Tag: yadda ake

  • Mijin Marigayiya Babi Na Bakwai

    Mijin Marigayiya Babi Na Bakwai

    Haka Khadeeja ta kwana a asibitin ƙarƙashin kulawar Anti Iyami. Tun dare likita ya gama da ita aka ba ta duk wasu magungunanta, ya sanar da Anti Iyami za a iya tafiya da ita gida. Don haka gari yana wayewa ƙarfe takwas na safe Anti Iyami ta gama aiki za ta tafi gida ta shiga ɗakin da Khadeejan take.

    Bayan sun gaisa tace ‘Yanzu akwai inda yake miki ciwo Khadeeja.’ Ta jijjiga kai tace ‘A a, ko ina ya warware, yanzu ma na gama breakfast ɗin da kika aiko min da shi.’ ‘Ok, so ki kirawo Mustapha kice masa zan wuce da ke gida sai mu tafi na kai ki gidan Mommy ɗin.’

    Ba ta son ta yi magana da shi sai ta je gidansu don haka cikin sauri tace ‘Ai yanzu na kirawo shi bai ɗauka ba, ina jin yana bacci ko baya kusa da wayar amma na san da ya gani zai kira. Mu wuce kawai tunda tun jiya na gaya masa za mu wuce gidan.’

    ‘Ohk, to tashi mu tattara kayan mu wuce. Ni ma tun dare na kirawo Mommyn naki na sanar da ita, da safe ma mun yi waya. Na dai ce mata kada ta kirawo ki ne don duk lokacin da na shigo sai na same ki kina bacci, shi yasa nace ta bari idan kin tashi zan kirawo ta ku yi magana.

    But ba komai idan mun je za ta ganki tunda mun shirya.’ Nan suka haɗa kayan Khadeejan waɗanda daman ba yawa ne da su ba suka shiga motar Anti Iyami suka kama hanya.

    Khadeeja tana zama a mota ta lalubo wayarta ta saka ta a silent ta jefa a jaka don ba ta so Mustapha ya kirawo ta a gaban Anti Iyami domin ba ta san me zai ce ba idan ya ji ta wuce gidan Mommy. Duk inda suka je checkpoint aka tsayar da su da an ga uniform ɗin Anti Iyami kuma ta nuna ID card sai a bar su su wuce, haka har suka isa gidan Mommy.

    Tun suna asibitin Anti Iyami ta sanar da Mommy za su taho don haka kafin su isa an ɗorawa Khadeeja ruwan wanka, suna shiga ta wuce ɗakin Mommy inda Azumi mai aikinsu ta sirka mata ruwan a banɗaki. Ba tare da ɓata lokaci ba ta faɗa wanka.

    A parlor Mommy suka zauna da Anty Iyami; bayan sun gaisa sun jajantawa juna Mommy tace ‘Ina Mustaphan? Ai na zata tare kuke da shi.’ Ta gyara zama tace ‘Bai zo ba ma yau da safen duk da dai tace ta gaya masa nan za mu huto, amma don Allah ƙawata a duba yarinyar nan.’

    Cike da kulawa Mommy tace ‘In sha Allahu kuwa, ke ma kin san ba zan barta haka ba ko akwai wata matsala ne da ta samu ko rashin lafiya.’Ta jijjiga kai ‘Babu fa, kawai dai tace min tana son dawowa gida. Duk dai wasu tambayoyi da zan yi mata na yi ta nuna min babu komai, to amma kin ga akwai yaransa guda huɗu.

    Wataƙila hidimar gida da ta yaran ce take mata yawa ga ciki shi yasa ta sume masa. Baccin da ta dinga yi kawai ya tabbatar min da cewa ba ta samun isasshen bacci wallahi, don shi yasa ma na ƙi tashinta ku yi waya. Gaskiya ku bincika, ya nema mata mai aiki ko ya san yanda zai yi da yaransa.’

    ‘Umm! To kin ga dai idan ma da wata matsala ba ta faɗa ba, koda yake kwanaki tace mai aikinsu ba ta nan a bata aron Nabila amma Baffansu ya ƙi amincewa. Wataƙila saboda babu mai aikin ne abun ya yi mata yawa ga laulayi.’

    ‘Gaskiya dai ku duba, ko da za ta koma ku bar ta ta huta ta sami natsuwa sannan kuma a ɗaukar mata mai aiki.’ Suka ƙarasa hirarrakinsu daga baya suka yi sallama Anti Iyami ta kama hanya.

