Tag: yadda ake

  • Wanene Dele Giwa?

    Wanene Dele Giwa?

    (Ɗan jaridar da aka kashe ta hanyar aika masa wasiƙa mai ɗauke da bam a ciki)? Yau shekaru 37 ke nan da mutuwar ɗan jarida Dele Giwa, babban edita kuma jami’in kamfanin Newswatch, wanda aka kashe ta hanyar aika masa wasiƙa mai ɗauke da bam.

    An haifi shi a ranar 16 ga watan Maris na shekarar 1947 a garin Ile-Ife. Ya halarci Makarantar Local Authority Modern School da ke Lagere a garin Ile-lfe. Lokacin da mahaifinsa ya koma Kwalejin Oduduwa da ke Ile-Ife a matsayin mai wanki, Dele ya samu gurbin karatu a Kwalejin. Daga nan ya samu damar tafiya Amurka domin yin digiri inda ya yi digirinsa na farko a kan Turanci a Kwalejin Brooklyn a 1977.

    Ya samu damar yin digiri na biyu a Jami’ar Fordham duk dai a Amurkan. Ya yi aiki da jaridar The New York Times a matsayin mai taimaka wa ‘yan jaridu na tsawon shekara huɗu kafin ya dawo gida Najeriya ya kama aiki da jaridar Daily Times. Dele ya rasu a ranar 19 ga watan Oktoban 1986 ta hanyar wani bam da aka haɗa da ambulak wanda aka kai masa gida a zamanin mulkin soja na tsohon shugaban mulkin soja, Manjo Janar Ibrahim Badamasi Babangida.

    An kashe shi a lokacin da yake karin kumallo tare da abokinsa Soyinka a gidansa da ke 25 a unguwar Talabi ta Ikeja da ke birnin Lagos. Ya rasu yana da shekaru 39 a duniya. Idan muka dubi yadda mutuwar tasa ta kasance, mutuwa ce a gidansa ta hanyar fashewar bam, wanda hakan shi ne abu mafi damuwa fiye da mutuwar. Wannan na iya zama dalilin da ya sa hatta bayan mutuwarsa ba a daina tambayar wanene ya kashe shi ba? Kuma me ya sa? Tambayar da har yau ba a daina yi ba.

    Abin takaici ne ƙwarai da gaske yadda ‘yan jaridar Afirka suka fuskantar keta haƙƙoƙi da ‘yanci saboda bayyana gaskiya ko ‘yancin faɗin albarkacin baki ta hanyar tsorata su ko tsangwamarsu ko barazana gare su da hare-hare da duka har tsarewa ba bisa ƙa’ida ba; da kuma kamawa ko ɗauri tare da ƙwace kayan aikinsu a wasu lokutan.

    Waɗannan suna cikin matsaloli da ‘yan jaridar Najeriya suke fuskata a lokacin da suke aikin tono wata gaskiya ko kuma almundahana. A Najeriya akwai wasu ‘yan jaridu da suka rasa rayukansu a yayin da suke tona asirin miyagu waɗanda suka aikata ba daidai ba.

    Dangane da kisan Dele kuwa, Janar Ajibola Kunle Togun (tsohon shugaban SSS na lokacin) ya ce, “Akan Dele Giwa aka fara amfani da bam ɗin takarda wajen kashe mutum a Najeriya.” Ya bayyana hakan a lokacin da ya yi hira da Ridwan Kolawole na Jairdar Legit.ng a Abuja.

    Ɗalibinku,
    Mohammed Bala Garba, Maiduguri.
    08098331260
    Marubuci/manazarci.
    10 Ogusta, 2023.

    Karanta Asalin Yadda Aka Samo Sunan Hausa Bakwai Da Banza Bakwai

    Edita@rumasau-kallamu

  • Asalin Yadda Aka Samo Sunan Hausa Bakwai Da Banza Bakwai

    Asalin Yadda Aka Samo Sunan Hausa Bakwai Da Banza Bakwai

    Wasu sun san garuruwan da ake kira ‘Hausa Bakwai’ da ‘Banza Bakwai’ amma ba su san dalilin da ya sa ake kiransu da waɗannan sunayen ba. Wannan ne ya sa na ga dacewar yin wannan ɗan takaitaccen bayanin kamar yadda na taɓa karantawa a littafin ‘Kano Ta Dabo Cigari’ na Marigayi Wazirin Kano Alhaji Abubakar.

    Bayan Bayajidda ya gudo daga ƙasar Borno shi da matarsa mai suna Magaram saboda yunƙurin kashe shi da Sarkin (Shehu) Borno ya yi, sai suka zo wani gari da ake kira Garun Gabas a ƙasar Haɗeja. A nan ya bar matarsa saboda tsohon cikin da take ɗauke da shi ya wuce Daura.

    Bayan ya isa Daura cikin dare, ya sauka a gidan wata tsohuwa, sai ya nemi ruwa amma bai samu ba. Tsohuwar take faɗa masa dalilin da ya sa ba sa samun ruwa sai sau ɗaya a sati saboda wata macijiya da take hana ɗibar ruwan. Da Bayajidda ya ji haka, sai ya karɓi guga a wajen tsohuwar, ya nufi rijiyar Kusugu inda macijiyar take ciki, ya kashe ta ya ɗebi ruwa.

    Da gari ya waye, Sarauniya Kabara (wacce take mulkin Daura) ta ji labari, sai ta sa aka yi bincike aka gano Bayajidda ne ya kashe macijiyar. Ta kira shi ta ce za ta basa rabin mulkinta. Amma ya ƙi amincewa, ya ce mata sai dai a ɗaura musu aure da ita idan ta amince. Sarauniya ta yarda, aka ɗaura musu aure da Bayajidda.

    Sai jama’ar garin suka fara kiransa da ‘Makas-Sarki.’ Daga baya kuma suka koma ce masa ‘Sarki’ kawai. To daga nan ne aka samo kalmar Sarki da ake faɗawa wasu sarakuna a yau. Da Sarauniya Kabara ta haifi ɗa namiji, sai aka sanyawa yaron suna Bawo.

    A lokacin da Bawo yake mulkin Daura, an yi wata masifaffiyar yunwa a ƙasar Hausa, wacce ta zama babu inda ake samun abincin mai yalwa sai a wani wuri wanda shi ne Kano a yanzu. Don haka ƙabilu suka riƙa ƙaura zuwa wurare masu ɗan yalwan abinci domin su tsira da rayuwarsu.

    Bayan jama’a sun fita kowa ya samu in da ya fake, sai ya zamana babu shugabanci kowa zaman kansa yake. Daga nan sai zalunci ya yawaita a tsakanin jama’a. Masu ƙarfi su ƙwace kayan raunana. Wannan ne ya sa raunana suka fara kai kukansu Daura wajen Sarkin Bawo.

    Da ƙararraki suka yawaita, sai Sarki Bawo ya yi shawarar kafa shuwagabanci a dukan waɗannan wuraren da abin ya dama. Sai ya tura ɗansa Bagauda zuwa Kano, ya tura ɗansa Gunguma zuwa Zariya, ya tura ɗansa Duma zuwa Gobir, ya tura ɗansa Kumayo zuwa Katsina, ya ba wa ɗansa Gazori riƙon Daura, ya ba wa ɗansa Zamna Biram, ya tura ɗansa Kogo zuwa Rano. Waɗannan garuruwa da Sarki Bawa ya ba wa ‘ya’yansa ko ya tura su, su ake kiran Hausa Bakwai.

    Akwai kuma Banza Bakwai, wanda Sarki Bawo ya sake tura wasu ‘ya’yan nasa bakwai zuwa can. Sai dai kuma wasu masana sun ce ba ‘ya’yansa na cikinsa ba ne, ‘ya’yan ɗan uwansa mai suna Karaf-da-gari ne wanda Bayajidda ya haifa da wata baiwarsa mai suna Bagwariya. Waɗannan garuruwa bakwai da aka tura ‘ya’yan su ne: Zamfara da Gwari da Nupe da Yaruba (ilori) da Kwarrafa da Kebbi da Yawuri. Su ne ake kira Banza Bakwai.

    Wannan shi ne asalin yadda aka samo sunan ‘Hausa Bakwai’ da kuma ‘Banza Bakwai’.

    Mohammed Bala Garba, Maiduguri.
    08098331260.

    Karanta Ta’aziyyar Hauwa Ƙamshi

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Uku

    Mijin Marigayiya Babi Na Uku

    Ranar Juma’a suna gida da yake yara babu islamiyya; ranar ne kuma suke gyara gashin yaran mai kitso za ta zo. Tun da wuri Afaf ta tsefe nata kan, ita kuma Shukra da yake tun suna makaranta Khadeejan ta tsefe mata babu wanda ya ji kansu. Tun da suka gama cin abincin rana take faman lallaɓa Nasreen ta bari a tsefe mata amma har aka kusa kiran la’asar guda biyu suka tsefe. Bata  son a taɓa gashinta kwata-kwata don haka ta ƙi ma zama a tsefe.

    Khadeeja ta kamo hannunta tace ‘Zo kin ji Nas, kin ga fa Shukra za ta fi ki kwalliya tunda ta tsaya  an gyara mata nata. Ta zauna, har an fara tsifar ta zame kanta ta matsa tana zumɓura baki. Afaf tace ‘Anti wallahi  idan ba ki zare mata ido ba haka za ki yi ta fama da ita, sai a yi sati ana tsefe kanta a gidan Mama.’

    Ta cigaba da lallaɓata amma sam ta ƙi tsayawa; don haka ta kama hannunta ta zaunar da ita  tana cewa ‘Idan kika sake tashi sai na zane ki Nasreen, ko na sa almakashi na aske gashin kan  ya koma kamar na Yaya Habib.’ Ta dubi Afaf tace ‘Yaya Afaf ɗauko min slippers mai zafi idan  ba ta tsaya an tsefe ba zane ta zan yi.’

    Da sauri Afaf ta ɗauki slippers ta zo ta ajiye a gaba Nasreen wadda ta fara shessheƙar kuka tana  fizge-fizge. Khadeeja ta ɗan riƙe gashin tace zan dake ki fa Nasreen, ki rufe min baki bana son  jin kukanki.’

    Nan da nan ta haɗiye kukanta tana shessheka aka cigaba da tsifa Shukra tana mata dariya.

    Daga masallacin Juma’a ya wuce gida don ya gaida Hajia, da ya gaishe ta sai ya wuce gida don  Khadeeja tace idan ya dawo zai kai su saloon ita da yara a wanke musu kai da yamma kuma  akwai mai kitso a maƙota dama ita take musu.

    Yana shiga gidan ya sami Yaya Jidda da yaranta biyu ‘yan mata Naja da Farida, bayan sun gaisa  gaba ɗaya Yaya Jidda ta dube shi tace ‘Gidanka fa za mu tafi yanzu ni da yara, Hajia tace mu je  mu dubo su Afaf.’

    Yace ‘To ai sai ku tsaya mu tafi, don ni ma gaisawa kawai za mu yi na wuce.’  Kafin minti goma sun gama, suka shiga mota ya ja su suka kama hanya, suna tafe suna hira.  ‘To ya yaran? Ana kula da su dai ko?’ Ta tambaye shi.

    ‘Ah Alhamdulillah, gaskiya tana ƙoƙari.’ Ya faɗa cike da fara’a.To ai haka ake so, Allah ya sa ta ɗore.’ Tun a bakin gate ya yi hon, gaba ɗaya yaran suka fito ban da Nasreen. Habib ya taya shi buɗe  gate, bayan ya shigo da motar gaba ɗayansu suka yi masa sannu da zuwa.

