Tag: yadda ake

  • Sababbin Karin Maganar Hausa

    Sababbin Karin Maganar Hausa

    Sakamakon zagayowar ranar Hausa ta duniya ta shekarar 2025, ga wasu sabbin karin magana:

    1. Abin nema ya samu matar Bakano ta haifi buhun kuɗi.

    2. Abin nema ya samu matar Basakkwace ta haifi buhun taba.

    3. Abin nema ya samu matar Bazazzage ta haifi kunyar doya.

    4. Abin nema ya samu matar Ɗangaruwa da cikin tulu.

    5. Abin nema ya samu matar Marubuci ta haifi biro.

    6. Abin nema ya samu matar Ɗanjarida ta haifi amsa-kuwwa (Speaker)

    7. Abin nema ya samu matar liman ta haifi ladan.

    8. Abin nema ya samu matar Likita ta haifi allura.

    9. Abin nema ya samu matar mai-shayi ta haifi mummuƙi (burodi)

    10. Abin nema ya samu matar malami ta haifi alli.

    11. Abin nema ya samu matar Bafulatani ta haifi saniya.

    12. Abin nema ya samu matar direba ta haifi mota.

    13. Darajar sana’a wanzami yake taɓa gemun sarki.

    14. Ba kuka na ba, ɗan kishiya ya faɗa rijiya ya mutu.

    karanta Isra’i Da Mi’iraji

    Edita@rumasau-kallamu

  • Gudunmawar Sarki Abdulazeez Da Birtaniya Wajen Kafa Ƙasar Saudi Arabia

    Gudunmawar Sarki Abdulazeez Da Birtaniya Wajen Kafa Ƙasar Saudi Arabia

    Abdulaziz Ibn Saud da Kafuwar Ƙasar Saudi Arabia: Binciken Tarihi Kan Rawar Da Birtaniya Ta Taka

    Taƙaitaccen Bayani

    Ƙirƙirar masarautar Saudi Arabia a shekarar 1932 ba ta kasance wani abu da ya zo kwatsam ko kuma sakamakon ƙoƙarin gida kawai ba. A haƙiƙanin gaskiya, ta samo asali ne daga jerin yaƙe-yaƙe da dabarun siyasa da Abdulaziz Ibn Saud (1876–1953) ya gudanar har ya daidaita mulki a yankin Larabawa.

    Nasarorinsa na farko sun samo asali daga jarumta, basira, da kuma aƙidar Wahabiyya, amma daga baya rawar da Birtaniya ta taka ta zama tilas wajen tabbatar da ƙarfinsa. Wannan maƙala ta yi nazari kan yadda aka ci garuruwan Riyadh (1902), Makka (1925), Madina (1929), da Jidda (1932), tare da binciken yadda Birtaniya ta shiga wajen taimakawa kafuwar ƙasar Saudi Arabia.

    Gabatarwa

    Tashin Abdulaziz Ibn Saud, wanda aka fi sani da Ibn Saud, ya zama babbar alama a tarihin zamani na Larabawa. Rushewar ikon daular Usmaniyya bayan yaƙin duniya na ɗaya ya bar giɓi da shugabannin Larabawa daban-daban suka yi ƙoƙarin cikawa. Ibn Saud ya fito fili a matsayin babban mai kafa sabon ƙasa.

    Duk da cewa tarihin ƙasashen Larabawa na nuna cewa nasarorinsa sun fito daga ƙoƙari na cikin gida, shaidu na tarihi sun nuna cewa Birtaniya wadda take son tabbatar da tasirinta a Tekun Fasha da hanyoyin zuwa Indiya, ta taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar masa da iko.

