Tag: yadda ake

  • Menene Ƙaiƙayi? (ITCHING)

    Menene Ƙaiƙayi? (ITCHING)

    Kaiyayi shi ne jin waiwayi (creeping sensation), ko tsikari (tingling), ko rashin jin daɗi (irritation) a dukkan jiki ko kuma wani ɓangare na jiki. A likitance ana kiran ƙaiƙayi “pruritus”. Ƙaiƙayi yana faruwa ne idan wani baƙon abu ya taɓa fatar jiki, ko kuma ya shiga wata halitta (organ) da take cikin jiki. Idan haka ya faru, to, sai sashin da abin ya shafa ya aike da saƙo zuwa ga ƙwaƙwalwa cewa akwai buƙatar ta bayar da umurni domin a ɗauki matakin kawar da baƙon.

    RABE-RABEN ƘAIƘAYI (CLASSIFICATION OF ITCH)

    Ƙaiƙayi ya rabu zuwa manyan gidaje huɗu bisa la’akari da abubuwan da da suke haddasa shi, kamar haka:

    1. Ƙaiƙayin da rashe-rashen lafiyar laka suke haddasawa (neurogenic itch). Sun ƙunshi:

    a. Cututtukan ƙoda na tsawon lokaci (chronic renal failure) kamar su polycystic kidney disease (taruwar ruwa a cikin ƙoda), multicystic dysplastic kidney (kasa yin fitsari yadda ya kamata ga yara saboda toshewar hanyar fitar fitsarin daga ƙoda), renal artery stenosis (ciwon jijiyoyin da suke kai jini zuwa ga ƙoda), renal tubular acidosis (ciwon da yake sanya ƙoda ta kasa tace sinadaran acids daga cikin jini da kasa tura su cikin fitsari), solitary functioning kidney (kasancewar mutum da ƙoda guda ɗaya mai aikin tace fitsari), simple kidney cyst (ciwon kumburin ƙoda), da sauransu.

    b. Cututtuka jini ko kuma halittun da suke da alhakin samar da jini (hematologic diseases) kamar su sickle cell (sikila), anaemia (ƙarancin jini), HIV/AIDS (ƙanjamau), leukaemia (cutar daji ta jini), chemotherapy (jinyar cutar daji), transfusion (ƙarin jini), bone marrow disorder (cutar ɓargo), da sauransu.

    c. Cututtukan hanta (liver diseases) kamar su hepatitis A B C D & E, cirrhosis (ciwon lalacewar hanta), allagille syndrome (ciwon rashin iya fitar da sinadarin matsarmama daga cikin hanta), autoimmune hepatitis (ciwon da yake sanya ƙwayoyin halittar garkuwar jiki su koma suna kai farmaki ga hanta), da sauransu.

    d. Cututtuka masu haddasa kaluluwa (lympho-proliferative disorders) kamar su lymphoblastic leukemia, chronic lymphocytic leukemia, lymphoma, monoclonal gammopathies, da sauransu.

    2. Ƙaiƙayin da ƙwaƙwalwa take riya cewa ana jinsa (psychogenic itch). Wannan ƙaiƙayin yana faruwa ne ba domin wani abu ko wata rashin lafiya ta shafi wurin da ake jinsa ba. A a, riyawar ƙwaƙwalwa ce kawai. Ana alaƙanta samuwar wannan yanayin da damuwa (depression), ko tsoro (anxiety), ko shaye-shayen miyagun ƙwayoyi (substance abuse), ko ruɗewa (psychosis), ko rikicewar ƙwaƙwalwa (mania), ko ‘yar-ƙaramar hauka (somatoform disorders), da sauransu.

    3. Ƙaiƙayi mai tsanani wanda yake da alaka da laka (neuropathic itch). Bambancin wannan ƙaiƙayin da neurogenic itch wanda na faɗa tun farko shi ne neuropathic itch ya fi tsanani domin yana sanya mutum ya ji kamar ana sukarsa da allura ne.

    4. Ƙaiƙayin jikin fata (pruritoceptive). Yana faruwa ne sakamakon wani abu ko kuma wata rashin lafiya da ya shafi jikin fata, kuma shi aka fi sani domin likitocin fata sukan iya gane sanadinsa cikin hanzari ta hanyar duba fata a ga abinda ya same ta na ƙuraje, kumburi, ko rauni, ko cizon ƙwaro, ko duk wani abinda ya taɓa ta.

    YADDA ƘAIƘAYI YAKE FARUWA (ANATOMY OF ITCH)

    Kasancewar ƙaiƙayin fata shi ne ya fi shahara, to, bayaninsa zai fi sauƙin ganewa. Ƙaiƙayi yakan fara ne sakamakon abinda ya taɓa fata na kakkaɓin ƙura (speck of dust), ko cizon ƙwaro (insect bite), ko ƙurzunu-ƙurzunun tufafi (cloth fibres), ko gurbataccen ruwa (contaminated water), ko ruwan sinadarai (chemical compounds). Idan ɗaya daga cikin waɗannan ya taɓa fatar jiki, to akwai jerin-gwanon halittu guda shida masu amsar saƙon taɓawar su aika da shi zuwa ga ƙwaƙwalwa, ana kiransu “receptors”, kamar haka:

    1. Hair follicles (ramin gashi)

    2. Meissner corpuscles (‘yan-sako na ƙasan fata)

    3. Pacinian corpuscles (‘yan-saƙo na cikin tsokar jiki)

    4. Merkel complexes (‘yan-saƙo na ƙarshen jijiya masu tantance zafi da sanyin idan ya taɓa fata)

    5. Ruffini corpuscles (‘yan-sako na ƙasan ramin gashi masu iya gane duk motsin da ya taɓa fata)

    6. C-fiber LTM – low threshold mechanoreceptors (jijiyoyi masu aikawa da saƙo zuwa ga ƙwaƙwalwa a kan saƙonnin da aka tattaro na abinda ya taɓa fata)

    Da zarar ƙwaƙwalwa ta amshi saƙon ta hanyar receptors, to, za ta fahinci cewa akwai wani baƙon abu da yake ƙoƙarin shiga cikin jiki ta hanyyar fata, don haka ana buƙatar agajin gaggawa wajen kawar da shi. Sai ƙwaƙwalwa umurci hannu da ya sosa wurin domin kawar da baƙon. Hakan yana faruwa ne saboda babban aikin fata shi ne bayar da kariya ga tsoka, da jijiyoyi, da sauran halittun jiki daga shigar ƙwayoyin cuta.

    To idan aka sosa wurin da yake ƙaiƙayin sai ƙwaƙwalwa ta zubo da wani sinadarin kashe ƙaiƙayi ko zafi mai suna “serotonin”. Wannan sinadarin zai gangara inda ƙaiƙayin yake, kuma ya kashe shi, daga nan sai mutum ya ji daɗi kuma ya daina jin ƙaiƙayin. Rashin sosa wurin da yake ƙaiƙayin zai sanya ya cigaba, kuma ya haddasa rashin natsuwa da rashin jin daɗi.

    Amma idan mutum ya sosa wurin da yake ƙaiƙayi fiye da kima, to, hakan zai sanya wurin ya sami rauni ko ya kuje. Ya kamata mu fahimci cewa ƙaiƙayi (itch) da zafi (pain) duk abu ɗaya ne. Abinda ya bamabanta su kawai shi ne tsanani. Ma’ana, ƙaiƙayi zafi ne amma maras tsanani.

    Idan kuma ƙaiƙayin ya faru ne ba domin wani abu ya taɓa fata ba, to, susa ba za ta sanya a ji sauƙi ko daɗi ba. Ma’ana idan dalilin ƙaiƙayin ya kasance rashin lafiya ne, ko laulayin amfani da magani, ko riyawar ƙwaƙwalwa, to, susa ba za ta yi warkar dashi ba, dole sai anyi amfani da maganin matsalar da ta kawo rashin lafiyar.

    SAURAN ABUBUWAN DA SUKE HADDASA ƘAIƘAYI

    Waɗannan sun haɗa da:

    1. Bushewar fata (dryness of skin) sakamakon rashin shafa mai bayan wanka. Ana magance wannan ta hanyar daina amfani da sabulu mai ƙarfi, da kuma shafa mai bayan fitowa daga wanka.

    2. Cututtukan fata (skin diseases) kamar yadda bayani ya gabanta, irinsu ƙarzuwa (eczema), karambau (chickenpox), ƙyanda (measles), da sauransu. Ana magance wannan ta hanyar magance waɗannan cututtukan.

    3. Laulayin magunguna (side effects of drugs) kamar chloroquine, amitriptyline, citalopram, fluoxetine, paroxetine, sertraline, carbamazepine, da sauransu. Ana magance wannan ta hanyar tutuntuɓ ar likita domin ya bayarda maganin da ya dace.

    Danna nan don karanta Lalurar Mele (Vitiligo)

    Edita@rumasau-kallamu

  • Matsayin Hausawa A Yau

    Matsayin Hausawa A Yau

    Wannan duniya da muke ciki tana ƙunshe da al’ummomi daban-daban masu magana da harsuna da adabi da al’adu mabambanta. An ƙiyasta a yanzu akwai al’ummomi masu magana da harsuna daban-daban kimanin dubu shida da ɗari shida da sittin (6660) a wannan duniya tamu, kuma kowane daga cikin su na cin gashin-kansa. Misali, akwai Larabci da Turancin Ingilishi da na Faransanci da na Jamusanci da Sinanci da Indiyanci da dai sauransu.

    Kowane daga cikin waɗannan harsuna suna da masu yin magana da shi, kuma kowane yana da sigogin yaɗuwarsa. Daga cikin su za a tarar wani harshen masu yin magana da shi ‘yan ɗaruruwa ne a wani tsukin wuri, wani kuma za a tarar mutane ne dubbai suke yin amfani da shi, wani kuma miliyoyi ne waɗanda suka barbazu a wurare na nahiyoyin da suke cikin wannan duniya (Yahaya, 1991:3).

    Idan muka dawo nan gida Afrika akwai al’ummomi daban-daban waɗanda suke magana da harsuna kimanin 1850 wanda harshen Hausa na daga cikinsu. Yana daga cikin harsunan Afrika irinsu Swahili da Mande da Wolof da Ashanti da Yoruba da Bambara da sauransu. Daga waɗannan harsuna 1850 da suke Afrika an tantance an gano akwai kimanin harsuna 394 waɗanda ake yin amfani da su a sassa daban-daban da suke cikin Nijeriya.

    Duk da kasancewar waɗannan harsuna suna da dangantaka da wasunsu kowane daga cikinsu yana zaman kansa a matsayin harshe. Daga cikin harsunan da ake amfani da su a Nijeriya baya ga harshen Hausa akwai Yarbanci da Ibo da Fulatanci da Barbarci da Efik da Nufanci da Ibibio da Tiv da Angas da Edo da Bade da Igala da Idoma da Igbirra da Mandara da Karekare da Kanakuru da sauransu. A halin yanzu ana amfani da waɗannan harsuna a tsakanin al’ummomin da suke magana da su don yin hulɗoɗin rayuwa na yau da kullum (Yahaya, 1991:3-4).

    Hausawa suna daga cikin manyan al’ummomin da suke a wannan duniya a wannan zamani, kuma harshen Hausa wanda Hausawa suke magana da shi a matsayin harshen uwa na daga cikin manyan harsunan wannan duniya. Idan aka ɗebe harshen Larabci, masu magana da harshen Hausa a matsayin harshen uwa sun fi kowace al’umma yawa a duk faɗin Nahiyar Afrika, harshen Swahili ne kaɗai yake yi masa cin dudduge.

    Haka kuma harshen Hausa ne harshen da kowa yake yin magana da shi a mafi yawancin sassan arewacin Nijeriya ciki har da waɗanda ba Hausawa ba (Schuh, 1982:1). A Jamhuriyar Nijar mafi yawancin mutanen wannan ƙasa na magana da harshen Hausa (Hira da AHSA, a garin Agadez, a ranar 8/5/2005).Wannan ya bayyana mana ke nan, masu magana da harshen Hausawa sun fi kowace al’umma yawa a duk faɗin Afrika.

    Idan muka dawo kan batun da muke son magana a kansa watau matsayin Hausawa a yau, za mu ga kamar yadda aka yi bayanai a baya, kasancewar al’ummar Hausawa sun fi kowace al’umma yawa a duk faɗin Afrika, ya taimaka ƙwarai wajen yaɗuwa da haɓakar harshe da adabi da al’adun Hausawa da kuma mamaye na maƙwabtan ƙasar Hausa. Kamar yadda wani ɗan ƙabilar Babur ta jihar Borno ya bayyana min cewa: “Hausawa al’umma ce wadda take mamaye dukkan wata al’umma da ke kusa da ita” (Hira da AYB, a ranar 24/9/2004).

    Wani Badakkare daga Zuru ya bayyana min cewa: “Al’ummar Hausawa da harshensu da al’adunsu da adabinsu suna ƙara haɓaka a kullum, don kuwa ba wani wuri da mutum zai shiga a cikin Nijeriya da kuma ƙasashen waje da ba a san Hausawa ba”(Hira da IIPZ, a garin Zuru, a ranar 18/9/2005).