    A nan suka fara gaida Yaya Jidda, bayan ta amsa tace ‘Ina Nasreena?’ Afaf tace ‘Tana ciki tsifa Anti Khadeeja take mata.’

    Suka wuce gaba ɗaya suka shiga gidan; kafin Khadeeja ta amsa sallamarsu Nasreen ta fizge  kanta wanda saura ɗaya a gama tsefe shi ta tashi tana share hawaye tace ‘Abbaaa.’ ta faɗa tana  zumɓura baki.

    Da sauri ya rungumeta ‘Ya haka na ganki wujiga-wujiga? Wa ya taɓa ki?’ Shukra ta tintsire ta dariya ta daga slippers ɗin da aka ajiye tace ‘Kukan tsifa take Abba shi ne  Anti za ta zane ta da slippers, ka ga nawa Anti yalash ɗin ko kuka ban yi ba har aka tsefe yanzu za  mu je saloon amma ban da ita. Anti tace tunda ba ta so a taɓa kanta aske shi za ta yi kamar na  Yaya Habib.’ Sannu da zuwa Yaya.’ Khadija ta faɗa tana karkaɗe jikinta. Yauwa.’ ya amsa ba yabo babu fallasa.

    Ta ƙare musu kallo tana ƙoƙarin zama tana cewa ‘To yanzu kuma tsifar ce sai an yi zaniya ni ‘ya  su?’ Kafin Khadeeja tace wani abu Afaf tace ‘Anti wallahi idan aka biye mata sai an yi sati ana wannan  tsifar, kullum haka ake fama da ita.’ Khadeeja tace ‘Ai ba a ma yi zaniyar ba ta bari an tsefe.’ Ta tsuguna ta gaida ita yayin da shi kuma ya ja hannun Nasreen ɗin suka shige ciki.

    Sai da ta kawowa Yaya Jidda ruwa sannan ta bi shi ɗakin. Tana shiga ta same shi a tsaye yana  cire kaya yayin da Nasreen take kwance a kan kujerar ɗakin, kafin tace wani abu yace ‘Wai me  yasa ne sai an yi duka sannan za a yi tsifar? Na ga tun tuni dama ana mata kitson ban taɓa ji an  doke ta ba.’ Tace ‘Yanzun ma ba a doke ta ba, ko Nasreen? Ta dai ƙi tsayawa a tsefe ne na takurata na tsefe  mata, amma ba a yi duka ba.’

    Ya kawar da kai ‘Ni dai bana son dukan yara, don Allah duk abinda yaro ya yi kada a dokar min shi. Uwarsu ma ba ta dukansu, ba na bari gaskiya.’ Ta sunkuyar da kai cikin ƙosawa tace ‘In sha Allah za a kiyaye.’

    Ta ajiye masa ruwan da ta kai masa tana cewa ‘Lunch ɗinka yana nan a table.’ sannan ta fito ta  bar shi a ɗakin.

    Bayan ta dawo parlor ɗin ta tarar Yaya Jidda tana ta yi wa Afaf tambayoyi, ta wuce su ta shige  kitchen. Ta tsaya a tsakiyar kitchen ɗin gaba ɗaya kanta ya kulle; daga shigowarsu suna nema suce ta  doki Nasreen, to yanzu haka suke so a bar Nasreen ɗin ta dinga yawo da kanta? Ga shi Afaf tace makarantarsu ana duba kitso duk ranar Monday. Ta jijjiga kai ta ƙarasa ta ɗauki saucer ta zuba  cake da cin-cin ta ɗebo lemo a fridge ta jera a tray ta kawo wa Yaya Jidda da yaranta, bayan ta  ajiye a gabanta tace ‘Ya wajen su Hajiya?’

    ‘Lafiya ƙalau.’ Ta amsa ba yabo babu fallasa. Suka yi shiru sai surutun Afaf da take ta bawa Naja labari. Shukra ta matso ta kwanta a jikin  Khadeeja tace ‘Anti ni ma lemon.’ Ta shafa kanta ta dubi Afaf tace ‘Yaya ki ɗauko mata lemon wanda babu sanyi.’ Ta miƙe, har ta kama hanyar kitchen ɗin Yaya Jidda tace ‘Ku ba za ku sha lemon ba?’ Afaf tace ‘Ai da shi muka je school.’

    Shukra tace ‘Anti tace idan an kawo wa baƙi abinci mutum ya daina cewa zai ci, ni ma dai kawai  lemon zan sha.’ Khadeeja tace ‘Ki ɗauko muku lemon idan kuna so.’

    Jimawa kaɗan Abbansu ya fito daga ɗakin ya wuce dining ya zauna ya fara cin abinci; yana cikin cin abincin ya juyo yace ‘Kai Habib kun ci abinci ne?’ Yace ‘Tun ɗazu Abba, acici har ta yi round 2.’ Ya faɗa yana zungurar Nasreen.

    Khadeeja ta miƙe ta shige ɗaki, don gaba ɗaya jikinta ya yi sanyi. Ta kula ƙiri-ƙiri neman laifinta ake yi; kamar ma Yaya Jiddan zuwa ta yi ta bincike ta. Ta ƙarasa ta zauna a kan gadonta ta zuba  tagumi. Bayan ya gama cin abincin ya shiga ɗaki ya fito da mukullin motarsa, ya dubi Khadijan yace ‘Idan  kun shirya muje na kai ku saloon ɗin.’

    Gaba ɗaya suka fice har da su Yaya Jidda, ya ajiye su a hanya sannan ya wuce. Tun daga wannan lokacin kuma sai Yaya Jidda ta mayar da shi ɗabi’a, duk Juma’a sai ta zo gidan.  Haka za ta zauna a parlor ta yi ta ƙare musu kallo tana kula da duk wani motsinsu, ga tambayoyi  waɗanda idan ta gama yi wa yaran za ta bi Khadeeja da neman ƙarin bayani. Sai dai ba ta taɓa  samun wani abu na zargi ba kuma Khadeejan ba ta taɓa ba ta dama ta yi wata fitna ba don duk abinda ta tambaya tana daure zuciyarta ta ba ta amsa gwargwadon iko, kuma cikin girmamawa.

    Ranar Talata ce kuma a ranar Khadeeja take sa ran za ta koma makaranta, tun dare ta sanarwa Mustapha. Ya amsa mata ba tare da wata matsala ba.

    Haka ta tashi tun kafin asuba ta shirya yaran tsaf, suna tafiya makaranta ta yi maza ta yi wanka sannan ta ɗan rage aiki don tana da lecture 9am. Bayan sun gama breakfast ta miƙe daga dining table tana tattara plates ɗin tana cewa ‘Babe bari na saka hijabi na sai ka yi dropping ɗina a school.’

    Yace ‘Ok, but kada ki ɓata lokaci don kada ki makarar da ni.’ Kusan a lokaci guda suka fito daga ɗakin kowa a shirye, sun kawo tsakiyar parlor ta dube shi tace ‘Yau kai za ka ɗauko yara ko? Don ni ina da lectures 9am to 4pm.’

    Ya ɗan ɓata rai cikin nuna damuwa yana cewa ‘I thought za ki dawo ki ɗaukosu, kin san ni sai 5pm nake tashi daga wajen aiki.’ ‘To ai ka ga ni ma sai 4pm zan tashi, kuma I can’t miss these lectures don last week ma ka ga ban je ba. Gara dai ka sami wani ya ɗauko su kawai.’

    Ya buɗe motar ya zauna yayin da ita ma ta zauna a kujerar gaba, yace ‘To ai ko an ɗaukosu ma wajen wa za a kawo su tunda ba kya gidan?’ ‘Haka ne fa, most days ma lectures ɗina har 4pm ne.’

    Suka yi shiru na ɗan lokaci; gaba ɗaya ma shi ya manta tana wata makaranta. Yanzu ya take so ya yi da yaran? Wa zai ɗauko su kuma wa zai zauna da su? Wannan ai shi ne an gudu ba a tsira ba. Muryarta ce ta katse masa tunani tana cewa ‘Babe ka ga da muna da mai aiki sai ta ɗaukosu ta shirya su su tafi islamiyya kafin na dawo; musamman idan Babba ce.’

    Cikin jin daɗi yace ‘Ƙwarai kuwa, zan yi wa Yaya Jidda magana sai a sami mai aikin kafin next week.’ ‘No, ka bari idan na yi wa Mommy magana za ta sa a samo mana a garinsu, mutanen suna da amana sosai ga aiki.’ Ba tare da ya kalle ta ba yace ‘Ki bari tukunna idan aka rasa a wajen Yaya Jidda sai a gayawa Mommy ɗin.’ Ba ta ji daɗin wannan maganar ba kuma ta san da ya kalle ta da zai gane sai dai son zuciyarsa ne a gabansa; don haka sai kawai ta yi shiru. Ba ta son abinda zai haɗa ta da Yaya Jidda don gaba ɗaya matar ta fice daga ranta, ta kula kamar tana neman laifinta ne ido rufe.

    A bakin department ƙawayenta Maryam da Jamila suka tare ta, ana ta ihu ana murna ga amaryar Babe. 9am to 11am suka fito daga lecture, wanda zai yi musu 12pm to 2pm ya aiko aka gaya musu ba zai zo ba. Don haka suka wuce hostel ɗakin su Maryam. Suna shiga Khadeeja ta nemi waje ta kwanta, Jamila ta taɓata tace ‘Ke da za ki bamu labarin amarci kuma sai ki kama wani bacci.’

    Ta bige hannunta tana cewa ‘Bar ni wallahi baccin da yake kaina ya fi na wata guda.’ Maryam ta yi dariya tace ‘Bar ta Jamila, kin san kwanan ibada take yi.’ Haka suka yi ta hirarrakinsu a kanta tana ta faman bacci. Har suka gama hirarrakinsu tana bacci, don haka ba su tashe ta ba suka fice sayen abinci. Basu daɗe da fita ba ta farka, bayan ta wanke fuska ta yi alwala ta yi Sallah. Ta zauna a kan dadduma tana tunani; tun ba a yi nisa ba ta gaji da auren Mustapha. To amma tana son shi, matsalarta kawai yaransa kuma da yanda ba zai bari ta yi musu tarbiyya ba. Kusan tun da ya kawo mata yaransa ba ta huta ba, wannan baccin da ta yi ji ta yi kamar an ɗauke wani dutse da ta daɗe tana dakonsa. Ko ina a jikinta ciwo yake, fatan ta kawai a samo mai aikin nan ko za ta huta. Duk da tana tsoron a kawo mai aiki daga gidan Yaya Jidda; gani take kamar CCTV camera ce kawai za a kawo mata.

    Tana zaune tana wannan lissafin wayar Yaya Mama ta shigo; bayan sun gaisa tace ‘Ya na ji ki haka ne amarya? Ko bacci kike yi ne?’

    ‘Wallahi ina hostel Yaya, kin ganni gyangyaɗi na gama.’ ‘To ya maganar mai aikin, tunda dai gaskiya aikin gidan nan ya fi ƙarfinki ga yara huɗu.’

    ‘Ya ce yayarsa za ta kawo mai aikin.’ ‘To ai shikenan, duk ɗaya ne. Kawai dai idan ta zo sai ki sa ido, kada ki bari ta shisshige miki; ke ko a cikin gidan ki kula kada ki kuskura ki dinga barinta tana shigar miki ɗaki, kitchen da store ma duk ki kula da motsinta. Yaran ma ki dinga kula da alaƙarta da su idan ba haka ba sai ta zame muku fitna.’ Yaya Mama ta faɗa.