    Yaƙin Ƙwace Riyadh (1902)

    Mataki na farko na kafa Saudi Arabia ya kasance a 15 ga Janairu, 1902, lokacin da Ibn Saud ya sake ɗaukar Riyadh daga gidan Rashid. Da ƙaramar tawaga, ya kai farmaki, ya kashe gwamnan Rashid, sannan ya maido da mulkin dangin Al Saud a Najd. A wannan lokaci, nasarar ta fito ne daga jarumta da ƙoƙarin kansa, ba tare da wani taimako daga ƙasashen waje ba. Birtaniya a lokacin tana fiye da kula da Kuwait da sauran ƙasashen Tekun Fasha, ba ta ba shi goyon baya kai tsaye ba.

    Yaƙin Hijaz da Ƙwace Makka (1925)

    Bayan ya tabbatar da iko a Najd, Ibn Saud ya nufi Hijaz, wanda Sharif Husayn bin Ali ke mulka shugaban juyin Larabawa a lokacin yaƙin duniya na ɗaya. Dangantakar Husayn da Birtaniya ta lalace saboda ya ƙi amincewa da tsarin da Turawa suka shimfiɗa a yankin. A 1924–1925, Ibn Saud ya shiga Hijaz, ya fatattaki sojojin Sharif, ya kuma mamaye Makka.

    Kodayake ba da taimakon kai tsaye Birtaniya ta yi ba, ƙin tallafa wa Sharif Husayn ya zama taimako a gefe ga Ibn Saud. Daga bisani kuma, Birtaniya ta amince da mulkinsa domin samun abokin hulɗa mai sauƙin sarrafawa a Hijaz.

    Ƙwace Madina da Yaƙin Ikhwan (1929)

    Bayan Makka, Ibn Saud ya mamaye Madina a shekarar 1929. Amma wannan nasara ta jawo cece-kuce tsakaninsa da Ikhwan, mayaƙan Wahhabi da suka taimaka masa a yaƙe-yaƙe. Ikhwan sun nuna rashin jituwa saboda tattaunawarsa da Birtaniya da kuma hana su ƙara faɗaɗa mulki zuwa Iraq da Kuwait (masu ƙarƙashin Birtaniya).

    Wannan rikici ya kai ga Yaƙin Sabilla (1929) inda Ibn Saud, da taimakon makamai, harsasai, da har ma jiragen saman yaƙi daga Birtaniya, ya fatattaki Ikhwan. Wannan ya nuna cewa a wannan lokaci, Birtaniya ta taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da nasararsa.

    Ƙwace Jidda da Ayya­na Saudi Arabia (1932)

    Birnin bakin teku na Jidda ya faɗi ƙarƙashin ikon Ibn Saud a 1932 bayan doguwar kakkabo. A wannan lokaci, Birtaniya ta riga ta amince da ikon sa ta fuskar diflomasiyya, ta kuma rattaba hannu kan yarjejeniyoyi da suka tabbatar da shi a matsayin shugaba na Najd da Hijaz. Ranar 23 ga Satumba, 1932, aka ayyana masarautar Saudi Arabia a hukumance. Wannan nasara ta samo asali ne daga haɗin gwiwar yaƙin soja da kuma goyon bayan diflomasiyyar Birtaniya.

    Kammalawa

    Shaidun tarihi sun nuna cewa tashi da nasarar Abdulaziz Ibn Saud ba za a iya raba su da muradun siyasar Birtaniya ba. Duk da cewa nasararsa ta farko a Riyadh ta fito daga ƙarfin kai, mamaye Makka, Madina, da Jidda ya kasance da taimako kai tsaye ko a kaikaice daga Birtaniya. Masarautar Saudi Arabia ta fito ne ba kawai daga jihadi da ƙoƙarin gida ba, amma har da hulɗar siyasar mulkin mallaka. Wannan fahimta ta taimaka wajen gane asalin Saudi Arabia da kuma dangantakarta da siyasar duniya tun asali.

    Ƙafafun Bayani

    1. Madawi al-Rasheed, A History of Saudi Arabia (Cambridge: Cambridge University Press, 2010), 34–36.

    2. Joseph Kostiner, The Making of Saudi Arabia, 1916–1936: From Chieftaincy to Monarchical State (Oxford: Oxford University Press, 1993), 82–85.

    3. John S. Habib, Ibn Sa‘ud’s Warriors of Islam: The Ikhwan of Najd and Their Role in the Creation of the Saudi Kingdom, 1910–1930 (Leiden: Brill, 1978), 205–210.

    Karanta Tarihin Kafuwar Ƙasar Iran

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ciwon Baki Yake (Mouth ulcers)

    Yadda Ciwon Baki Yake (Mouth ulcers)

    “Mouth ulcers” Ɗaya ne daga cikin ciwukan baki da a turance akan kirasa da canker sore (shankaso), Ƙaramin ciwo ne na kwailewar fata dake faruwa a cikin baki musamman a jikin leɓe ta ciki daga sama ko ƙasa, ko gefen leɓen daga hagu ko dama, wani lokacin kuma a ƙasan harshe. Yana da matuƙar zafi, zugi da raɗadi.

    Asali yana farawa ne daga ƙanƙanin kumburi kafin ya kwaile ko a ga yayi ja, inda daga nan sai fari-fari da ja inda nan take yakan iya fara zafi sosai, musamman idan aka ci abinci mai zafi, yaji, zaƙi ko mai ɗaci.

    Galibi girmansa ba ya wuce girman ƙwayar dawa ko ɗan abinda ba-a-rasa ba. Duk da yana hana sukuni amma lokuta da yawa yana warkewa da kansa cikin sati 1 zuwa 2.

    ME KE HADDASA SHI

    Wani lokacin akan rasa dalilinsa kai tsaye, amma a wasu garkuwar jikinsu ce ke cin kanta da kanta wato Autoimmune stomatitis wanda shi ke jawowa,  wanda za a ga har jini yake ya ƙi ya warke, ko ya warke bayan magani sai ya kuma dawowa, a ɗau shekaru ana fama, tunda Autoimmune ba shi da magani zuwa yanzu. Amma masu wancan nau’in ba su da yawa amma suna shan azaba.

    Sai a sauran mutane;

    1. Taune leɓe ko rauni a baki na daga abinda ke jawo shi, wanda wannan kuwa na nufin ko da ta hanyar taune leɓen ko harshe yayin cin abinci ko a mutane masu sanye da Braces na haƙora.

    2. Sannan rayuwa cikin matsatsi, wahala da damuwa wato dai “stress” kowanne iri ciki har da na lokacin Haila a Mata wato “stress during menstruation” na jawo irin wannan sore ɗin saboda motsawar Hormones daga normal zuwa Higher concentrations.

    3. Ƙarancin sinadaran bitamins da minirals musamman nau’in bitamin B12, iron, forlate da zinc, duk suna sanya mutum cikin hatsarin samun canker sore.

    4. Ciye-ciye ko mu’amala da abubuwan da jikin mutum ba ya so wato Allergic wanda wannan hatta a makilin akwai wanda bakinsa baya son wani nau’i na ingredients dinsa, ko abinci irin su; Ayaba, lemon ɓawo, chocolate, coffee, strawberries, gyaɗa, da cheese.

    5. Rashin samun isasshen bacci tare da gajiya wannan ma na ta’azzara matsalar.

    6. Sannan wani lokacin hakan na iya zama dalilin wani ciwo da ake da shi a jika ko dalilin wani magani da mutum ke sha, kamar magungunan chemotherapy a masu cutar Cancer, HIV, Magungunan tarin T.B, magungunan cutar farfaɗiya ko Sara (epilepsy seizures)

    7. Hakazalika shan taba sigari, wiwi ko SHISHA duk kan iya haddasa wannan yanayin, ko shan abu me zafi da ƙarancin tsaftar baki.

    MAGANIN MATSALAR

    1- Kamar yadda nace galibi yana warkewa da kansa, amma za ku iya: Riƙa wanke baki da ruwan gishiri sau 3 ko 4 a yini a riƙa kurkurawa ana wankewa musamman kafin kwanciya bacci.

    2- Shafa maganin rage zugi; irin su benzocaine gel ko alpa-xylocaine gel, ko magungunan shafawa da ke kashe ƙwayoyin cuta irin su BONJELA GEL ko wanke baki da CHLORHEXIDINE MOUTH WASH maimakon ruwan gishirin. Duk ana Saida su a manyan pharmacy store.

    3- Sai kiyaye cin abinci mai yaji, mai zafi ko mai zaƙi sosai.

    4- Sai kuma a riƙa shan ruwa sosai.

    IDAN DUK BAYAN WANNAN AKA GA YA CIGABA:

    Ta hanyar ganin yana ƙara a girma sosai, ko yana ciwo matuƙa wataƙila har da jini, ko bai warke cikin sati biyu ba, ko yana yawan dawowa bayan ya warke. To yana da kyau a zo a ga likita ko likitan haƙori don a duba ko akwai wata matsala ta cikin jiki da ke jawo hakan walau ƙarancin waɗancan vitamins ɗin, Autoimmune ko wasu cuttukan na ciki domin ulcer ma iya jawowa idan duodenal ce tunda jiki ba ya amfana da iron ɗin da ake samu idan akwai ta. Da fatan an ilmantu.

    Karanta Zubar Da Ruwa A Farko Da Kuma Ƙarshen Juna Biyu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Zikiri In An Zauna A Wani Majalisi

    Zikiri In An Zauna A Wani Majalisi

    Ibn Umar ya ce: an kasance an ƙirgawa ga Manzon Allah (Sallallahu alaihi wasalam) a majalisi kafin ya tashi, yana cewa sau ɗari:

    “Rabbigfir lii watub alayya innaka antat tauwaabul gafuuru”.

    {Ya Ubangijina! Ka gafarta mini, ka yi tuba a gare ni. Lallai kai ne Mai yawan karɓar tuba, Mai yawan gafara}.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Addu’ar Tashi Daga Majalisi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Sallar Walaha danna nan.

  • Tarihin Kafuwar Ƙasar Iran

    Tarihin Kafuwar Ƙasar Iran

    Tarihin Kafuwar Ƙasar Iran: Daga Tsoffin Dauloli zuwa Jamhuriyar Musulunci

    Tsakure

    Wannan maƙala ta yi nazari kan tarihin kafuwar ƙasar Iran, tun daga daulolin gargajiya na Persia har zuwa juyin juya halin musulunci na 1979.

    An bayyana yadda tsarin siyasa da al’adu suka samo asali daga daular Achaemenid, suka ci gaba da tasiri a zamanin Musulunci, sannan suka sauya zuwa tsarin zamani na Pahlavi kafin a kafa Jamhuriyar Musulunci ta Iran. Wannan bincike ya yi amfani da tarihin gargajiya, nazarin addini da tsarin siyasa don nuna muhimmancin Iran a matsayin cibiyar tarihi da tasiri a duniya.

    Gabatarwa

    Ƙasar Iran, wadda aka fi sani da Persia a tarihi, na daga cikin tsofaffin ƙasashen da suka taka muhimmiyar rawa wajen siyasa, al’adu, da addini a Gabas ta Tsakiya. Tsoffin masarautu irin su Achaemenid da Sassanid sun kafa tubalin al’adun Farisa, yayin da zuwan Musulunci ya sauya tsarin addini da siyasa.

    A ƙarni na ashirin, mulkin Pahlavi ya kawo gyare-gyaren zamani amma ya gamu da ƙalubale daga jama’a, wanda ya haifar da juyin juya halin 1979 da ya kafa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ƙarƙashin jagorancin Ayatollah Khomeini. Wannan maƙala za ta bi diddigi a matakai domin fahimtar kafuwar Iran a matsayin ƙasa ta zamani.

    1. Daulolin Gargajiya (Medes zuwa Sassanid)

    Daular Medes (728–550 K.Z.) ita ce ta fara kafa tsarin siyasa a yankin Zagros, kafin a gaji ta daular Achaemenid (550–330 K.Z.) ƙarƙashin Cyrus Mai Girma, wanda ya kafa babbar masarauta ta farko a duniya mai bin doka da adalci. Daular ta Achaemenid ta mamaye yankuna daga Indiya zuwa Masar, ta kafa tsarin gudanar da mulki mai tsari.