    Bayan ta fito daga ta tarar da farfesun kaza mai rai da lafiya wanda Mommy ta dafa mata sannan ga shayi mai kauri Azumi ta haɗa mata da burodi a gefe, cikin sauri ta gyara jikinta ta sa kaya sannan ta shimfiɗa dadduma a gaban gado ta miƙe ƙafafu ta zauna ta fara cin abinci.

    A nan Mommy ta shigo ta same ta ita ma ta zauna, sai da ta gama cin abinci sanna ta fara yi mata tambayoyi. Ba ta ɓoyewa Mommy komai ba ta sanar da ita halin da ake ciki, ta tabbatar mata cewa idan dai da mai aiki musamman babba wadda ba za ta sa ta surutu ba.

    Sai dai ta kasa gaya wa Mommy cewa gaba ɗaya ma ko da da mai aikin ita ji take kamar ma Mustaphan baya ƙaunarta, gani take kamar yanda take zama kullum cikin hidima ya sa ba ta gane kulawarsa a gareta. Don haka ta bar wannan a ranta tana fatan idan an sami mai aiki ya zama suna samun lokaci a tare to za ta fuskanceshi.

    Muryar Mommy ce ta katse ta tana cewa ‘To yanzu yaushe zai zo ya ɗaukeki?’ Ta kalle ta suka haɗa ido ta sunkuyar da kai sanna cikin muryar shagwaɓa tace ‘Mommy kin ga yanzu mai aikin ba ta dawo ba, kuma na gaya miki shi ba zai taya ni komai ba kuma ba zai bari yaransa su tayani ba.

    Kawai ki bar ni sai bayan sallah ko kuma duk lokacin da mai aikin ta dawo ko aka sami wata.’ Mommy ta jijjiga kai tace ‘Na fahimce ki, amma me kike so na gayawa Baffanku? Shi kuma Mustaphan wane dalili za a ba shi na riƙe ki a nan ɗin. Tunda dai ciki ya fice an riga an wake; kuma ga ki nan kowa yana ganinki ras.’

    Ta karyar da kai kamar abin tausayi tace ‘Umma ni dai don Allah ki san yanda za ki yi a bar ni na huta. To bari mu gani. Idan kuma akwai wani abun da Mustaphan yake yi miki wanda kike so a yi masa magan to ki gaya min.’

    ‘Babu komai tunda ma bai hana a ɗauki mai aikin ba, in sha Allahu da ta dawo ko kika samo min wata zan koma.’ Ta gyara zama ta kafa tagumi ‘Hmm! bari mu ga yanda za mu yi da Baffan naki tukunna.’

    Sai da suka gama wannan hirar sanna ta tuna tunda suka shigo ba ta ma nemi wayarta ba, ta san yanzu haka Mustapha yana ta faman kiranta. Cikin sauri ta miƙe ta ɗauko wayarta daga jakarta, ai kuwa tana dubawa taga missed calls ɗinsa har guda goma sha ɗaya.

    Tana gani danna masa kira, ko ringing ba ta yi ba ya ɗauka ‘Hello, wai ina kika shiga ne naje asibiti ina ta nemanki? Na rasa mai ba ni tsayayyiyar amsa, sai ce min kawai ake kin tafi da Anti Iyami, na za ta gida za ta kawo ki na dawo gidan kuma baku zo ba. Kin sa ina neman haukacewa na rasa wanda zan kira don ban san me zan ce musu ba.’

    ‘Subhanallah! Ka yi hakuri Babe, wallahi ka ganni nan ai gidan Mommy ta kawo ni. Na kirawo ka ba ta shiga ba kuma shi ne na jefe wayar a jaka na manta sai yanzu da na fito daga wanka na tuna. Amma shi ne ba ki gaya min ba? Kin san wulaƙancin da aka dinga yi min a checkpoint kuwa?’

    Ta tausasa murya ‘Sorry Babe, wallahi laifi na ne don tun a asibitin Anti Iyami tace na kirawo ka sai wayar ta ƙi shiga.’ Ya ɗan saki numfashi ‘To me yasa ba ku taho nan ba ko kuma a jirani na zo? Me ya sa za a kai ki gidan Mommy?’

    Ta ɗan yi shiru, shi ma bai yi magana ba yana sauraronta; ta murguɗe baki kamar yana kallonta tace ‘Ai ka san dai idan an haihu ana zuwa wanka gida, may be shi yasa da suka yi waya Mommy tace a kawo ni gida.’

