jiya wani al’amari ne wanda ya zama dole a yi shi.

    Kayan Aikin Yin Wanzanci

    Wanzamai suna amfani da kayayyaki iri daban-daban domin yin ayyukan wanzanci. Ire-iren waɗannan kayayyaki sun haɗa da askar aski da kwanon aski da kalaba da ƙoshiya da ‘yaR tsaga da hantsaki da tankolo da zabira da ƙaho da kura ta cire haƙori da sauransu.

    Askar Aski

    Askar da ake amfani ita wajen yin aski ƙarama ce madaidaiciya kuma ba ta da tsawo sosai. Akwai bambanci tsakanin wadda ake askin jarirai da wadda ake yi wa manya aski.Ta askin jarirai ba ta kai girman wadda ake yi wa manya aski ba. Da kuma askar aski ake amfani wajen yin kaciya, ana amfani ne da irin wadda ake yi wa manya aski wato mai kaifi da nauyi wajen yin kaciya. Kafin zuwan wannan zamani ana amfani da askar baƙin ƙarfe wajen yin aski da kaciya, irin wannan aska ita wanzamai suka gaji amfani da ita, kuma maƙeran Hausawa ne suke samar ta ita ga wanzamai.

    Wani muhimmin abu da ya kamata a sani a nan shi ne, askar baƙin ƙarfe ta fi kowace irin aska riƙe kaifi. Idan wanzami ya wasa askar baƙin ƙarfe sai ya yi wa mutane da yawa aski ko gyaran fuska ba tare da ya sake wasa ta ba. Akwai maƙera na daban waƙanda suke ƙerawa da kuɗar asaken aski.

    Dutsin Washin Asaken Aski

    Dutsin washin asaken aski dutsi ne ƙarami mai sulɓi da ake amfani da shi domin yin washin asaken aski idan kaifinsu ya dakushe, wato idan kaifinsu ya ragu. Idan kuwa kaifinsu ya dakushe duka, to sai a kai ga maƙeri domin a sake koɗa su. Ana amfani da dutse ta hanyar goga askar bisa dutsen sannu a hankali har sai an tabbata askar ta wasu.

    Hanyar da ake gane aska ta wasu ita ce, sai a ɗan fera fatar hannu, idan askar ta fere fatar sosai aska ta wasu ke nan. Kafin zuwan wannan zamani duwatsu iri biyu da ake amfani da su wajen wasa asaken aski. Na farko shi ne na gatarin aradu, watan dutsen da yake faɗowa idan an yi tsawa lokacin ruwan damina.

    Hanyar da ake bi domin samun dutsen gatarin aradu ita ce, da zarar an yi tsawa, aka kuma yi dacen ganin wurin da ta faɗi, sai a yi gaggawa a je a zuba madara ko nonon shanu a wurin da tsawar ta faɗi. Idan an tona sai a tarar da dutsin da ya faɗo, don kuwa madara ko nonon da aka zuba zai hana shi yin ƙasa da nisa. Dutsi iri na biyu da ake amfani da shi domin washin asaken aski shi ne na ƙanƙara mai sulɓi da ake samu a kogi ko wurin da yake da duwatsu. 

    Fatar Washin Asaken Aski

    Fatar wasa asaken aski fatar dabbobi ce ake samu daga wajen dukawa wadda aka jeme. Ana amfani da mai faɗin misali inci ɗaya da rabi, tsawonta kuma misalin inci goma sha biyar zuwa ashirin. An fi amfani da mai kauri irin ta manyan dabbobi domin kuwa ta fi inganci da ƙara wa aska kaifi.

    Amfanin fatar washin asaken aski shi ne, idan aka wasa askar da dutsi kaifinta ba zai kai sosai ba, sai an wasa da fata. A nan ne sai a shafa ruwa ga fatar a bi da askar ana shafawa bisa fatar sannu a hankali. Wannan ne zai daidaita kaifin askar yadda idan an zo yin aski askar za ta tuje gashin da sauƙi. Mafi yanwancin wanzamai suna ɗaura fatar wasa asaken askin wurin zabira daga gefe.