    Bayan mamayar Alexander the Great, an kafa Daular Seleucid, wadda daga bisani aka maye gurbinta da Daular Parthian (247 K.Z.–224 M.D.), wacce ta dawo da ƙarfin Persia. Daga baya kuma aka kafa Daular Sassanid (224–651 M.D.), wacce ta yi hamayya da Daular Roma da Byzantium, ta kafa harshen Farisa da addinin Zoroastrianism a matsayin ginshiƙai.

    2. Zuwan Musulunci da Tasirin Shi’a

    A shekarar 651 M.D., sojojin Musulmi suka doke Sassanid, suka kawo ƙarshen daular Farisa ta gargajiya. Iran ta shiga ƙarƙashin Daular Musulunci ta Umayyawa da Abbasawa. Daga baya, an samu dauloli masu zaman kansu kamar Buyids da Safavid (1501–1736), wadda ta kafa Shi’anci (Shi’a Islam) a matsayin addinin gwamnati. Wannan ya tabbatar da bambanci tsakanin Iran da makwabtan ƙasashe na Sunni.

    3. Mulkin Zamani: Qajar da Pahlavi

    Daular Qajar (1789–1925) ta fuskanci rauni saboda mamayar Rasha da Birtaniya, har aka raba wasu yankuna daga Iran. A 1925, Reza Shah Pahlavi ya kafa Daular Pahlavi, inda ya fara gyaran zamani da ƙarfafa tsarin mulkin mallaka na zamani. Sai dai ɗansa, Mohammad Reza Shah, ya zama ƙarƙashin tasirin kasashen yamma, musamman Amurka, abin da ya jawo ƙiyayya daga jama’a saboda rashin adalci da danniya.

    4. Juyin Juya Halin Musulunci Na 1979

    A ƙarƙashin jagorancin Ayatollah Ruhollah Khomeini, jama’a suka tashi suka kifar da mulkin Shah a 1979. An kafa Jamhuriyar Musulunci ta Iran, wacce ta haɗa tsarin dimokuraɗiyya da addinin Shi’a ƙarƙashin Velayat-e Faqih (Jagorancin Malamin Addini). A wannan tsarin, Shugaban ƙasa da Majalisa suna aiki ne ƙarƙashin ikon Jagoran Addini (Supreme Leader). Wannan ya bambanta Iran da sauran ƙasashen Musulmi.

    5. Matsayin Iran A Siyasar Duniya

    Bayan 1979, Iran ta zama cibiyar siyasa da addini ta Shi’a, tana da tasiri a Gabas ta Tsakiya da ma duniya saboda albarkatun man fetur, gas, da matsayinta a fagen yaƙin ideoloji tsakanin yamma da gabas. Iran ta ci gaba da zama ginshiƙi a harkokin duniya, musamman a rikicin Gabas ta Tsakiya.

    Kammalawa

    Tarihin kafuwar Iran ya sha bamban da kowane ƙasa a duniya, domin ya samo asali daga tsoffin dauloli, ya shiga karkashin Musulunci, sannan ya sauya zuwa tsarin zamani kafin juyin juya hali ya kafa Jamhuriyar Musulunci. Iran ta zama ƙasa mai ƙarfi wacce take da tasiri a al’adu, addini da siyasar duniya. Wannan tarihi ya nuna cewa Iran ba kawai ƙasa ba ce, amma cibiyar da take haɗa tsohon tarihi da zamani cikin tsari na musamman.

    Manazarta

    1. Richard N. Frye, The History of Ancient Iran (Munich: C.H. Beck, 1984).

    2. Touraj Daryaee, Sasanian Persia: The Rise and Fall of an Empire (London: I.B. Tauris, 2009).

    3. Patricia Crone, The Nativist Prophets of Early Islamic Iran (Cambridge: Cambridge University Press, 2012).

    4. Rula Jurdi Abisaab and Malek Abisaab, The Shi‘ites of Lebanon: Modernism, Communism, and Hizbullah’s Islamists (Syracuse: Syracuse University Press, 2014).