    ‘To kuma shi ne aka rasa wanda zai gaya min.’ Cikin ƙosawa tace ‘To ba ga shi na gaya maka ba, kuma ai nace maka mantawa na yi.’ Ya ɗan ja numfashi ‘Uhm! To ya jikin naki? Shike nan an gama yi miki alluran?’

    ‘Na sami sauƙi, ga ragowar magungunana na taho da su daman yawanci na kwana bakwai ne, amma na sami sauƙi. To idan an buɗe gari sai na zo na ɗauke ki, ina ga ranar Saturday za su ɗan buɗe mu, nan da kwana uku kenan.’

    ‘Uhm, to ka dai zo amma gaskiya sai bayan sallah zan dawo kafin nan na dan huta na gama arba’in tunda ka san shi ma ɓarin ai sai an yi wanka. Ɓarin, gaskiya ban taba ji ba. Ma’u ma fa su biyu tana yin ɓarin amma na biyun babu wanda ma muka gaya wa a nan ta yi zamanta ta cigaba da hidimarta.

    Hutawa kawai ta yi na kwana biyu. Idan ka zo dai ma yi maganar.’ Ta tamabye shi yaran ya ba ta su suka gaisa sannan suka yi sallama suka ajiye waya.

    Tunda yake bai taɓa ganin son zuciya irin wannan ba, ya za a yi a ɗauke masa mata kuma a ce sai bayan sallah za ta dawo? Kawai saboda ta yi ɓari. Asma’u ma ai ta yi ɓari har sau biyu ma; na farkon shi ne bayan haihuwar Habib, bayan an yi mata wankin ciki a ranar suka dawo gida.

    Ko maganar ta je gidansu ma ba a yi ba kawai dai an kawo mata ƙanwarta tunda dama tana da mai aiki. Na biyun kuwa ma bayan haihuwar Nasreen babu wanda suka gaya wa, suna zuwa asibiti aka ce musu ya fice gaba ɗaya ba sai an yi wankin ciki ba aka ba su magunguna suka dawo gida.

    Kawai dai ya san ba za ta koma ɗakinsa ba sai bayan kwana arba’in, kuma ba shi da matsala da wannan. Amma su iyayen Khadeeja saboda son zuciya sai akwai su ɗauke ‘yarsu? Kuma ko gaya masa ba za ayi ba.

    Haka ya gaji da saƙe-saƙensa ya sake daga wayar ya kirawo Alhaji ya gaya masa, don bai gaya musu cewar a asibiti ma ta kwana ba yana so ya je da safen ya gani tukunna. Shi ma Abban ya nuna rashin jin daɗinsa da aka tafi da ita, musamman da ya gaya masa ba su ma tambaye shi ba suka tafi da ita.

    Bayan sun gama waya da Alhaji ya kirawo Ummansu ita ma ya sanar da ita. Suma su Afaf sai da ya yi musu bayani don tunda ya dawo ba su ganshi tare da Khadeeja ba suke ta faman yi masa tambayoyi. Babu yanda za a yi ya iya ɓarin Khadeeja ta zauna a gidansu, ya suke so ya yi?

    Ga lockdown an hana mutane fita sannan kuma su ɗauke masa mata. Kwana ukun nan ma da zai yi da yaran bai san ta ina zai fara ba don yana tuna yanda a kwana ɗayan nan suka gama firgita shi; ga gari a kulle balle ya kai su gidan Umma. Gaskiya da an buɗe gari ranar Asabar zai je ya ɗauko ta tunda dai ko shi ya tambaye ta jiki ta ce da sauƙi.

    Sai can da yamma dabara ta faɗo masa; ya ɗauki waya ya kirawo Baffan Khadija, bayan sun gaisa ya jajanta masa jikin Khadeejan sannan ya sanar da shi cewa ranar Asabar idan aka buɗe gari zai zo ya ɗauki Khadeejan.

    Ba tare da matsala ba kuma Baffan ya amsa masa da hakan ya yi, don haka cikin walwala ya ƙarasa wuninsa. Bayan Ummi ta gama haɗa musu kayan shan ruwa shi da yara ta wuce ta tafi gidansu ta bar su.

    Tun bayan dawowar Khadeeja gidan sau ɗaya Baffanta ya shiga ɗakin Mommy ya same ta ya yi mata sannu. Yana zaune a parlor bayan ya dawo daga sallar tarawih Mommy ta shiga ta same shi, ta zauna a gefensa suna kallon labarai a tashar Aljazeera tare. Bayan sun ɗan taɓa hira yace ‘Ɗazu Mustapha ya kirawo ni yana duba Khadeeja, ya ma ce min idan an buɗe gari ranar Asabar zai zo su tafi.’

    Ta ɗan gyara zama ‘Ranar Asabar fa kwana uku kenan, haba ai sai ta kwana arba’in. A ah to ai ni na za ta sun gama magana da ita ne a kan hakan.’ Ta jijjiga kai tace ‘Gaskiya dai ba su yi wata magana ba don da kanta tace min tana so ta yi arba’in ɗin. Suna zuwa da na sa ruwan zafi nayi mata wanka ta ji dadin jikinta da kanta tace a bar ta ta yi arba’in ɗin.

    Haba, kuma haka za a mayar da ita haihuwar fari babu wani gyara? Sai kace ‘yar tsana.’ ‘To ai na ga ɓari ne ba haihuwa ba.’ ‘To ai Baffan Nabila ɓari ya fi haihuwa wahala sosai ma, sannan kuma na fari ne haka za a ba shi matar ya ma kasa ɗaga mata ƙafa a kwana arba’in ɗin.’

    ‘To na ga dai ai matarsa ce ko? Ina laifi, kuma ma ai shi ma ba zai ce bai san waɗannan hukunce-hukuncen ba tunda ga yara nan har huɗu an haifa masa.’ Ta sake gyara zama ‘Ku dai yi haƙuri Baffa a bar ta ta yi kwana arba’in ko a ƙalla talatin, kafin nan ta ji daidai a jikinta sai ta koma.’

    Ya ɗaga wayarsa ya cigaba da dubawa yana cewa ‘To ai shikenan idan ya zo sai ku yi masa bayani, ni bani da matsala da hakan.’ ‘Yauwa, ai lalacewar zamanin ba ta kai an daina wanka da gyara a haihuwar fari ba. Amma dai idan ya zo sai ka yi masa bayanin idan kana nan tunda ka ga kai ya nema, gara ku cigaba da magana man to man.’

    Ya yi dariya yace ‘To babu laifi.’ Ya san halin matarsa da kishi, yanzu haka haushi ta ji shi Mustaphan bai kirawo ta ya duba Khadeejan ba ko a ƙalla ya gaya mata zai tafi da Khadeeja ranar Asabar tunda ya san ita ce za ta shirya Khadeejan amman ya kirawo Baffa. Jimawa kaɗan kuma ta fice ta ba shi waje.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Shida

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Shida

    Mijin Marigayiya Babi Na Shida

    A gajiye ya shiga gidan wajen ƙarfe tara na dare, yana shiga yaran suka taso da gudu gaba ɗaya tun kafin ya gama rufe ƙofar motar suba cewa ‘Abba ina Anti Khadeeja?’ Ya ɗauki shukura ya kama hannun Nasreen yana cewa ‘Tana asibita, likita ya kwantar da ita, amma gobe in sha Allahu zan je na taho da ita.’

    Ya tattara su suka shige cikin gidan. Yana shiga bayan Ummi ta yi masa sannu da zuwa ya sallame ta ya fito ya raka ta sai da ta shiga gida ta kirawo masa babanta ya yi godiya sannan ya koma gida. Sai da ya biya sallar Magriba da Isha’I duk da yunwar da yake ji sannan ya zo ya zauna a parlor a gajiye, ya dubi Afaf wadda take kwance tana yin game a tab ɗinta yace ‘Afaf ɗauko min flask da kayan shayi.’

    Ta miƙe ta shiga kitchen ɗin, jimawa kaɗan ta fito ɗauke da kayan shayin bayan ta ajiye tace Abba babu ruwan zafi a flask ka jira na dafa maka, wanda Anti ta zuba mun sha shayi da shi mu da Ummi.’

    ‘No, bar shi kawai. Ɗauko min zoɓo ki kawo min ragowar abincin da kuka ajiye na ci, yunwa nake ji.’ Kafin ta ba shi amsa Habib yace ‘Abba ai tun kafin ku fita zoɓon ya ƙare a nan, ka manta? Kuma dama shi kenan wanda Anti ta zuba ragowar na jiya ne.’

    Kafin yace wani abu Afaf tace ‘Abba babu fa abincin ma sai dai ragowar rice and stew, gaba ɗaya dankalin muka cinye kuma da peppersoup ɗin, amma akwai ragowar watermelon a fridge. Ko na dafa maka indomie?’