    Kwanon Aski

    Kwanon aski ana amfani da shi ne domin zuba ruwan da za a riƙa amfani da shi wajen yin aski da gyaran fuska da kaciya da tsaga. A da can kafin zuwan Turawa wanzamai suna amfani da ƙoƙo domin zuba ruwan aski. Wannan ne ma ya sa ake kiran wanzaman da suke yin aski da gyaran fuska da sunan ‘wanzaman ƙoƙo’. A halin yanzu ana amfani da kofin roba ko na ƙarfe domin zuba ruwan aski

    Kalaba

    Kalaba ƙarfe ne ƙarami wanda tsawonsa misalin inci shida zuwa bakwai, kuma ba shi da kauri sosai. Maƙera ne suke ƙera kalaba, ba kuma dukkan maƙeri ne yake ƙirar kalaba ba, akwai maƙera na daban masu ƙera ta. Ana yin ta ne da kaifi a gefe ɗaya na kanta sai a lanƘwasa kan ya zamo kaifi ciki. Ana yi wa gindinta kauri domin a ji daɗin riƙewa idan za a yi aiki da ita. Amfanin kalaba wajen ayyukan wanzanci shi ne a riƙa cire belin- wuya da ita.

    Ƙoshiya

    Ƙoshiya itace ne ƙarami ake sassaƙawa da ɗan faɗi ga kai da kuma kauri ga gindi. Tsawon ƙoshiya misali inci shida ne zuwa bakwai, faɗin kanta kuma bai kai inci ɗaya ba. A taƙaice tsawon ƙoshiya ɗaya yake da na kalaba. Ana amfani da ƙoshiya wajen wanzanci domin taushe harshen jariri a lokacin da za a cire belun-wuya. Ita ƙoshiya masassaƙa ne suke samar da ita ga wanzamai, akwai kuma wasu wanzamai da suke iya sassaƙa ƙoshiya.

    ‘Yar Tsaga

    Yartsaga aska ce ƙarama da maƙera suke ƙerawa, tsawonta ya kai misalin inci huɗu zuwa biyar, kanta kuma ana yin sa da faɗi da tsini da kaifi. Ana amfani da ‘yartsaga wajen ayyukan wanzanci domin yin wasu ayyukan da wanzamai suke yi a farjin mata kamar cire angurya da yanke linzami da cire haƙoran shuwa.Ana kuma amfani da ita domin yin tsagar gado da ta magani da kuma ta kwalliya.

     Hantsaki

    Hantsaki ƙarfe ne da maƙera suke ƙerawa da baki a gindi da kuma tsini a kai. Ba shi da kauri sosai, kuma tsawon sa misalin inci huɗu ne. Ana amfani da hantsaki wajen wanzanci domin cire angurya a farjin mata.

    Ƙaho

    Wanzamai suna amfani da ƙahon sa ne domin yin ƙaho. Ana amfani da ƙaho madaidaici wanda ba babba ba ƙwarai, ba kuma ƙarami ba, ana yanka misalin tsawon inci biyar ko shida. Ana yi wa wajen tsininsa ‘yar ƙaramar ƙofa. Ana amfani da ƙaho ne domin yin ƙaho. Mahauta ne suke samar da ƙaho ga wanzamai, su ne suke fitar da shi daga kan sa da aka yanka sai su sayar wa wanzaman da suke yin ƙaho.

     Jijiya

    Wanzamai suna amfani da jijiyar agarar ƙafar akuya ko tunkiya domin a riƙa liƙe ƙofar tsinin ƙahon da aka kafa wa mutum domin ya liƙe a wurin da aka kafa shi a jikin mutum. Wanzamin zai sanya wannan jijiya a cikin bakinsa yana taunawa sai ya liƙa ta a wurin ƙofar, da an liƙa shi ke nan sai ƙahon ya liƙe a wurin da aka kafa shi, ba zai fita ba sai in an cire wannan jijiya. Ita ma jijiya mahauta ne suke samar da ita ga wanzamai.

    Kura ta Cire Haƙori

    Ita kura ƙarfe ne ake samu domin cire haƙori, yanayinta ya yi kama da abin da kafintoci suke cire ƙusa a wannan zamani, amma ita kura ba ta kai girman abin cire ƙusa ba. Wanzamai suna amfani da kura ne domin cire haƙori. Wanzami yana amfani da kura ne ya kama haƙori mai ciwo ko mai girgiɗa sai ya cire shi daga wurin da yake.

    Tankolo

    Tankolo ‘yar jaka ce wadda dukawa suke ɗinkawa da fatar akuya ko tinkiya domin wanzamai su riƙa sanya askar aski ɗaya ko kuma babba wadda za a sanya asaken aski masu yawa.

    Zabira

    Zabira jaka ce babba mai aljihuna da yawa misali uku ko huɗu. Ana yi mata maratayi domin a riƙa ratayawa. Ita ma dukawa ne suke ɗinka ta da fatar akuya ko tinkiya domin yi wa wanzamai jakar da za su riƙa sanya dukkan kayan aikin wanzanci waɗanda aka yi bayaninsu a baya.

    Don karanta Matsayin Hausawa A Yau danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu