Tag: yadda ake

  • Fitattun Iyayen Gida Na Ɗanƙwairo A Kiɗan Fada

    Fitattun Iyayen Gida Na Ɗanƙwairo A Kiɗan Fada

    Bisa dukkan hasashe, ubangida a wajen Makaɗi yakan zama mutum wanda ya nuna damuwa a harkoki da al’amurran makaɗi; wataƙila kuma makaɗin nan ya fi daidaita tunaninsa da zubin waƙoƙin da yake yi masa.

    Ubangida yakan zama murabbi ta fuskar kyautata ayyukan makaɗa don su zama na ƙwarai.

    Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo tun a farko-farkon tsundumarsa a cikin waƙoƙin baka, Allahu ya hore masa irin waɗannan dattawan iyayengida.

    Muhimmai daga cikinsu sun haɗa da:

    a) Abubakar na Birnin Ƙaya a Gundumar Maradun
    b) ‘Yandoton Tsahe, Alhaji Aliyu II (1960-1991)
    c) Sardaunan Sakkwato, Firimiyar Jihar Arewa, Alhaji Sir Ahmadu Bello Sakkwato (1962-1966)
    d) Sarkin Maradun Alhaji Abubakar (1939-1964)
    e) Sarkin Maradun Muhammadu Tambari (1964-1981)

    f) Sarkin Maradun Ibrahim II, Maigandi (1981-2003)
    g) Sarkin Daura, Alhaji Muhammadu Bashar (1966-2007)
    h) Sarkin Sudan, Alhaji Shehu Malami Wurno
    i) Sarkin Das, Alhaji Bilyaminu Usman
    j) Da sauransu

    Domin karanta cikakken bayani a kan Ƙungiyar Makaɗa Musa Ɗanƙwairo Ta Kiɗa danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Waƙa A Matsayin Sana’a danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Sauran Waɗanda Suka Yi Shahada Tare Da Husaini (Radiyallahu Anhu)

    Sauran Waɗanda Suka Yi Shahada Tare Da Husaini (Radiyallahu Anhu)

    Wani abun jan hankali shi ne sunayen waɗansu daga cikin ‘ya’yan Husaini da ƙannansa waɗanda suka gamu da ajalinsu a wannan lokaci a Karbala.

    Waɗannan sunaye su ne:

    1-Abubakar ɗan Aliyu ɗan Abi Talib (Radiyallahu Anhuma)
    2-Umar ɗan Aliyu ɗan Abi Talib (Radiyallahu Anhuma)
    3-Usman ɗan Aliyu ɗan Abi Talib (Radiyallahu Anhuma)
    4-Abubakar ɗan Husaini ɗan Aliyu (Radiyallahu Anhuma)
    5-Umar ɗan husaini ɗan Aliyu (Radiyallahu Anhuma).

    Wannan yana nuna yadda Ahlul Baiti (Radiyallahu Anhuma) suke matuƙar ƙaunar waɗannan sahabbai har suke sanyawa ‘ya’yansu sunayensu, wannan bai tsaya kan sayyidina Au da Husaini ba, a a kusan dukkan Imamai sha ɗaya sun bi sahu.

    Ɗan uwa karanta waɗannan sunaye:

    1-Umar ɗan Aliyu ɗan Abu Ɗalib (Al-atraf)(Radiyallahu Anhuma)
    2-Umar ɗan Muhammad ɗan Umar ɗan Aliyu (Radiyallahu Anhuma)
    3-Umar ɗan Husaini ɗan Au (Radiyallahu Anhuma)
    4-Umar ɗan Ali ɗan Husaini ɗan Ali (Al Ashraf)(Radiyallahu Anhuma)
    5-Umar ɗan Aliyu (Al-asgar) ɗan Umar (Al Ashraf) ɗan Aliyu zainul Abidina ɗan Husaini (Radiyallahu Anhuma)
    6-Umar ɗan Hasnul Aftus ɗan Aliyul Asgar ɗan Aliyu Zainul Abidin ɗan Husaini (Radiyallahu Anhuma)
    7-Umar ɗan Husaini ɗan Zaidu ɗan Aliyu ɗan Husaini ɗan Aliyu (Radiyallahu Anhuma)
    8-Umar ɗan Musal Ƙasim ɗan Ja’afarus Sadik (Radiyallahu Anhuma)
    9-Umar ɗan Husaini Sibti ɗan Aliy ɗan Abu Talib (Radiyallahu Anhuma)
    10-Umar ɗan Ja’afar ɗan Muhammad ɗan Umar Al-traf ɗan Aliyu (Radiyallahu Anhuma)

    11-Umar ɗan Muhammad ɗan Umar ɗan Aliyu ɗan Husaini Asshadi (Radiyallahu Anhuma)

    12-Umar ɗan Yahaya ɗan Husaini ɗan Zaid (Radiyallahu Anhuma)
    13-Umar ɗan Hasan ɗan Aliyu ɗan Husaini ɗan Aliyu Bin Abi Talib (Radiyallahu Anhuma).
    14-Abubakar ɗan Aliyu ɗan Abu Talib (Radiyallahu Anhuma)
    15-Abubakar ɗan Husaini ɗan Aliyu (Radiyallahu Anhuma)
    16- Abubakar ɗan Hasan ɗan Aliyu (Radiyallahu Anhuma)

    17-Abubakar ɗan Abdullahi ɗan Ja’afar ɗan Abu Talib (Radiyallahu Anhuma)
    18-Usman ɗan Aliyu ɗan Abu Talib (Radiyallahu Anhuma)
    19-Usman ɗan Akilu ɗan Abi Talib (Radiyallahu Anhuma)
    20-Usman ɗan Akilu ɗan Abi Talib (Radiyallahu Anhuma)
    21-A’isha ‘yar Musal Ƙazim ɗan Ja’afarus Sadik (Radiyallahu Anha)
    22-A’isha ‘yar Aliyu Rida ɗan Musal Kazim (Radiyallahu Anha)
    23-A’isha ‘yar Aliyu Abul Hasan ɗan Muhammad Jawad ɗan Aliyu Rida (Radiyallahu Anhuma)
    24-Mu’awiyya ɗan Aliyu ɗan Ja’afar ɗan Abu Talib (Radiyallahu Anhuma)
    25-Ɗalha ɗan Hasan ɗan Aliyu ɗan Abu Talib (Radiyallahu Anhu)

    Ya ɗan uwa mai karatu ka dubi yadda waɗannan bayin Allah suka sanyawa ‘ya’yansu sunayen waɗannan manyan sahabbai musamman Umar domin su nunawa kowa cewa su fa ba sa gaba da su ko a kusa ko a nesa, saboda ai babu yadda za a yi mutum ya yi ta sanyawa ‘ya’yansa sunayen waɗanda yake ganinsu a matsayin maƙiya, koma munafikai ko kafirai.

    A nan na ƙara kira ga ‘yan uwa masu da’awar son da bin Ahlul Baiti da su yi koyi da su, su daina ƙin sahabbai, musamman Abubakar, Umar, Usman, A’isha, Ɗalha da Mu’awiya, su daina zaginsu da tsine musu, su daina yi musu ƙage, saboda su Ahlul Baitin (Radiyallahu Anhuma) ba su yi haka ba. Ya Allah ka ganar da mu ka bamu ikon bin gaskiya. Amin.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Wa Ya Kashe Husaini (Radiyallahu Anhu) danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Azumin Tasu’a Da Ashura danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gaskiyar Magana A kan Ashura wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Waiwaye Kan Tattalin Arzikin Hausawa Na Gargajiya

    Waiwaye Kan Tattalin Arzikin Hausawa Na Gargajiya

    TUNA BAYA SHI NE ROKO: WAIWAYE KAN TATTALIN ARZIKIN HAUSAWA NA GARGAJIYA

    DAGA

    Kabiru Abdulkarim

    Kabiruabdulkarim996@gmail.com  08034510967

    Da

    HauwaMuhammadMaikudi

    hawwammaikudi@gmail.com  08098191994

    School of Languages,

    Kano State College of Education and Preliminary Studies.

    Takardar da aka gabatar a Bikin Taron Ranar Hausa ta Duniya a Kwalejin Ilimi da Share Fagen Shiga Jami’a Ta Kanoa ranar Talata 26 ga Agusta, 2025.

     TSAKURE

    Hausawa kan ce “Waiwaye adon tafiya”. Wannan takarda ta yi waiwaye ne a kan tattalin arziƙin Hausawa na gargajiya domin abin nan da Bahaushe ke cewa “Tuna baya shi ne roƙo”. An yi nazarin sana’o’in gargajiya na Hausa, saboda su ne ginshiƙan rayuwa da tattalin arziƙin yau da kullum na Hausawa (Garba 1991:1).

    Takardar ta gano cewa watsi da aka yi da waɗannan sana’o’i  namu na gargajiya, shi ya jefa mu cikin wannan hali na ƙaƙa-ni-ka-yi da matsin tattalin arziki da muke fama da shi a halin yanzu. Sannan an kawo shawarwari da ake ganin za su iya taimakawa sosai wajen rage wannan raɗaɗi da ake ciki da kuma mawuyacin hali da matasannmu suka tsunduma kansu a ciki na shan miyagun ƙwayoyi da ƙwacen waya da kuma faɗan daba.

    Gabatarwa

    An shirya wannan takarda ne da nufin yin waiwaye kan tattalin arziƙin Hausawa na gargajiya, ba don komai ba sai don a waiwaya a kuma gyara halayyar da Hausawa suka ɗauka a halin yanzu na watsi da sana’o’inmu na gargajiya, muka koma bilayi da bilinbituwar neman arziƙi ta wasu hanyoyi da ba su dace da mu ba, sannan kuma suke wahalar da mu, har suka ke neman kai Hausawa ƙasa warwas.

    Bahaushe a da ba shi da wani abin da ya sanya a gaba sai sana’a, wato neman na kansa. Amma a halin yanzu an bar sana’a an koma neman wasu hanyoyi da za a azurta kai da gaggawa, kuma arziƙin ya ƙi samuwa. An koma ba mu ga tsuntsu ba mu ga tarko. Bahaushe yana cewa “Sana’a Sa’a, kuma rashin sana’a Sata” (Mu’azu da Satatima 2013:61).