    Ya kalle ta yana shafa kai na ɗan lokaci, ya ma rasa me zai ce mata saboda yanda gaba ɗaya ya jigata saboda yunwa, coke kawai ya samu a asibiti da wani guntun burodi ya ci. Ya zata za su rage abincin amma wai duk sun ciye. Muryar Afaf ce ta katse shi tana cewa ‘Bari kawai na dafa maka indomie ɗin Abba.’

    ‘No, bari na shiga kitchen ɗin na gani.’ Ya faɗa yana miƙewa tsaye. Ya ɗan ɗauki yana kallon kitchen ɗin bai ma san ta inda zai fara ba; har ya ɗauki tukunya zai dafa indomie sai kuma ya tuna ai akwai cereal, don haka ya mayar da tukunyar ya ajiyeta a muhallinta.

    Ya zuba ruwan zafi a kettle ya tafasa ya haɗa cereal, ya ajiye ya fiddo kankana daga fridge ya yanka sannan ya ɗauko ya dawo parlor ɗin. Yana zama Shukra ta matso tana dariya ‘Abba zan sha golden morn ɗin.’Ya bi ta da kallo da cokali a hannunsa; ba ta taɓa ba shi takaici ba kamar a wannan lokacin don ya tabbatar sun ƙoshi tunda gashi sun cinye duk wannan uban abincin da Khadeeja ta dafa.

    Ya dubi Afaf yace ‘Tashi ki ɗauko cereal, ki haɗo min da tea flask da komai na haɗa mata.’ Kafin Afaf ta dawo Nasreen tace ‘Abba ni ma zan sha.’ Don haka tana kawowa ya sa ta koma ta ƙaro kofi, ya haɗa musu cereal ɗin su biyun.

    Babu wadda ta sha cokali uku a cikinsu, suka tashi suka bar masa a nan. Kafin ya gama cinye nasa abincin duk sun fara gyangyaɗi don haka ya sa Afaf ta ɗauko musu kayan baccinsu ya shirya su bayan ya raka su sun yi brush sun yi fitsari. Bayan sun kwanta sannan Afaf da Habib su ma suka shirya, Afaf ta zauna a gefen gado ta yi tsuru-tsuru shi ma Habib sai ya hau katifarsa ya kwanta yana zare ido.

    Yana tsaye daga bakin kofa yace ‘Yaya dai Afaf? Ki kwanta mana, ko akwai wata damuwa ne?’ Ta jijjiga kai tace ‘Kawai tunawa na yi da Mommy, ita ma muna bacci ta mutu.’ Ya gaji sosai ga kansa yana sarawa, babu abinda zai iya yi musu na lallashi, ya buɗe baki a gajiye yace ‘In sha Allahu babu abinda zai sami Anti, ku yi addu’a ku kwanta ku yi bacci kawai.’

    Habib shi ma ya tashi zaune yana share ƙwalla ‘Wallahi Abba ni ba zan ma iya baccin ba, Allah ya sa dai kada Anti Khadeejan ma ta mutu ta bar mu. Har yanzu idan na tuna Mommynmu sai na yi kuka.’ Kafin ya yi magana ita ma Afafa ɗin hawaye ya fara bin fuskarta, ta sunkuyar da kai ta sa masa kuka har da shassheƙa.

    Ji ya yi kamar ya ɗora hannu a ka ya sa ihu; ina ma yaran nan za su bar shi ya huta, yanzu ya zai yi da su? Manyan cikinsu da yake ganin su ne ba za su bashi matsala ba su ne suke so su hana shi bacci. Ya ƙarasa ya zauna a kusa da Afaf ya rungumota yana cewa ‘In sha Allahu babu abinda zai sameta, ku daina kuka ku yi mata addu’a Allah ya ba ta lafiya. Goben nan ma zaku ga an sallamota.’

    Ta fara share hawayenta, Habib wanda shi ma ya taso ya dawo kusa da ita yace ‘Abba to ka kirawo mana ita a waya mu yi mata sannu.’ Ya zaro wayarsa daga aljihu yana cewa ‘To ai da bana son kiranta saboda kar na dame ta don an yi mata allurai, ban sani ba ko har da ta bacci a ciki. Amma bari na kirawo ta sau ɗaya idan ta ɗaga shikenan idan kuma ba ta ɗaga ba sai mu haƙura da safe ma sake kira.’