    Ga kuma ra’ayin wani ɗan ƙabilar Ibo mutumin jihar Anambra kan matsayin Hausawa a yau: ”Al’umma ce mai harshe wanda ake magana da shi a duk faɗin Nijeriya ta Arewa da maƙwabtanta ciki har da ma waɗanda ba Hausawa ba, kuma Hausawa mutane ne masu saurin karɓar baƙi, kuma masu son zaman lafiya”(Hira da DIJ, a Birnin Kabi, a ranar 16/9/2005).

    Haka kuma wani ɗan ƙabilar Ibo daga jihar Abia ya bayyana min cewa: “Hausawa al’umma ce mai yawan gaske, kuma suna samun bunƙasa a duk harkokinsu na rayuwar yau da kullum”(Hira da MAO, a Birnin Kabi, a ranar 16/10/2004).

    Wani Banufe bayyana min ya yi cewa: “Al’ummar Hausawa mutane ne da suka yi fice a dukkan al’amuran duniya, wannan ne ya sa suke da manyan mutanen da duniya ta san da zamansu a wannan zamani”(Hira da MNM, a garin Bida, a ranar 23/9/2004).

    A ra’ayin wani ɗan ƙabilar Ekoi ta jihar Cross Riɓer bayyana min ya yi cewa: “Al’ummar Hausawa mutane ne masu gaskiya da riƙon amana da kuma karɓar baƙi cikin mutunci. Kuma mutane waɗanda suke bin dokokin addininsu sau da ƙafa. Haka kuma harshensu ya yaɗu a kowane lungu da saƙo da yake cikin Nijeriya da maƙwabta (Hira da EEO, a garin Gusau, a ranar 10/9/2005).

    Wata Bayarabiya kuma bayyana min ra’ayinta ta yi kan matsayin Hausawa a yau kamar haka: “Al’ummar Hausawa mutanen kirki ne wanda a yanzu yana da matuƙar muhimmanci ga dukkan ‘yan Nijeriya su koyi harshen Hausa don samun sauƙin tafiyar da harkokin rayuwarsu ta yau da kullum”(Hira da MGAA, a garin Zariya, a ranar 30/9/2004).

    Bisa la’akari da waɗannan ra’ayoyi da waɗanda ba Hausawa ba suka bayar kan matsayin Hausawa a yau, na tabbata za a amince da ni al’ummar Hausawa suna da babban matsayi a wannan zamani a idanun mafi yawancin mutanen da suke cikin Nijeriya da ma waɗanda suke a ƙasashen da suke maƙwabta.

    Haka yake a idanun mutanen da suke ƙasashen da suke nesa da ƙasar Hausa don kuwa a wata hira da na gudanar da wani wanda ya ziyarci Ingila ya bayyana min cewa “A ƙasashen Turai al’ummar Hausawa suna da babban matsayi, kuma ana duban su a matsayin mutanen kirki saboda halayensu masu kyau sun sanya da wuya ka same su suna aikata munanan laifuffuka irinsu sata da zamba cikin aminci da fashi da makami da rashin gaskiya” (Hira da AASD, a garin Katsina, a ranar 14/12/2005.

    Saboda matsayin al’ummar Hausawa da harshensu a wannan zamani ya sa harshen Hausa ya zama na farko daga cikin harsunan Afrika ta Yamma da aka fara rubuce-rubuce da shi. Haka kuma shi ne harshe na farko da aka fara gabatar da labarai da shirye-shirye a gidajen Radiyon ƙasashen waje kamar a Sashen Hausa na BBC London da Muryar Amirka (ƁOA) da Muryar Jamus (Radiyo Deutche Welle) da Radiyo China da Radiyo Alƙahira da Radiyo Iran da dai sauransu (Yahaya, 1991:10 – 11).

    A nan gida kasancewar Hausawa suna da tsararren mulki wanda suka riƙa tafiyar da harkokin rayuwarsu lokaci mai tsawo tun kafin zuwan Turawan Mulkin Mallaka, ya sa sun mamaye fagen siyasar Nijeriya a wannan zamani. A halin yanzu duk wani mai son mulkin ƙasar nan dole sai ya haɗa kai da Hausawa zai ci nasara.

    Saboda haka ne Hausawa a wannan zamani suka shahara a fagen tafiyar da harkokin mulki cikin nasara da kwanciyar hankali, kuma suka zama jagora ga dukkan al’ummomin da suke a cikin wannan ƙasa. A iya ganin haka idan aka waiwaya aka duba waɗanda suka shugabancin Nijeriya tun daga samun mulkin kai zuwa wannan zamani. Daga cikin shugabanni goma sha biyu da suka shugabanci Nijeriya shida ko bakwai daga cikinsu Hausa/Fulani ne.

    Na farko Alhaji Abubakar Tafawa Ɓalewa da Janar Murtala Ramat Muhammad da Alhaji Shehu Usman Aliyu Shagari da Janar Muhammadu Buhari da Janar Ibrahim Badamasi Babangida da Janar Sani Abacha da Janar Abdulsalam Abubakar da kuma Alhaji Ummaru Musa ‘Yar’aduwa.

    Haka kuma a ƙasashe maƙwabta waɗanda Hausawa suka yi ƙaura suka koma, sun sami babban matsayi a waɗannan ƙasashe. Wannan kuwa ya faru ne sakamakon ire-iren gudummuwar da suke bayarwa don ci gaban waɗannan ƙasashe. A ire-iren waɗannan ƙasashe akwai Hausawa da daman gaske waɗanda suka yi fice a harkokin tafiyar da mulki da na soja da na tattalin arziki da na ilimi da dai sauran fannonin rayuwa.

    Misali, a yanzu Mataimakin Shugaban Ƙasar Ghana Alhaji Aliyu Muhammad Bahaushe ne wanda asalinsu mutanen Talatar Mafara ta jihar Zamfara ne. Bayansa akwai ‘Yan Majalisar Dokoki ta Ghana waɗanda Hausawa ne (An samo wannan bayani daga wani rahoto da Idi Ali, Wakilin Sashen Hausa na BBC London a Accra, Ghana).

    Duk da kasancewar al’ummar Hausawa suna da babban matsayi a wannan zamani akwai matsalolin da suke neman dakushe wannan matsayi. Wannan kuwa ya faru ne saboda wasu daga cikin waɗanda suke jagorancin al’ummar Hausawa da kuma wasu waɗanda ake jagoranta na neman su watsar da kyawawan al’adu waɗanda aka san Hausawa da su kamar nuna ƙauna da ‘yan’uwantaka da kara da alkunya da haɗin kai da nuna gaskiya da riƙon amana da dai sauran ire-iren waɗannan kyawawan al’adu.

    A yanzu ire-iren waɗannan Hausawa suna son su zama marasa gaskiya da nuna son kai da son tattara abin duniya da rashin taimaka wa al’umma da rashin haɗin kai da dai sauran munanan abubuwa. Saboda haka matuƙar ba a gyara waɗannan matsaloli ba, to matsayin Hausawa na jagorancin al’ummar Nijeriya zai fita daga hannunsu kuma mutuncinsu ya zube.

    Kamar yadda aka gani, wannan babi an yi bayani a kan farfajiyar ƙasar Hausa jiya da yau. An kuma duba yanaye-yanayen ƙasar Hausa da mutanenta da halin zamantakewarsu da shugabancinsu da addininsu da kuma hanyoyin tattalin arzikinsu da bayani kan ƙaura da shigowar baƙi a sassa daban-daban na ƙasar Hausa da dalilan da suka sanya su zaɓar ƙasar Hausa don yin zama na ci-rani ko zama na dindindin da kuma matsayinsu a yau.

    Don karanta Ƙaura Da Shigowar Baƙi Ƙasar Hausa danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Ƙaura Da Shigowar Baƙi Ƙasar Hausa

    Ƙaura Da Shigowar Baƙi Ƙasar Hausa

    Tun cikin shekarun 1960 zuwa wannan lokaci masana da manazarta da ɗalibai masu binciken tarihi suke ta kai-kawon nazari kan ƙaura da shigowar baƙi da kuma sakamakon da wannan ƙaura ta haifar ga al’ummomi daban-daban da suke cikin faɗin Nijeriya.

    Saboda haka ne ire-iren waɗannan masana da manazarta da ɗalibai suka kawo irin tasu fassarar kan kalmar ƙaura. Misali,”ƙaura na nufin tashin mutane daga ƙauyuka ko garuruwa zuwa manyan birane, wasu na wani ɗan lokaci (ci-rani), wasu kuma sun koma don su yi zama na dindindin a wannan sabon wuri” (Osaghae, 1994:20).

    Wani masanin kuma yana ganin ƙaura a matsayin “tashi daga wata gundumar mulki zuwa wata, wadda sakamakon wannan ƙaura yake samar da sabon wurin zama na dindindin” (Prothero, 1981:51).

    A wata fassarar kuwa ana ganin ƙaura a matsayin “mutum ko ƙungiyar mutane masu yawa su yi sauyin wurin zama su koma wani wuri na daban wanda za su yi zama na dindindin, amma ba irin sauyin wurin da makiyaya ko ‘yan ƙodago ko ‘yan ci-rani da makamantansu suke yi ba waɗanda ba sa yin zama na dindindin a sabon wurin da suka koma” (Bello, 1999:1).

    Dangane da haka ne wannan nazari ya yi ƙoƙarin kawo bayani kan ire-iren baƙin da suka yi ƙaura daga ƙasashensu na asali waɗanda suke maƙwabtaka ta kusa da ƙasar Hausa. Waɗannan baƙi sun haɗa da Fulani da Nufawa da Barebare da Buzaye da Yarabawa. An kuma kawo bayanan dalilan da suka sa sanya su zaɓar ƙasar Hausa a matsayin wurin da suka ga ya dace su zauna don ci-rani ko don su yi zama na dindindin.

    Idan muka dubi ire-iren baƙin da suke zaune a ƙasar Hausa kuma aka waiwayi tarihi, za a fahimci sun shigo ƙasar ne a lokuta daban-daban. Dangane da wannan nazari an kasa waɗannan lokuta zuwa biyu. Lokaci na farko ya fara daga ƙarni na goma sha huɗu zuwa ƙarni na goma sha takwas. Lokaci na biyu kuma ya fara daga farkon ƙarni na goma sha tara zuwa ƙarni na ashirin.

    Idan muka ɗauki lokaci na farko watau ƙarni na goma sha huɗu zuwa ƙarni na goma sha takwas lokaci ne da ƙasashen da a yanzu ake kira ƙasar Hausa kowace daga cikinsu take cin gashin kanta. A wancan zamani babu abin da a yanzu ake kira haɗaɗɗiyar ƙasar Hausa, kowane Sarki na mulkin iyakar riƙonsa,tsakaninsa da sauran sarakuna danginsa maƙwabta na kusa da na nesa sai yaƙi.A lokacin kuma hamayya a tsakanin waɗannan sarakuna don mallakar hanyoyin kasuwanci da tattalin arzikin wannan ƙasa ya zama ruwan dare.

    Wannan kuwa ya faru ne saboda dukkan ƙasar da ta mallaki babbar kasuwa za ta jawo baƙin ‘yan kasuwa daga sassa daban-daban.Wannan irin damar ce Katsina ta samu a wajajen tsakiyar ƙarni na goma sha biyu, inda fatake Larabawa da Azbinawa da Wangarawa suka riƙa haɗuwa.A wannan lokaci saboda yawan yaƙe-yaƙe da sarakunan Kano suka yi fama da shi ta rasa wannan dama (Ibrahim,1982:74-75).

    Haka abubuwa suka yi ta faruwa sannu a hankali baƙi suna ta shigowa cikin ƙasar Hausa a wannan lokaci daga ƙasashe maƙwabta na kusa don yin kasuwanci da wasu hulɗoɗi. Daga cikin ire-iren waɗannan baƙi akwai Fulani da Barebari da Buzaye da Nufawa da Yarabawa.

    Lokaci na biyu da baƙi suka shigo ƙasar Hausa watau farkon ƙarni na goma sha tara zuwa na ashirin, shi ne lokacin da aka yi jihadin Shehu Usman Ɗanfodiyo a cikin shekarun 1804 zuwa 1809. Wannan jihadi da kuma kafuwar Daular Sakkwato ya taimaka ƙwarai wajen ƙara shigowar baƙi ƙasar Hausa, misali Buzaye da Adarawa daga arewacin ƙasar Hausa (Hammani, 1975:197-198).

    A babi na biyar da na shida za a bi diddigin shigowar waɗannan baƙi ƙasar Hausa da kuma yadda wasu al’adunsu suka yi naso cikin al’adun Hausawa musamman sana’ar wanzanci a wannan zamani.

    Domin Karanta Tattalin Arziƙin Ƙasar Hausa danna nan

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tattalin Arziƙin Ƙasar Hausa

    Tattalin Arziƙin Ƙasar Hausa

    Ƙasar Hausa kamar kowace ƙasa tana da manyan hanyoyi da dama waɗanda suke taimaka wa tattalin arzikinta bunƙasa. Daga cikin waɗannan hanyoyi akwai waɗanda aka gada tun iyaye da kakanni, wato su ne na asali. Ire-irensu sun haɗa da noma da kiwo da fatauci da sana’o’in gargajiya. Bayan waɗannan akwai waɗanda aka samu sakamakon cuɗanya tsakanin Hausawa da wasu baƙin al’ummu kamar sana’ar kanikanci da kafinta da ɗinkin keke da mesin da dai sauransu.