    Cikin sanyin murya tace ‘To Yaya.’ Yanda ta ji muryarta bai gamsar da ita ba tace ‘Ko da wata matsala ne?’ No, ba wani problem. Ni ga ni ma a school na dawo sai yamma zan koma gidan.’’Ok, Mommy ma tace min kun je weekend ke da yaran naki.’ ‘Eh.’ Suka dan taɓa hira daga baya suka yi sallama suka ajiye wayar.

    Khadeeja ta bi wayarta da kallo kawai sai ji ta yi tana hawaye; ta yi kewar gida sosai, gaba ɗaya a yanzu ma ba ta san me take so ba, kawai dai ta gaji. Motsin su Maryam ya sa ta share hawayenta ta basar.

    Kwana biyu da yin maganar kuwa sai ga mai aiki; dattijuwa ce Baba Habi. Yaya Jidda da kanta ta kawo ta. Sai da ta tafi sannan Khadeeja ta nuna mata ɗakin yara inda a nan za ta dinga kwana.

    Ta nunnuna mata ayyukan kafin yaran su dawo daga islamiyya. Nan da nan ta fara ba tare da nuna wata kyuya ba, ga shi tana da hanzari wajen yin aikin.

    Yan kwanakin nan gaba ɗaya ba ta jin daɗin jikinta, gaba ɗaya ba ta san me yake damunta ba. Ranar Laraba ce, tana jin Mustapha yana tashinta daga bacci kafin asuba yana cewa ‘Ki tashi yara za su makara fa.’ Ta juyo tana yamutsa fuska tace ‘Babe bana jin daɗi wallahi, daga kwancen nan ma ni jiri nake ji ga headache. Bana jin zan iya tashi yau.’

    Ya miƙa hannu ya taɓa jikinta yana cewa ‘Subhanallah, me yake damunki?’ Ni ma ban sani ba, ta amsa muryarta na rawa. Ya matsa ya leƙa fuskarta, sai kuma ya sauka daga kan gadon yana cewa ‘Bari na gama da yara sai na kai ki asibiti, amma ki daure ki tashi ki shirya.’

    ‘To, ka bari gobe ma je asibitin mana.’ No, yau za mu je kin ga ana maganar za a saka lockdown saboda COVID 19 idan aka rufe ban san lokacin da za a buɗe garin ba. Gara mu je mu gama komai a siyo miki magani yanzu haka malaria ce.’ Ya faɗa sannan ya fice daga dakin.

    Baba Habi ce ta shirya yaran, duka da kasancewar ita ba ta iya girki ba haka suka haƙura Afaf ta nuna mata ta dafa musu indomie. Bayan sun sha shayi da burodi ta zuba musu indomie a lunchbox. Duk yanda ya so ya koma baccin bayan asuba ranar haka ya hakura ya zauna a parlor ɗin yana taya su shiryawa. Bayan ya kai su makaranta ya dawo ya shirya, ya taimakawa Khadeeja ita ma ta shirya suka wuce asibiti suka bar Habi a gidan.

    Suna zuwa likita ya tabbatar musu da cewa ciki ne da ita, aka ba ta magungunan suka taho. Kafin su isa gida sai da ya siyo magungunan, suna dawowa ya miƙawa Baba Habi magungunan ya yi mata bayani. Ya shiga ɗakini inda Khadeeja take kwance ya tsaya a kanta yace ‘Ki daure Habi ta haɗa miki abinci ki ci ki sha magani, shi ne za ki ji daɗin jikinki. Kin ga waɗannan magungunan ita Ma’u idan tana sha ko laulayin kirki ba ta yi, haka take ci gaba da harkokinta har ta haihu.’

    ‘Yanzu zan fito ai.’ Ya yi mata sallama ya tafi office. Indomie ɗin dai Baba Habi ta dafa mata sannan ta shiga ɗakin ta taso ta, ta sha maganin ta ɗan ci abinci sannan ta koma ta sake kwanciya. Kafin Habi ta ɗauko yara daga makaranta ta ɗan ji ƙwari, zuwa dare rashin ƙwarin jikin ya ragu don da kanta ta lallaɓa ta yi musu tuwo miyar kuka. Kwana biyu laulayin ya yi wa Khadeeja sauƙi don tana dagewa tana shirya yara makaranta kuma tana shiga kitchen ta yi abinci da taimakon Baba Habi.

    Ranar laraba suna zaune a parlor da magriba ita da yara da Abbansu; tana zaune a tsakiyarsu tana yi musu homework yayin da shi kuma Abbansu yake zaune a kan kujera yana ta faman danna waya yana kuma kallon labarai a BBC. Baba Habi ta fito daga dakin yara da sallama, bayan Khadeeja ta amsa sallamarta ta tsuguna daga gefe ta dubi Khadeeja tace ‘Uwar dakina ina so zuwa gida gobe, na ji an ce za a kulle garin. Zan je na dubo yarana idan na kwana ɗaya sai na dawo kafin a rufe garin.’

    Abbansu ya ɗago kansa daga kallon wayar yace ‘Baba ai da kin bari mu ga abinda hali zai yi tunda kin ga ita ma Khadeejan ba ta da lafiya.’ Ta juya Kai ‘To ai Yallaɓai kafin a kulle garin, na baro yara gara na je na dubo tunda ana maganar idan an rufe garin za a yi watanni kafin a buɗe.’

    Kafin ya yi magana Khadeeja ta dube shi tace ‘Ka bari ta je ai na ɗan ji sauƙi, gara ta je ta dawo kafin a rufe garin ga azumi ma yana tahowa.’ ‘Haka ne.’ Ya amsa ya cigaba da abinda yake yi.

    Gari yana wayewa bayan ya dawo daga kai yara makaranta ya ba wa Baba Habi kuɗin mota Khadeeja kuma ta haɗa mata abin da za ta ba ta ta kama hanya a kan jibi za ta dawo.A ranar da daddare aka sanar da total lockdown a Nigeria, an hana duk wata zirga zirga sai dai kowa ya zauna a gida a ga abinda hali zai yi.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na biyu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Ta’aziyyar Hauwa Ƙamshi

    Ta’aziyyar Hauwa Ƙamshi

    1. Rabbana Sarki Ilahu,
    Rabbi mai tayar da ruhu,
    Rabbi ga baiwarka Hauwa.

    2. Babu mai tsarki ya naka,
    Babu mai rahama kamarka,
    Rabbi kai rahama ga Hauwa.

    3. Babu mai jin ƙai kamarka,
    Babu mai tausai irin ka,
    Don Rasulu ka dubi Hauwa.

    4. Duk Karamci na wurinka,
    Ragwame ita ce sifarka,
    Rabbi rangwantawa Hauwa.

    5. Yadda duk ka yi babu mita,
    Ba mu jayayya da yin ka,
    Rabbi kai rahama ga Hauwa.

    6. Hauwa Ƙamshi jaruma ce,
    Babu shakka malama ce,
    Mai rubuce-rubuce Hauwa.

    7. Rabbi duk an mata shaida,
    Kamila ce mai ibada,
    Sayyada laƙabi na Hauwa.

    8. Rabbi ta yabi mai Madina,
    Kuma ta yi riƙon amana,
    Sa Rasulu ya san da Hauwa.

    9. Rabbi kai rahama gare ta,
    Rabbi kai jin ƙai wurin ta,
    Rabbi don kakarmu Hauwa.

    10. Rabbi sanyaya kabarinta,
    Rabbi kyautata kwanciyarta,
    Faɗaɗa shi saboda Hauwa.

    11. Sa Rasulu ya zo gare ta,
    Sa ya yo murnar zuwanta,
    Har ya ce “sannunki Hauwa.”

    12. Hauwa sai mun zo gare ki,
    Wataran za mu biyo ki,
    Za mu sadu ki ji ni Hauwa.

    13. ‘Yan uwa nai ta’azziya,
    Marubuta ga marsiyya,
    Na ta’aziyya ta Hauwa.

    14. Rabbana ka daɗo salati,
    Gun Habibu da yai wafati,
    Shi masoyi ne ga Hauwa.

    15. Ɗanbala suna Mohammed,
    In ka so ka kirani Ahmed,
    Ke ta’azziya ta Hauwa.

    ©
    Mohammed Bala Garba
    12:03pm
    2 October, 2025.

    Karanta Gyara Kayanka

    Edita@rumasau-kallamu

  • Gyara Kayanka

    Gyara Kayanka

    Rabbana tuba nake yi,
    Nayi saɓo ba kaɗan ba.

    Na yi alƙawari gare ka,
    Zan yi bauta ba da ɗar ba.

    Dana zo shaiɗan ya ja ni,
    Ban yi bautar ko kaɗan ba.

    Ya raba ni da kai masoyi,
    Bai bari na zaunu lau ba.

    Ya hana ni saninka Allah,
    Bai bari nai ilimi ba.

    Shi yake ta zuga gare ni,
    Ko zumunta ban idar ba.

    Ka hana ya sa ni nayi,
    Ban tunanin zunubai ba.

    Ka umarta ya hana ni,
    Bai bari na aikata ba.

    Ya haɗa ni Walidaina,
    Ba su yo fahari da ni ba.

    Nai wulakanci ga bayi,
    Ban ragwantawa na jini ba.

    Kuma na yayyaɗa karya,
    Ban ko binciki gaskiya ba.

    Na yi sata na yi karce,
    Ban ji tausan ‘yan uwa ba.

    Na yi zunɗe na yi gulma,
    Nai harara ba kaɗan ba.

    Na yi zamba cikin amince,
    Duk da dai ba ka fallasa ba.

    Na yi shaidar zur a fili,
    Ban tunanin mutuwa ba.

    Kana na ha’inci bayi,
    Har maƙwabta ban bari ba.

    Rabbi nai wasa Sallah,
    Ban yi san da kace a yo ba.

    Ka haramta na halarta,
    Ban zaton haɗuwa da kai ba.

    Babu mai ikon hana ni,
    Ko ya ce nayi ba da ni ba.

    Duka na’u’o’in kaba’ir,
    Ɗanbala bai bar guda ba.

    Duniya ita ce ƙawata,
    Ko da ɗai ba ta kunyatan ba.

    Ban tunanin za na ƙaura,
    Gunka wai domin na tuba.

    Ba shiri mutuwa ta zo min,
    Ba ta yo sallama da ni ba.

    ‘Yan uwana nata kuka,
    Ba su so mutuwa a nan ba.

    Suka min suturar Musulmi,
    Ba su ce Allah tir da ni ba.

    Har waɗanda na yi wa cuta,
    Suka zo mini ba kaɗan ba.

    Suka min sallah da roƙon,
    Gafara ba su gajiya ba.

    Suka kai ni cikin kushewa,
    Addu’a ba su daina yi ba.

    Suka juya za su koma,
    Nai kiran ba su waiwayo ba.

    Daga nan na gano bala’i,
    Ban zaton haka a ciki ba.

    Ga duhu zafi macizai,
    Ko kaɗan ba su tausayan ba.

    Sai Mala’iku sukka zo,
    Ba su yo sallama da ni ba.

    Suka min wasu tambayoyi,
    Ban ko amsa guda ciki ba.

    Daga nan na shige masifa,
    Wanda ban yi zaton gani ba.

    ‘Yan uwana sai mu farga,
    Duniya ba gun zama ba.

    Za mu girbi abin da mukkai,
    Walla ba maganar wasa ba.

    Rabbana shirye mu Allah,
    Rabbi ba don nai batu ba.

    Har iyayye da ‘yan uwana,
    Da Musulmai ban baro ba.

    Rabbana ninko salati,
    Ga Rasulu ba ka ƙi ya ba.

    Ɗanbala daga Borno yai ta,
    Ɗan Bahaushe ba Ibo ba.

    ©
    Mohammed Bala Garba
    8:27pm
    13 August, 2024

    Karanta Duka A Murɗe

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Biyu

    Mijin Marigayiya Babi Na Biyu

    Kamar yanda aka yi alƙawari ranar Asabar 18th February, 2020 waliyyan Mustapha suka sami  karɓa ta girmamawa a gidan kakan Khadija. Bayan sun gaisa an musu maraba suka gabatar da  sadaki N100,000 da kuma kuɗin aure N50,000. Baba Sani ƙanin mahaifin Khadija ya sa hannu ya karɓi kuɗin ya matsa ya ajiyesu a gaban mahaifinsu Alhaji Baba. Cike da fara’a da murmushi Alhaji yace ‘Ma sha Allah, Allah ya sa albarka Allah ya nuna mana.’

    Gaba ɗaya mutanen da ke wajen suka amsa da Amin. Baba Safiyanu wanda Yaya ne a wajen mahaifin Khadija ya yi gyaran murya yace ‘Alhaji ni ina ga tunda ga sadaki an kawo kuma ga waliyyan ango ai sai kawai a ɗaura auren nan yanzu. Yanda  abubuwa suke tafiya rufe garin nan fa za ayi, tunda ka ga ƙasashen duniya suna ta rufewa fa.  COVID 19 ɗin nan ana maganar ta shigo ƙasar nan sosai, ko da wanne lokaci za a iya shiga lockdown.’

    Alhaji yace ‘Ikon Allah, kace abun ya zo mana kenan. To Allah ya tsare mu da zuri’ar mu.’ Ya dubi  waliyyan Mustapha yace ‘To idan a shirye kuke sai a ɗaura auren ai, nan da sati mata sai su yi bikinsu su kai amarya kafin a ce an kulle ƙasar.’

    Cike da murna Alhaji Muhammad wanda shi ne Babba a waliyyan ango yace ‘Ah ai mu a shirye muke, hakan ai ya fi sauƙi Alhaji, Alhamdulillah Alhamdulillah. Shi Mustapha ai a shirye yake, lefe  ma da sauran kaya duk gobe sai mata su zo su kawo.’

    Nan da nan suka gyara zama, Baba Sani ya kirawo mahaifin Khadija ya sanar da shi wanda shi ma a take ya amince, sannan ya kirawo maƙota da wasu daga cikin dangi. Su ma ‘yan uwan Mustapha suka sanar da shi ya taho shi da abokansa mutum biyu. Kafin minti talatin guest room ɗin Alhaji ya cika da mutane ana ta murna. Ba tare da ɓata lokaci ba aka ɗaura auren Khadija da Mustapha.

    Tana kwance a parlor ɗinsu a kan doguwar kujera tana chatting a waya yayin da ƙanwarta Nabila take zaune tana kallon TV; ƙaninsu Ahmad ya shigo parlor ɗin da gudu yana ihu ‘Ta zama matar aure, Ya Khadija ta zama matar aure…’ Zumbur ta miƙe daga kujerar yayin da ita ma Nabila ta miƙe tana cewa ‘Kai fa kana da matsala, don Allah ji yanda ka firgita ni.’

    Khadija tace ‘Wai me kake cewa ne?’ Yana dariya yace ‘Wallahi an ɗaura miki aure da Mustapha yanzu a gidan Alhaji.’ Ta buɗe baki tana kallonsa cike da tsananin mamaki. Nusaiba ta daki kafadarsa tace ‘Kai Ahmad  ka ji tsoron Allah.’ Yace ‘Wallahi da gaske nake, kirawo Baffa a waya ki tambaye shi.’

    A take Mommy ta fito daga ɗaki riƙe da waya jiki a sanyaye, Ahmad ya kalle ta yace ‘Mommy ai an ɗaura auren Yaya Khadija ko?’ Ta ɗaga kai tana cewa ‘Eh, yanzu Baffanku yake gaya min an ɗaura auren.’ a juya ta dubi Khadija  tace ‘Khadija kin zama matar aure.’

    Ta faɗa kan kujera kamar wadda aka tura, to murna za ta yi ko me? Bata taɓa zata za a ɗaura aure yau ba, ta zata za a yi yanda aka saba; a kawo kuɗin aure a zo a sa rana sannan a shirya biki a nutse. Shikenan yanzu ta zama matar Mustapha? Ikon Allah. Ta kai hannu ta shafa kwarmin idonta inda ta ji danshi; ƙwalla ce ta faɗo. To kukan me take yi?  Murna take yi ko kuwa tsabar mamaki ne?

    Nabila ta zauna ta doro hannunta a kafaɗarta tana kallon Mommy tana cewa ‘To Mommy sai mu fara shirin bikin kenan ko kai ta kawai za a yi haka?’ Ta banka mata harara tana cewa ‘Sai kace wata kaza?’ Mommy tace ‘Uhm, sai dai mu jira Baffanku ya dawo mu ji.’ Ta koma daki ta bar su a nan.

    Gaba ɗaya tunanin Khadija ya tsaya, wannan ɗaura auren da aka ce an yi mata yana nufin nan  da ‘yan kwanakin za ta tare a gidan Mustapha. Fatanta ɗaya Daddy ya bari a yi biki don gaskiya tana son biki. Ƙarar wayarta ne ya katse mata tunani, tana kallon wayar ta yi murmushi “My love” shi ne sunan da ta yi saving lambar Mustapha da shi.

    ‘Hello.’ ta amsa murya ƙasa-ƙasa. Muryarsa zaƙwai cike da farin ciki yace ‘Ya na ji ki haka? Ko ba kya farin ciki ne? Alhaji ya hutar da mu, kin ga next weekend kawai sai a kawo min amarya ta.’ Ta yi dariya ‘I was just not expecting it to happen today, but Alhamdulillah. Ai babu abinda ya fi zama da masoyi daɗi.’

    ‘Haka ne. So me kike buƙata na bikin, ki sami Yaya Mama ku yi lissafi zuwa an jima sai ki gaya min na turo miki ta account ɗinki. In sha Allah ranar Tuesday za a kawo lefe.’ ‘Ok, hakan ya yi.’ ‘Common, ni ina so na ji muryarki ta yi zaƙi zaƙwai kamar tawan nan.’

    Tayi dariya ‘Ka kirawo ni in an jima kafin nan na sha zuma za ka ji zaƙin da muryar za ta yi.’ Suka yi sallama ta ajiye wayar ta koma ta kwanta a kan gadon cikin sanyin jiki. Dab da azahar Yaya Mama ta ƙaraso tare da yaranta Anisa da Jawad. Ita ce Babba a ‘ya’yan  gidan su Khadija. Bayan ta gama tsokanar Khadija ta shige ɗaki inda ta tarar da Mommy tare da  ƙanwarta Anti Naja’atu suna ta tattauna bikin; don Baffa ya sanar da su a shirya a yi biki ranar Asabar da Lahadi idan an gama sai a kai amarya.

    Bayan ta gaishesu ta zauna suka cigaba da tattaunawa a kan bikin. Jimawa kaɗan Yaya Mama tace ‘Ni wallahi Mommy tausayi ma Khadija take ba ni, Allah ya sa dai da gaske yake sonta kuma ya cigaba da kula da ita. Ga yara har huɗu yana shirin haɗa mata da  su, ai sai a hankali.’

    Anti Naja tace ‘Kada ki damu ai mace komai ƙanƙantarta raino ba ya gagararta.’ Mommy tace ‘Yaran ma fa yana kawosu nan wajenta, kamar suna da tarbiyya da sauƙin hali ma.’ ‘To kin ji ma. Kada ki yi mata magana ma ki sa ta zata wani tashin hankali ne don na ganta tun da  aka ce an ɗaura auren nan jikinta ya yi sanyi.’ Haka suka gama tattaunawarsu suka tashi.

    Ranar Lahadi bayan Magriba aka shirya Khadija a ka kai ta gidan Mustapha. Bai zo da abokansa ba sai mutum ɗaya wato Badaru, ba tare da ɓata lokaci ba suka sallami  ƙawayen amarya Badaru ya kwashe su. Bayan ya rufe gidan ya dawo ya same ta tana ta faman share hawaye. Ya zauna ya lallasheta har tayi shiru sannan suka yi Sallah ya buɗe musu abincin da ya zo da shi suka ci. Da kansa ya kwashe kayan da suka gama cin abincin sannan ya dawo ya same ta a zaune a inda ya bar ta.

    ‘Yauwa, tunda mun ƙoshi taso na nuna miki gidan naki kafin mu kwanta.’ ya faɗa yana murmushi. Ta miƙe a kunyace, har sun kama hanyar fita daga ɗakin ya juyo ya dube ta yana murmushi yace  ‘Bari mu fara daga nan, nan ne ɗakinki.’ Ta yi murmushi murya ƙasa-ƙasa tace ‘Ok.’

    Ya wuce ta bi shi a baya ya nuna mata ragowar gidan; bayan ɗakinta sai ɗakinsa sai kuma ɗakin yara inda nan ne kuma ɗakin baƙi. Sai kuma parlor guda ɗaya da dining area a dai-dai kofar  kitchen. Bayan sun gama zagayawa ya kashe fitulun sannan suka wuce ɗakinsa inda za su kwana.

    Ranar da Khadija ta cika kwana uku da tarewa a ranar bakin danginsa da suke ta zuwa ganin amarya sun lafa, don tunda gari ya waye babu wanda ya zo har azahar ta yi. Suna zaune a parlor suna hirarrakinsu aka fara kiran Sallah, ya miƙe yana cewa ‘Bari na je masallaci na dawo.’

    ‘Ok, by then ni ma na yi sallar na yi serving lunch.’ ta amsa ita ma tana miƙewa. Ta yi masa a dawo lafiya ya fice ita kuma ta shige kitchen. Kafin ya dawo ta yi Sallah ta gyara kwalliyarta sanna ta jera abincin a kan dininga table. Yana  dawowa ta yi masa sannu da zuwa sannan ya zauna a dining table ta zuba abinci suka fara ci.  Fried rice ne tare da sauce ɗin hanta da salad, daga gefe kuma ga haɗaɗɗen zobo.

    Shiru suka yi kowa yana ta kai loma, sai da Mustapha ya kusa cinye abincin nasa sannan ya ajiye cokalinsa ya ɗauki zobon da ta zuba masa a kofin tangaran ya kora. Yana ajiye kofin ya ɗauki cokalinsa yana gyara abincin ya dube ta yana cewa ‘Umm! Kin iya girki fa.’ Ta yi dariya tace ‘Ai da na zaci santin kurma kake da ka kasa magana.’

    ‘Au ashe ma sa min ido kika yi.’ ya faɗa yana sake cika baki da abincin. Ta yi dariya ita ma ta cigaba da cin abincin. Bayan ya haɗiye na bakinsa yace ‘Ina ga ai ya kamata in an jima mu je mu ɗebo su Afaf ko? Tun da suka ji an kawo ki suke ta zumuɗi.’

    Ta kalle shi tana wasa da cokalinta a kan abincin saboda ta riga ta ƙoshi, tace ‘Babe ai na zata za a bar su sai mun ɗan huta, ka ga shekaran jiya fa na tare. Ko gajiyar biki ma ai ban gama hucewa ba.’ ‘Haba, ai sai ku huta tare, kin san su ma fa they missed home don tunda mahaifiyarsu ta rasu rabonsu da gida.’

    ‘Allah sarki, ni kaina ina ɗokin dawowarsu nan but babe please ka bari koda zuwa next week ne na ɗan gama kwance kayana.’ ta faɗa da muryar magiya da lallashi. Ya ture farantin gabansa ya sake cika kofinsa na zobo, ya ɗan gatsina fuska yace ‘Ok, amma dai  ba za su ji dadi ba. Ɗazu muka gama waya da su suna ta ɗokin dawowa wajenki.’

    Ya miƙe ya nufi wajen TV yayinda ita ma ta miƙe ta fara tattara kwanukan tana cewa ‘Allah sarki,  in sha Allah next week da ni za mu je mu ɗaukosu ka ga daga nan ma sai mu biya gaba ɗaya mu gaida Mommy mu gaida su Hajiya sai mu dawo gida.’

    ‘Umm!’ ya amsa yana canza channel ɗin TV. Ta cigaba da kwashe kwanukan tunani kala-kala yana yawo a ƙwaƙwalwarta; ta yi zaton yana ɗokin kasancewa da ita, ta yanda zai bari su ɗan ƙara fahimtar juna kuma su more amarcinsu kafin ya ɗauko yaran amma shi yana maganar yau. Babu ƙananan yara a gidansu amma kusan  kullum suna tare da yaran Yaya Mama, ta san yara ba za su bari ta mori amarcinta ba tunda su rayuwarsu suna buƙatar kulawa ne kullum.

    Musamman tunda ga Shukra mai shekaru uku kacal.  Sati ɗayan ma da tace a ƙara kawai dai daurewa ta yi don ita da a tunaninta ta sami kamar wata uku a gidan kafin ya kawo mata yara tunda a can ma inda suke ana kula da su. To amma bata da wani zaɓi, zuwa next week ɗin sai ta bi shi su je su ɗauko yaran.

    Ana fara kiran magriba ya yi alwala ya ɗauki mukullin motarsa, ya same ta a kitchen tana tsugune a tsakiyar kitchen ɗin tana tuka tuwon shinkafa. Motsinsa ya sa ta saurara da tuƙin tuwon ta juyo, ta dube shi tace ‘Fita za ka yi? Ko masallaci za ka je?’

    ‘Eh, daga masallacin zan wuce na dubo yara sai kuma na wuce wajen Hajiya.’  Ta ɗan langabe kai ‘Babe ai da ka dawo, ni ma sai na shirya mu je na gaida Hajiyan.’ ‘No ki bari next week za mu je tare.’ Ya amsa yana duba wayarsa.

    Ta saki tuƙin tuwon ta miƙe ta nufeshi da niyyar ya rungume shi, sai dai ya ɗan kauce don haka ta gefe ta rungumo shi. Jikinta ya ɗan yi sanyi ta sumbaci kumatunsa tace ‘A dawo lafiya Babe, I  will wait for you idan ka dawo sai mu yi dinner tare. Ka gaida su Hajiya.’ ‘Ok.’ ya amsa sannan ya fice.

    A parlor ya sami Alhaji, bayan sun gaisa suka ɗan taɓa hira. Alhaji yace ‘Wai ka ɗebo yaranka  kuwa?’ ‘Ban ɗebo su ba, tace a bari sai zuwa next week idan ta gama hutawa.’ Yana wani kau da kai. ‘To babu laifi; amma fa idan ka ɗaukosu to ka saka ido, ka san mata yanzu ba sa son riƙo. Idan  ba ka yi wasa ba haka za a mayar maka da yara kamar almajirai a gidanka.’

    ‘In sha Allah zan kula, duk da ma na kula kamar ba ta da muguntar.’ ‘A a, basu fa da tabbas, kai dai ka sa ido. Kuma ka dinga bincikar duk motsinsu.’ Ya faɗa yana nuna shi da yatsa. Suka ɗan sake hira sannan ya shiga wajen Hajiya inda ya same su ita da Yaya Jidda suna hira; da yake ita gidanta kusa da gidan ne wataran ma sai an yi sallar Magriba take zuwa.

    Bayan sun gaisa suka cigaba da hirarsu gaba ɗaya. Jimawa kaɗan Yaya Jidda tace ‘Musty ina amarya? Tsohuwar sirikar taka ta baka yaran ko har yanzun ba za ta bayar ba?’ Ya gyara zama yace ‘Haba, sai kace ita ta haifa min su ai dole ta ba ni su.’ Hajiya tace ‘Sai yaushe za ka ɗauko su?’

    ‘Tace wai a bari ta huta zuwa next week, don ni da yau ma na so a ɗaukosu. Yanzu ma idan na fita zan je na kai musu biscuits ɗin da na saya musu.’ Yaya Jidda tace ‘Wai wacece tace a bari ta huta? Khadeejan?’ Yace ‘Eh, tace wai a bari ta huta ta gama ware kayanta kafin a kawo su.’ ‘Kai Musty! Yanzu kai har ka ba ta dama su da gidan ubansu sai ta ga dama za a kawosu, to me  ta yi ya gajiyar da ita har take buƙatar hutu.’

    ‘To ni ma dai haka na gani, amma dai zan ga yanda za mu yi.’ Ya faɗa yana kauda kai. Hajiya tace ‘To ka dai dinga kula sosai don kada ta dinga cutar da su, ka sa ido sosai don yanzu  mata ba tausayi ne da su ba.’ Yaya Jidda tace ‘Musamman gashi tun yanzu ta fara iyayi da kafa dokoki, a jira ta huta kafin a kawosu gidan ubansu.’

    Haka suka gama hirarrakinsu suna jaddada masa ya sa ido sosai kada Khadeeja ta cutar da yaransa; ya yi musu sallama ya wuce gidan iyayen Ma’u wajen yara. Sai da ya tsaya a hanya ya saya musu yoghurt da gasasshiyar kaza sannan ya wuce.

    Yana shiga bayan sun gaisa da Mama ta turo masa yaran suka same shi a guest room. Suka karɓi kajin da yoghurt suka kai wa Mama; wadda ta riga ta saba idan ya kawowa yaran abu to ba zai ba ta ba sai dai ya ba wa yaran a hannunsu su su kai mata; sannan suka dawo wajensa suna ta murna don su sun shirya kayansu tsaf yau za su tafi wajen Anti Khadeeja.

    Hakan ya yi masa daɗi don dama hakan yaso. Nan da nan suka sheƙa cikin gida suka fara fitowa da kayansu, Anti Nihla kanwar Ma’u ta taya su duk suka fito da akwatunansu. Mama ta fito ta same shi, bayan ta zauna tace ‘Ga mutanena nan tunda suka ji uwarsu ta tare sun kasa zaune sun kasa tsaye fa, ni da muka yi da su sai an kwana biyu amma ka ga suna ganinka sun fara fito da kaya. Kayan nasu ma fa wasu suna wajen wanki.’

    ‘Wallahi kuwa, ai babu komai daga baya sai na zo na karɓar musu sauran, kuma ma ai za su dinga zuwa in Sha Allah.’ Ya ba ta amsa. Haka aka gama fitar da kayan aka zuba masa a mota ya kwashe su suka kama hanya, suna ta murna za su je wajen Anti Khadija.

    Tunda ta gama tuwo ta yi Sallah sai ta yi wanka ta shirya cikin bum short ɗinta da wata figalalliyar riga, ta sha turare sai ƙamshi take yi ga gidan ma ta yi fes da ko ina ta kunna turaren wuta ƙamshi sai tashi yake a hankali.

    Tana kwance a kan three-seater tana danna waya ta jiyo motarsa ya buɗe gate yana shigowa, ta tashi zaune ta ɗan gyaggyara tana jiran ya shigo ta taro shi daga bakin kofa. Mintuna kaɗan ta fara jiyo motsinsu a kofar shigowa parlor, ya zura mukullin yana ƙoƙarin buɗewa yana cewa ‘Afaf riƙe hannun Shukra na buɗe kofar.’

    Ta ɗan yamutsa fuska tana ƙoƙarin ta gane shi da su waye; tas ta jiyo muryarsu gaba ɗaya. Ta ɗan rikice kaɗan tana mamakin dalilin da yasa ya taho da su bayan ya amince sai next week. Ta  jiyoshi yana zare mukullin daga jikin kofar; ta kalli jikinta yanda take kusan tsirara. Ta yi wuf ta zaga bayan kujera daidai lokacin da yake sako kai cikin parlor ɗin, ta ɗauki jilbab ɗinta wanda yake ajiye a saman kujera ta saka.

    Tana ƙarasa saka jilbab ɗin suka shigo da gudu bayan ya shigo, suka haɗa baki gaba ɗaya ‘Anti  Khadeeja, Anti Khadeeja.’ Suka karasa da gudu suka rungume ta suna murna. Haka ta yashe baki tana amsa gaisuwarsu, ta ɗauki Shukra tana cewa ‘Shukra baby, ya Mama?  Kin baro ta tana kuka ko?’

    Cikin muryarta ta gwaranci tace ‘Ba kuka take ba, ta ce ma na gaisheki.’ ‘Ina amsawa.’ Ta ajiyeta ta kama hannun Habib tace ‘Ya Habib, welcome.’ Ta kalli Mustapha suka haɗa ido, ya yi sauri yace ‘Sun ƙi bari na na taho sai da suka biyo ni, ga  kayansu nan sai ku shigar.’ ‘Uhm, bari mu gani.’ Ta amsa murya ƙasa-ƙasa.

    Ta ɗauki babban akwatin nasu ta ja ta nufi ɗakin yaran tana cewa ‘Afaf ɗauko wannan jakar mu kai ɗaki.’ Afaf ta kama jakar tana ƙoƙarin ɗagawa Abbansu yace ‘Ke ajiye jakar nan ba za ki iya ɗauka ba.’ Suna tsaye a ɗakin a gaban wardrobe tana tambayar Afaf ina jakar Abbansu ya shiga ɗakin ɗauke da jakar, yace ‘Ga ta nan, gani na yi ba za ta iya ɗaukowa ba na ɗauko mata.’

    Ta yi ‘yar dariya tace ‘Haba dai, Yaya Afaf ai ba raguwa ba ce, jakar ma da babu nauyi.’ Suka yi dariya gaba ɗaya, ya ja yaran suka fice daga ɗakin suka bar ta ita kaɗai tana ƙoƙarin samarwa akwatin kayansu waje. Bayan ta ajiye akwatin a kusa da mudubi ta ɗan ja baya ta ƙare  wa ɗakin kallo; komai tsaf yake tunda an share lokacin da ana kafi sai dai ba a shimfiɗa zanin gado ba a kan babban gadon nasu. Bata san a ya suke kwana ba kafin a aurota amma dai tana  jin a kan gadon suke kwana duka. Ta fito ta same su a parlor sun baje suna kallo suna ta yi wa  Abbansu surutu.

    Ta dube su tace ‘Bari na ciro hijabin nan Afaf sai ki tayani mu gyara ɗakin. Abbansu yace ‘Wannan ce za ta yi wani gyaran ɗaki? Babu abinda ta iya fa.’ Ta yi ‘yar dariya tace ‘Bari ka gani.’ Ta shige ɗakinta; tana shiga ta cire hijabin ta jefa kan gado, ta ƙarasa gaban wardrobe ta buɗe tana duban babban rigar da za ta saka. Wani malolo ya tokare mata maƙogoro saboda takaici; to ta ina za ta soma? Haka kawai ya kwaso mata yara a wannan daren. Da ya gaya mata ma ai da tuni ta gyara ɗakin. Ta ja gajeren tsaki a Fili.

    Motsin shigowarsa ne ya katse mata tunanin, ya nufota yana cewa ‘Na zata a nan ɗakinki za su kwana ai.’ Ta ɗan goge idonta ta juyo tana cewa ‘No, gara kawai na gyara musu ɗakinsu tunda babu wata ƙura da yawa a ɗakin sai su kwanta a can.’ Ya ɗan taɓe baki ‘Ok, amma dai za ki dinga zuwa kina duba su ko?’