    5. Ervand Abrahamian, A History of Modern Iran (Cambridge: Cambridge University Press, 2008).

    6. Hamid Dabashi, Iran: A People Interrupted (New York: New Press, 2007).

    7. Kenneth M. Pollack, The Persian Puzzle: The Conflict Between Iran and America (New York: Random House, 2004).

    Danna nan don karanta Tarihin Kafuwar Ƙasar Saudi Arabia

    Edita@rumasau-kallamu

  • Tarihin Kafuwar Ƙasar Saudi Arabia

    Tarihin Kafuwar Ƙasar Saudi Arabia

    Ƙasar Saudi Arabia tana daga cikin muhimman ƙasashe a duniya, musamman ta fuskar addini da tattalin arziki. Kafuwar ta ta samo asali ne daga haɗin gwiwa tsakanin dangin Al Saud da akidar Sheikh Muhammad ibn Abd al-Wahhab a ƙarni na 18. Wannan haɗin gwiwa ya samar da Daular Saudiyya ta farko (1744–1818), wadda daga bisani ta faɗi, sannan aka kafa daular ta biyu (1824–1891).

    Sai dai babbar nasara ta kasance a lokacin Sarki Abdulaziz ibn Saud wanda ya kafa daular Saudiyya ta uku a 1932, wadda ita ce ƙasar Saudi Arabia ta yau. Wannan bincike zai yi bayani kan yadda aka gina ƙasar daga matakai daban-daban na tarihi.

    Gabatarwa

    Ƙasar Saudi Arabia ita ce cibiyar Musulunci wadda ke da wuraren ibada mafi tsarki: Makka da Madinah. Tarihinta bai tsaya kawai ga addini ba, har ma ya haɗa da siyasa, tattalin arziki, da tsari na zamantakewa. Wannan bincike zai tattauna matakan da suka kai ga kafa ƙasar a 1932, inda za a bayyana dauloli uku na Saudiyya da suka gabata kafin samun daular Saudiyya ta yau.

    Daular Saudiyya ta Farko (1744 – 1818)

    Daular Saudiyya ta farko ta samo asali ne daga haɗin gwiwa tsakanin Muhammad bin Saud, shugaba daga Najd, da Sheikh Muhammad ibn Abd al-Wahhab, wani malamin addini da ya yi kira da a tsarkake Musulunci daga bidi’o’i da al’adun gargajiya. Wannan haɗin gwiwa ya samar da tsarin siyasa-addini wanda ya ba da damar faɗaɗa iko a cikin Najd da Hijaz. Sai dai daular Usmaniyya tare da taimakon Masarawa suka kawo ƙarshen wannan daula a 1818.

    Daular Saudiyya ta Biyu (1824 – 1891)

    Bayan mutuwar daular farko, Turki bin Abdullah Al Saud ya kafa daular Saudiyya ta biyu a 1824, inda ya mayar da Riyadh a matsayin babban birni. Wannan daula ta yi ƙoƙarin ƙarfafa ikon Al Saud a Najd, amma ta fuskanci rikice-rikicen cikin gida da yaƙe-yaƙe da dangin Rashid daga Ha’il. A ƙarshe, dangin Saud suka sha kaye a 1891, lamarin da ya tilasta musu gudu zuwa Kuwait.

    Daular Saudiyya ta Uku – Kafuwar Saudi Arabia (1902 – 1932)

    A 1902, Abdulaziz ibn Abdul Rahman Al Saud (Ibn Saud) ya dawo daga gudun hijira ya kuma ƙwace garin Riyadh, abin da ya zama matakin farko na kafa daular Saudiyya ta uku. Tsakanin 1913 zuwa 1925, ya ci gaba da faɗaɗa mulkinsa, inda ya mamaye al-Ahsa, Najd, da Hijaz, har ya ƙwace Makka da Madinah.