    Noma

    Hausawa suna yi wa noma kirari da suke cewa “noma na duƙe tsohon ciniki kowa ya zo duniya kai ya tarar”. Wannan kirari na bayyana sana’ar noma daɗaɗɗiya ce a wannan duniya ba wai ga Hausawa kaɗai ba. Wannan ne ya sa idan ana maganar tattalin arzikin ƙasar Hausa, noma ne za a fara kawowa don kuwa shi ne ƙashin bayan tattalin arzikin wannan ƙasa.

    Wannan kuwa ya faru ne saboda sana’a ce wadda kowa-da-kowa yake yi talaka da saraki, attajiri da matalauci, maza da mata, babba da yaro don a sami abincin da za a ci da kuma wanda za a sayar don yin hidimomin yau da kullum. Saboda haka ne manoma a dukkan faɗin ƙasar Hausa da kewayenta suke samun wurare masu nagarta waɗanda suka haɗa da fadama da jigawa don noma amfanin gona mai kyau.

    Al’ummar Hausawa na yin noma iri biyu, na abinci da na kasuwa. Kayan noma na abinci sun haɗa da gero da dawa da masara da maiwa da dai sauransu, na kasuwa kuma sun haɗa da auduga da gyaɗa. Haka kuma ƙasar Hausa tana da albarkar da ake noma wasu abubuwan kamar rogo da dankali da sauransu (Nadama, 1977:90 – 92).

    Kiwo

    Kasancewar ƙasar Hausa shimfiɗaɗɗiya ce ga kuma sarari da ciyayi a ko’ina ya sa kusan a kowane gida ana kiwon dabbobi ko tsuntsaye. Hausawa na tsare dabbobi da tsuntsaye a gidajensu ta hanyar ba su abinci ko kuma a kora su zuwa daji don su nemi abinci a can. Ire-iren dabbobin da Hausawa suke kiwo sun haɗa da shanu da tumaki da awaki don cin namansu da kuma sayarwa.

    Haka kuma ana sayar da fatunsu da ƙiragansu don yin amfani da su. Ana kuma ɗaukar kashin da suka yi don kaiwa gona a matsayin takin da zai ƙara wa gona albarkar ƙasa. Bayan waɗannan dabbobi, Hausawa na kiwon dawaki don hawa na ƙawa da jin daɗi. Haka kuma suna kiwon jakuna da alfadarai don ɗaukar kaya da yin wasu ayyuka irinsu fatauci. Ire-iren waɗannan dabbobi dukkansu ana kiran su da sunan dabbobin gida.

    Bayan dabbobi Hausawa suna kiwon tsuntsaye irin su kaji da agwagi da zabi don cin namansu da ƙwayayensu da kuma sayarwa. Haka kuma saraki da attajirai suna kiwon tsuntsaye na alfarma irin su aku da ɗawisu da kanari don sha’awa da nishaɗi.

    Fatauci

    Tun kafin wannan zamani al’ummar Hausawa suna da irin nasu tsari wajen tafiyar da harkokin kasuwanci. Wannan tsari ana iya dubansa ta fuska biyu, kasuwancin cikin gida da kuma na waje. A cikin gida akwai kasuwanni na garuruwa waɗanda ake tafiyar da harkokin kasuwanci ta hanyar furfure. A irin wannan kasuwanci ana musayar abubuwan sayarwa ne, misali manomi ya ba masaƙi kayan gona don ya amshi kayan saƙa, ko ya ba makiyayi don ya amshi wata dabba da sauransu.

    An daɗe ana yin irin wannan tsari na cinikayya a ƙasar Hausa har zuwa cikin ƙarni na goma sha takwas da aka shigo da hanyar yin amfani da kuɗin wuri da biringizau don yin saye da sayarwa a duk faɗin Afrika ta Yamma (Nadama, 1977:137 – 138). Ta fuskar kasuwancin wajen ƙasar Hausa ‘yan kasuwa daga ƙasar Hausa na yin fataucin kayayyaki daga wannan ƙasa zuwa garuruwan Adar da Azben da Nufe da ƙasashen Yarabawa da Gwonja.

    Bayan sun sayar da kayayyakinsu a can, suna kuma sawo wasu kayayyakin daga waɗannan ƙasashe su kawo ƙasar Hausa don su sayar. Ire-iren kayayyakin fatauci da suka riƙa saye daga ƙasar Hausa suna kaiwa waɗannan ƙasashe, sun haɗa da daddawa da kayayyakin sutura irin waɗanda aka saƙa a ƙasar Hausa da kuma shunin gadi da baba da dabbobi da sauransu.

    Haka kuma suna sawo kayayyaki irinsu bindigogi da kayan albarushi da riguna girken Nufe da kayan ƙarau daga ƙasar Nufe. Suna kuma sawo balma da kanwa da dabino da dawakin Azbin da awaki da tumaki da raƙuma daga ƙasashen Adar da Azbin da kuma Borno.’Yan kasuwar da suke zuwa fatauci kudu watau ƙasashen Yarabawa da Gwonja suna sawo goro don kawowa ƙasar Hausa da maƙwabtanta na arewa don sayarwa (Nadama, 1977:142 – 143).

    Sana’o’in Gargajiya

    Kafuwar garuruwa a ko’ina cikin ƙasar Hausa da kuma bunƙasar da noma ya samu ya ƙara taimakawa wajen samuwar sana’o’in gargajiya inda ake ƙera da kuma sarrafa kayayyaki iri daban-daban domin amfanin mutanen ƙasar Hausa da maƙwabtansu na kusa da kuma na nesa. Ire-iren waɗannan sana’o’i sun haɗa da ƙira da saƙa da rini da jima da dukanci da sassaƙa da sauransu.

    Akwai kuma sana’o’in da ake yin ayyukan taimaka wa rayuwa kamar wanzanci da fawa da ɗori da sauransu. Bayan waɗannan akwai ƙananan sana’o’i waɗanda mata suke tafiyar da su kamar kaɗi da kitso. Waɗannan sana’o’i na gargajiya sun taimaka matuƙa gaya wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar Hausa. Yanzu za a ɗauke su ɗai-ɗai da ɗai-ɗai domin ganin yadda suka taimaka wa tattalin arzikin ƙasar Hausa.

    Ƙira

    Ƙira sana’a ce wadda aka fi yi a lokacin rani domin tanadar kayan aikin noma, amma duk da haka ana yin ta a kowane lokaci na shekara domin samar da kayan amfanin gida na yau da kullum. Maƙera sun kasu zuwa kashi biyu, akwai maƙeran baƙi da maƙeran fari. Maƙeran baƙi su ne suke tono tama su narka ta don ta zama ƙarfe wanda suke amfani da shi domin yin nau’o’in kayan ƙira.

    Ire-iren kayayyakin da maƙeran baƙi suke yi sun haɗa da fartanya da masassabi da gatari da lauje da sungumi da adda da dai sauransu domin yin ayyukan gona. Haka kuma maƙeran baƙi suna ƙera takubba da gariyo da tsitaka da masu da kibau da sauran kayayyakin da ake amfani da su wajen yin farauta da yaƙi.

    Bayan waɗannan suna yin kalaba da wuƙaƙe ƙanana da manya waɗanda ake amfani da su wajen yin ayyukan cikin gida na yau da kullum. Haka kuma su ne suke samar da kayan aikin wanzanci waɗanda suka haɗa da asake domin yin aski da kaciya da kuma kalaba wadda ake amfani da ita wajen cire belun-wuya. Suna kuma yin askar tsaga wadda ake amfani da ita wajen cire angurya a farjin mata da yin tsagar gado da ta magani da ta kwalliya da sauransu.

    Saƙa

    Saƙa sana’a ce wadda ake sassarƙa zare ko gashi ko ɓawo ko kaba don a mayar da su wani abu mai faɗi kamar tufafi ko shimfiɗa. Saboda haka a iya cewa, saƙa ta kasu zuwa iri biyu, ta tufafi da ta kayan shimfiɗa. Ana amfani da zaren auduga ne wanda mata suke kaɗawa domin saƙar tufafi.

    Masaƙa wato masana’antar da ake sarrafa zare domin yin sutura ita ma ta kasu zuwa iri biyu. Akwai masaƙar tsaye wadda mafi yawanci mata ne suke amfani da ita don yin saƙar gwado ko zanen kujera ko ɗan goyo wanda ake goya jarirai. Akwai kuma masaƙar zaune wadda maza ne suka fi yin amfani da ita wajen yin saƙar sauran abubuwa.

    Hakika wannan sana’a tana da matuƙar muhimmanci a ƙasar Hausa domin kuwa ba domin ita ba da an riƙa tafiya tsirara. Wannan a fili yake, sutura ita ce alamar da take bayyana bambanci a tsakanin mutum da dabba. A cikin mutane ma da sutura ake iya rarrabe bambancin al’adu.

    Da ita ake gane cikakken mutum da akasinsa. Haka kuma da ita ake sanin mawadaci da mabuƙaci. Masana’antar saƙa ta taimaka sosai wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar Hausa. Wannan kuwa ya samu ne sakamakon kayayyakin da ta riƙa samarwa waɗanda ake sayarwa a kasuwannin cikin gida da na ƙasashe maƙwabta (Alhassan, 1982:52-54).

    Jima

    Jima sana’a ce wadda ake sulluɓe fata don a fitar da gashin da yake jikinta. A irin wannan masana’anta da ake kira majema ana sauya fata daga halinta na asali na gashi da kaushi a sarrafa ta, a gyara ta yadda za ta yi laushi kamar sutura.

    Bayan an gyara fata ta yi kyau ana sayar da ita ga dukawa, kuma mafi yawancin fatar da aka gyara tana daga cikin manyan muhimman hajoji da ake safararsu daga ƙasar Hausa zuwa ƙasashe maƙawabta na kusa da na nesa. Ana yin wannan safara tun lokaci mai tsawo da ya gabata kafin shigowar Turawa wannan ƙasa.

    Irin wannan fata na daga cikin kayayyakin da aka riƙa fataucinsu daga Kano da Katsina da Zamfara da Sakkwato ana ƙetare hamadar Sahara da su ana kaiwa Morocco da sauran ƙasashen da suke arewacin Afrika ana sayarwa. Daga nan ne kuma Turawa suke sayen ta su kai ƙasashensu inda suke sarrafa ta domin yin jikunkuna da takalma da riguna maganin sanyi da sauran abubuwa waɗanda kuma suke kawo wasu daga cikinsu zuwa ƙasashen Afrika da sauran ƙasashen duniya don sayarwa.

    Dukanci

    Dukanci sana’a ce wadda ake sarrafa fata don mayar da ita wani abu na amfanin yau da kullum. Ire-iren abubuwan da dukawa suke yi sun haɗa da jikunkuna da takalman fata da igiyar linzamin doki da burgami da zabira wadda ake zuba kayan wanzanci da jakar zuba ma dawaki dawa ko dusa. Haka nan kuma suna yin warki da gafaka da tandun kwalli da kuben wuƙa da na takobi da sauran abubuwa.

    Bayan dukawa sun yi waɗannan abubuwa suna sayar da su ne ga waɗanda suke buƙata da kuma masu yin sari waɗanda suke kaiwa kasuwanni na cikin gida da na waje. Haka kuma ‘yan kasuwa na waje na shigowa cikin ƙasar Hausa don sayen ire-iren waɗannan kayayyaki da dukawa suka sarrafa.Wannan masana’anta ta dukanci ta bayar da gagarumar gudummuwa wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar Hausa.

    Rini

    Rini na nufin sauya launin tufa ko zare don ya zama wani iri. Ana kiran masana’antar da ake yin rini marina. Abubuwan da ake amfani da su wajen yin rini sun haɗa da muciya da kwatarniya da guga da itace da ƙaiƙayi da ɗan kutuɓu da baba da katsi da shuni da zarta da marina da ruwa.

    Wannan masana’anta ta taimaka sosai wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar Hausa. An fahimci haka ne kuwa ta la’akari da kayan rini irin na ƙasar Hausa na daga cikin muhimman abubuwan da fatake suke yin safararsu daga ƙasar Hausa zuwa ƙasashen maƙwabta don sayarwa.

    Sassaƙa

    Sassaƙa sana’a ce wadda ake gyara icce don a mayar da shi wani abu na amfani. Masassaƙan ƙasar Hausa na sassaƙa turmi da taɓarya da kujerar zama ta mata da kujerar gwado ta maza da ƙotar fartanya da ta masassabi da ta gatari da ta garma. Haka kuma masassaƙa suna sassaƙa akushi da ƙoshiyar dama fura da ludayin itace da allunan karatun Alƙur’ani mai girma da dai sauran abubuwa masu yawan gaske.

    Wannan sana’a ta sassaƙa tana taimaka wa tattalin arzikin ƙasar Hausa matuƙar gaske. A iya ganin haka ta yadda take samar da wasu kayan aiki ga sauran masana’antun gargajiya. Misali, manoma na amfani da ƙotoci, wanzamai na amfani da ƙoshiya don cire belun-wuya, makaɗa na amfani itacen da ake yin kayan kiɗa, masaƙa na amfani da gwafa wadda ake kafa masaƙa ta zaune da ta tsaye da sauran abubuwa.

    Wanzanci

    A Hausance, sana’ar “wanzanci” tana nufin amfani da askar aski domin yin aski da gyaran fuska da yin kaciya da kuma amfani da kalaba da ƙoshiya don cire belun-wuya. Sana’ar wanzanci ba ta tsaya a nan ba don kuwa ana amfani da ‘yar tsaga don yin ƙaho da cire angurya a farjin mata da yin tsagar gado da ta kwalliya da ta magani.