    ‘Eh mana wannan ai dole ne.’ Ta amsa tana ɗan juya jikinta. Ya juya ya fita ba tare da ya ko kalli jikin nata ba. Ta kalle jikinta ta ɗan murguɗe baki; yau dai  kwalliyarta ta tashi a aikin banza kenan. Ta janyo babbar riga a wardrobe ɗin ta saka, ta sa hula ta rufe gashinta sannan ta fito. Kai tsaye  ta wuce kitchen ta ɗauki tsintsiya da parker, ta fito parlor ɗin ta dube su tace ‘Taso Afaf, maza mu gyara ɗakinku ku sami wajen kwanciya.’

    Ta wuce ta barsu, a tunaninta yarinyar za ta biyo bayanta. Sai dai har ta shiga ɗakin ta fara ƙoƙarin sharewa babu motsin tahowarta, ta ɗan dakata da sharar da take yi ta kwala mata kira. A maimakon yarinyar ta amsa sai Abbansu yace ‘Abinci muke ci.’

    Ba tare da ta amsa ba ta sunkuya ta cigaba da sharar, har ta ɗan yi nisa a sharar sai kuma ta tuna cewa ya yi abinci suke ci fa; to wanne abincin? Tuwon da ta tuƙa da shinkafa gwangwani 1 da Rabi ɗin ya tasa yaransa a gaba suke cinyewa? Bayan ta gaya masa za ta jira shi ya dawo su ci abincin dare tare? Tuwon ma da gaba ɗayansa malmala uku ne ta tuƙa saboda ta san miyar ba za ta isa su ci ɗumame ba.

    Har ta ajiye sharar ta nufo parlor ɗin sai kuma ta tuna idan ta zo me za ta yi a kai, don haka sai  kawai ta cigaba da sharar ta tana fatan Allah ya sa su rage mata tuwon. Ta share ɗakin ta karkaɗe ko ina sannan ta shimfiɗa zanin gadon da ta ɗauko daga ɗakinta. Ta kalli ɗakin ta ga ko ina ya yi tsaf, sannan ta ɗauko sharar da ta kwashe ta fito.

    Suna zaune a kan dining table suna ta cin tuwo shi da ‘yayansa, kafin ta yi magana Abbansu ya dubeta yace ‘Yauwa ɗan ƙaro mana tuwon nan Habib bai ƙoshi ba, ga Shukra ma kamar za ta ƙara.’ Ta ɗan zaro ido tace ‘Wai kun ciye na flask ɗin?’ ‘To nawa yake, ai ba shi da yawa.’ Kafin ta ba da amsa Nasreen tace ‘Kuma miyar ta yi daɗi Anti.’ Ta yi murmushin yake tace ‘Shikenan dama na dafa, ko ni ma ban ci ba.’

    Habib yace ‘Abba ni fa ban ƙoshi ba, dama bamu ci abincin dare ba lokacin da muka taho gashi mun manta ba mu karɓo kazar mu ba a wajen Mama.’ Abbansu ya dube ta yace ‘Yanzu ya za ki yi da Habib? Yunwa yake ji.’ ‘Akwai ragowar bread sai mu raba ni da shi mu sha da tea, don gaskiya yanzu ba zan so ɗora tukunya ba.’ ba tare da ta saurari amsarsu ba ta wuce kitchen da sharar a hannunta.

    So take ta sami waje ta yi kuka ko ta ji sanyi a ranta, don haka ba tare da ta kalli wajen ba ta jefa sharar ta juya sink ta fara wanke hannunta. Abbansu ta jiyo a bayanta yace ‘Khadeeja, daurewa fa za ki yi ki dafa wa Habib Indomie don shi ba ya cin bread kuma kin ga ai ba ya kwana da yunwa  ba.’

    Ta kalle shi suka haɗa ido tace ‘Babe na gaji ne wallahi, ni ma ina son tuwon amma na haƙura zan ci bread.’ Ta ɗan saurara tana kallon yanda yake ƙara haɗe rai, sai kuma cikin sanyin murya tace ‘Amma Afaf ta zo na kunna mata cooker ta dafa musu Indomie ɗin.’

    Ya kalle ta sheƙeƙe yace ‘Wai ke me kika ɗauki Afaf ne she’s only eleven babu abinda ta iya na aikin gida. Idan ta girma dai ta koya but ki daure kawai ki dafa masa.’ Ta juya ta ba shi baya saboda hawaye ne yake shirin ƙwace mata, ya juya ya fice ya bar mata  kitchen ɗin.

    Ta share hawayenta ta sauko da tukunya ƙarama ta zuba Indomie ɗin da ruwa da komai ta kunna wuta ta ɗora. Ta koma ta jingina da sink ta tsaya ta kafa tagumi; yanzu shikenan har ta gama amarcin, ko awa biyu yaran nan ba su yi da zuwa ba amma sun gundire ta, anya kuwa za ta iya wannan rayuwar. Ko da yake dai yanzu suka zo ta san ba su fahimce ta ba ita ma kuma ba ta fahimcesu ba; amma dai za ta ɗora su a saiti kwanan nan.

    Tana cikin juye Indomie ɗin suka shigo kitchen ɗin suka wanke hannuwansu, sai dai abinda ya b ata mamaki babu wanda ya ɗauko plate ɗin da ya ci abincin ya kawo kitchen ɗin; duk a dining table ɗin suka baro mata. Ta gama juye Indomie ɗin ta miƙawa Habib bayan ya gama wanke hannu; haka ta fito ta kwashe kwanukan daga dining su kuma suna zaune suna kallon TV. Ta  haɗo shayi ta ɗauki guntun bread ɗinta ta wuce ɗaki.

    Bayan ta gama shan shayin ta ɗauko kofin ta fito, tana isa gaban sink ɗin za ta ajiye kofin ta ga Indomie ɗin da ta dafawa Habib ko rabi bai ci ba kuma ga dukkan alamu ya ƙoshi kenan. ‘Mtsewww’ ta ja tsaki a Fili. Ta wanke hannunta ta fito daga kitchen ɗin. Har za ta wuce ɗaki Abbansu yace ‘Ki zo ki shirya su sun fara jin bacci kin ga goma har ta gota.’

    Ta juyo ta dawo, ta ɗauki Shukra wadda ta riga ta fara gyangyaɗi Afaf, Habib da Nasreen suka bi bayanta. Sune suka nuna mata kayan baccinsu ta taimaka musu duk suka yi brush sannan suka shirya, ‘yan matan gaba ɗaya suka haye gadon. Ta kalli gadon ta ga ma ba zai ishesu ba don haka ta koma dakinta ta dauko katifar da aka kawo mata saboda baƙi ta shimfiɗawa Habib a ƙasa. Ta gama tsaf za ta kashe musu fitula Nasreen yace ‘Anti ba a kashe mana fitila sai mun yi barci.’

    Ta mayar da fitilar ta kunna musu sannan ta fice daga ɗakin, ta wuce Abbansu a parlor ta shige ɗakinta. Ta riga ta gaji sosai don haka ita ma kayan bacci kawai ta saka ta rufe ɗakin nata ta wuce ɗakinsa, ta kwanta ta rufe idonta.

    Lokacin da Khadeeja ta fito daga ɗakinsa ya zata ɗakinsu Afaf za ta koma don su kwana tare, amma sai ya ga ta shige ɗakinsa. Ya tashi ya shiga ɗakin yaran inda ya tarar dukansu sun yi  bacci, don haka ya kashe musu fitilar ya fito daga ɗakin. Ya kashe fitilun falon ya shige ɗaki.

    Tana kwance a kan gado kamar ma bacci take yi, don haka ya ƙyaleta. Bayan ya gama shirinsa ya kwanta, ya miƙa hannu ya taɓa ta, ta juyo ta buɗe ido tace ‘Babe, ka shigo?’ ‘Um.’ Ya amsa a gajarce. Ta fara ƙoƙarin matsowa jikinsa, ya tashi zaune yana cewa ‘Kin baro yara su kaɗai, kin ga daga nan ma ai ba lallai ki jiyo motsinsu ba. Ni da na zata ma tare za ki kwana da Shukra a ɗakinki fa,  she’s just 3 ba ta saba kwana ita kaɗai ba.’

    Ta ɗan matsa ta koma inda ta baro tana cewa ‘No, they will be fine fa, ba ka ga a tsakiyar yayunta na sata ba kuma duk fa sun yi bacci. Ka ga na ma saka alarm wajen biyun dare zan je na dubasu sai kuma da asuba.’ ‘Uhm, amma dai da kin daure kin kwana da su ɗin.’

    ‘Kada ka damu ina jinsu.’ Ta faɗa sannan ta gyara kwanciyarta ta juya masa baya ta rufe ido.  Haka kawai zai ce ta je ta kwana a cikin yara; to ai ko ‘yar da ta haifa ce shekara uku ai raba wajen kwana za su yi. Ba zama ta fara wannan aikin ba balle ya sallamawa yaran ita.

    Har barci ya fara ɗaukanta suka ji an murɗa ƙofar, ya riga ya murɗa mukullin da ya shiga don haka sai ƙofar ba ta buɗe ba. Aka ƙwanƙwasa a hankali, suka tashi zaune tare shi da Khadeejan. Kafin suce wani abu Nasreen tace ‘Abba Shukra ce ta tashi za ta sha shayi.’ Ya kalli Khadeeja yace ‘Oh, na manta ban gaya miki ba tana farkawa shan tea da daddare, tunda  aka yaye ta ta saba. Ki je ki haɗa mata shayi, daga ta sha za ta koma bacci.’

    ‘Shayi? A wannan daren? Ko fa 4 hours ba su yi ba da cin tuwo, ikon Allah.’ ‘Idan ba ki ba ta ba haka za ta yi ta yi wa mutane kuka har sai an ba ta, kije ki haɗo mata gobe sai  ki haɗa ki sa a flask kafin ta kwanta.’ Ya faɗa yana sake ɓata rai. Ta ɗaura zaninta a ƙirji ta sauka daga kan gadon ta fice daga ɗakin cike da takaici.

    A tsakiyar gadon ta sami Shukra tana kuka, duk yanda zuciyarta ta kai ga ƙuna a wannan lokacin dole ta danne fushinta. Ta miƙa mata hannu tana ɗan murmushi tana cewa ‘Ahh! Sorry Shukra, ya aka yi? Kukan me kike yi? Cikin shessheƙar kuka da gwarancinta tace ‘Tea.’

    Ta zauna a gefen gadon ta rungume ta tana shafa bayanta tana mata magana cikin lallashi ‘Ya  isa, ya isa. Da safe ke zan fara haɗawa shayi kin ji Baby Shukra, kin ga dare ya yi ko? Mu yi bacci da safe sai mu sha tea ko, har da bread ma da ƙwai ko?’

    Ta gyaɗa kai alamar eh, amma fa hawayenta ya ƙi daina zuba har da shesshekar. Ta cigaba da shafa bayana tana lallaɓa ta yayin da Nasreen ta koma ta kwanta har bacci ya fara ɗaukanta. Abbansu ya ya turo ƙofa ya shigo ɗakin, Shukra ta leƙo ta kafaɗar Khadija cikin shessheƙa tace  ‘Abba tea zan sha.’