    A 1927, ta hanyar Yarjejeniyar Jeddah, Birtaniya ta amince da ikon Ibn Saud a matsayin mai zaman kansa. A ranar 23 ga Satumba 1932, aka ayyana haɗewar dukkan yankuna a matsayin Ƙasar Saudi Arabia, ƙarƙashin mulkin Sarki Abdulaziz ibn Saud.

    Ci Gaban Ƙasar Bayan Kafuwa

    Bayan kafuwar ta, Saudiyya ta fara samun ƙarfi ne ta fuskar man fetur, wanda aka gano a 1938. Wannan ya sa ta zama ɗaya daga cikin ƙasashe mafi arziki, tare da kafa tsarin mulki bisa ga Alƙur’ani da Sunnah. Haka kuma, kasancewar ta da Makka da Madinah ya ƙara daɗa muhimmancinta a duniya.

    Kammalawa

    Tarihin Saudiyya ya ta’allaka da haɗin gwiwar siyasa da addini tsakanin dangin Al Saud da aƙidar Wahhabiyya. Duk da sauyin dauloli na farko da suka sha kaye, ƙoƙarin Sarki Abdulaziz ya haifar da kafa ƙasar Saudiyya ta yau a 1932. Wannan kafa ta sanya Saudi Arabia zama muhimmin ƙasa wajen addini, siyasa, da tattalin arzikin duniya.

    Manazarta

    1. Madawi al-Rasheed, A History of Saudi Arabia (Cambridge: Cambridge University Press, 2010).

    2. Alexei Vassiliev, The History of Saudi Arabia (London: Saqi Books, 2013).

    3. William Ochsenwald, Religion, Society, and the State in Arabia: The Hijaz under Ottoman Control, 1840–1908 (Columbus: Ohio State University Press, 1984).

    4. Joseph Kostiner, The Making of Saudi Arabia, 1916–1936: From Chieftaincy to Monarchical State (Oxford: Oxford University Press, 1993).

    5. Mai Yamani, Changed Identities: The Challenge of the New Generation in Saudi Arabia (London: Royal Institute of International Affairs, 2000).

    6. Madawi al-Rasheed, Politics in an Arabian Oasis: The Rashidis of Saudi Arabia (London: I.B. Tauris, 1991).

    7. Robert Lacey, The Kingdom: Arabia and the House of Saud (New York: Harcourt Brace Jovanovich, 1981).

    Karanta Tarihin Abubakar Malami SAN

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Falalar Suratul Falaƙi Da Nasi Take

    Yadda Falalar Suratul Falaƙi Da Nasi Take

    An karɓo daga Uƙubatu ɗan Amir (Radiyallahu Anhu) yace; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasalam) yace; “Ba ka ga waɗansu ayoyin da aka saukar da su jiya da daddare ba, ba a taɓa ganin irinsu ba”. Su ne ƙul’a’ uzu bi rabbi falaƙi” da ƙul’a’uzu birabbinnasi” (Muslim 814).

    Faɗakarwa

    Ina nasiha da ba da shawara ga ‘yan uwa musulmi da mu kula sosai da Alƙur’ani ta wajen haddace shi; da yawan karanta shi, da koƙarin fahimtar ma’anonisa da kuma yin aiki da shi; domin samun tsira da arziki da wadata a duniya da lahira.

    Allah ka sa mu dace, Allah ka sanya mu zama ahalinka a halin Alƙur’ani. Amin.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Zikiri Ya Ke danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Falalar Zikiri danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Zikiri Yayin Shiga Gida

    Zikiri Yayin Shiga Gida

    “Bismillaahi walajnaa, wa Bismillaahi kharajnaa, wa alal-laahi Rabbanaa tawakkalnaa”.