    A sana’ar wanzanci dai ana yin hujen kunne da yanke yatsan cindo (shiddaniya) da yanke linzami a cikin bakin jarirai da wasu ayyuka da dama. Haka kuma masu yin sana’ar wanzanci na bayar da magungunan gargajiya ga waɗanda suke buƙata.

    A taƙaice a iya cewa sana’ar wanzanci ta taɓo aikin likita a ƙasar Hausa kafin zuwan asibitin zamani. Dalili kuwa shi ne wani daga cikin ayyukan wanzanci shi ne kula da lafiya musamman ta jarirai da ƙananan yara, ta wani fannin ma har da lafiyar manya. Masu yin ire-iren waɗannan ayyuka ana kiran su wanzamai waɗanda dole su kasance masu cikakkiyar lafiya, masu hankali da natsuwa.

    A mafi yawanci maza ne suke yin sana’ar wanzanci, amma ana samun wasu mata waɗanda saboda rashin wani namiji a gida, ko kuma don wani dalili sukan koyi wannan sana’a daga mahaifansu. Ana gadon wannan sana’a a wajen iyaye ko kakanni na wajen uba. A gargajiyance yana da matuƙar wuya a sami wani mutum wanda bai gaji wannan sana’a ba yana yin dukkan ayyukan wanzanci.

    A wannan zamani ana samun waɗanda kan koyi yin askin zamani na saisaye wanda suke yi da kayan askin zamani, amma iyakarsu askin don kuwa ba sa iya yin sauran ayyukan wanzanci. Haka kuma wajen yin ayyukan wannan sana’a gado na taka muhimmiyar rawa, don kuwa kowane wanzami yana da gidajen da yake zuwa don gudanar da ayyukansa. Wani wanzami daban ba ya zuwa gidan da wani wanzami ɗan’uwansa yake yin aiki ya yi.

    Kowane gida ko zuri’a suna da wanzamin da suka gada wanda yake yi masu aiki, daga shi sai ‘ya’yansa ko wani da ya wakilta ne kaɗai suke iya zuwa waɗannan gidaje nasa don yin waɗannan ayyuka. Haka su ma masu gidajen ba sa kiran wani wanzami daban don yin ayyukan wanzanci a gidajensu dole sai wanda suka gada tun asali daga iyayensu.

    Wani tsari mai ban sha’awa dangane da aiwatar da sana’ar wanzanci shi ne, wanzami ba shi da iyakar ƙasar da zai riƙa gudanar da ayyukansa. Yana iya fita daga garinsu ko ƙasar dagacinsu ko hakiminsu ko sarkinsu, kai a wannan zamanin har jiharsu ya tafi wuraren da mutanensa suke domin yi masu ayyukan wanzanci.

    Misali, idan Bahaushe ya auri Bafulatana wadda ita a al’adarsu mace ba ta yin haihuwar fari a gidan mijinta, sai dai ta tafi goyon-ciki gidan mahaifanta. To, idan ta haihu ba mahaifanta ne za su kira wanzami ba, mijinta ko mahaifansa ne za su kira wanzaminsu na gida don ya yi ayyukan. Haka kuma a wannan zamani idan mutum na aikin Gwamnati a wani gari, idan matarsa ta haihu sai ya aiko garinsu don wanzaminsu na gida ya je domin yin ayyukan.

    Misali, lokacin da nake gudanar da wannan bincike, da na ziyarci Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya na sadu da Dr.Kabir Chafe wanda shi ne Shugaban Sashen Koyar da Tarihi kuma Shugaban Tsangayar Fasaha da Zamantakewa na wannan Jami’a. A lokacin da nake tattaunawa da shi ya bayyana min cewa, a duk lokacin da aka haihu gidansa nan Zariya, yana aikawa garinsu Tsafe don wanzaminsu na gida ya zo ya yi ayyukan wanzanci.

    Ni ma a halin yanzu mutanen da nake yi wa aikin wanzanci waɗanda kuma muka gaji juna waɗanda suke aikin Gwamnati a Katsina da Abuja da Kaduna da sauran wurare, idan matansu suka haihu suna aikowa don in je waɗannan garuruwa da suke don yin aikace-aikacen wanzanci.

    A wani lokaci takan kama a sauya wanzamin da aka gada. Dalilan da kan sa a yi wannan sauyi sun haɗa da sauyin wurin zama. Wato idan mai gida ya tashi daga garinsu ya koma wani gari da yake nesa da garinsu na asali, to a sabon wurin da ya sauka idan aka yi masa haihuwa, ko yana bukatar a yi wa wasu yaransa kaciya ko dai wata bukata ta aikin wanzanci a gidansa, sai ya nemi wani wanzami don ya yi masa waɗannan ayyuka. Daga wannan lokaci shi wannan wanzami ya zama na gidansa, sai kuwa idan wani dalilin ya tilasta a sauya shi.

    Haka kuma idan wanzamin gida ya rasu ko wata lalura ta rashin lafiya ta same shi, idan ba shi da mai gadonsa sai waɗanda yake yi wa aiki su sami wani wanda zai maye gurbinsa. Shi ma daga nan ya zama wanzamin waɗannan gidaje. Idan kuma rashin fahimtar juna ko wani saɓani ya shiga tsakanin wanzamin gida da mai gidan da yake yi wa aiki, misali maita ko siyasa ko aure da sauransu sukan tilasta a sauya wanzami.

    Idan ba ta waɗannan hanyoyi da aka yi bayaninsu ba, matuƙar wani wanzami ya yi shisshigi ya shiga gidajen da wani wanzami yake yin aiki ba tare da izininsa ba, ɓarna na iya shiga. Domin kuwa kowannensu zai yi ta ƙoƙarin yin ire-iren surkulle da sihirce-sihircen da ya iya domin nakasa abokin hamayyarsa ko ya lalata ayyukan da ya yi.

    Wanzaman Hausawa sun kasu zuwa rabo biyu. Akwai wanzaman gado da wanzaman ƙoƙo. Wanzaman gado su ne waɗanda suka gaji yin sana’ar wanzanci a wajen iyayensu da kakanninsu, kuma suna yin dukkan ayyukan wanzanci waɗanda suka haɗa da yin aski da kaciya da cire belun-wuya da cire angurya da bayar da magungunan gargajiya da yin tsagar gado da ta magani da ta kwalliya.

    Ire-iren waɗannan wanzamai ne suke gadon gidajen da za su riƙa yin ayyukan wanzanci. Haka kuma daga cikin irinsu ne ake naɗa Sarkin Aska ko Magajin Aska. Idan buƙatar aikinsu ta tashi a mafi yawancin lokaci a gidajensu ake zuwa don a sanar da su wuri da lokacin da ake bukatar su je don yin ayyukansu.

    Kuma a mafi yawancin lokaci ire-iren waɗannan wanzamai ba su da rainuwa domin kuwa duk abin da aka ba su a matsayin ladar aikinsu, sai su karɓa suna masu yin murna da godiya. An bayyana cewa dalilin haka shi ne suna yin waɗannan ayyuka ne don gado ba don ladar da ake biyan su ba.

    Su kuma wanzaman ƙoƙo ba sa yin dukkan ayyukan wanzanci, iyakar ayyukan da suke yi sun haɗa da aski da gyaran fuska. Wanzaman ƙoƙo barorin wanzaman gado ne. A wani lokaci irinsu na yin ƙaho, kuma irinsu ne suke yawo da zabira rataye a kasuwanni da cikin garuruwa suna neman wanda za su yi wa aski ko gyaran fuska ko ƙaho.

    Haka kuma ire-iren waɗannan wanzamai ne suke yin rumfuna a kasuwanni da shaguna a cikin garuruwa domin yi wa mabuƙata aski da gyaran fuska. Idan suka yi wa mutum ayyukansu suna gaya masa adadin kuɗin da zai biya ba kamar wanzaman gado ba. Hausawa na yi wa ire-iren waɗannan wanzamai kirari kamar haka:

    Wanzaman ƙoƙo a ci tuwo a yi aski,

                                     Cire belun-wuya da belun-mata sai ‘yan gado”.

    Ba a tsakanin Hausawa kaɗai ake yin sana’ar wanzanci ba, akwai al’ummomi da ƙabilu masu yawa waɗanda ake yi masu ire-iren ayyukan wanzanci. Wasu ana yi masu dukkan ayyukan ne, wasu kuwa ana yi masu waɗansu ne daga cikin ayyukan kawai.

    Wannan dalili ne ya sa kowace al’umma ko ƙabila tana da sunan da take kiran wanzami ko mai yin ayyuka irin na wanzanci. Misali, Larabawa suna kiran wanzami da sunan al-Hallaƙ. Fulanin da suke zaune a ƙasar Hausa suna kiran sa da sunan wanzamijo, su kuma Fulanin da suke zaune a gabacin ƙasar Hausa a Yola da Gwambe suna kiran sa da sunan wanjam ko wanjamjo.

    Turawan Ingilishi suna kiran sa da sunan barber, su kuma na Faranshi suna kiran sa da sunan coiffure ko coifere. Barebari suna kiran wanzami da sunan diyeji ko wanzama, shugaban wanzamai kuma suna kiran sa da sunan Zanna Ɗambusuma. Buzaye kuma suna kiran wanzami da sunan aghachaou, su kuma Adarawa na kiran sa da sunan wanzami. Su kuma Yarabawa na kiran wanzami da sunan bonjamo, wanda yake yin aski kawai kuma suna kiran sa da sunan fari-fari ko akola. ’Yan ƙabilar Ekoi waɗanda suke zaune a Jihar Cross Riɓer suna kiran wanzami da sunan anu-uka.

    Nufawa kuma suna kiran sa da sunan gozan. Su kuwa ‘yan ƙabilar Ibo suna kiran mai yin aski da sunan okpa-isi, wanda yake yin kaciyar maza kuwa suna kiran sa obe-ugwu, wanda yake yin tsagen gargajiya kuma suna kiran sa da sunan ogbu-ichi. Dakarkari waɗanda suke zaune a ƙasar Zuru da kewaye a Jihar Kabi na kiran wanzami da sunan sah’pana ko u’oro.

    Idan muka ƙetara a ƙasashen da suke Afrika ta Gabas za mu ga akwai wasu ƙabilun waɗannan ƙasashe waɗanda suke aiwatar da ire-iren ayyukan wanzanci da ake yi a ƙasar Hausa kamar yadda Hausawa suke yi. Wasu daga cikin al’ummomin waɗannan ƙasashe na cire belun-wuya da belun-mata da yin askin suna ga jarirai da dai sauran ayyuka irin waɗanda wanzaman Hausawa suke yi.

    An ce kamar yadda wanzaman Hausawa suka gaji yin wannan sana’a, al’ummomin waɗannan ƙasashe masu yin waɗannan ayyuka suna yin gado ne a wurin mahaifansu. Akwai waɗanda suke koyon yin waɗannan ayyuka bayan sun girma, ire-irensu suna bayyana cewa iskoki ne suka sanar da su hikimomin yin waɗannan ayyuka (Hira da JMT da PMT da KMK da AGU a ranar 20/12/2004 da MEHT a ranar 22/12/2004). A Uganda ƙabilun Sabiny da Kapchori, a Kenya kuwa ‘yan ƙabilar Kisii, a Tanzania kuma ‘yan ƙabilar Wakurya ne suke yin ire-iren ayyukan wanzanci na Hausawa.

    A gabacin Afrika ana amfani da harshen Swahili a matsayin harshen ƙasa a ƙasashen Uganda da Kenya da Tanzania don yin hulɗoɗin gwamnati da harkokin yau da kullum a tsakanin al’ummomin waɗannan ƙasashe. A saboda haka akwai sunayen da ake kiran wanzami ko mai yin ayyuka irin na wanzami a waɗannan ƙasashe. Misali, ana kiran mai cire belun-wuya da sunan kukata-kilimi, mai yin aski kuma kinyozi.

    Shi kuma mai yin kaciyar maza ana kiran sa da sunan tohara ya wanaume, mai yin kaciyar mata kuwa tahora ya wanawake ko ngariba. Shi kuma mai yin tsagar gado ana kiran sa da sunan ndonya ko makonde, mai yin tsagar kwalliya kuwa alama za nyuso (Hira da AGU, a ranar 20/12/2004 da kuma MEHT], a ranar 22/12.2004).

    Bayan waɗannan sana’o’i waɗanda mafi yawancinsu maza ne suke aiwatar da su, akwai waɗanda mata ne kawai suke yin su kamar kaɗi wanda ake yi don samar da zare da abawa ga masana’antar saƙa. Haka kuma mata ne suke yin sana’ar kitso ga ‘yan uwansu mata. Suna yin salon kitso iri-iri don yin kwalliya ga kan mata wanda suke ƙara masu kyau da jawo hankalin maza.

    Akwai kuma sana’ar tauri ko koda wadda mata suke amso hatsi don yin dakau na fura ko garin da za a yi amfani da shi don yin abinci. Waɗannan sana’o’i waɗanda mata suke yi suna taimaka wa matan yin hidimominsu na yau da kullum da kuma yin bikin dangi ba tare da sun dogara da wani ba.