    Daga nan za mu fahimci cewa lallai Hausawa na wannan zamani, musamman matasa an doshi hanyar rugujewar al’umma. Don haka,  ya zama wajibi a koma ga sana’o’inmu na gargajiya domin ita ce kaɗai hanya mai ɓillewa wadda kuma ba ta da tangarɗa.

    Wannan tattalin arziƙi da muke magana a gargajiyance ya ƙunshi hanyoyin da Hausawa suka bi a dauri, suka zauna cikin ƙoshin lafiya da kwanciyar hankali da wanzuwar arziƙi, har ya kasance sun zama abin koyi da kuma ban sha’awa a idon duniya.

    Hausawa dai su ne al’ummar nan waɗanda harshen Hausa shi ne harshensu, kuma al’adunsu da ɗabi’unsu suka yi kama da na addinin Musulunci (Zarruq 1992:2). Gargajiya kuma tana nufin hanyoyin da aka saba bi na rayuwa. A nan gargajiyar Bahaushe ta kasu gida biyu: (a) kafin zuwan Musulunci da kuma (b) bayan zuwan Musulunci.

    • Kafin zuwan Musulunci: A nan ana nufin duka abubuwan da Hausawa suka saba yi na rayuwa tun daga farkon samuwarsu , wato lokacin Maguzanci har zuwa lokacin da suka haɗu da Larabawa.
    • Bayan zuwan Musulunci: Addinin Musulunci ya zo ƙarsar Hausa a tsakiyar ƙarni na sha huɗu zamanin Sarkin Kano Aliyu Yaji (1349-80), (Maiyama 2008:40-41), kimanin shekaru 676 da suka gabata. Bayan zuwan Musulunci Hausawa sun karvi addinin hannu bi-biyu. Dukkanin wasu kyawawan halaye da ɗabi’u sai suka cigaba da su, amma duk wasu abubuwa da suka ci karo da koyarwa da tarbiyyar addinin Musulunci sai suka yi watsi da su. Dalilin daɗewar musuluncin a ƙasar Hausa, sai ya sanya su ma al’adun da aka samu daga Larabawa, sai suka zama gargajiyar Bahaushe.
    • Lokacin zuwan Turawa(zamani):Zuwan Turawa tare da mulkin mallaka shi ne ake kira zamani. Turawa sun karɓe ikon ƙasar Hausa a 1903. Don haka duk wani abu da ya samu bayan zuwan Turawa ƙasar Hausa, to shi ba gargajiyar Bahaushe ba ne ya zama na zamani ke nan.

    Togaciya: Wannan takarda ta yi togaciya kan abubuwa kamar haka:

    • Akwai sana’o’i da dama da takardar ba ta dube su ko nazarce su ba, domin an tsara wasu Makarantu ko Kwalejoji  za su gabatar da su a wannan taro na ranar Hausa ta Duniya. Sana’o’in sun haɗa da Saƙa, Sassaƙa, Koli, Ƙira (babbaƙu), Dillanci da sauransu.
    • Akwai wasu sana’o’in da ko dai Hausawa na tababarsu cikin sahihancinsu kamar roƙo da raraka da tsibbu da makamantansu, takardar ba ta dube su ba. Haka sana’ar ƙunshi da wasu ke kallonta a gargajiyance kamar ba sana’a ba ce wato kwalliya ce, daga baya ne zamani ya ba ta gurbi ta zama cikakkiyar sana’a kuma mai gwaɓi.
    • Sana’o’in da takardar ta yi bayani, ana so ne a kafa hujja ko buga misali da su, ba wai su kaɗai ne suka fi sauran muhimmanci ba.
    • Wasu sana’o’in kuma an haƙura ba a kawo su ba saboda yanayin lokaci da gudun ka da abin ya yi yawa wai “shege da hauka”, misali Arkomi,da Asako,da Kiri,da Bugu,daAikatau wato Dakau,da Sirfau,da Niƙau da makamantansu.

    SANA’A

    Garba (1991:1) ya dubi sana’a da cewar ita ce ginshiƙin rayuwa da tattalin arziƙin yau da kullum na Hausawa tare kuma da ɗaya daga cikin muhimman manyan hanyoyin gano martabar mutum da ƙasaitarsa da matsayinsa cikin al’umma. Watau ban da noma wadda take ruwan dare, Hausawa suna kuma ƙara wa kansu wata sana’a wadda da rani ana samun abinci ta hanyarta, har ma ko da daminar akan taɓa wasu sana’o’i ƙari a kan noma.

    Umar (1983) a cikin D/Iya (2006:1) ya bayyana sana’a da cewa; “wata hanya ce da ɗan Adam kan ta’allaƙa a kanta domin samin abin masarufi wadda ta shafi sha’anin kasuwanci, wato sha’ani na saye da sayarwa”. Ya ci gaba da cewa; “sana’o’in suna da babban matsayi a al’adun kowacce al’umma”. Ga Bahaushe su ne ƙashin bayan tattalin arziƙinsa.

    A nan sana’a ta zo da sigogin ma’ana, akwai zaɓaɓɓun lokuta da yanayi ke tabbatar da sana’a. Wannan ya yi dai dai da azancin da ke cewa lokacin abu a yi shi. Ma’ana kowace sana’a da lokacin yinta, wannan yana haska yadda Al’ummar Hausawa suke da abin yi rani da damina, dare da rana, mace da namiji, yaro da babba. Haka shi yake nuna ba sa zaman kashe wando  koyaushe akwai abin yi.

    Rabe-raben Sana’a

    Masana da dama sun yi ƙoƙarin bayyana ko tsara sana’o’in Hausawa bisa kashi-kashi dangane da ra’ayoyinsu da fahimtarsu.

    Yahya da Ɗangambo (1986:173-174) sun tsara rabon sana’o’i zuwa gida uku. Sana’ar noma, da sana’ar sarrafa wani abu domin samar da wani abu. Misali ƙarfe-ƙira; zare – saƙa; fata – dukanci; sai sana’ar sarrafa jari da ƙwarewa, misali, kasuwanci, da gini, da tallau, da sauransu.

    Haka kuma Yahya (1992:4) su ma a cikin littafin sun raba sana’o’i zuwa gida uku inda suka tsara sana’o’i na noma da kasuwanci da waɗanda suke dafe-dafe.

    Ragowar rabe-raben sana’o’in na Hausawa, su ne rabo ta ɓangaren jinsi, ma’ana an raba sana’o’in a ɓangaren jinsi zuwa gida uku, jinsin maza da jinsin mata da kuma na tarayya. Abin nufi a nan shi ne, bisa ƙa’idojin al’adun Hausawa, ba kowacce sana’a kowa yake yi ba, a a kowace da mai yinta, waɗansu na mata ne, waɗansu na maza ne, waɗansu kuma kowane jinsi na iya aiwatar da su. Misali:

    Na maza Na mata Na tarayya

    Ƙira (babbaƙu) kitso saƙa

    Dukanci sussuƙa ƙira (farfaro)

    Jima dafe-dafe d.s dillanci

    rini aikatau

    wanzanci, da makamantansu.

    Noma

    Noma tushen arziki,

    Noma na duƙe tsohon ciniki,

    kowa ya zo duniya kai ya tarar.

    A bisa tsarin gargajiya, noman nan shi ne tushen rayuwa, domin ta nan ne ake samar da abinci da kuma bunƙasar tattalin arzikin al’umma. Burin kowanne magidanci ne ya noma isassahen abincin da zai ci da iyalinsa tsawon shekara. Haka kuma dole ne akwai buƙatar a noma abin sayarwa irin su auduga da gyaɗa don samun ‘yan kuɗin biyan buƙatun rayuwa. Haka kuma sana’ar noma ta haifar da wasu sana’o’i musamman na abinci daban-daban.

    Al’adar sana’ar noma ta yi wa rayuwar Bahaushe riga da wando, har ma da hula da takalmi. Bayan wadatuwa da abinci da abin masarufi, noman nan ya hana Bahaushe ragwanci da zaman kashe–wando. Ya tsare masa gabas da yamma ta fuskar cikar mutunci da kwarjini da cancanta ta kowace fuska. Don haka sana’ar  noma ta haifar da wasu sana’o’i irin su kiwo da saƙa da kaɗi da akasari sana’ar abinci da mata kan aiwatar daga cikin gida.

    Fawa

    Maza na Sarkin fawa,

    Kuna yawa ana rage gona,

    Fawa ko ta kwana ta fi tallan ƙosai,

    Sarkin fawa rikici gado,

    Kaɗauki bashi ka biya bashi,

    Na Inna kashin shanu,

    Hankaka mai da ɗan wani naka,

    Bungare mai billen ‘yanci,

    Na kulluru mayen ɗanye,

    Maƙiyinki ya dama fura ya fasa.

    Fawa sana’a ce ta yanka dabba a feɗe ta, a yanka ta gunduwa-gunduwa, tsoka-tsoka domin sayarwa ta yadda za a iya amfani da naman yadda ake sonsa. Ana iya sayar da shi a ɗanyensa, ko a gasa, wato tsire ko balangu ko kilishi da makamantansu.

    Farauta

    Gwarzon daji,

    Mai tsare ƙauyuka,

    Barde mai tsaron daji,

    Wanda baya tsoron daji,

    Masanin dabarun naman daji,

    Kai ne mai kawo tsoron-tsoro.

    Farauta ita ce sana”a

    Su

    Mai su uwar ɗaka.

    Wanda ke kawo ɗanɗano ga abinci,

    Mai ba wa duniya ƙanshin ƙanshi,

    Ɗawisu na alheri,

    Mai zuba wa rayuwa ɗanɗano.

    Su sana’a ce ta kamun kifi, musamman ga waɗanda suke zaune a gefen ruwa. Sana’a ce da ake kama kifi don ci ko don sayarwa.

    Jima

    Romon Jaɓa,

    Mai yi wa saurayi aure,

    Mai sai wa saurayi wando,

    Mai kula da lafiyar mutane

    Jima hannun magani,

    Ka sha baƙar wahala don farar fata,

    Ka zama ma ji ɗaukar alhini.