    {Da sunan Allah muka shiga, kuma da sunansa muka fita, kuma ga Allah kaɗai, Ubangijinmu, muka dogara}.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Addu’ar Tafiya Zuwa Masallaci danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Ake Tafiya Sujudah danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Garkuwar Musulmi Ta Addu’o’i Daga Alƙur’ani Da Sunna; wanda Sheikh Sa’id Ibn Ali Ibn Wahf Al-Kahdani ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Musa Ɗanƙwairo A Koyo Da Biyayyar Waƙa

    Musa Ɗanƙwairo A Koyo Da Biyayyar Waƙa

    Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun ya tashi, ya girma a gidansu; ya tarar da ana harka ta kiɗa da waƙa. Magabatansa tun daga Kaka Maiganga da mahaifinsa dukkansu makaɗa ne na noma; da yaƙi da kuma Sarauta da suka aiwatar da kiɗa da farar ganga da kuma gangar kotso.

    A bisa ɗabi’a ta gadon gida, mutum zai koyi abin da ya tarar ana gudanarwa a gidansu. Hausawa sukan ce, gadon gida alala ga rago, a yayin da Musa Ɗanqwairo ya fara tasawa, sai ya karkata wajen koyon abubuwa na hukunce-hukuncen addinin Musulunci da kuma hidimomin kiɗa da waƙa waɗanda suka shafi wasu harkoi na zamantakewar Hausawa.

    Musa Ɗanƙwairo ya fara biyayya ta sanin makamar waƙar baka tun a wajen mahaifinsa, Makaɗa Usman Ɗankwanagga24. A wajen mahaifin nasa ya koyi kaɗa kanzagi da karɓin waƙa da jajircewa a karin waƙa da samar da rauji na waƙa (Gusau, 2019: sh. 10-11).

    Haka kuma Musa Ɗanƙwairo ya daɗa gwangwajewa a zuba ɗiya na waƙar baka a biyayyar da ya yi a yayin Halifantakar da ya yi wa wansa Abdu Kurna. Domin himmar Musa Ɗanƙwairo da ƙwazonsa da basirarsa, wansa Sarkin Kiɗan Sarkin Maradun Abdu Kurna, ya naɗa shi ya zama Daudun Kiɗa kuma Ɗangaladimansa.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Musa Ɗanƙwairo a Gayaunar Waƙa danna nan.

    Don karanta cikakken bayani a kan Waƙar Shawara Ga Mai Bilicin danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Maganganu Na Ƙarya A Kan Kashe Husaini (RA)

    Maganganu Na Ƙarya A Kan Kashe Husaini (RA)

    Waɗanda suka rawaito labaran kashe Husaini (Radiyallahu Anhu) da kashe Usman (Radiyallahu Anhu) da sauran yaƙe-yaƙe sun ƙara ƙarerayi da yawa a cikin labaran.

    A cikin malamai da suka yi rubutu a kan kashe Husain (Radiyallahu Anhu); akwai manyan malamai irinsu su: Al-bagawi da lbn Abid Dunya; amma duk da haka akwai ruwayoyin da ba su inganta ba, har ma da na ƙarya a cikinsu.

    Su kuwa waɗanda suke kawo labaran ba tare da wani Isnadi ba, waɗannan su suka fi kawo ƙarerayi. Kamar yadda suke cewa wai ranar da aka kashe Husaini sai aka ga sama ta yi jawur; alhali wannan abu ne da yake faruwa-tun kafin wannan lokacin.

    Wai kuma a ranar duk dutsen da aka ɗaga sai an ga jini a ƙarƙashinsa; wai an yi wa zuri’ar Husaini (Radiyallahu Anhu) tsirara an ɗora su a kan raƙuma ko sirdi babu ana ta yawo da su wuri-wuri, ƙarya ne.

    Musulmi ba su taɓa kama wata mace daga banu Hashim ba a matsayin ribar yaƙi; sai dai masu son zuciya ba sa rabo da ƙarya.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wane Ne Ya Ba Da Umarni A Kashe Husaini? danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Dabarun Yaƙi danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gaskiyar Magana Akan Ashura wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.