    Shigowar baƙi ƙasar Hausa wato Larabawa da Turawa sun taimaka wa tattalin arzikin ƙasar Hausa ya ƙara bunƙasa.Wannan kuwa ya faru ne ta yadda aka sami shigowar wasu sababbin sana’o’i waɗanda wasun su ci gaba ne ga waɗanda Hausawa suke yi kafin zuwan waɗannan baƙi.

    Ire-iren waɗannan sana’o’i sun haɗa da ta makanikanci don yin gyaran kekuna da babura da motoci da rediyo da rikoda da talabijin da kwamfyuta da wayar hannu da dai sauransu. Akwai kuma masana’antar kafinta wadda ci gaba ce ga sana’ar sassaƙa ta gargajiya. Kafintoci na sassaƙa kujerin zama na zamani da tebura da tagogi da ƙofofin ɗaki da yin rufin ɗaki wanda ake amfani da katako da kwanon rufi da dai sauran ayyuka don a ƙara sauƙaƙa rayuwar yau da kulllum.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

  • Addinin Mutanen Ƙasar Hausa

    Addinin Mutanen Ƙasar Hausa

    Hanyar bauta wa wani abu wanda mutum yake tsammanin shi ne zai biya masa bukatun rayuwar yau da kullum shi ne addini. Addinin farko na mutanen ƙasar Hausa shi ne addinin gargajiya, wato tsafi ta hanyar bautar iskoki ko mutanen ɓoye da kuma bori da camfi.

    Irin wannan addini ya faru ne ta bin wasu hanyoyi da mutane suka ƙaga wa kansu ta bautar waɗansu abubuwa don cimma biyan buƙatunsu na rayuwa. Wannan hanyar bauta ta daɗe ƙwarai a dukkan sassan duniya ba ƙasar Hausa kawai ba. Mutanen da suka fara zama a duniya ne suka ƙirƙiro ta, daga nan sai abin ya zama al’ada ga sauran ƙabilun da suke biye da su har ya zo ga Hausawa.

    A sakamakon shigowar addini Musulunci cikin ƙasar Hausa da kuma karɓar sa da mafi yawancin Hausawa suka yi, irin wannan addini ya sami rauni. Amma duk da haka ba a bar yin wasu abubuwa waɗanda suka danganci addinin gargajiya na Hausawa ba. Don kuwa za a ga yana yin tasiri a kan wasu al’amuran da suka shafi rayuwar wasu Hausawa ta yau da kullum.

    Idan muka waiwaya muka duba yadda al’ummar Hausawa suka gudanar da addininsu na gargajiya, za mu ga ba wai suna sassaƙa wani gunki ne suna bauta masa ba, a a, suna yin bautarsu ne ta hanyar yin tsafi. Bauta ta hanyar tsafi tana nufin bauta wa wani iska da aka ɗauka yana zaune a wani wuri na daban. Ire-iren wuraren da aka ɗauka iskoki suna zama sun haɗa da wata kwankwamar dutsi ko cikin wata sarƙaƙƙiya ko wurin wata tsohuwar bishiya, irinsu kuka da tsamiya da marke da dai sauransu.

    Misali, a Kano an bauta wa iska Tsumburbura wanda aka ɗauka ya zauna a Dutsen Dala, Kainafara-Arnan Birchi suna bauta wa iska Ɗantalle wanda suka ce yana zaune a cikin Dutsin Birchi. Arnan Kwatarkwashi kuma suna bauta wa Ƙunƙurutu wanda suka ɗauka yana cikin Dutsin Kwatarkwashi, arnan Sauna kuma suna bautar Magiro.

    Haka kuma a duwatsun Kufena ta Zariya mazaunan farko a wannan wuri sun ɗauka akwai wasu iskoki da suke zaune a wannan wuri. Saboda suna biya masu buƙatunsu shi ya sa suke bauta masu. A ƙasar Katsina ma akwai wasu arna da suke bautar Magiro a Safana da Ɗan-musa da Ƙanƙara da Dutsin-ma wanda suka ce yana zama a wurin tsamiya mai sarƙaƙƙiya da duhu, kuma ba mai iya zuwa wurin da yake sai masu yi masa hidima

    Bayan addinin gargajiya sai addinin Musulunci wanda addini ne da Allah Maɗaukakin Sarki ya aiko ta hannun Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) don ya zama hanyar shiriya ga al’ummomin duniya, ya kuma zama hanya madaidaiciya a gare su. Wannan kuwa ya faru ne a cikin shekara ta 610 Miladiyya.

    Addinin Musulunci ne ya biyo bayan addinin Kirista wanda Allah Maɗaukakin Sarki ya aiko ta hannun Annabi Isa, Allah ya ƙara yarda da shi. An sami shekaru ɗari shida a tsakanin waɗannan addinai (Ibrahim, 1982:63 da Gusau, 2005:18-19). Ba kamar sauran addinan da suka gabace shi ba, addinin Musulunci an aiko da shi zuwa ga dukkan al’ummomin duniya don ya zama hanyar shiriya ga kowa.

    Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) ya fara da kiran ‘yan’uwansa zuri’ar Banu Hashim don su karɓi wannan addini. Wasu suka karɓa wasu kuwa suka ƙi. Sannu a hankali yana wa’azi shi da waɗanda suka fara ba shi goyon baya, cikin ɗan ƙanƙanin lokaci sai da dukkan ƙasashen Larabawa suka amshi addinin Musulunci.

    Wannan ne ya sa aka kafa Ƙungiyar Al’ummar Musulmi wadda take da cibiya a Birnin Madina, Annabi shi ne shugaban wannan al’umma. Dukkan abin da zai zartar, sai ya yi shawara da sahabbansa. Wajen tafiyar da wannan al’umma ba a nuna ƙabilanci ko fifiko a tsakanin jama’ar da suke cikinta. Abin da ta sa gaba shi ne haɗin kai da son juna da nuna ‘yan’uwantaka a tsakanin Musulmi. Babban tsarin mulkin wannan al’umma shi ne shari’ar Musulunci. Kafin Annabi ya yi ƙaura, ya bar wa al’ummar Musulmi Alƙur’ani mai tsarki da kuma Hadisai don su yi masu jagora dangane da addininsu (Ibrahim, 1982:63).

    Manyan shika – shikan addinin Musulunci biyar ne:

    • Shaidawa ba abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) bawansa ne kuma manzonsa ne.
    • Tsayar da salla.
    • Bayar da zakka.
    • Yin azumin watan Ramalana.
    • Ziyartar ɗakin Allah don yin aikin Hajji ga wanda ya sami iko.

    Bayan ƙaurar Annabi Muhammadu (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) da kuma zaɓaɓɓun halifofi huɗu da suka biyo bayansa. An sami wasu daga cikin sahabbai da wasu malamai da suka biyo bayansu, sun kawo hanyoyin da suke ganin ya dace a riƙa yin aikace-aikacen addini don samun sakamako mai kyau a duniya da lahira. Wannan ne ya sa aka sami ɗariƙu da ƙungiyoyin addini mabambanta masu yawa waɗanda suke da magoya baya a ko’ina.

    Daga cikin ire-iren waɗannan ɗariƙu akwai Ƙadiriyya da Tijjaniyya da dai sauransu da dama. Haka kuma akwai ƙungiyoyin addini waɗanda suka haɗa da Ƙungiyar Jama’atu Izalatul Bid’a wa Iƙamatus Sunna wato Ƙungiyar Kawar da Bidi’a da Tsayar da Sunna. Akwai kuma Ƙungiyar ‘Yan’uwa Musulmi (Shi’a). Waɗannan ɗariƙu na Ƙadiriyya da Tijjaniya suna da magoya baya sosai a cikin ƙasar Hausa. Haka su ma waɗannan ƙungiyoyi suna da nasu magoya baya a sassa daban-daban na ƙasar Hausa (Ibrahim, 1982:98-99, ‘Yanɗaki, 1997:46-50 da Suleman, 1997: 58-59).

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Hanyoyin Zamantakewar Hausawa

    Hanyoyin Zamantakewar Hausawa

    Al’ummar Hausawa ba haka nan suke zaune kara-zube ba, wato zama irin na ba-kai-ba-gindi, suna da tsararriyar ingantacciyar hanya wadda ta shafi yadda suke tafiyar da harkokin rayuwarsu na yau da kullum.

    A gaskiya ma ko da addinin Musulunci ya shigo ƙasar Hausa ya tarar da Hausawa suna tafiyar da harkokin rayuwarsu bisa ingantaccen tsarin da ya shafi harkokin aure da haihuwa da mutuwa da sauran ma’amalolin rayuwa. Wannan ne ya sa ba a sami wata matsala ba a lokacin da Hausawa suka karɓi addinin Musulunci wajen tafiyar da rayuwarsu kamar yadda shari’ar addinin Musulunci ta tsara wa mabiya addinin.

    Dangane da haka tsarin zaman Hausawa na yau da kullum an tsara shi daga kafuwar iyali. Daga iyali ne al’umma ko jama’a suke faruwa har su zama babban gida (gidan-gandu) daga nan sai ‘yar unguwa. Ire-iren waɗannan unguwanni ne suke haɗuwa su kafa ƙauyuka, ta haka ne kuma aka sami garuruwa da birane waɗanda sarakuna suke mulki (Smith, 1957:241- 42).

    Domin tafiyar da rayuwarsu ta yau da kullum cikin sauƙi, al’ummar Hausawa suna tafiyar da rayuwarsu bisa tafarkin cuɗan-in-cuɗe-ka, watau taimakon-kai-da-kai. Ta wannan fuska idan abin arziki ya sami wani mutum a wannan unguwa ko ƙauye ko gari, misali aure ko haihuwa, sai ‘yan’uwa da abokan arziki su taru don taya shi murna. Kuma kowa kan kawo irin tasa gudummuwa wadda wasu kan kawo hatsi ko abinci ko kuɗi ko sutura da sauran abubuwan arziki.

    Dalilin yin haka shi ne don a taimaka wa wannan ɗan’uwa da abin da zai yi wannan hidima ba tare da ya fuskanci wata matsala ba. Irin wannan halayya ce ta haifar da ƙungiyoyin taimakon kai-da-kai domin a ƙara taimaka wa juna. Za a tarar ‘ya’yan waɗannan ƙungiyoyi akwai maza da mata da ma waɗanda ba Hausawa ba a cikinsu, kuma ana yi wa kowane ɗan ƙungiya dukkan abin da ya dace a yi wa wani ba tare da la’akari da jinsi ko ƙabila ba.

    Haka kuma idan abin baƙin ciki ya sami wani mutum misali, rashin lafiya ko mutuwa ko wata masifa ‘yan uwa da abokan arziki na kusa da na nesa suna zuwa wurinsa don su yi masa jaje da taya shi jimamin wannan hali da ya shiga ko wani nasa ya shiga. Idan rashin lafiya ya kama mutum, a nan ma za a tarar cikin masu zuwa don jajantawa akwai maza da mata da ma waɗanda ba Hausawa ba, duk suna zuwa ne saboda zaman lafiya da mutuntaka da take tsakaninsu da Hausawa a wuraren da suke zaune.

    Bayan wannan al’ummar Hausawa suna tafiyar da ayyukan gayya don taimaka wa kansu-da-kansu. Ana yin ayyukan gayya a gidaje inda ake yin sababbin ɗakuna da gyara tsofaffi da yin darnin gida ko na garka da ɗora ɗan bisan ɗaki da na rumbu da sauransu. Su kuma mata suna yin ayyukan gayya don yin daɓen ɗaki da shafen jangargari da na farar ƙasa da sauransu.

    Ana kuma yin ayyukan gayya a gonaki inda ake yin sassabe da huɗa da shuka da noma da girbi da ɗaurin amfanin gona da kawo shi gida. Haka kuma a cikin ƙauyuka da garuruwa ana yin ayyukan gayya wajen gyara masallatai da maƙabartu da magudanun ruwa da mashayar ruwa da gyaran hanyoyin da ake bi don kawo amfanin gona gida da kasuwa.

    A wannan zamani ire-iren waɗannan ayyukan gayya da Hausawa suke yi sun yi rauni saboda tasirin zamananci a kan wannan al’umma. A yanzu mafi yawancin mutane suna zaune a bisa tafarkin kowa-tasa-ta-fisshe-shi, amma duk da haka ana samun ɗaiɗaikun al’ummomi a wasu wurare cikin ƙasar Hausa da suke aiwatar da ayyukan gayya a garuruwansu.

    Tsarin Shugabanci a Tsakanin Hausawa

    Shugabanci na nufin yi wa mutane jagora a halin zamantakewarsu na yau da kullum. A nan duk wanda aka ba ragamar tafiyar da mulkin al’umma, nauyi ya hau kansa na tsare lafiyarsu da dukiyarsu da mutuncinsu. Su kuma waɗanda ake shugabanta haƙƙinsu ne su ba mai mulkinsu haɗin kai, su kuma riƙa bin umurninsa don ya sami sauƙin tafiyar da mulkinsu cikin kwanciyar hankali.

    A ƙasar Hausa shugabanci yana farawa daga gida ne, don kuwa a kowane gida wanda yake ƙunshe da mutanen da suka kai biyu ko waɗanda suka wuce haka, akwai maigida wanda nauyin dukkan mutanen wannan gida ya rataya a wuyansa. Shi yake jagorancin wannan gida a dukkan wasu harkokin rayuwar yau da kullum.