    Jima sana’a ce da ake tusarrufi da fata. Jima dai ita ce sana’ar sulluɓe fata don fitar da gashin da ke jikinta (Alhassan da wasu,1980:43) Jima tsohuwar sana’a ce a ƙasar Hausa da har yau take cin ganiyarta. Kamar yadda Alhaji Sule Garo, shugaban masu Masana’antun jima na zamani, ya faɗa a wata hira da aka yi da shi (a Radiyo France International,R.F.I.ranar Litinin,17 ga watan Augusta,2009 da misalin ƙarfe 3:17 na yamma), cewa ya yi duk da shigowar zamani, har yanzu sana’ar jima ta gargajiya tana da tasiri. Domin kamar yadda ya faɗa, su kamfanonin sarrafa fatar sun fi buƙatar waɗanda aka jeme su a gargajiyance don haka ma sukan yi masu ƙima ta musamman wajen saya (Ɓatagarawa 2013: 328).

    Rini

    Baban dubu mai kamu,

    Kowane ganye ya ruɓe ya lalace,

    Amma ban da kai na Sarkin Marina,

    Katsi katse tsiya,

    Toka takore tsiya na Makaman Marina,

    Kowa ya bar ka gidansa a sha lami.

    Rini kuwa sana’a ce ta gargajiya da ta shafi canza launin tufa ko zare daga fari ya koma wata kala daban. Wajen rini ana amfani da abubuwa irin su muciya da kwatarniya da guga da itace da baba da katsi da shuni da tukunyar baba da ruwa da sauransu

    Rini, sana’a ce ta gargajiya da a waɗansu wurare a ƙasar Hausa, har yanzu ana ado da ita. Duk da cewa an sami hanyoyi da dama na zamani inda ake amfani da launuka iri daban–daban, amma duk da haka har yanzu ana ba wa sana’ar ƙima  daraja ta musamman.

    Wanzanci

    Kala-kala magani gizo Ɗan Wanzam,

    Aska na cikin kube tana cin gashi,

    Ka ci gashi ka sha jini na Magaji Aska,

    Kai wa Sarki rotse ka tashi da martaba.

    Wanzanci sana’a ce da ake yin amfani da aska da ƙaho da tankolo da ƙugiya wajen aiwatar da ita. Masu wannan sana’a wato wanzamai suna tallafa wa rayuwar al’umma ta fuskar aiwatar da abubuwa kamar aski da ƙaho da kaciya (shayi ko kugunu) da tsagar anfill da shasshawa da cire beli ko hakin wuya da makamantansu.

    Ɗinki

    Ɗinki sana’a ce da ake amfani da zare a samar da sutura ingantacciya, yalwatacciya kuma kyakkyawa. Ɗinki hikima ce ta yin amfani da sililin zare, tare da allura a riƙa haɗa geffan kyallayen yadudduka a samar da tufafi ga maza da mata. Ɗinki ya rabu gida biyu wato ɗinkin tufafi da kuma ɗinkin huluna.

    Ƙira

    Huntu ubangijin mai riga.

    Ƙira sana’a ce mai dangantaka da ma’adanai da tsirrai da dabbobi. Sana’a ce da ake sarrafa ƙarfe da itace don samar da ma’aikaci. Ita ma wannan sana’a a iya cewa tana daga cikin sana’o’in farko-farko ma’ana tun lokacin da ɗan Adam ya fara zama wuri ɗaya. Ƙira ta zama tamkar uwa ma ba da mama a wurin sauran sana’o’i domin maƙeri ne yake samar masu kayan aikin sana’ar su.

    Sana’ar ƙira ta kasu gida biyu. wato maƙeran fari, da kuma maƙeran baƙi. Maƙeran fari su ne masu ƙera abubuwa dangin farin ƙarfe da azurfa da zinare da makamantansu. Su kuma maƙera baƙi su ne suke sarrafa  baƙin ƙarfe  dangin tama da tagulla.

    Ta hanyar ƙira ake samar da abubuwan amfani (ma’aikaci) irin su wuƙaƙe da gatura da adduna da faretani, da kuma makamai irin su takubba da masu da da kibiyoyi da makamantansu. Ka ga wannan ba ƙaramin tasiri suke da shi ba ta fuskar tattalin arziki da kuma harkokin tsaro a gargajiyance.

    Fatauci

    Fatauci sana’a ce da ta danganci kasuwanci. Akan bar gari a tafi wani garin domin kai haja can, sannan kuma a sayo wata a kawo gida. Masu wannan sana’a ana kiransa fatake. Da wannan sana’a ta fatauci Hausawa suka shahara a idon duniya. Sukan ɗauki kaya (haja) kamar fata da gyaɗa da auduga su kai sauran sassa na kudancin ƙasar nan ko ƙasashen ƙetare su sayo wasu kayan da ba a samunsu a ƙasar Hausa.

    Sukan ya-da zango a wasu garuruwa. Wanda a halin yanzu waɗannan wurare suka zama mallakin Hausawa a wajen ƙasar Hausa misali Zango ta Gwanja a ƙasar Ghana in da daga nan ne ake kawo goro zuwa ƙasar Hausa.

    Gini

    Gini sana’a ceta sarrafa abubuwa don samar da muhalli, daɗaɗɗiyar sana’a ce a ƙasar Hausa. Hasali ma dai a iya cewa ga al’ada kowa magini ne. Ma’ana ko da dai ba a nuna ƙwarewa ba to a ƙalla kowa yana iya sarrafa ƙasa, ko laka don yin gini. Waɗanda suka ƙware, sukan maishe ta sana’a, kuma su ake cewa magina. Magina sun kasu kashi biyu, akwai magina na ƙasa ko laka (siminti a zamanance) da suke sarrafa ƙasa don samar da muhalli.

    A ɗaya ɓangaren kuma akwai magina na yumɓu, waɗanda suke sarrafa yumɓu su samar da abubuwa irin su tukwane da kasake da murahu (amare) da tuluna da asusu da butoci da mazubai iri daban-daban. Akwai ire-iren waɗannan magina masu tarin yawa a ƙasar Hausa, kuma sun taka muhimmiyar rawa wajen baza harshe da al’adun Hausawa a wurare daban-daban ciki da wajen ƙasar Hausa. Adamu (1978:34).

    Matsayin Sana’a Wajen Bunƙasa Tattalin Arziƙin Hausawa:

    Ma’anar Tattalin Arziki

    Tattalin arziki shi ne yadda al’umma ke samar da abin da take buƙata da yadda take sarrafa shi, da amfani da albarkatun ƙasa domin samun ci gaba da walwala da biyan bukatunsu na yau da kullum.

    Ibrahim (2010) ya bayyana ma’anar tattalin arziki da cewa: “Tattalin arziki shi ne tsarin da al’umma ke bi wajen samar da abin da take buƙata daga albarkatun da ke hannunta da kuma yadda take sarrafa su.”

    Bunza (2002) ya bayyana cewa, “Tattalin arziki shi ne yadda al’umma ke tsara rayuwarta ta hanyar albarkatun da take da su, domin ci gaba, zaman lafiya da kuma walwala.”

     Bunƙasar Tattalin Arziƙin Hausawa

    Tattalin arzikin Hausawa ya bunƙasa sakamakon waɗannan sana’o’i da suke gudanarwa. Babu shakka Hausawa sun tsaya tare da jajircewa da bin wasu hanyoyi da ƙarfafa wa juna domin ganin tattalin arzikinsu ya bunƙasa daga waɗannan sana’o’i.

    Saboda irin jajircewar da suke yi a kan sana’o’insu har sai da ya zamo sun yi fice a fuskar noma ta inda suke noma, wannan ba ƙaramin bunƙasa tattalin arziƙinsu ya yi ba a wancan lokaci. Daga cikin hanyoyin da suka taimaka wajen bunƙasa wannan tattalin arziƙi sun haɗa da:

    Yadda wasu sana’o’in suke haifar da wasu sana’o’in: Ta hanyar haifuwar wasu sana’o’in a dalilin wasu, tattalin arzikin Hausawa ya bunƙasa matuƙa. Hakan na faruwa ne sakamakon duk lokacin da aka fari wani abu na sana’a to babu shakka za a samu majuɓunta a kan abin da suke samarwa.

    Wannan zai haifar da samun kuɗi ga masu wannan sana’a kai tsaye da ma sauran al’umma baki ɗaya. Misali Sana’ar noma, ta haifar da sa sana’o’i irin su kasuwanci, fatauci, ban gishiri na ba ka manda da nakamantansu.

    • Kiwo ya haifar da sana’ar fawa.
    • Fawa ta haifar da sana’ar jima.
    • Jima ta haifar da sana’ar dukanci.
    • Sana’ar kaɗi ta haifar da sana’ar saƙa da rini.
    • Saƙa ta haifar da sana’ar ɗinki.

    Bayan wannan akwai Sana’o’in da yawa da suka haifar da wasu sana’o’in, hakan ba ƙaramin bunƙasa tattalin arziƙin Hausawa ya yi ba.

    Samar da kayayyakin da suke na buƙatu a matakin farko: Yawa-yawan kayan da Sana’o’in suke samarwa, kaya ne da ake buƙatar su ko ma a ce suka zama dole a mallake su. Hakan ya sa da zarar an samar da su da an saye su (ga waɗanda ake ƙirƙira ko samarwa) Haka abun yake ga sana’o’i na hidima irin su aski, kitso da makamantansu. Ƙarin bayani a nan, a zamanin da Hausawa ba su fiya ɗora kansu a sana’o’i na jin daɗin rayuwa ba da suke haifar da almubazzaranci da rashin adani ba.

    Hanyoyin Bunƙasa Tattalin Arziƙin Hausawa

    Akwai hanyoyi da dama waɗanda suke taimaka wa Hausawa wajen bunƙasar tattalin arziƙi. Kaɗan daga ciki sun hada da:

    Gado: A da mutane suna gadar sana’o’i da suke yi ne daga magabatansu (gida). Wannan ya sa da wuya ka samu wanda yake ba shi da sana’ar yi, don kuwa mutum tun yana ƙarami yake koyan sana’ar da ya gani ana yi a gidansu. Hakan kan sanya ƙwarewa da kishin sana’ar ga masu yin ta. A dalilin haka da wuya ka ga mai zaman banza a wancan lokaci. Wannan ya sa kowa yana da abin yi, kuma tattalin arziƙin al’umma ya daɗa bunƙasa.

    Ban gishiri na ba ka manda: Wannan wani kasuwanci ne da ake yi ba da kuɗi ba. Ana yin sa ne ta hanyar musaya na abubuwan buƙata. Misali manomi zai iya ɗaukar hatsinsa ya kai wa mai fawa don ya ba shi nama. Ko ya ba wa wanzami don ya yi masa aski. Wannan shi ake kira da ban gishiri na ba ka manda . Haƙiƙa wannan ya taimaka wajen bunƙasa tattalin arziƙin Hausawa domin kuwa babu yadda za a yi kana da sana’ar ka ka rasa wani abu da kake buƙata ko da kuwa ba ka da kuɗin saye.

    Kiwo: Kiwo sana’a ce mai sirrin gaske ga al’ummar Hausawa. Ga mata har ma mazan a da ba a rasa su da yin kiwo. Idan biki ya taso ko haihuwa ko wata buƙata, mutum kan kama wata dabba tasa ya je ya sayar ya samu kuɗin biyan bukata nan take. Baya ga wannan, a lokacin da ake ciyar da dabbobi ciyawa akan zuba a ƙasa, to duk lokacin da dabbobin suka yi kashi, kashin kan haɗe da ragowar ciyawar da suka ci suka rage.

    Idan sun ruɓe sai su ba da takin noma. Irin wannan taki ya fi ba da albarkar noma da lafiya ga abin da aka shuka a gonar da aka zuba shi. Wannan ba ƙaramin kawo bunƙasar tattalin arziki ya yi ba a zamanin da, musamman idan an kwatanta shi da zamanin yanzu da ake sayen taki da tsada.

    Haɗin kai da tallafa wa juna: Yanayin yadda Hausawa suke aiwatar da sana’o’insu ya taimaka musu matuƙa wajen ƙara hada kawunansu. A sanadiyyar haka ya zamo akwai taimakon juna a duk lokacin da buƙatar hakan ta taso. Misali ko ba ka da jari za ka samu aron kayan aiki daga ‘yan’uwa ko abokan arziƙi don gudanar da sana’arka. Wannan shi ma ba ƙaramin taimaka musu ya yi ba wajen bunƙasa tattalin arziƙinsu.

    Mafi yawan masu sana’oi’n nan, suna ba da taimakon magunguna a cikin sana’o’in nasu, wannan yana ƙara masu kuɗaɗen shiga, kuma ya ƙara bunƙasa tattalin arziƙinsu. Misali manoma ne ke bayar da maganin ciwon baya da maganin rana.

    Haka kuma maƙera ne suke ba da maganin ƙunar wuta. Su kuma marina ana samun maganin lalurar fata kamar ƙyasbi da  ƙurajen bar- ni-da-mugu da katsi ga masu juna-biyu. Masunta suke bayar da maganin sanyi da ƙayar kifi. Mahauta suke bayar da maganin kaifi da kuma tsini da sauransu.

    Shawarwari

    • Saka gasa a wajen samar da kayayyaki daga lokaci zuwa lokaci don bunƙasa sana’o’in kamar yadda Ƙungiyar Zauren Hausa Nijeriya ta ɗauki gaɓaren yi.
    • Hukumar ilimi ta sanya shi a manhajar makarantu domin sanya shi cikin manyan darussa koyarwa a matakai daban-daban na ilimi.
    • Masu riƙe da sarautun gargajiya lallai ne su zama sun yi kira da wayar wa da jama’a kai tare da cusa sha’awa don amfani da irin kayayyakin da sana’o’in na gargajiya suke samarwa.
    • Jama’ar gari su ma ba a bar su a baya ba, lallai ne sai sun dawo daga rakiyar da ba ta ƙarewa, wato sun yi riƙo  hannu bibiyu wajen rungumar kayayyakin da sana’o’in mu suke samarwa.
    • Ba da tallafi na kuɗi da kayan aiki ga masu sana’o’in da shawarwari da dabaru daga ƙwararru na masana iri daban-daban.
    • Hukumomi na gwamnati su dinga amfani a kayayyakin da ake samarwa ta fuskar sana’o’in Hausawa na gargajiya.

    Kammalawa

    Waiwaye a kan sana’o’in gargajiya na Hausawa ya nuna cewa jajircewa da tsayawa tsayin daka a kan wasu sirrika da taimakon juna su ne tushen tattalin arziki da ci gaban al’umma a wancan lokaci, kuma har yanzu suna da daraja wajen kare martabar al’adu da samar da ayyukan yi a cikin al’umma.

    Manazarta

    Adamu, M. (1978), The Hausa Factor In West African History. Zaria/Ibadan A.B.U. and Oxford,.

    Alhassan H. da wasu, (1980), Zaman Hausawa, Littafi Na Ɗaya  Zaria. .I.E.P.,A.B.U.

    Aliyu, U. (2015). Kasuwanci da Cigaban Al’umma. Zaria: Ahmadu Bello University Press.

    Aminu, K. (2000). “Saka Sana’ar Sarrafa Auduga a Kasar Hausa: Tasirinta da Muhimmancinta.” Kundin Degree na Farko. Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano.

    Asiru, A. (2017). Sana’ar Dinki Da Ci Gabanta. Zaria: Amadu Bello University Press Limited.

    Bashir, I.S. (1990). “Take da Kirarin Sana’o’in Gargajiya: Nazarin Ma’anarsu da Muhimmancinsu ga Rayuwar Hausawa.” Kundin Digiri na Biyu. Jami’ar Bayero, Kano.

    Batagarawa , S.A.(2013). Nason Wasu Al’adu a Kan Sana’o’in  Gargajiya na Hausawa Mazauna Lokoja. Takardar da aka gabatar a taron ƙarawa juna sani na kasa da kasa mai taken “Tavarvarewar Al’adun Hausawa a Yau” wanda Sashen Koyar da Harshunan Nijeriya  na Jami’ar Umaru Musa Yar’adua tare da hadin gwiwar Hukumar Adana Tarihi da Al’adu ta Jihar Katsina a ranakun 25-26 ga watan Yuni, 2013.

    Dan’iya, M. A. (2006). Tasirin Kimiyya da Ƙere-ƙeren Zamani a kan Sana’o’in Hausawa na Gargajiya. Kano: Kabs Print Services Nigeria.

    Garba, C. Y. (1991). Sana’o’in Gargajiya a Ƙasar Hausa. Ibadan: Spectrum Books Ltd.

    Ibrahim, M. (2010). Tattalin Arzikin Hausawa. Kano: Benchmark Publishers.

    Madabo, M.H. (1979). Ciniki da Sana’o’i a Kasar Hausa. Lagos: Nelson.

    Madauci, I. da wasu (1968). Hausa Customs. Zaria: Northern Nigeria Publishing Company Ltd.

    Maiyama, U.H. (2008): Sata A Zamantakewar Hausawa (Nazarin Waƙoƙin Barayi Na Muhammadu Gambo Fagada) Kundin Digiri Na Uku Da Aka Gabatar A sashen Nazrin Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.

    Mu’azu, A da Satatima,I.G. (2013). Kwaɗon Al’adun Hausawa da na Wasu Ƙabilu. Takardar da aka gabatar a taron ƙarawa juna sani na kasa da kasa mai taken “Tavarvarewar Al’adun Hausawa a Yau” wanda Sashen Koyar da Harshunan Nijeriya  na Jami’ar Umaru Musa Yar’adua tare da hadin gwiwar Hukumar Adana Tarihi da Al’adu ta Jihar Katsina a ranakun 25-26 ga watan Yuni, 2013.

    Sani, A. (2003). Hanyoyin Rayuwa da Aikin Yi a Najeriya. Kaduna: Fisbas Media.

    Smith, A. (1776). An Inquiry into the Nature and Causes of the Wealth of Nations. London: W. Strahan and T. Cadell.

    Yahya,  I.Y. da Ɗangambo, A. (1986). Jagoran Nazarin Hausa. Zaria: Northern Nigeria Publishing Company Limited.

    Yahya, I. Y. da wasu (1992). Darussan Hausa don Manyan Makarantun Sakandare. Ibadan: University Presss Plc.

    Karanta Hanyoyin Zamantakewar Hausawa 

    Edita@rumasau-kallamu

  • Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 15th August 2025

    Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya Daga Masallaci Mai Alfarma 15th August 2025

    Huɗubar Juma’a daga Masallaci mai alfarma:21 Safar 1447
    15 August 2025
    Mai huɗuba: Sheikh Dr. Bandar bin Abdul-Aziz Badila
    Mai fassara: Dr. Usman Muhammad Ahmad
    Shugaban sashi: Dr. Abdulkarim Tahir Abdullahi

    Huɗuba ta farko:
    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Ya halicci halittu kuma Ya ƙaddara ƙaddarori, Ya rarraba arziki kuma Ya rubuta ajali, muna yaba masa tsarki ya tabbata a gare Shi kuma muna gode masa, Ya fari halittar rayuwa kuma Ya gudanar da ƙoramu, Ya shimfiɗa ƙasa kuma Ya tsaga tekuna.

    Kuma ina shaidawa lallai babu abin bauta bisa cancanta sai Allah, Shi kaɗai ba Shi da abokin tarayya, Ya hore rana da wata, da dare da yini. Kuma ina shaidawa lallai Annabi Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa, kuma zaɓaɓɓen Annabinsa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, da alayensa tsarkaka, da sahabbansa nagartattu, da waɗanda suka biyo su da kyautatawa a dukkan darare da yini.

    Bayan haka:
    Ya ku mutane! Ina muku wasici da ni kaina da tsoron Allah, ku ji tsoron Allah, Allah Ya muku rahama, kuma ku sani cewa babu abin da ke faruwa a cikin wannan rayuwa face sai da ƙaddarar Allah da kuma nufinsa, da hikimarsa da iradarsa; na dare da yini, da iska da ruwan sama, da sanyi mai tsanani da zafi, da sauye-sauyen yanayi da maimaituwarsa, abin da zai sa mumini ya tabbatar da cewa wannan duniya ba gidan dawwama ba ce.

    Kuma wannan gaba ɗayansa yana daga cikin ayoyin Allah na halitta masu nuna girman ƙarfinsa da ikonsa, da yalwar iliminsa da hikimarsa, da zurfin nufinsa da rahamarsa, da kuma cewa kowane abu a wurinsa tsarki ya tabbata a gare Shi yana da iyaka.
    ((Lallai a cikin halittar sammai da ƙasa da sassaɓawar dare da rana, tabbas akwai ayoyi ga ma’abota hankula Su ne waɗanda suke ambaton Allah a tsaye da kuma zaune da kuma kishingiɗe, suna kuma tunani a kan halittar sammai da ƙasa (suna cewa: “Ya Ubangijinmu, ba Ka halicci wannan a banza ba, tsarki ya tabbata gare Ka, Ka tsare mu daga azabar wuta)).

    Ya ku bayin Allah!
    Waye a cikinmu da zafin rani bai taɓa cutar da shi ba? Kuma waye a cikinmu da ƙunar rana ba ta taɓa ƙona fuskarsa ba? Dukanmu mun samu rabonmu daga wannan, ko dai kaɗan ko ko dayawa, lallai wannan shi ne zafin rani, mai wa’azin nan da Allah Yake tunatar da bayinsa zafin taron alƙiyama da azabar wuta da shi.

    An rawaito daga Miƙdad ɗan Aswad Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa: (Za a kusanto da rana ga halittu a ranar alƙiyama har ta kasance kamar tazarar mil daga gare su). Sulaim ɗan ‘Amir ya ce: Na rantse da Allah ban san me yake nufi da mil ba, yana nufin na tazarar ƙasa, ko ko mil da ake amfani da shi wajen sanya kwalli a ido? Ya ce: (Sai mutane su kasance cikin zufa gwargwadon ayyukansu; daga cikinsu akwai wanda zufa za ta kai masa idanuwan sawu, akwai kuma wanda za ta kai masa gwiwoyi, akwai wanda za ta kai masa zuwa ga kwuiɓinsa, akwai kuma wanda zufa za ta yi wa bakinsa linzami sosai). Sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yi nuni zuwa ga bakinsa da hannunsa. Muslim ne ya rawaito shi.

    Ya ku musulmi!
    Lallai tsananin zafi yana daga cikin ayoyin da Allah yake aiko wa bayinsa don tsoratarwa da tunatarwa, da zama wa’azi da ɗaukan izina, kamar yadda Allah Ya ce: ((Kuma ba Ma aiko da ayoyi sai don tsoratarwa)).

    An rawaito aga Abu Huraira Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Wuta ta kai kokenta ga Ubangijinta, ta ce: Ya Ubangiji, sashina na cin sashi, sai Ya ba ta izinin numfasawa sau biyu; numfasawa a lokacin sanyi, da numfasawa a lokacin zafi, to wannan shi ne mafi tsananin zafin da kuke ji a lokacin rani, da kuma mafi tsananin sanyi da kuke ji a lokacin hunturu). Bukhari da Muslim ne suka rawaito.

    To, ya ku muminai! Mai rabo, shi ne wanda ya yi guzuri daga zafin duniya domin kuɓuta daga zafin lahira, da kuma wanda ya yi haƙuri da ibada a lokacin tsananin zafi, domin ya more ni’imar da ba ta ƙarewa a ranar da za a tona ɓoyayyun sirrikan zukata.
    ((Ya ku waɗanda kuka yi imani, ku kare kanku da iyalanku daga wuta, wacce makamashinta mutane ne da duwatsu, masu kula da ita mala’iku ne masu kaushin hali, masu tsananin gaske, ba sa saɓa wa Allah abin da Ya umarce su, kuma suna aikata abin da aka umarce su da aikata shi)).

    An rawaito daga Abu Sa’id Alkhudri Allah ya ƙara masa yarda ya ce: Na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa: (Duk wanda ya yi azumin yini ɗaya saboda Allah, Allah zai nesanta fuskarsa daga wuta na tsawon shekara saba’in). Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi.

    Kuma Abu Darda Allah ya ƙara masa yarda ya kasance yana cewa: “Ku azumci yini mai tsananin zafin rana saboda kuɓuta daga zafin ranar tashin alƙiyama, kuma ku yi raka’a biyu cikin duhun dare saboda ku kuɓuta daga duhun ƙaburbura”. Abu Nu’aim ne ya rawaito shi a Hilya.

    Kuma ku sani Allah Ya jiƙan ku cewa dukkan abin da zai samu mumini a cikin zafi na tsanani da wahala, da gajiya da ƙosawa, to, dukkansu za a rubuta su, za a kiyaye su kuma za a ƙididdige su, a wajen Wanda ayyukan ƙwarai ba sa tozarta a wajensa, kuma ba a rasa ayyukan ɗa’a a wajensa, da su za a kankare zunubai, kuma a ninka kyawawa, kuma a ɗaga darajoji.

    An rawaito daga Abu Sa’id da Abu Huraira Allah Ya ƙara musu yarda, sun ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Babu wani abu da zai samu musulmi, na ciwo, ko wahala, ko jinya, ko bakin ciki, har ma da damuwa da za ta sauko masa, face sai an kankare masa zunubansa da shi). Muslim ne ya rawaito shi.

    Kuma lallai ayyuka ana ninninka ladansu, kuma ana ƙara sakamakonsu, kuma ma’auninsu na nauyaya, da gwargwadon abin da ya tabbata na niyya da ikhlasi da juriya da haƙuri a zukatan ma’abotansu. Ibnul Asir Allah Ya yi masa rahama ya ce: “Kuma neman lada a cikin ayyuka nagartattu da kuma lokacin da ake ƙi, shi ne gaugawa zuwa ga neman lada da kuma samun sa ta hanyar miƙa wuya da haƙuri”. Ƙarshen maganarsa kenan.

    Kuma yana daga cikin rahamar Allah ga bayinsa shar’anta musu abin da za su iya yi na ayyuka da ya yi, kuma bai ɗaura musu abin da zai wahalar da su ba, an rawaito daga Abu Huraira Allah Ya ƙara masa yarda, daga Annabi tsirda da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: (Idan zafi ya tsananta, to ku sanyaya sallarku, saboda tsananin zafi daga hucin Jahannama yake). Bukhari da Muslim ne suka rawaito. Abin da ake nufi da sanyaya salla, shi ne jinkirta ta zuwa ƙarshen lokacinta, lokacin da zafin garji zai yi sauƙi, kafin shigar lokacin sallar da za ta biyo bayanta.

    Kuma za a gwama dukkan wata ibada da ke cikin jinsinta da ita, cikin abin da ya halatta a jinkirta shi, don haka, duk wanda ake bin shi azumi na watan Ramadan, ko kuma kaffara ta azumi ko makamancin haka, to, ya halatta a gare shi ya jinkirta shi zuwa ga lokutan sanyi, idan biyansa a lokacin zafi zai ba shi wahala, akwai hadisin A’isha Allah Ya ƙara mata yarda da yake nuni a kan haka, ta ce: “a kan samu wani lokaci da ake bi na azumi da na sha tun a watan Ramadan, amma na kasa samun daman biya sai a watan Sha’aban”. Bukhari da Muslim ne suka rawaito. Amma gaggauta biya shi ya fi,

    Don haka, ya ku bayin Allah!
    Ku gode wa Allah a bisa dukkan hali da yanayi, kuma ku gade masa a kan abin da Ya tanada muku na hanyoyi da sabuba, waɗanda Ya sauƙaƙe muku wahalar zafi da tsananinsa da su, da ƙunarsa da hucinsa, da na’urorin sanyayawa da wuraren hutu a lokacin zafin rani, kuma ku riƙa bincikan halin ‘yan uwanku talakawa da marasa abin hannu, kuma ku sauƙaƙa musu abin da suke fama da shi na tsananin zafi da ƙunar rana, kowa ya yi dai dai ƙarfinsa da ikonsa, kuma daga cikin haka akwai shayar da ruwa mai sanyi a waɗannan lokuta na zafi, saboda hakan yana daga cikin sadokoki mafiya falala, kamar yadda Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ba mu labarin hakan.

    Kuma ku riƙa tunawa da wasu ‘yan’uwanku a Addini, waɗanda raɗaɗin rashi da tawaya ta dukiya da rayuka da ‘ya’yan itacuwa suka ƙaru a gare su a kan abin da suke fama da shi na tsananin zafi, ya Allah Ka yaye musu abin da ya sauko musu, ya Allah Ka sauya tsoronsu da aminci, biƙin cikinsu da farin ciki, yunwarsu da ƙoshi, kuma Ka taimake su a kan maƙiyanka kuma maƙiyansu ya Mai ƙarfi ya Mabuwayi.

    Ina faɗin wannan magana tawa, kuma ina nema wa kaina gafarar Allah, da ku da sauran musulmi, daga kowane zunubi, don haka ku nemi gafararsa, lallai Shi Mai yawan gafara ne kuma Mai jinƙai.

    Huɗuba ta biyu:

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, Wanda dukkan al’amura suke samuwa daga aikinsa da nufinsa, muna yaba masa tsarki ya tabbata a gare Shi kuma muna gode masa a bisa falalarsa mai yalwa da ni’imominsa, da kyakkyawar afuwarsa da gafararsa, tsira da amincin Allah su ƙara tabbata ga mafificin Manzanninsa kuma zaɓɓaɓensa, da alayensa, da sahabbansa da tabi’ai, da waɗanda suka biyo su da kyautatawa har zuwa ranar rarrabewa da tashin alƙiyama.

    Bayan haka: Ku sani, Allah Ya muku rahama, cewa lallai bayyana fushi da raki don tsananin zafi yana daga cikin suka ga hukuncin Allah da ƙaddararsa, da nufinsa da ganin damansa, da kuma cewa lallai babu abin da zai auku a wannan duniya face sai da wata hikima da maslaha da fa’ida da amfani, daga cikin haka akwai yadda muke ganin dayawa daga cikin shukoki da ‘ya’yan itatuwa ba sa yin daɗi kuma ba sa daidaituwa har sai lokacin da rani ya kai maƙurarsa, haka kuma dayawa daga cikin cututtuka da annoba ba sa ɓacewa har sai lokacin da zafi ya kai ƙololuwar matakinsa, Ibnul Ƙayyim Allah Ya masa rahama ya ce:

    “A lokacin rani, iska na rikiɗewa ta yi zafi sosai, sai ‘ya’yan itatuwa su nuna, kuma sauran ababe marasa amfani da ababen da suka cakuɗu da jiki su gushe a lokacin hunturu, kuma sai sanyi ya kutsa ya shiga cikkuna, don haka ne ma maramaren ruwa da rijiyoyi suke yin sanyi”. Ƙarshen maganarsa kenan.

    Saboda haka, ku ji tsoron Allah, ya ku bayin Allah, kuma ku kiyaye zukatanku da harsunanku daga dukkan abin da zai rage imaninku, ya lalata tauhidinku, domin yana daga cikin cikar tauhidi yarda da kuma miƙa wuya ga dokokin Allah na shari’a da tsarinsa na gudanar da duniya.

    Sannan ku yi salati da sallama ga mafi alherin halittun Allah, Muhammadu bin Abdullahi, domin Ubangijinku Ya umarce ku da hakan, sai Ya ce: ((Lallai Allah da mala’ikunsa suna salati ga Annabi; ya ku waɗanda kuka yi imani, ku yi salati a gare shi da sallama mai yawa)).

    Ya Allah, Ka yi salati da sallama, da ƙarin daraja da albarka ga bawanka kuma ManzonKa, Annabinmu Muhammadu, kuma ka ƙara yarda da sahabbai baki ɗaya, da tabi’ai, da waɗanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.
    Ya Allah, ka ɗaukaka Musulunci da Musulmai, Ka kiyaye shingen addini, Ka taimaki bayinka muminai masu tauhidi.

    Ya Allah, ka yaye damuwar masu damuwa daga cikin musulmai, ka kwaranye baƙin cikin masu baƙin ciki, Ka biya bashin wadanda ake bi bashi, Ka warkar da marasa lafiya daga cikinmu da na sauran musulmai.

    Ya Allah Ka amintar da mu a ƙasashenmu, Ka shiryar da shugabanninmu kuma jagororinmu, Ka ƙarfafi Shugabanmu kuma jagoranmu Hadimin Masallatai Biyu Masu alfarma da gaskiya da dace da gamonkatar, Ya Allah, ka tsawaita rayuwarsa cikin waraka da ƙoshin lafiya, da ni’ima mai yalwa kuma cikakkiya, kuma Ka datar da shi da magajinsa amintacce ga abin da alheri ne ga ƙasa da mutane, da ɗaukaka ga Musulunci da musulmi ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah Ka kasance Mai ƙarfafawa da kawo ɗauki da agazawa da taimako ga ’yan’uwanmu masu rauni, ya Allah, Ka taimake su a ƙasar Falasɗinu a kan yahudawa ‘yan ƙwace, ya Allah, Ka ƙididdige adadin yahudawa, Ka halaka su ɗaya bayan ɗaya, kuma kada Ka bar ko ɗaya daga cikinsu.

    Ya Allah Ka kiyaye dakarunmu masu dako a kan iyakoki da fagage, Ya Allah, Ka kiyaye su da idonka da ba ya barci, Ka tsare su da ƙarfinka da ba a iya rinjayarsa ya Ubangijin talikai.

    Ya Allah Ka azurta mu da haƙuri akan jarrabawa, da yarda da ƙaddara, da godiya a lokacin yalwa, kada Ka ɗora mana abin da ya fi ƙarfinmu, domin aminci daga gare Ka shi ya fi yalwa a gare mu ya Mafi tausayin masu tausayi.

    Ya Allah Ka tsare mu daga azabarka a ranar da Za Ka tashi bayinka, ya Allah Ka tsare mu daga azabarka a ranar da Za Ka tashi bayinka.
    ((Ubangijinmu, Ka ba mu alheri a duniya, da alheri a lahira, kuma Ka tsare mu daga azabar wuta))
    ((Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin buya daga abin da suke sifantaShi da shi () Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni () Kuma dukkan yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai)).

    Karanta Fassarar Huɗubar Juma’a Rubutacciya 1st August 2025

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Falalar Karanta Amanar Rasulu Take

    Yadda Falalar Karanta Amanar Rasulu Take

    An karɓo daga abu Mas’ud Albadri (Radiyallahu Anhu) haƙiƙa Annabi (Sallallahu Alaihi Wasalam) ya ce; “Wanda ya karanta ayoyi biyu na ƙarshen Baƙara a cikin dare sun isar masa” (Bukhari: 3786, muslim 807).

    Malamai sun bayyana ma’anar “sun isar masa” da cewa; za su zama garkuwa a gareshi daga dukkan sharri; ko kuma za su tsaya a masa a matsayin ƙiyamul laili”.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Yadda Falalar Ayoyi Goma Na Farko Ko Ƙarshen Suratul Kahfi Ta Ke danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Karatun Surah A Cikin Sallah danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga littafin Ingantattun Nafiloli Da Falalarsu; wanda Usman Abubakar Muhammad (Shehu Mansur Dala) ya wallafa shi; Domin karanta cikakken littafin danna nan.

  • Sauya Akalar Kiɗan Gado Zuwa Na Fada Da Na Game-Gari

    Sauya Akalar Kiɗan Gado Zuwa Na Fada Da Na Game-Gari

    Makaɗa Musa Ɗanƙwairo Maradun tun yana cikin aiwatar da kiɗa na Gayauna; wato tun kafin a naɗa shi Sarautar Sarkin Kiɗan Sarkin Maradun yake shigowa da wasu halaye masu jan hankali; da buɗa ido a yanayin kiɗan da ya taras iyaye da kakanni suna yi a gidansu.

    Domin haka tun a aiwatar da waƙoƙin baka na Gayauna Musa Ɗanƙwairo yake shiryawa da sadar da:

    i) Waƙoƙin Noma

    A waƙoƙin noma, Makaɗa Musa Ɗanƙwairo, ya yi farin jini sosai, jama’a sun so waƙoƙinsa, musamman waƙoƙi na noma; waƙoƙi ne da suke ƙunshe da lugga da zaɓaɓɓun kalmomi. Ga kuma zayyana faruwar abubuwa da adonta harshen waƙa tun ma ba a turken yabo; da ɗiya na zambo da ba’a da sauransu ba. Sannan ga Ɗanƙwairo da murya mai zaƙi da kaurara zance kuma mai jan hankali mai sauraro.

    ii) Waƙoƙin Fada

    Waƙoƙin fada, waƙoƙi ne waɗanda Ɗanƙwairo ya yi wa ‘ya’yan Sarakuna da Sarakuna kansu da Hakimai; da Dagatai da masu riƙe da muƙaman Sarauta da sauran masu jinin Sarauta da makamantansu.

    iii) Sarkin Kiɗa

    Makaɗa Abdu Kurna Maradun (1899-1962) yayan Ɗanƙwairo, ya lura da irin tumbatsa cikin ƙwarewar da Alhaji Musa Ɗanƙwairo ya samu a kiɗan noma da na fada (Sarauta); inda kuma ya dinga kai gayaunan kiɗa, ya sutta kuma ya jima.

    Abdu Kurna ya dinga jan kunnuwan Musa Ɗanƙwairo, yana yi masa kandarki, har dai wata rana ya gaya wa ubangidansa, Sarkin Ƙayan Maradun da bakin waƙa yana shaida masa:

    Jagora: Sarkin Ƙaya wa Ƙwairo faɗa,
    ‘Y/Amshi: Bai barin halinai,
    Jagora: Daga zuwa Maƙera, ni maikiɗi,
    : Ban ji labarinai ba,
    : Sai can zuwa Ɗanmanau,
    : Na Ruwan Kiɗi sa sirdi,
    ‘Y/Amshi: Hau ko kana gane shi,
    : Na Ruwan kiɗi hau doki,
    : Tahi ko kana iske mai,
    : Shi yay yi damben girma,
    : Jikan Hassan ɗan Iro,
    : Sarkin Ƙaya mai gayya,
    : Na Magaji ba tagewa.

    (Musa Ɗanƙwairo, Waƙar Shi yay yi dambe girma & Gusau, 1988: sh. 224).

    iv) Waƙoƙi Game -Gari

    Kurwar Musa Ɗanƙwairo ta waƙar baka ba ta keɓe shi ya tsaya a rera waƙoƙin noma ko na fada ba. Musa Ɗanƙwairo ya kawo wani yanayin sussuka da daddare; yayin da ya shigo da aiwatarwa da rera waƙoƙin da a yau nake kira da waƙoƙi Game-Gari (Gusau, 2008a, sh. 161-162).

    Waƙoƙi Game-Gari kuwa sun ƙunshi waƙoƙin Malamai da Alƙalai da Lauyoyi da Attajirai; da sauran ‘Yan Kasuwa da Ma’aikata da ‘Yansiyasa da siyasar kanta da Sojoji da Jarumai da Dakaru da sauran Mayaƙa; da Mafarauta da Maharba da masu sana’o’i da Samari da ‘Yanmata da Dabbobi da Tsuntsaye da Ƙwari da Gulabe da Dazuzzuka da sauran madangantan waɗannan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Fitattun Iyayengida Na Ɗanƙwairo a Kiɗan Fada danna nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin; Tarihin Rayuwa Da Halifofin Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun A Aiwatarwa Da Sadar Da Waƙoƙin Baka Na Hausa; wanda Prof. Sa’idu Muhammad Gusau ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

  • Bayanin Manyan Malaman Sunna A Kan Matsayin Sayyidina Husaini (RA) Da Ranar Ashura

    Bayanin Manyan Malaman Sunna A Kan Matsayin Sayyidina Husaini (RA) Da Ranar Ashura

    Haƙiƙa Sayyidina Husaini (Radiyallahu Anhu) yana da maɗaukakiyar daraja da alfarma a zukatan dukkan musulmi na ƙwarai musamman ma malamai.

    Wannan ya sa bakinsu ya zo ɗaya wurin bayyana darajojinsu da falalarsa da nuna alhini da takaicin yadda ƙarshen rayuwarsa ta kasance. Wannan yana tabbatar da ƙaryar masu cewa wai Ahlussunna suna ƙin Ahlulbaiti ko kuma wai suna murna ga abinda ya faru ga Husaini da sauransu na zaluntarsu da aka yi wannan sharri ne ƙage ne.

    Amma a lokaci guda Ahlussunna basa goyon bayan bidi’o’i da fitintinu da ake yi duk shekara idan ranar ashura ta zo har zuwa kwana arba’in, da sunan nuna juyayi da ta’aziyyar Husaini (Radiyallahu Anhu) da ‘yan tawagarsa, saboda babu wani daga cikin shugabannin Ahlul Baitin ko malamai na ƙwarai da suka aikata hakan. Su kuwa sun fi kowa son Ahlul Baiti da goyon bayansu (Radiyallahu Anhuma) da damuwa da halin da suke ciki.

    Maganganun malamai suna da yawa dangane da falalar Husaini (Radiyallahu Anhu) da kuma matsayinsu a kan kashe shi da aka yi a ranar ashura a shekara ta 61 daga hijra, saboda haka zan kawo kaɗan daga cikinsu domin su wakilci sauran.

    1- Ibn Abdulbarri Abu Amr Yusuf (A.H.S368 Y.M.S 495H)

    Ibn Abdulbarri Ibn Abdulbarri haɗaɗɗen malami ne mai tsoron Allah da faɗin gaskiya, masanin hadisi, a cikin littafinsa na tarihin sahabbai mai suna “Al-Isti’ ab yana cewa:

    “Husaini ya kasance mutum ne mai daraja, da tsananin riƙo da addini, da yawan azumi da salla da aikin hajji. Ya yi aikin hajji sau ashirin da biyar a ƙasa, an kashe shi ranar Juma’a goma ga watan Muharram shekara ta 61 daga hijira”.

    2- Ibnul Arabi Al-Maliki (A.H.S. 468 Y.M.S543)

    Shaihin malami Alƙali Abubakar Ibnul Arabi Almaliki bayan ya yi bayanin abinda ya faru a taƙaice na shahadar Husaini (Radiyallahu Anhu) sai ya ce:

    “Ina ma dai a ce mai girma ɗan mai girma, sharifi ɗan sharifiya Alhusaini ya yi zamansa a gidansa, cikin iyalansa, yaƙi sauraran duk wanda ya zo da maganar ya nemi halifanci, koda kuwa irinsu lbn Abbas ne da Ibn Umar, ina ma dai a ce ya tuna abinda kakansa ya faɗa a kan wansa Hassan(ɗan nan nawa shugaba ne Allah zai sasanta rundunoni biyu manya masu yaƙar juna saboda shi).

    Da ya tuna da ɗan uwansa ya rasa halifancin nan alhali yana da goyon bayan dukkanin rundononi kuma duk wasu manya a lokacin Suna tare da shi, sai ya ga to shi yaya za a yi ya samu wannan halifanci ta hanyar goyon bayan tarkacen mutanen Kufa. Ga kuma manyan sahabbai sun hana shi, Suna janye jikinsu daga neman halifancin da yake?

    Kai ni dai na rasa ta cewa sai dai kawai na miƙa wuya ga hukuncin Allah, da kuma alhinin rasuwar jikan Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ba don manyan sahabbai sun san cewa Allah bai ƙaddara halifanci ga iyalan Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) ba, kuma bai kamata a shiga cikin fitina ba, ai da ba zasu taɓa ƙyale shi ba.

    3. Shaihul Islam Ibn Taimiyya (A.H.S 660 Y.M.S 728)

    A iya ɗan ƙaramin sani na, a cikin dukkan malamai da suka yi Magana akan abinda ya faru ga Hussaini (Radiyallahu Anhu) da kuma matsayinsu game da Yazidu da mahaifinsa Mu’awiyya, da kuma shi’anci, babu wanda ya fi shan zagi da tsinuwa da tsana har ma da Kafirtawa a wurin ‘yan Shi’a Kamar Ahmad Ibn Abdulhalim Ibn Abdussalam Ibn Taimiyya.

    Ibn Taimiyya ya wallafa wani babban littafi mai mujalladi tara mai suna “Minhajussunnatin Nabawiyya fi naƙdhi kalamis shi’a wal kadariyya” kan bayanin ɓacin aƙidun shi’a, a ciki yayi bayanai kan wannan mas’ala.

    Kuma matsayin da ya ɗauka, ba wani abu da ya keɓanta da shi ba, a’a akwai malamai da suka gabace shi da kuma waɗanda suka zo bayansa da suke akan wannan matsayi, amma shi suka fi jin haushi, har ma da yi masa ƙazafin ƙin Ahlul Baiti da ma Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam), saboda kawai tsanain kiyayya, da kwarewa a cikin karya da karya da kage.

    Wani babban malami wanda ya yi fice kan tattara littatafai da fatawowin Ibn Taimiyya, musamman waɗanda suke a rubutun hannu da buga su, mai suna Muhammad Ibn Ƙasim Rahimahullah, ya tattara maganganun da lbn Taimiyya yayi akan Ahlul Baiti, da sahabbai da matsayin Ahlusunna da ‘yan shi’a akansu, kasancewar masu zargin Ibn Taimiyya da ƙin Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) da iyalansa suna yawan ƙin maganganunsu daga wannan littafi.

    Amma fa a gaskiyar Magana, basa kula da amanar ilimi a wajen ciro maganganun nasa, saboda suna yanko iya wurin da ya dace da son ransu sai kawai Su gina hukunci a kai, su yanke duk wurin da suka san asirinsu zai tonu in sun kawo shi.

    Domin bayanin gaskiyar lamari kan matsayin Ibn Taimiyya akan wannan mas’ala da ma waɗansu mas’alolin zan kawo gaba ɗayan babin da malamin ya kawo a cikin littafin, sannan kuma in kawo bayanin matsayin wasu daga cikin fitattun almajiransa, domin in tabbatarwa da mai karatu cewa Ibn Taimiyya cikakken masoyin Manzon Allah ne (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) da iyalansa.

    Amma kifin wannan ga abinda yake faɗa a cikin “fatawa” ɗinsa da manyan baƙaƙe: “Tsinuwar Allah da ta Mala’iku da ta mutane gaba ɗaya ta tabbata  akan wanda ya kashe Hussaini, ko ya taimaka aka kashe shi. Kada Allah ya karɓi ibadunsa na farilla da na nafila.

    “Ƙaunar Ahlul Baiti, tilas ne wajibi ne a kanmu, shi ne ya sa kullum muke yi musu salati a cikin sallolinmu Tsinuwar Allah da ta mala iku da mutane baki ɗaya ta tabbata a kan maƙiya Ahlul Baiti.
    To mai karatu mu je zuwa da fatan ba za ka Ƙosa ba. Shaihul Islam Ibn Taimiyya ya ce:

    Domin karanta cikakken bayani a kan Manufar Makokin Husaini Da ‘Yan Shi’A Sukeyi danna nan.

    Domin karanta cikakken bayani a kan Azumin Annabi Dawud (Alaihis salam) domin nan.

    Wannan bayanin an ciro shi ne daga Littafin Gaskiyar Magana A kan Ashura wanda Shehu Mansur Dala ya wallafa shi; domin karanta cikakken Littafin danna nan.

    Edita@rumasau-kallamu

  • Sunayen Wasu Kayan Abinci Da Itatuwa Da Turanci

    Sunayen Wasu Kayan Abinci Da Itatuwa Da Turanci

    Mu san sunayen turanci na wasu kayan abinci da itatuwa waɗanda muke yawan mu’amala da su, domin masu binciken amfaninsu ga lafiyar jiki.

    1 – Ɗoɗɗoya (Scent Leaf)

    2 – Ɗinya (Black Plum)

    3 – Ɗorawa (Honey Locust)

    4 – Gujjiya (Bambara Nut)

    5 – Goruba (Doum Palm)

    6 – Kaɗanya (Shea)

    7 – Kabewa (Pumpkin)

    8 – ’Ya’yan Kalaba ko Kuka (Baobab Fruit)

    9 – Kurna (Ziziphus)

    10 – Lansir (Cress)

    11 – Riɗi/Kantu (Sesame Seed)

    12 – Rinji (Senna)

    13 – Aya (Tigernut)

    14 – Zogale (Moringa)

    15 – Magarya (Jujube)

    16 – Tsamiya (Tamarind)

    17 – Aduwa (Balanites)

    18 – Mummuƙi (Bread)

    19 – Kanya (Ebony tree)

    20 – Danya (Sclerocarya Birrea)

    21 – Goro (Kolanut)

    22 – Gwate (Porride)

    23 – Tuwo (Fufu)

    24 – Kunu (Gruel)

    25 – Awara (Tofu)

    26 – Ɗumame (Recheuffe)

    27 – Dambu (Chicoins)

    28 – Fura (Millet Flour Balls)

    29 – Rama (Jute)

    30 – Abarba (Pineapple)

    31 – Kankana (Watermelon)

    32 – Ayaba (Banana)

    33 – Lemun Tsami (Lemon)

    34 – Kanumfari (Cloves)

    35 – Hulba (Fenugreek)

    36 – Kirfa (Cinnamon)

    37 – Kanwa (Potash)

    38 – Shuwaka (Bitter Leaf)

    39 – Albasa Mai Lawashi (Spring Onions)

    40 – Na’a Na’a (Mint Leaf)

    41 – Tafarnuwa (Garlic)

    42 – Shambo (Chilli)

    43 – Alayyahu (Spinach)

    44 – Gauta (Bitter Egg)

    45. – Yalo (Garden Egg)

    46 – Dabino (Date)

    47 – Masoro (Black Pepper)

    48 – Barkono (Birds Eye Chilli)

    49 – Kimba (African Black Pepper)

    50 – Ɓaure (Fig)

    52 – Accha (Fonio)

    53 – Habbatus Sauda (Black Seed)

    54 – Farar Wuta (Sulphur)

    55 – Namijin Goro (Bitterkola)

    Karanta Abubuwan Da Ya Kamata Mu Kiyaye Don Inganta Lafiyarmu
    Edita@rumasau-kallamu

  • Abubuwan Da Ya Kamata Mu Kiyaye Don Inganta Lafiyarmu

    Abubuwan Da Ya Kamata Mu Kiyaye Don Inganta Lafiyarmu

    MU DAINA AIKATA WAƊANNAN HALAYEN

    Aikata waɗannan ɗabi’un marasa kyau ga mutum na iya jawo masa ciwon ƙoda (Nephritis) don haka in ka ji ko kin ji wani abu da kin san halinki ne to ki daina don Allah.