    Ta ƙwace daga jikin Khadijan ta sauko ta taho wajensa, ya rage tsawo ya ɗauke ta ya rungumeta yana cewa ‘Ya isa, Anti ba ta ba ki shayin ba?’ ‘Tace sai da safe.’ ta faɗa tana shessheƙa. Ta mike ta rungume hannuwanta a ƙirjinta ta kalle shi da fuskar tausayi tace ‘Babe, ka bar ni da ita za ta koma bacci kuma a hankali za ka ga ta ma daina farkawan shan shayi da daddaren. Ka barni na lallaba ta idan ta yi bacci zan taho.’

    Kallonta yake da mamaki a fuskarsa, sai da ta gama sannan yace ‘Yunwa fa take ji, haka za ta kwana da yunwa. She’s only 3, idan ta girma da kanta za ta daina duk yayyenta ma haka babarsu take rainonsu.’ Cikin ƙosawa tace ‘Kai dai ka bar ni da ita mana, I promise you she will be just fine.’

    Ta ƙaraso kusa da shi, ta miƙa hannu ya dafa kafaɗarta yana cewa ‘Kin ga, ki yi haƙuri ki haɗo mata shayi kada ki saka ta kwana da yunwa tunda ba ta saba ba. A hankali za ki ga da kanta za ta daina.’ Murya ƙasa-ƙasa tace ‘Ohkk!’

    Ta wuce ta bar shi a nan ta nufi kitchen; tea at 1pm, wannan wane irin tashin hankali ne? Idan da ya kyale su ta san tabbas za ta raba ta da wannan shan tea ɗin amma har wani cewa yake yi kada ta barta da yunwa. Ta ƙarasa kitchen ɗin ta haɗo mata tea a kofi ta ɗauko ta fito. Tana zuwa ta same shi zaune a gefen gadon ragowar yaran duk suna ta baccinsu yayin da yake zaune rungume da Shukra; har bacci ya fara ɗibanta amma tana shiga ya ɗagata yace ‘Yauwa  Baby tashi ga shayinki.’

    Ta tashi tana muttsike ido, ya miƙe tsaye ya nunawa Khadijan wajen ta yana cewa ‘Zauna sai na ajiye miki ita idan kin gama ba ta tayi bacci kya taho.’ Ya ajiye mata ita a kan cinyarta ta fara ba ta shayin sannan ya fice ya bar su.

    Bayan ta gama ba ta shayin ta saka ta ta yi fitsari sannan ta kwantar da ita ta ɗan jijjigata bacci ya  fara kwasarta sannan ta wuce ɗakin. Ko da ta shiga ɗakin ya riga ya yi bacci, don haka ba tare da  ta kunna fitila ba ta lalubi waje ta kwanta a gefen gadon. Motsin kwanciyarta ne ya farkar da shi, ya ɗan matso ya rungumota ta baya yana sumbatar bayan wuyanta. Ta ɗan motsa tace ‘Mmmm!’

    Yace ‘Kin san gobe yara za su school ko? Sai ki tashi da wuri don ki shirya su.’ A take jikinta ya yi sanyi; gaba ɗaya ma ta manta da wannan tunda ita ta riga ta sanar da ƙawarta su yi mata attendance ba zata koma ba sai ta yi sati. Ya cigaba da lalubenta tana ƙoƙarin zamewa, saboda ita gaba ɗaya ma komai ya fita daga ranta;  a halin yanzu ma kuka take son yi. Sai dai haka ta haƙura ta bar shi ya yi yanda ya so sannan ta  kwanta tana fargabar yanda za ta tashi nan da awowi kaɗan ta cigaba da hidima.

    Ana fara kiran assalatu ya tasheta daga bacci, sai da ta yi da gaske sannan ta iya saukowa daga kan gadon. Ta yi alwala ta wuce kitchen tunda da ɗan sauran lokaci kafin a tada Sallah. Ta tsaya a tsakiyar kitchen ɗin tana tunanin inda za ta fara; a hankali dabara ta faɗo mata; macaroni da sauce za ta dafa musu in ya so sai ta dafa indomie da kwai su yi breakfast. Nan da nan ta ɗora  sannan ta ɗebo tsofaffin flasks ɗinsu da ta gani a store ta wanke sannan ta je ta yi Sallah.

    Ta zata idan ya dawo daga masallaci zai tsaya ya taya ta shirya su amma ga mamakinta sai ya wuce su a parlor ya koma ɗaki ya kwanta ya cigaba da baccinsa. 7:15 am ta gama komai duk ta yi musu wanka sun shirya, suka zauna a dining table ta kawo musu abinci ta zubawa kowa Indomie da dafaffen ƙwai guda ɗaya. Daga fuskokinsu ta san ba  indomie suka so ci ba, suna cikin cin abincin yayin da ita kuma take zaune a table ɗin tana ba wa Shukra a baki Nasreen ta kalle ta tace ‘Anti da ma dankali da ƙwai kika soya mana.’

    Ta kalle ta tana murmushi tace ‘Saboda kar ku makara shi yasa na yi sauri na dafa Indomie, but insha Allah weekend idan babu makaranta sai a soya muku dankali kin ji. Yanzu maza ki cinye kafin Abba ya fito ya kai ku school.’

    Suka cigaba da cin abincinsu. Jimawa kaɗan Abbansu ya fito yana riƙe da mukullin mota, suka haɗa baki gaba ɗaya suka gaishe shi. Bayan ya amsa yace ‘Maza ku gama mu wuce school kada ku makara.’ Ya kula da ragowar ƙwai a plate ɗin kowa banda Habib, ya dube shi yace ‘Kai ina naka ƙwan?’ Yace ‘Shi na fara cinyewa Abba.’ Nasreen tace ‘Abba ni ina son dankali, Anti tace ba za a dinga soya dankali ba sai weekend.’ Ta  langabe kai kamar abun tausayi.

    Ba tare da ya kalli Khadeejan ba yace ‘No, za a dinga soyawa kada ki damu, maza ki ci abinci mu tafi.’ Tana jinsu ta kawar da kanta, don sai dai idan shi zai dinga tashi ya soya ita ba za ta iya soya dankali da sassafe ba. Nan da nan suka gama; Habib ne ya fara miƙewa har ya juya tace ‘Ɗauke plate ɗinka da cup ɗin ka kai kitchen.’

    Ya ɗauke plate ɗin ya tafi da shi, suma ‘yan uwan da suka ga haka kowa idan ta miƙe sai ta ɗauke plate ɗinta ta wuce da shi. Suka ƙarasa shiryawa suka fice tare da Abbansu. Kafin ya dawo ta soya dankali da ƙwai ta jera a dining table sannan ta wuce ɗaki; wanka za ta shiga sai kuma ta tuna ko da ta yi wankan dai kitchen za ta shiga ta yi wanke-wanke ga shara, don haka ta ga gara ta bari idan ta gama aikin ta yi wankan.

    Sai da ya yi wanka ya shirya sannan ya fito a shirye, kai tsaye ta riga ta shirya abincin a dining  table don haka suka zauna. Yana buɗe kwanon yace ‘Sai da suka tafi kuma kika soya dankali?  Sun fi son soyayyen abinci idan za su tafi school.’ Ta ɗan langabe kai ‘To ai Babe ba zan iya soya wani abu before 7am ba, da a ce ma dai ina da mai aiki ne. Amma hakan ma weekend zan soya musu in sha Allah.’

    ‘To ai da kin bari sai weekend ɗin ma ci gaba ɗaya, yanzu idan sun dawo ai za su ga ɓawon ba daɗi ai kuma ma Shukra za ta gaya musu tunda ita ta ci. Mai aikin ma kuma za a ɗauka.’’Uhm.’ Suka cigaba da cin abincin ba tare da kowa ya ce komai ba.

    Gaba ɗaya ma abincin sai ya fice daga ranta; kenan duk abinda ba za ta ba wa yaransa ba baya so ita ta ci. Haka tunani kala-kala suka yi ta yawo a kanta. Ya gama cin abincin ya fice ya bar su ita da Shukra. Sai wajen 10am ya kirawo ta a waya, bayan ta ɗauka yace ‘Mantawa na yi ban gaya miki ba idan 1pm ta yi sai ki je ki ɗauko yara daga school.’

    Ta ɗan yi shiru don ta zata shi zai ɗaukosu, tace ‘Ohk, but zan iya zuwa a ƙasa?’ ‘No, kin san school ɗin ai ba nisa sosai amma dai ku hau a dai-daita sahu sai ki tafi da Shukra.’ ‘Ok.’ Suna gama wayar ta miƙe ta ɗora abincin rana don ta gama da wuri. Lokaci yana yi ta ɗauki  Shukra suka tafi suka ɗauko ‘yan makarantar. Suna dawowa bayan sun huta ta shirya su suka tafi  islamiyya.

    Dab da magriba ya dawo. Bayan ya huta yana zaune a parlor shi da yaran tana jiyo shi yana  tambayar Afaf abinda aka yi da baya nan, an ɗauko su da wuri daga school? Sun ci abincin rana?  Me suka ci? Sun makara a islamiyya? Haka dai ya cigaba da tambayoyinsa tana kitchen tana jiyo su, kamar ta fito ta yi magana sai kuma ta share ta cigaba da abinda take yi; tunda dai ta san  ba ta yi musu komai ba. A haka suka ƙarasa satin nan tana bakin ƙoƙarinta wajen kula da yaran nan gaba dayansu.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Ɗaya

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Cire Tufafi

    Yadda Ake Addu’ar Cire Tufafi

    بِسْمِ الله.

    Bismillah

    Da sunan Allah.

    Addu’ar Sanya Tufa

    .الْحَمْدُ لِلّهِ الذِي كَسَانِي هَذَا الثَّوْبَوَرَزَقَنِيهِ مِنْ غَيْر حَوْل مِني وَلاَ قُوَّةٍ
    Alhamdulillahil lazi kasani hazas sauba warzuƙnihi min gairi haulin minna wala ƙuwwa

    Dukkan yabo ya tabbata ga Allah, wanda ya tufatar da ni wannan tufa, kuma ya arzurta ni da ita, ba tare da wata dabara daga gare ni ba ko wani ƙarfi.

    Addu’ar Wanda Ya Ji Tsoron Zaluncin Wani Mai Iko

    Edita@rumasau-kallamu

  • Matsayin Harshen Hausa A Ƙarni Na 21 Da Tagomashinsa

    Matsayin Harshen Hausa A Ƙarni Na 21 Da Tagomashinsa

    sahalaliyu@gmail.com
    Kira: 059 671 4064
    WhatsApp: +2347065994177
    SASHEN NAZARIN HARSUNAN NIJERIYA DA KIMIYYAR HARSHE, JAMI’AR JIHAR KADUNA, NIJERIYA.

    Maƙalar Da Aka Gabatar A Taron Ranar Hausa Ta Duniya a Ƙasar Ghana (Kumasi) Don ƙara Wa Juna Sani. Mai Taken: Zango: Ƙaura Daga Keɓancewa Zuwa Fahimta: Rawar Da Gwamnati Ke Takawa Wajen Aiwatar Da Manufofi. Wanda Ƙungiyar Matasan Zongo-Hausa Ta Ghana Suka Shirya A Ƙarqashin Jagorancin Masarautar Sarkin Zango.

    AGUSTA, 2025.

    Tsakure
    Manufar wannan takarda ita ce bayyana tunanin da Majalisar Ɗinkin Duniya (UN) don keɓe wannan rana ta Talata 26 ga watan Ogosta, don ta kasance muhimmiyar rana ga harshen Hausa don ƙara nuni matsayinsa da kuma tagomashinsa a idon duniya baki ɗaya.