    Dukkan mutanen gidan waɗanda suka haɗa da matansa da ‘ya’yansa da matan ‘ya’yansa da ƙannensa da matansu da ‘ya’yansu da jikokinsa da barorinsa da ‘yan cin arziki da dai sauran duk wanda yake ƙarƙashinsa na bin ummurninsa. Shi yake yi masu kome wanda ya shafi sutura da abinci da tsaro da kare mutuncinsu da nema masu magani idan sun kamu da wata rashin lafiya.

    Idan ire-iren waɗannan gidaje suka yi yawa sai su kafa unguwa. Daga cikin masu gidajen sai a sami wani mai kwarjini daga cikin su wanda ya iya tafiyar da harkokin al’ummarsa, a ba shi mai unguwa. Mutanen wannan unguwa ne tare da amincewar dagacinsu suke zaɓar sa, daga nan shi kuma nauyi ya hau wuyansa na mulkin al’ummar wannan unguwa. Shi kuma ne zai riƙa wakiltar su a duk wasu hidimomi da kuma yin sasanci a tsakanin talakawansa (Usman, 1972:176).

    Samuwar unguwanni da yawa yake samar da dagaci wanda dukkan masu unguwanni suke ƙarƙashinsa. Dukkan abubuwan da suke faruwa a waɗannan unguwanni sai an sanar da shi, kuma duk wani sasanci da ya gagari mai unguwa wurin sa ake zuwa don ya yi sasanci. Dagaci yake wakiltar al’ummominsa da suke unguwanni a wasu ma’amalolin rayuwa.

    Garuruwan dagatai da yawa suke samar da ƙasar Hakimi wanda shi yake shugabancin dukkan garuruwan dagatai da suke ƙarƙashinsa. Dukkan abubuwan da suke faruwa a garuruwan dagatai sai an sanar da shi, kuma shi yake wakiltar su a duk wata hidima. Idan dagatai sun gaza wajen yin wani sasanci, sai su miƙa maganar gare shi, don ya yi tasa hikimar ya sasanta saɓanin.

    Waɗannan garuruwa na hakimai ne suke taruwa su yi ƙasar sarki. Sarki shi ne wuƙa da nama a duk harkokin da suke faruwa a wannan masarauta. Dukkan mutanen wannan ƙasa suna ƙarƙashin mulkinsa, kuma hakimai na sanar da shi dukkan abubuwan da suke faruwa a ƙasashensu. Idan hakimai sun gaza wajen yin sasanci a tsakanin talakawansu, sai su kai ga sarki wanda ta hanyar shawartar ‘yan majalisarsa zai yanke hukunci ko da daɗi ka ba daɗi. Wanda hukuncin bai yi wa daɗi ba dole sai ya yi haƙuri, wannan ne ya sa ake yi masu laƙabi da ‘wuƙar yanka’ (Usman: 1972:176).

    A kowace masarauta akwai ‘yan majalisar wannan sarki, su ne suke taimaka wa wannan sarki da shawarwarin da za su taimaka a aiwatar da mulkin wannan ƙasa cikin nasara da adalci. Waɗannan ‘yan majalisa sun haɗa da Waziri wanda shi ne babban mai ba sarki shawara kuma shi yake wakiltar sarki a lokacin da ya fita daga masarautarsa. Bayansa akwai Alƙali da Magatakarda da Shamaki da Shantali da Ma’aji ko Ajiya da Sarkin Fada da Galadima da Sarkin Gida da dai sauransu da dama.

    Bayan waɗannan sarautu akwai kuma sarautun da ake ba masu sana’o’in gargajiya. Kowace sana’a akwai wanda ake ba jagorancin mutanen da suke gudanar da irin wannan sana’a don ya yi sasanci a tsakanin ma’abota sana’ar da kuma tafiyar da ita bisa ingantaccen tsari. Ire – iren waɗannan sarautu sun haɗa da sarkin noma ga masu yin noma da sarkin maƙera ga masu yin ƙira da sarkin aska ga masu yin sana’ar wanzanci da sarkin makaɗa ga masu yin sana’ar kiɗa da sanƙira ko sarkin roƙo ga masu yin sana’ar roƙo da sarkin fawa ga masu yin sana’ar fawa da sauransu da dama (Adamu, 1978:5).

    Dukkan waɗannan sarautu da aka yi bayani a kansu tun daga mai unguwa zuwa ga sarki da ‘yan majalisar sarki da masu riƙe da sarautun sana’o’in gargajiya, an tsara su ne bisa tafarkin gado. Wato idan wanda yake riƙe da sarautar ya mutu ko ya yi murabus ko aka tuɓe shi, a mafi yawancin lokaci ana zaɓar wani daga cikin ‘ya’yansa don ya gaje shi, wani lokaci kuma ana ba ƙanensa ko wani ɗan uwansa don ya gaje shi.

    Wannan na faruwa ne saboda irin ƙima da mutunci da martaba da muhibbar kowane daga cikin ‘ya’yan sarkin ko danginsa. Hanyar da ake bi wajen zaɓar sarki a ƙasar Hausa kafin jihadin Shehu Ɗanfodiyo ba tsari ne na bai ɗaya ba. Akwai bambanci a tsakanin wannan masarauta da waccan. Daga kafuwar Daular Usmaniyya zuwa mulkin mallakar Turawa an sami canji dangane da yadda ake tafiyar da wannan tsari.

    Don kuwa dukkan sarkin da aka zaɓa, a fadar Mai Martaba Sarkin Musulmi ne za a yi naɗinsa, kuma Sarkin Musulmi ne yake amincewa da zaɓensa kafin a naɗa shi, saɓanin tsarin da suke bi kafin wannan lokaci. Kafuwar mulkin mallaka kuma, sai ya ƙara sauya tsarin don kuwa dukkan sarkin da za a zaɓa sai Gwamna ya amince kafin a naɗa shi ya hau gadon sarauta.

    Kafin jihadin Shehu Ɗanfodiyo a shekarun 1804 zuwa 1809 dukkan ƙasar Hausa tana rarrabe ne masarauta-masarauta. Kowane sarki na mulkin iyakar garuruwan da suke ƙarƙashin ikonsa. A babban birnin wannan masarauta ne ake gudanar da harkokin mulki da na tattalin arziki. Wannan dalili ne ya sa ba a sami dunƙulalliyar ƙasar Hausa wadda take ƙarƙashin mulkin sarki ɗaya ba. Sai bayan da aka yi jihadi kuma aka kafa Daular Usmaniyya, sannan ne aka haɗe su a ƙarƙashin daula ɗaya mai cibiyar mulki a Sakkwato. A wancan zamani tsakanin su sai dai yaƙe-yaƙe da kai hari don kamen bayi.

    Tun daga mulkin Hausawa har zuwa mulkin Fulani a ƙarƙashin Daular Sakkwato zuwa mulkin mallaka na Turawa, tsarin sarautar ƙasar Hausa bai sauya ba. To, amma ayyukan da sarakunan suke yi ya sauya, kuma a wajen mulki ba su da izinin aiwatar da wasu hukunce-hukunce kamar yadda suke yi a da can. A yanzu an ɗauke su iyayen ƙasa kawai, ba su da cikakken iko da ƙasa da talakawa, duk sun koma ƙarƙashin gwamnati.

    Idan ma za su yi wani abu, sai sun nemi izini daga gwamnatin ƙaramar hukumar da suke ko jiha ko gwamnatin tarayya idan abin mai ƙarfi ne sosai. A wannan zamani sarautun gargajiya an mayar da su ƙarƙashin ikon ma’aikata mai kula da ƙananan hukumomi da masarautun gargajiya ta kowace jiha a faɗin Tarayyar Nijeriya. A Jamhuriyar Nijar ma suna da tsari irin nasu wanda shi ma dai sarautun gargajiya na wannan ƙasa suke ƙarƙashin irin wannan ma’aikata wadda take kula da yadda suke tafiyar da harkokinsu.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya 1st August 2025

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya 1st August 2025

    Huɗubar 07/02/1447H 01/08/2025M

    Mai huɗuba: Sheikh Dr. Yasir Ibn Rashid Addausari

    Mai fassara: Malam Salisu Alhaji Abdullahi

    Huɗuba ta farko:
    Dukkan yabo tabbata ga Allah, Wanda Ya koyar da alƙalami. Ya koyar da mutum abin da bai sani ba. Muna gode Masa bisa ni’imominSa masu bibiyar juna, da baiwarwakinSa waɗanda ba a iya ƙirga su ko a ƙididdige su. Ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah Shi kaɗai, ba Shi da abokin tarayya, Ya kewaye dukkan komai da iliminSa, kuma Ya sanya iyaka ga kowane abu.

    Kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa, mafi alherin wanda ya bi tafarkin shiriya, kuma ya gargaɗi al’umma game da bin hanyoyin halaka.
    Tsira da amincin Ubangijina su tabbata a gare shi, da Alayensa da Sahabbansa ma’abota hankula, da Tabi’ai da waɗanda suka biyo su da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.
    Bayan haka, ku ji tsoron Allah matuƙar tsoronSa, kuma ku hararo kulawarSa gare ku a sarari da yayin ganawa, kuma kada rayuwar duniya ta ruɗe ku.

    Allah Maɗaukakin sarki Ya ce: (To, amma duk wanda ya yi ɗagawa () Kuma ya fifita rayuwar duniya () To lallai wutar Jahimu ita ce makoma () Kuma duk wanda ya ji tsoron tsayuwa a gaban Ubangijinsa, kuma ya hana zuciya bin abin da take so () To lallai Aljanna ita ce makoma).

    Ya ku mutane:
    A zamanin nan namu, bil’adama na fuskantar cigaba na ban mamaki ta fuskar rayuwa, da bunƙasa ta musamman a fagage na fasaha da na’urori masu ƙwaƙwalwa, da kafafen sadarwa na dijital, da su ne sadarwa ta sauƙaƙa, kuma nesa ta zo kusa, kuma aka taƙaita lokuta, kuma aka aiwatar da ayyuka, aka kuma inganta hidindimu, kuma aka sauƙaƙa isa ga ilimi ta kafafen zamani, don haka, sai fasahar zamani ta zama wani ɓangare da ba zai iya rabuwa da rayuwarmu ba.

    Kuma idan al’ummu suna yin gasa a fagen fasaha, to lallai ƙasarmu mai albarka ta bambanta da hangen nesanta, kuma ta yi fice a matakan da ta ɗauka, sai ta zama jagora a wannan fanni, tana ribatar fannin fasaha kuma tana amfani da ita wurin hidimtawa al’umma da ɗan’adam, har ta zama abin kwaikwayo da ake yabawa kuma ake koyi da ita a cikin wani yanayi mai ban sha’awa da ke tabbatar da matsayinta a mataki na duniya a fannonin fasahohin zamani masu zurfi.

    Kuma haƙiƙa ƙasarmu ta tabbatar da cewa cigaba ba ya cin karo da ɗabi’u na ƙwarai, kuma ba ya saɓa wa al’adu, bari-dai, yana gina su ne kuma yana dogaro da su, sai ƙasar ta daukaka ba tare da ta manta da tushenta ba, kuma ta cigaba ba tare da ta yi watsi da tabbatattun al’adunta ba.

    Madalla da wannan a matsayin wata ni’ima daga Ubangiji, kuma kyauta daga Allah, wadda take wajabta yabo da godiya, don haka, dukkan yabo ya tabbata ga Allah da Ya hore mana waɗannan hanyoyi, kuma Ya buɗe mana kofofin alheri da sauƙi, kuma Ya datar da jagororimmu shiryayyu zuwa ga amfani da su da kuma inganta su.

    Ya ku bayin Allah
    Kuma idan har wannan ni’ima na daga cikin manyan ni’imomi, kuma na daga alamomin samun rinjaye a wannan zamani, to lallai ita ni’ima idan aka sanya ta a inda bai dace ba, sai ta koma azaba da bala’i.

    Kuma a yayin da fasahar zamani take rasa alƙiblarta, kuma aka rasa wayewar addini tattare da masu amfani da ita, to a wannan lokaci sai na’urori su koma tarko, hanyoyin kuma su koma ababen da suke zamarwa, daga nan ne wata cuta da aka jarrabi wasu mutane da ita ta bayyana, duk da bambancin shekarunsu da wayewarsu da jinsinsu, wannan kuwa ita ce cutar ɗamfaruwar zuciya da kafafen sadarwa na zamani, da nutsewa a cikin duniyar yanar gizo da ba ta da iyaka, har ma a wajen wasu wayoyi suka sauya daga kasancewarsu hanyoyin sada zumunci zuwa hanyoyin kaɗaici da yanke alaƙa.

    Sai ka ga mutum cikin jama’a tamkar gangar jiki ne da babu zuciya da hankali a tare da shi; yana kai-komo tsakanin kafafen sadarwa, yana shiga manhajoji sai shafukan yanar gizo su riƙa fizgar sa, kuma yana kallon bidiyoyi masu yawa, bai ma san abin da yake nema ba, kuma bai samu wani abu mai amfani ba.

    Wannan wata fitina ce mai hallakarwa, mutum yana rayuwa a cikinta cikin ruɗani ba tare da wasu manufofi ba; kamar ƙaramin kwale-kwale ne a tsakiyar teku ba tare da na’urar gane hanya ko abin tuƙa shi ba, kuma kamar matafiya ne wanda bai isa inda zai je ba kuma ga shi ya halakar da abar hawansa. Tir da shekaru da ke wucewa kamar gajimare, kuma suke ƙarewa ba tare da wani guzuri don ranar hisabi ba.