    1. Riƙon fitsari: Jinkiri wajen yin fitsari cutar da kai ne mutum ya kasance yana jin fitsari amma ya ƙi zuwa ya yi yai ta riƙon sa yana takurewa, to ku sani duk sanda ƙoda ta tace fitsari ta turo shi ga mafitsara ba abinda da ake so irin a fitar da shi domin in kana riƙe shi to a hankali wani zai fara komawa ga ƙoda (kidney) wanda daga nan kuma matsala za ta fara afkuwa.

    2. Ƙin shan ruwa: Rashin shan ruwa wadatacce yadda ya kamata nan ma matsala ne, ko mutum yana jin ƙishi sai ya sha kaɗan ko kuwa ma mutum ya gama cin abinci amma ya ƙi shan ruwan kwata-kwata musamman abinci mai nauyi da mai gina jiki irin su (carbohydrate & protein). Mai irin wannan hali ya kuka da kansa shi ruwa ana so ka dinga shan sa ba sai in kana jin ƙishi ba. Sannan in da hali in abinci ka gama ci to ka sha tea ko ruwan ɗumi ba ruwan sanyi ba.

    3. Yawan shan gishiri akwai matsala ga ƙoda ba sai ga mai hawan jini ba, musamman mutanen da ke da irin ɗabi’ar nan ta ƙarawa abinci ko miya ɗanyen gishiri idan bai musu daidai ba, to su ma su kiyaye yana interfering da aikin cortex cikin ƙoda.

    4. Rashin shan magunguna ga ƙananun cututtuka da ake ganin ko ba a sha ba za a warke kamar jin zafi ko murɗawar ciki, zafin fitsari ko ƙaiƙayin maƙogwaro.

    5. Sannan kuma shan magunguna ba bisa ƙa’ida ba kuma ba bisa umarnin likita ba wato (self medication) wannan na cutar da ƙoda ƙwarai da gaske don haka duk mai irin wannan shi ma to ya sani ya miƙawa ciwon ƙoda takardar gayyata.

    6. Yawan cin nama fiye da ƙa’ida: Su ma masu wannan al’adar su sani cewa ba burgewa ba ne a ce ka mayar da cin nama kullum kullum ko kuwa kwana 1 ko 2 kurum kake ɗaga ƙafa, hasali ma ƙila ba ka ko ba ki da ƙoƙarin motsa jiki, Sannan in kuka samu sai kun ji kun ci kun yi hani’an to mutum ya kiyayi kansa.

    6. Rashin cin wadataccen abinci: Mutum ya riƙa ma kansa ƙwauro da gangan saboda tsurfa ko kuwa tunanin kar ya yi ƙiba, to masu irin wannan suma su kula.

    SHAWARA TA A GAREKU

    Shi fa jiki yana son service kamar mota ce in ana mata juye ta fi lafiya. Don haka jiki ma na buƙatar hutu, wanka, sanya tsaftataccen tufafi da kuma abinci mai kyau ba mai tsada ba. Yana da kyau kar ka mayar da cikin ka kodayaushe abinci iri guda, wato ka yi ta cin carbohydrate ko protein, jiki baya son haka shi yasa masu yawan cin carbohydrate kan yi fama da kitse a jika haka su ma masu cin protein kan yi ta fama da nauyin jiki.

    Ki sani in kina cin waɗannan (masara, tuwo, dankali, doya, rogo, garin kwaki, flower,) ko da ba rana ɗaya kike haɗa su ba, abu ɗaya kike ci kullum domin duk carbohydrate ne, don haka ake gaurayawa da vitamins, lipids, water, protein, and minerals a yi tsari me kyau.

    Da an ga alamun cuttukan sanyi wato ƙaiƙayin gaba, ko fitar ruwa a gaba ga mace ko namiji a nemi magani, ku daina yadda da zancen cewa ko ba magani yana tafiya ko ka ji wasu ma ana ce musu wai mataccen maniyyi ne, duk ƙarya ce ba wani mataccen maniyyi a likitan ce.

    Karshe Da An Ji Alamun;

    Yawan ciwon baya daga kasa ko sama wajen kafada, canzawar ɗanɗanon baki zuwa kalar kanwa ko ƙarfen da ya yi tsatsa, canzawar fitsari zuwa duhu-duhu kuma kaɗan-kaɗan in an je yi, yawan ganin jiri da kasa samun nutsuwa, yawan kasala, to a hanzarta zuwa a ga likita domin waɗannan alamun ciwon ne.

    Allah ya kare mu! Ya ƙara mana lafiya da zama lafiya!!!

    Karanta Yadda Ciwon Baki Yake
    Edita@rumasau-kallamu

  • Illolin iPhone Ga Tarbiyyar ‘Ya’yanmu

    Illolin iPhone Ga Tarbiyyar ‘Ya’yanmu

    Galibi mutane suna ɗaukar annobar cututtuka da masifun rashin zaman lafiya su ne kaɗai masifu; ana mantawa da wasi abubuwa da ke yaƙar mu kuma suke yin galaba sau tari ba tare da mai da hankalinmu a kansu ba.

    Musulunci da ya zo ƙasar Hausa ya tarar da Hausawan wancan lokacin a kan ɗabi’u kala-kala, sai ya tsame na gari bai yi hani a kansu ba amma waɗanda suka danganci baɗala, tsafi ko kafirci nan take ya taka musu birki. Alhamduluillahi; Al’ummar Hausawa suka kasance masu ɗa’a da yakana da amana da taimakekeniya da rufin asirin junansu, a ƙolololuwa kuma masu tsoron Allah da gaske, ga shi wasu ba su da tarin ilimin addinin musulunci irin na wannan zamanin.

    An sannu sannu Malam Bahaushe ya yi watsi da waɗannan gwalagwalan ɗabi’u na gari wanda ya sa ko a da a kudancin Najeriya iidan za a yi alƙalanci tsakanin mutane, Bahaushe ake nema kokuma ana son a ba da ajiya ko amana shi ma Bahaushe ake nema. Na san mutanen kudu da dama waɗanda a wancan lokacin manyan abokanensu Hausawa ne har ma su suka kasance musu manyan abokai lokacin aurensu a can ƙasashen nasu na kudu.

    Zuwan Turawa da kuma mutanenmu da suke yawan zuwa Turai sun zo da ɗabi’un Nasara amma a wancan lokacin ƙyamatarsu ake yi, yanzu kuwa rungumarsu ake yi. A sannu-sannu yanzu Yahudanci da Nasaranci ya ratsa Hausawa har wasu na ganin abin kunya ne a ce ‘ya’yansu sun fi iya Hausa a kan Turanci. Bature ya yi tasiri wajen yaɗa manufofinsa da muradansa ta hanyar mutanenmu saboda haka har yanzu wannan igiyar ta “Indirect Rule” ba ta tsinke ba.

    Jama’a ina so ku yi nazari cikin hankali da nutsuwa wajen tantance abubuwan Nasara da suke amfanar mu da waɗanda suke cutar da mu. Da yawa wasu suna ganin in suka ƙyale ‘ya’yansu suna yin abin da suke so shi ne wayewa, ci gaba da kuma zaman lafiyarsu. A da talaka ya tsaya a matsayinsa amma a yau haɗa kansa yake da kowa, wannan shi ne musabbabin jefa al’ummar Hausawa cikin yanayin da suke, kowa ya bar matsayinsa yana kokawar komawa na wani.

    Daga ƙarshe ina so in jawo hankalin iyaye, yayye da duk wanda tarbiyya take hannunsa da ya duba irin barnar da kafofin sadarwa suke yi mana sannan babbar masifar iPhone da take yaɗuwa kamar wutar daji a tsakanin ‘ya’yanmu musamman mata. Kashi sama da casa’in na ‘ya’yan marasa ƙarfi da suka mallaki iPhone sun mallake su ne ba ta hanya mai kyau ba.

    Babu abin da ba a yi da ‘ya’yan Hausawa don kawai a ba su iPhone a nan Kano da kuma wajen Kano. Zina, luwaɗi, maɗigo, shaye-shaye, tsafi, guduwa daga gida da dai sauransu, yin su ake a ‘kulli yaumin’ amma mun yi biris ko kuma mun yi kunnen-uwar-shegu, ba ta wannan muke ba.

    To wallahi wutar dajin nan ta kusa ƙone mu ƙurmus, sai dai tokar mu idan ba mu tashi haiƙan wajen kashe ta ba. Wayar iPhone ba ƙaramar masifa ba ce, kuma ta saka yara da dama yi wa iyayensu maza rashin kunya da rshin yi musu biyayya da tsanar su da kallon su a matsayin waɗanda suka gaza don kawai ba su mallaka musu iPhone ba, duk sun manta da ɗawainiyar da iyayen suka yi da su da iyayensu mata har zuwa girmansu da yanzu suke jin sun kawo ƙarfin su mallaki iPhone.

    Wayar iphone ta kasance hanya da take kangarar da yara take iskantar da yara take sa yara yin shirka da dai sauransu. Ya kamata gwamnati da jama’a su yi wani babban motsi wajen ganin wannan masifa ba ta ƙara gaba ba.

    Ɗan uwanku Taufiq Aminu Yahya, Jami’ar Bayero Ta Kano

    08035972272 taufiqyahya29@gmail.com

    Karanta Zikiri Yayin Shiga Gida

    Edita@rumasau-kallamu