    Akwai wani ƙiyasi da aka fitar, wanda yake nuna cewa akwai kimanin adadin harsuna a duniya wanda yawansu ya kai kusan dubu bakwai da ɗari shida (7,600), amman kuma harshen Hausa shi ne wanda zakaransa ya yi cara har ya kai matsayin harshe na goma sha ɗaya a duniya(11) (Bunza, A.M 2023). Kuma wani abin lura shi ne, harshen Hausa ya kai shekaru ɗari da ashirin (120) a matsayin karatun boko musamman a ƙasar Nijeriya.

    Sannan kuma akwai wata nasara da shi wannan harshen na Hausa ya samu wannan nasara kuwa ita ce: yadda ake samun kafafen yaɗa labarai cikin gida Afirka da ma ƙasashen Turawa. Alal misali: akwai gidajen rediyo kamar irin su: BBC da VOA da RFI da DW ƙasar China da Ghana dai sauran su. Baya ga wannan kuma, takardar ta fito da yadda ake samun ƙara yaɗuwar harshen a wasu kafafen sada zumunta na zamani kamar irin su: Facebook da WhatsApp da Instagram da Twitter har ma da shafukan yanar-gizo.

    Gabatarwa

    Babu wata wayewa da mutum zai yi tunƙaho da ita face sanin wanene shi? Kuma daga ina yake? Sannan da me yake magana?. A sanadiyyar mulkin mallaka da kuma sakaci da harshenmu da al’adunmu ne ya janyo cewa wasu daga cikinmu suke ganin cewa wai har akwai wani harshe da ya fi harshensu na gado (harshen uwa). Duk wani wanda ya rasa harshensa na asali, to ya rasa wani babban jigo na rayuwarsa, domin kuwa da harshen ne zai iya ɗaga hannunsa ya bugi ƙirji ya nuna kansa.

    Muddin aka ce an yi watsi da harshen uwa (Hausa), to haƙiƙa an yi watsi da al’adunmu da tarbiyyarmu da kyawawan ɗabi’unmu. Babu wata waye da ta wuce mutum ya san harshensa da kuma abin da harshen ya ƙunsa. Bayanai sun nuna cewa wannan rana ita ce karo na goma sha ɗaya (11) da ake gudanar da wannan taron na Ranar Hausa ta Duniya.

    Haƙiƙa Majalisar Ɗinkin Duniya (United Nation) sun yi la’akari ne da wasu abubuwa da suka shafi harshen Hausa har suka ware wannan rana ta musamman don harshen Hausa, waɗannan abubuwan kuwa sun haɗa da:

    • Yawan yaɗuwar harshen
    • Yawan masu magana da harshen
    • Yawan aikace-aikace (rubutu) da harshen
    • Yawan samun kafofin yaɗa labarai da harshen
    • Yawan amfani da shi a kafofin sada zumunta na zamani
    • Yawan amfani da shi a harkokin siyasa
    • Yawan amfani da shi a gidajen jaridu

    HARSHEN HAUSA DA ƘASAR HAUSA

    A wannan ɓangaren kuma, batutuwa biyu ne za a warware su: wato mecece Hausar ita kanta? Da kuma ina da ina ne ƙasashen Hausa? Bari mu fara da batun Mecece Hausa?
    A ma’anar da ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero Kano ya bayar, ya ce:

    “Hausa shi ne harshe da ake magana da shi.”
    Sannan kuma ya ce: “Hausa harshe ne.”
    Ya ƙara da cewa: “Hausa na nufin azanci ko hikima.”
    Shi kuwa Hornby, A.S (2015) cewa ya yi:

    “Harshen Hausa shi ne harshen da Hausawan Afirka ta Yamma suke amfani da shi musamman a Nijeriya da Nijar sannan kuma ake amfani da shi a wasu sassa na Yammacin Afirka a matsayin harshen sadarwa a tsakanin al’umma mabambanta.”

    WANENE BAHAUSHE?

    A nan kuma za mu yi magana ne a kan shin wai wane ne Bahaushe?
    Bunza, A.M (2019) ya ba da wannan amsa da cewa: Bahaushe shi ne:

    • Wanda yake bugun gaba da zama Bahaushe.
    • Wanda ba shi da wasu al’adu da harshe sai na Hausa.
    • Wanda iyayensa da kakanninsa Hausawa ne.
    • Wanda yake da dangantaka da tushe daga tussan karuruwan Hausa kamar su: Zazzaganci ko Katsinanci ko Kananci ko Gobiranci ko Katsinanci ko kuma Sakkwatanci.
    • Wanda yake da tsaga (shasshawa) ta fuska daga cikin tsagetsagen Hausawa na zuriya.

    HAUSA A IDON MAJALISAR ƊINKIN DUNIYA (UNITED NATION)

    Wannan gaɓar ita ta haifar da wannan takarda, domin kuwa Majalisar ɗinkin Duniya ta yi amfani da irin kallon da ta yi ma harshen Hausa ne a matsayin na 11 a faɗin duniya, inda ta kawo cewa:

    • Mandarin (China) mutane 1,009,000,000 masu magana da shi
    • English mutane 983,000,000 masu magana da shi
    • Hindustani mutane 544,000,000 masu magana da shi
    • Spanish mutane 527,000,000 masu magana da shi
    • Arabic mutane 422,000,000 masu magana da shi
    • Malay mutane 281,000,000 masu magana da shi
    • Russian mutane 267,000,000 masu magana da shi
    • Bengali mutane 261,000,000 masu magana da shi
    • Portugues mutane 229,000,000 masu magana da shi
    • French 229,000,000
    • Hausa mutane 150,000,00 (https://www.gistmania.com/talk/.353020.0html)

    Daga wannan ƙididdiga da suka gabatar, hakan ya tabbatar mana da cewa lallai harshen Hausa karansa ya kai tsaiko kuma wuyansa ya isa yanka, keɓe rana ta musamman da Majalisar ɗinkin Duniya ta yi don ƙara raya wannan harshen namu, abin a yaba ne kuma yin hakan zai ƙara kima da tagomashi ga harshen har ma da masu harshen.

    HAUSA A ƘASASHEN ƘETARE

    Shin me ya kai harshen Hausa zuwa wasu ƙasashen da ba na Hausawa ba? Ba tare da tsawaita magana ba, daga cikin dalilan da suka kai Hausa da Hausawa wata duniyar da ba ta Hausa sun haɗa da:

    • Fatauci
    • Neman ilimin addini
    • Yaɗa Addinin Musulunci
    • Cinikin bayi
    • Aikin hajji
    • Aikata wani abin kunya
    • Neman ilimin book
    • Aikin gwamnati (www.amsoshi.com)

    Waɗannan da ma wasu dalilai masu yawa da suka kai harshen Hausa da Hausawa wasu ƙashen da ba nasu ba.

    KAMMALAWA

    Daga bayanai da suka gaba, mun fahimci cewa lallai harshen Hausa ba ƙyalle ba ne kuma ba ƙashin yarwa ba ne. Sannan kuma mun ga irin yadda Majalisar Ɗinkin Duniya ta kalli harshen Hausa wanda ake ganin wannan daraja da martaba da harshen yake da shi ya sa ta ware rana ta musamman don gudanar da taro da yin bita a kan wasu al’amura da suka shafi harshen Hausa da kuma irin gudunmawar da harshen yake bayarwa a rayuwarmu ta yau da kullum.

    Mun ga yadda aka samu wasu gidajen rediyo da kafafen sadarwa na zama suke mu’amala da harshen Hausa. Sannan mun fahimci wanene Bahaushe da kuma inda harshen Hausa yake matsayinsa a duniya tare da masu Magana da shi. Sannan mun ga wasu dalilai da suka kai harshen da ma masu harshen wasu ƙasashen da ba ƙasar Hausa ba.

    Manazarta

    Bunza, A.M (2013), “Don Me Ake Karatun Hausa?” Harsunan Nijeriya Volume XXIII. 2011-2013. Center for the Study of Nigerian Languages, Bayero University: Kano.
    Hornby, A.S (2015), Oxford Advanced Learner’s Dictionary of Current English 9th Edition. Oxford University Press: United Kingdom.
    Ƙamusun Hausa Na Jami’ar Bayero (2006). Cibiyar Nazarin Harsuna Nijeriya: Kano.
    www.amsoshi.com
    A Wata Hira da Aka Yi da Bunza, A.M a Shekarar (2023)
    https://www.gistmania.com/talk/topic.353020.0html

    Domin karanta Gudunmawar Ali Gumzak Wajen Samarwa Da Kuma Haɓaka Finafinan Hausa danna nan

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Tafiyar Da Ƙuncin Zuciya

    Yadda Ake Addu’ar Tafiyar Da Ƙuncin Zuciya

    لاَ إِلَهَ إلا اللهُ الْعَظِيمُ الْحَلِيمُ، لاَ إِلَهَ إلا الله رَبِّ الْعَرْشِ الْعَظِيمُ، لاَ إِلَهَ إِلَّا اللهُ رَبُّ السَّمَوَاتِ وَرَبُّ الأَرْضِ وَرَبُّ الْعَرْشِ الْكَرِيمُ .

    La’ilaha illallahul azeemul haleem, la’ilaha illallahu rabbil arshil azeem, la’ilaha ilallahu rabbus samawati warabbul ardi wa rabbul arshil kareem.

    Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Mai girma (wanda babu abin da yake girmama a gare Shi), Mai haƙuri (Mai jinkirin azaba tare da cikakken ikon aiwatar da ita). Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin Alarshi, Mai girma. Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, Ubangijin sammai, Ubangijin ƙasa, Ubangijin Al’arshi, Mai yawan baiwa.

    اللّهُمَّ رَحْمَتَكَ أَرْجُو فَلا تَكِلْنِي إِلَى نَفْسِيطَرْفَةَ عَيْنٍ وَأَصْلِحْ لي شأني كلهلا إله إلاأَنتَ.

    Allahumma rahmataka arju fala takilni ila nafsee ɗarfata aini wa’aslih lee sha’ani kullah, la’ilaha illa anta.

    Ya Allah! Rahamarka nake kauna, don haka Kar Ka kyale ni da kaina ko da kiftawar ido ne, kuma Ka kyautata mini sha’anina dukkansa; babu abin bautawa da gaskiya sai Kai.

    لاَ إِلَهَ إلا أنتَ سُبْحَانَكَ إِنِّي كُنْتُ مِنَ الظالمين

    La’ilaha illa’anta subhanaka inni kuntu minaz zalimeen

    Babu abin bautawa da gaskiya sai Kai. Tsarki ya tabbata gare Ka, lalle ni na kasance daga cikin azzalumai.

    الله الله رَبِّى لاَ أُشْركُ بِهِ شَيْئاً
    Allah Allah rabbi la ushrika bihi shai’an

    Allah! Allah ne Ubangijina, ba na yin tarayya da Shi da wani abu a cikin bauta.

    Karanta Yadda Ake Addu’a A Kan Abokan Gaba

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’a A Kan Abokan Gaba

    Yadda Ake Addu’a A Kan Abokan Gaba

    اللَّهُمَّ مُنْزِلَ الْكِتابِ ، سَرِيعَ الْحِسابِ ، اهْزِمِ الأَحْزَابَ ، اللّهُمَّ اهْزِمُهُمْ وَزَلْزِلْهُمْ .

    Allahumma munzilal khitabi, sari’al hisabi, ihzimil ahzaaba, allahumma ihzimuhum wazalzilhum.

    Ya Allah! Mai saukar da Littafi, Mai gaggawan sakamakoKa karya kungiyoyin abokan gaba. Ka karya su, Ka girgiza su.

    Karanta Addu’ar Wanda Ya Ji Tsoron Zaluncin Wani Mai Iko

    Edita@rumasau-kallamu