    An karɓo daga Ibn Abbas Allah ya ƙara musu yarda ya ce: Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Akwai wasu ni’imomi guda biyu da ake yi wa yawancin mutane kamunga a cikinsu, su ne lafiya da lokaci). Bukhari ne ya rawaito shi.
    Ibnul-Ƙayyim Allah Ya masa rahama ya ce: “ɓata lokaci ya fi tsanani fiye da mutuwa; domin mutuwa tana raba ka ne da duniya, amma ɓata lokaci yana raba ka ne da Allah da kuma rabauta a lahira”

    Ya ku Musulmi:
    Lallai zuciya idan ba a shagaltar da ita da ayyukan ɗa’a ba, to sai ta shagaltu da saɓo, musamman ma a wannan zamanin na kafafen sadarwa na zamani, da yawan bibiyar hotuna da labaran yau da kullum, da ƙawata shafuka, sai ka ga mutum ya nutse cikin ruɗanin da ba shi da ƙarshe, da burace-burace waɗanda ba sa ƙarewa, kuma abin da ya fi wannan muni shi ne wanda yake rayuwarsa cikin bibiyar rayuwar wasu kuma yake ɓata lokutansa, kuma yake sa ido a rayuwar mutane amma yake manta tasa rayuwar.

    Kuma haƙiƙa lallai gargaɗi ya zo daga shari’a game da irin wannan shagaltuwa abar zargi, kuma ɗabi’a mai guba, wadda ke lalata wa mutum addininsa, kuma ta ɓata masa lokacinsa. An karɓo daga Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: “Yana daga cikin alamomin kyawun Musuluncin mutum, barin abin da bai shafe shi ba” Tirmizi ne ya rawaito shi.

    Kuma Abubakar Allah ya ƙara masa yarda ya ce: “Lallai wasu mutane sun sadaukar da rayuwarsu ga wasunsu, kuma sun manta da kawunansu, saboda haka, ina hana ku ku zamto kamar su”.

    Kuma ya kamata a sani, ya ku bayin Allah, cewa: Lallai kafafen sada zumunta na zamani a mafi yawan lokuta sun zama matattarar rayuwa ta ƙarya, kuma wajen gasa marar amfani, sai cutar hassada da ƙiyayya ta shiga zukatan wasu, kuma fushi da ƙin juna ya yi naso a zukatansu, sai godiya da yabo ga Allah bisa nani’imominSa da baiwarwakinSa su yi ƙaranci.

    Kuma daga cikin sharrori da masifu akwai shafukan ƙarya na bogi da ke fesa gubarsu cikin al’umma, kuma suke yaɗa fitintinu da ƙarairayi, suna ƙirƙirar maganganu da jita-jita, kuma suna fatawowi na ƙarya da sunan malunta, a cikin wasu shirye-shirye da aka ɗau nauyinsu, da kuma ɓatanci da ake yi da gangan, waɗanda ba sa la’akari da addini ko kyakkyawar ɗabi’a.

    Abin mamaki baya ƙarewa game da wanda ke bibiyar irin waɗannan shafuka ba tare da tantancewa ba, yana gaggauta yaɗa abin da suka wallafa ba tare da jinkiri ba, kuma ba tare da komawa ga majiyoyin hukuma da amintattun tashoshi ba.
    Allah Maɗaukaki Ya ce:

    (Ya ku waɗanda kuka yi imani! Idan wani fasiki ya zo muku da wani labari, to ku yi bincike, don kada ku cuci mutane cikin rashin sani, sai ku wayi gari kuna masu nadama game da abin da kuka aikata)

    Ya ku mutane,
    Kuma akwai wata fitina da ke lalata zukata a lokutan kaɗaici, lokacin da mutum ya ke keɓancewa da wayarsa a wuraren da babu kowa, sai ya keta alfarmar addini, yana kallon haramtattun abubuwa, yana raina umarnin Allah, ba ya damuwa da abin da Allah Ya hana, yana mai manta irin cututtuka da annoba da irin waɗannan abubuwan kallo ke jawowa, da keta mutunci, da ɓata shekaru da lokuta, da kuma salwantar da kyawawan ayyuka.

    An karɓo daga Sauban Allah Ya ƙara masa yarda, daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Lallai ina sane da wasu mutane daga cikin al’ummata, za su zo a ranar alkiyama da kyawawan ayyuka masu girma kamar manyan duwatsun garin tihama farare, amma sai Allah Ya mayar da su ƙura abar sheƙewa)

    Sauban ya ce: Ya Manzon Allah, ka siffanta mana su, ka fito mana da su fili mana, saboda kada ya zama muna cikinsu alhali ba mu sani ba, sai ya ce: (Lallai su ‘yan’uwanku ne kuma daga cikin danginku, kuma suna ibada a wani sashe na dare kamar yadda kuke yi, sai dai su wasu irin mutane ne waɗanda idan suka keɓe da dokokin Allah sai su keta su) Ibn Majah ne ya rawaito shi.

    Ya ku bayin Allah, Allah Ya mana albarka cikin Alƙur’ani mai girma, kuma Ya amfanar da mu abin da ke cikinsa na ayoyi da ambato mai hikima, ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina neman gafarar Allah gare mu, don haka ku nemi gafaraSa, lallai Shi Mai yawan gafara ne da jinƙai.

    Huɗuba Ta Biyu

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah wanda Ya shiryar da mu zuwa ga hanyar samun rabo, kuma Ya nusantar da mu zuwa ga hanyar tsira, kuma Ya saukar da haske da rahama a cikin littafinSa, kuma Ya sanya shiriya da hikima a cikin sunnar AnnabinSa, kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba shi abokin tarayya, kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa, tsira da aminci da albarkar Allah su tabbata a gare shi, da Alayensa da Sahabbansa da wanda ya bi tafarkinsa zuwa ranar ƙarshe.

    Bayan haka, Ya ku ‘yan’uwa Muminai!
    Lallai daga cikin mafiya girman ni’imomin Allah akwai cewa mutum ya faɗaku game da tasgaronsa kafin ƙurewar lokaci, kuma ya lura da zuciyarsa kafin rufi ya mamaye ta, sau dayawa muna buƙatuwa ga maganin wannan alaƙa mai cutarwar a wannan duniya ta dijital da fasaha, hakan zai kasance ne ta hanyar ɗaga kafa, wanda da shi ne za mu daƙile guguwar amfani da waɗannan na’urori, ba wai don mu ƙaurace wa rayuwa ba, bari dai, sai don mu sabunta daidaito game da tasgaro da aka samu a rayuwarmu.

    Ibnul Jauziy ya ce: Ban taɓa ganin abin da ya fi amfani ga zuciya ba, fiye da ƙauracewar da mutum zai gano aibobinsa kuma ya riƙa nazari cikin makomar al’amuransa).

    Ya ku bayin Allah!
    Lallai addininmu addini ne na tsaka-tsaki da daidaito, don haka, ku ware wa ibada lokaci, haka rai ma a ba shi nasa kason, kuma iyalai ma a ba su rabonsu, haƙiƙa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya gaskata maganar Salman ga Abu Darda’i Allah Ya ƙara musu yarda cewa: (Lallai Ubangijinka Yana da hakki a kanka, kuma kai kanka kana da hakki a kanka, kuma iyalanka suna da hakki a kanka, don haka ka ba wa duk wani ma’abocin hakki hakkinsa) Bukhari ne ya rawaito shi.

    Kuma ku sani Allah Ya muku rahama cewa: Lallai fasaha ni’ima ce mai girma idan aka fuskantar da ita zuwa ga alheri kuma aka dabaibaye ta da dabaibayin shari’a da hikima, don haka ita ba tsagwaron sharri ba ce, kuma ba abar ƙyama ba ce a asalinta, bari dai, ita kamar takobi ne mai kaifi biyu, saboda haka ka zamto wanda yake amfani ba wanda ake amfani da shi ba, kuma na’urarka ta kasance hadima ba shugaba ba, kuma gada zuwa ga ɗa’a ba ramin da zai kai ka zuwa ga saɓo ba, kuma ta kasance tsani na samun ilimi da fahimta ba filin wasa na son zuciya da jahilci ba.

    Saboda haka ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah, kuma ku yi riƙo da sabbuban tsira, kuma ku riƙa tunawa koda yaushe cewa lallai za a tsayar da ku a gaban Ubangijinku, kuma za a tambaye ku game da gaɓɓanku, haƙiƙa Allah Mai girma da ɗaukaka Ya ce: (Lallai ji da gani da kuma tunani, duk waɗannan sun zama abin tambaya ne game da su).

    Don haka, ku ribaci shekarunku kuma ku mori lokutanku, domin duk wanda yaƙininsa ya gaskata, to zai yi da gaske kuma zai yi ƙoƙari, kuma duk wanda burinsa ya taƙaita, to zai yi guziri da tanadi, ya zo cikin Sahihu Muslim daga Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: ( Ka yi kwaɗayi kan abin da zai amfane ka, kuma ka nemi taimakon Allah kada ka yi ƙasa a gwiwa).

    Ya ku bayin Allah,
    Wannan kenan,
    Kuma ku yi salati da sallama ga wanda aka aiko shi da hikima da kuma shiriya, mafi alheri cikin halittu kuma mafi darajar wanda ya taka ƙasa, kamar yadda Ubangijinku Mai girma da ɗaukaka Ya umurce ku da hakan cewa: (Lallai Allah da Mala’ikunSa suna yi wa Annabi salati, ya ku waɗanda kuka yi imani, ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa).

    Ya Allah Ka yi salati ga Annabi Muhammad Manzo amintacce, da Alayen Annabi Muhammad, kamar yadda Ka yi salati ga Annabi Ibrahim da Alayen Annabi Ibrahim cikin talikai, lallai Kai Abin yabo ne Mai girma, kuma Ka yi albarka ga Annabi Muhammad da Alayen Annabi Muhammad kamar yadda Ka yi albarka ga Annabi Ibrahim da Alayen Annabi Ibrahim cikin talikai lallai Kai Abin yabo ne Mai girma.

    Ya Allah Ka yarda da Halifofi huɗu shiryayyu, jagorori masu shiryarwa, Abubakar da Umar da Usman da Aliyu, ya Allah Ka yarda da Sahabbai baki-ɗaya, da Tabi’ai da waɗanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar sakamako, Ka haɗa da mu cikin baiwarKa da karamcinka da kyautatawarKa ya Mafi karamcin masu karamci.
    Ya Allah Ka ɗaukaka Musulunci da Musulmi, Ka kare shingen addini, Ka sanya wannan ƙasa ta kasance mai aminci da lumana da yalwa, tare da sauran ƙasashen Musulmi ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah muna roƙon Ka dace da gamonkatar ga shugabanmu kuma majiɓincin al’amarinmu hadimin Masallatai biyu masu alfarma da magajinsa amintacce, kuma Ka saka musu da mafi alherin sakamako game da ƙasa da mutane da Musulunci da Musulmi. Ya Allah Ka taimaki jami’an tsaronmu da sojojinmu a kan iyakoki, Ka kare su da kariyarKa, Ka jiɓince su da kulawarKa ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah Ka yaye damuwar waɗanda suke cikin damuwa, Ka kwaranye baƙin cikin masu baƙin ciki, Ka biya bashin waɗanda ake bi bashi, Ka warkar da marasa lafiyarmu da na sauran Musulmi. Ya Allah Ka jiƙan mamatanmu da na sauran Musulmi, Ka taimaki masu rauna daga cikin Musulmi a kowane wuri, da kuma ƙasar Falasɗinu, ya Allah Ka ba su waraka daga dukkan damuwa, da mafita daga dukkan ƙunci, da kuɓuta daga dukkan bala’i, ya Allah Ka warkar da masu rauninsu, Ka tsare jinanensu, Ka tabbatar da zukatansu, ya Allah Ka kare Masallacin Ƙudus, Ka sanya shi ya zamto mai ɗaukaka da buwaya har zuwa ranar Alƙiyama.

    Ya ku bayin Allah
    Lallai Allah Yana umurni da yin adalci da kyautatawa da kuma bai wa makusanta taimako, kuma Yana hana alfasha da mummunan aiki da zalunci, Yana gargaɗin ku don ku wa’azantu, don haka ku ambaci Allah Maɗaukaki mai girma, Shi ma Zai ambace ku, kuma ambaton Allah shi ne abin da ya fi girma, kuma Allah yana sane da abin da kuke aikatawa.

    Don karanta Yadda Falalar Karanta Ayatul Kursiyyi Ya Ke danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Farfajiyar Ƙasar Hausa Jiya Da Yau

    Farfajiyar Ƙasar Hausa Jiya Da Yau

    Wannan babi yana ƙunshe da bayanan da suka danganci farfajiyar ƙasar Hausa a jiya da yau. An kuma duba yanaye-yanayen ƙasar Hausa dangane da mutanenta da halin zamantakewa da shugabanci da addininsu da kuma hanyoyin tattalin arzikinsu. Daga nan sai aka yi bayani kan ƙaura da shigowar baƙi ƙasar Hausa da matsayin Hausawa a yau.

    Farfajiyar Ƙasar Hausa Jiya da Yau

    Yana da matuƙar mahimmanci kafin mu baje kolin wannan nazari mu yi waiwaye domin sanin wurin da ƙasar Hausa take a jiya da kuma a yau. Ƙasar Hausa ta asali tana a Afrika ta Yamma ne, a farfajiyar da take tsakanin hamadar Sahara da dazuzzukan da suka doshi gaɓar tekun Atlantika daga kudu. Kuma ana kiran ƙasar da sunan Sudan ta Yamma, wato tsakanin Tafkin Chadi da gwiwar Kogin Kwara a can Yamma (Alhassan, 1982:1).

    A wata faɗar kuma an bayyana cewa ƙasar Hausa tana shimfiɗe ne a can Arewacin Nijeriya da kuma kudancin Jamhuriyar Nijar cikin Afrika ta Yamma. Daga Gabas ta yi iyaka da ƙasashen Borno. Daga Yamma ta yi iyaka da ƙasashen Dahomey a gaɓar Kogin Kwara. Daga Arewa ta yi iyaka da ƙasar Adar a cikin Jamhuriyar Nijar. Daga wajen Kudu kuma ta yi iyaka da ƙabilun Gwari da kuma ƙabilun kudancin Zariya da na Kudancin Bauchi (Ibrahim, 1982:1).

    Ƙasar Hausa wadda tana shimfiɗe a shiyyar Sudan ta tsakiya, a tsari irin na gargajiya a iya cewa ta haɗa da ƙasashen sarakunan Katsina da Kano da Daura da Zazzau (idan aka ɗebe kudancin Zazzau) da Argungu da Gwandu da Gumel da Haɗejiya da Ƙwanni da Maraɗi da Tassawa.

    Ni kuma a nawa hasashen ina ganin a yau, ƙasar Hausa yanki ne wanda ya mamaye dukkan Jihohin Katsina da Kano da Zamfara da Sakkwato da Arewacin Jihar Kaduna da wasu ɓangarori na Jihohin Kabi da Bauchi da Gwambe da Neja da kuma kudancin Jamhuriyar Nijar.

    Yanaye-Yanayen Ƙasar Hausa

    Mafi yawancin sassan ƙasar Hausa yana shimfiɗe ne kuma yana da yawan sarari, amma duk da haka akwai tsaunuka da tuddai a wasu wurare kamar Dutsin Dala da na Gwauron Dutse a Kano da Dutsin Dutsin-ma a jihar Katsina da Dutsin Kwatarkwashi a jihar Zamafara da Duwatsun Kufena a Zariya da sauransu.

    Akwai ‘yan dazuzzuka waɗanda suka haɗa da dajin Rugu wanda ya ratsa jihohin Katsina da Zamfara da dajin Falgore wanda ya ratsa jihar Kano da wani ɓangare na lardin Zazzau a jihar Kaduna. Yanayin dajin da yake a ƙasar Hausa iri biyu ne, da wanda ake kira “Sahel”, wato irin dajin da ake samu a arewa, da kuma dajin “Savanna” wanda ake samu a kudancin ƙasar.

    Akwai ƙarancin itatuwa a dajin “Sahel” kuma mafi yawancinsu gajeru ne. A lokacin rani da yawa daga cikin ganyayen da suke wannan daji sukan kakkaɓe, idan kuma damina ta kusa zuwa sai su fara tohuwa. Ciyawar da ake samu a wannan daji dabbobi kan cinye rabi su tattake rabin, amma da an yi ruwan tohon geza duk sai ta tsiro a ko’ina. Wuraren da wannan daji ya mamaye sun haɗa da dukkan kudancin Jamhuriyar Nijar da arewacin ƙasar Hausa a sassan jihohin Katsina da Kano da Jigawa da Zamfara da Sakkwato da Kabi.

    Daga dajin “Sahel” idan aka yi kudu kaɗan sai dajin “Savanna”. A irin wannan daji, itatuwa sun fi tsawo da kusanci da juna, haka kuma ana samun ganyaye da ciyayi da suke shekara cikin ɗanyantakarsu wato kore. Ana samun yanayin irin wannan daji a kudancin jihar Katsina da Lardin Zazzau a jihar Kaduna da Lardin Kabi da Yawuri a jihar Kabi da Kwantagora a jihar Neja (Alhassan, 1982:2-3).

    Duk faɗin ƙasar Hausa manyan koguna biyu ne suka ratsa ta cikinta da kogin Rima da kogin Haɗejiya. Kogin Rima shi ne ya taso daga ƙasar Zamfara ya malala ya yi Arewa zuwa cikin Jamhuriyar Nijar, daga nan sai ya karkata kudu ya bi ta yammacin Sakkwato ya je ya faɗa cikin kogin Kwara. Kogin Haɗejiya kuwa ya fara daga ƙasar Kano ya gangara ya yi gabas, ya bi ta Jama’are a jihar Bauchi, ya bi ta Gashuwa da Gaidam a jihar Yobe ya faɗa tabkin Chadi (Alhassan; 1981:3).

    Ta fuskar yanayin shekara ƙasar Hausa tana da yanayi iri biyu, lokacin damina da lokacin rani. Ana samun ruwan sama a lokacin damina wanda yakan fara daga watan bakwai na Hausa (Mayu) zuwa watan sha ɗaya na Hausa (Oktoba), kuma ruwan da ake samu ba mai yawa ne ƙwarai ba, amma duk da haka yana da albarka da biyan buƙatun manoma. Shi kuma lokacin rani yana farawa daga watan goma sha biyu na Hausa (Nuwamba) zuwa watan shida na Hausa (Afrilu), ya kuma rabu biyu wato lokacin ɗari da lokacin zafi ko bazara.

    Mutanen Ƙasar Hausa

    Mutanen ƙasar Hausa su ne ake kira Hausawa waɗanda masana da manazarta daban-daban suka kawo ra’ayoyinsu kan waɗanda suke ganin cewa su ne Hausawa. A ra’ayin wani masani ya bayyana cewa Hausawa su ne mutanen da suke zaune a ƙasar Hausa tun tuni, kuma suna magana da harshen Hausa a matsayin harshen uwa (Ibrahim, 1982:1)

    Wani masanin kuma yana ganin, Hausawa sun haɗa da mutanen nan waɗanda saboda ƙaura da magabatansu suka yi daga ƙasar Hausa zuwa wasu sassa da ke maƙwabtaka ta kusa ko ta nesa da ƙasar Hausa, ko da kuwa ba sa magana da harshen Hausa ko yin al’adun Hausawa sun ɗauka su Hausawa ne. Misali, Abakwariga da suke zaune a Jihar Taraba ta Nijeriya da kuma wasu da suke iƙirarin su Hausawa ne waɗanda suke zaune a ƙasashen Cote de Voire da Burkina Faso da Mali (Adamu, 1974:3).

    Akwai kuma waɗanda saboda ƙaura da magabatansu suka yi zuwa ƙasar Hausa sun manta da harshensu da adabinsu da al’adunsu na asali sun ɗauki na Hausawa. A taƙaice sun koma Hausawa a harshe da adabi da al’ada. Misalin ire-iren waɗannan mutane sun haɗa da Barebari da Kambarin Barebari da Barebarin Katsina da Buzaye da wasu Fulani (Adamu, 1974:4).

    Wani masanin kuma ya bayyana cewa Hausawa dai su ne mutane waɗanda harshensu shi ne Hausa, sannan dukkan al’adunsu da tadodinsu na Hausa. Haka kuma addinin Musulunci ya yi cikakken tasiri a kansu (Magaji, 1986:3).

    Mutanen ƙasar Hausa suna tafiyar da hanyoyin zamantakewarsu da shugabancinsu da addininsu da tattalin arzikinsu don cimma burin rayuwarsu na yau da kullum daidai da yanaye-yanayen ƙasarsu. Wannan ne ya ƙara taimaka masu suka kai ga matsayin da suke a yanzu, ya kuma ƙara taimakawa wajen shigowar baƙi wannan ƙasa.

    Danna don karanta Sana’ar Wanzanci Da Sauye-sauyen Zamani Jiya Da Yau (Shimfiɗa) 

    Wannan bayani an ciro shi ne daga kundin bincike mai taken: SANA’AR WANZANCI DA SAUYE-SAUYEN ZAMANI JIYA DA YAU wanda BASHIR ALIYU SAFANA SALLAU ya wallafa WANDA AKA GABATAR A TSANGAYAR FASAHA DA ADDININ MUSULUNCI SASHEN KOYAR DA HARSUNAN NIJERIYA JAMI’AR BAYERO, KANO, DOMIN CIKA WANI ƁANGARE NA SAMUN DIGIRI NA UKU (Ph.D) A FANNIN HAUSA

    MAYU 2009/JUMADA ULA 1430

    Edita@rumasau-kallamu

     

  • Yadda Falalar Karanta Ayatul Kursiyyi Ya Ke

    Yadda Falalar Karanta Ayatul Kursiyyi Ya Ke

    An karɓo daga Ubayyu ɗan ka’ab (Radiyallahu Anhu) ya ce: “Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) yace; “Ya baban Munzir, Shin kasan wacce aya ce mafi girma a cikin Al-ƙur’ani?

    Sai na ce: Allahu laa’ilaha illa huwal hayyul ƙayyum” yace: Sai ya bugi ƙirji na ya ce; ” Ina taya ka murnar ilimi, ya baban Munzir (Wato yana taya shi murnar sanin hakan).

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Karanta Amanar Rasulu Ta Ke danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Buɗe Karatun Alƙur’ani Da Bismillah A Cikin Sallah danna nan.

    Wannan bayani an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya walfa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Tarihin Alaramma Malam Salisu Ɗanruwantsa

    Tarihin Alaramma Malam Salisu Ɗanruwantsa

    An haifi Alaramma Malam Salisu ɗan Malam Ahmad ɗan Usmanu ɗan Ahmad a garin Ruwantsa. An ce asalin zuriyarsu sun fito daga ƙasar Mali, Alaramma Malam Salisu ya taso a garin Ruwantsa a inda ya fara karatu a wurin Malam Abdul’Aziz ɗan Malam Ibrahim.

    Lokacin da ya ƙara datawa kuma idonsa ya yi ƙwari, sai tsananin kwaɗayinsa ga Alƙur’ani ya ƙaru, ya ƙara duƙufa. Malam Salisu ya kasance tun ƙuruciyarsa ba ya zama wuri guda face yana tsakanin wancan gari da waccan tsangaya izuwa waccan cibiya ta makaranta. Wannan ya ba shi damar huɗuwa da gwarazan malaman zamaninsa irin su Malam Haruna Ningi wanda a wurinsa ne ya haddace AIƙur’ani Mai Girma.

    Koda Alaramma Malam Salisu ya sami labarin bayyanar Gwani Hamad a garin Taura kuwa; sai ya zabura ya haɗa kayansa ya nufe shi kuma ya kamfata daga marmaron ilmin Gwani Hamad. Daga nan kuma ya wuce garin Malamawa wurin Bajimin malami Malam Abdullahi. Malam Sal ısu bai gushe ba yana kutsawa cikin kowane loko da saƙo na ƙasar Kano da kewayenta; har sai da ya dangana da garin Insharuwa cikin Jamhuriyar Nijar.

    Bayan Dawowar Malam Salisu daga ƙasar Nijar ne ya yi aure a mahaifarsa. Daga nan ne ya taso tare da Wani adadi na almajiransa ya dawo Kano ya sauka Unguwar ƙofar Wambai; wurin Malam AbdulKarim inda ya karanta ilimin Tajwidi da Fiƙihu. Manyan malaman Malam Ɗanruwantsa sun haɗa da Shehin Malami Rabi’u Ɗantinki da Shehu Mai Hula. Bayan nan ne kuma ya sake zabura izuwa garin Ɗabbatta wurin babban malami Malam Adam; don sanin ilimi littafin Shaɗibiyya da ilmin Rasmu.

    Sannan ya sake dawowa birnin Kano karo na biyu a inda ya sauka a wurin Malam Garba Tudun Nufawa.

    Ya zauna shekaru biyu a wurinsa yan karantar Alfiyyar ɗan Malik. A lokaci guda kuma, shi Malam Garba Tudun Nufawa (Malam Abubakar Ramadan) yana koyon ilmin Tajwidi da Kira’o’i a wurinsa; Daga nan ne ya koma Unguwar Yakasai ya kafa makarantarsa a shekarar 1945.

    Bayan ya tumbatsa da ilmi da Alƙur’ani; daga bisani kuma ya koma Gwauron Dutse kusa da Masallacin Juma’a na Sheikh Is’haka Rabiu a matsayin Na’ibin Limamin Masallacin.

    A takaice dai zamu iya cewa Malam Salisu Ɗanruwantsa shi ne magajin kambin Shehi Rabiu Ɗantinki a fagen ilmin Alƙur’ani; da ƙira’o’i a faɗin Kanon Dabo. Tsangayarsa ta shahara da tsare-tsare masu ban sha’awa tare da sanya cigaban zamani a Wasu ɓangarori daban-daban. Alal misali, akwai tsarin azuzuwa inda ake sanya yara goma sha bakwai; a Kowane aji ana biya musu rabin sumuni da safe har sai sun haddace. Da yamma kuma a ƙara musu rabi don a samu kyakkyawar haddar AIƙur’ani.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Tarihin Alaramma Gambon Takai danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Tsarin Tsangayun Alƙu’ani A Arewacin Najeriya; Tarihin Su Da Zamantakewar Su Da Hanyoyin Raya Su; wanda Dr. Sunusi Iguda Ƙ/Nasarawa ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.