    Ya lalubo lambarta ya danna mata kira, sai da wayar ta kusa tsinkewa sannan ta ɗaga. Murya ƙasa-ƙasa tace ‘Hello.’Yace ‘Hello, Khadeeja ba ki yi bacci ba?’ ‘Na ɗan yi, farkawa dai na yi kuma na ji wayar tana ringing. Ai tun ɗazu aka gama wankin cikin har na ɗan ci abinci.’ ‘Sannu. Wankin cikin ba wahala kenan?’

    ‘Hmmm! Akwai wahala ba kaɗan ba, kawai dai da an gama aka ba wa mutum maguguna sai ya sami relief.’ ‘Sannu. Afaf ce dama ita da Habib wai ba za su iya barci ba sai sun yi miki sannu.’ Ta yi murmushi mai sauti domin ta ji daɗi har cikin ranta, ta tabbatar cewa yaran nan suna ƙaunarta kuma da zai barta da su komai nasu zai zo da sauƙi amma shi komai gani yake kamar za ta cuce su.

    Muryar Afaf ce ta katse ta bayan da Abbanta ya ba ta wayar ‘Anti.’ ‘Na’am Afaf, ya aka yi ba ki yi bacci ba.’ ‘Babu komai Anti, ya jikin naki? Ke ya aka yi ba ki yi baccin ba? Ta yi ‘yar dariya tace ‘Yanzu zan yi Afaf, kuma na sami lafiya don likitan ma ya ce gobe za a sallame ni.’ Suka ɗan taɓa hira sannan ta yi mata sallama ta miƙawa Habib wayar. Bayan sun gama gaba ɗaya ya karɓi wayar ya katse ya yi mata sai da safe. Ya yi musu sai da safe suka kwanta, har zai kashe fitilar Afaf tace ‘Abba kada ka kashe mana fitilar, in an jima ka zo ka kashe.’

    Haka ya bar musu fitilar ya fice. Can bayan awa ɗaya ya gama abinda yake yana so ya kwanta saboda ya gaji ya zo zai kashe musu fitilar, yana kashewa Afaf da Habib suka haɗa baki a lokaci guda suka ce ‘Abba kada ka kashe fitilar.’ Da mamaki yace ‘Kai! Me kuke ba ku yi barci ba?’

    Afaf tace ‘Abba to ni dai na kasa bacci, da ma za ka taya mu kwana.’ Habib yace ‘Eh wallahi Abba don ni wallahi tsoro nake ji.’ Takaici ya kama shi, to yanzu ya zai yi? Taya su kwanan zai yi ko kuwa barinsu zai yi a haka suna zare ido ya je ya kwanta? Wannan wacce irin fitna ce a daren nan ga shi ya gaji.

    Baya son barinsu su kaɗai don haka ya wuce ɗakinsa yaje ya shirya ya rufo gidan sannan ya dawo nan ɗakin; katifar Habib ƙarama ce ya san ba za ta ishe su ba don haka kawai ya gyarawa Nasreen da Shukra kwanciya ya ɗan sami waje a gefen gadon ya kwanta bayan Afaf ta kwanta a ɗaya gefen. Ya yi addu’a ya tofa musu sannan yace kowa ya rufe idonsa kada ya sake jin motsinsu.

    Tunda ya kwanta yake jin wani ɗan ɗoyi haka, idan iska ta busa sai ya ji kamar ɗoyin ya buso cikin ɗaki idan iskar ta wuce kuma sai ya daina ji. A haka bai san lokacin da bacci ya ɗauke shi ba. ‘Subhanallahi!’ ya faɗa bayan ya yi firgigit ya tashi, ya kai hannunsa ya taɓa inda yake kwance daidai ɗuwawunsa ya ji shi a cikin ruwa sosai. Ya ɗaga hannun yana kallo da tsananan mamaki ‘Inna lillahi wa inna ilaihi raji’un.’ Ya sake fada a fili.

    To fitsarin kwance ya yi ko me? Gashi yaran duk sun yi bacci balle yace wani ne ya zuba masa ruwa; tunda shi dai ya san ba ya fitsarin kwance. Motsin Shukra da ya ji a kusa da shi ne ya tabbatar masa da cewa ita ce ta yi fitsarin, ya miƙa hannu ya taɓata ya ji ta a jiƙe amma tana ta baccinta hankali kwance.

    Ya kai hannu zai janye Nasreen daga kusa da ita ya jita itama a jiƙe ‘Tab!’ ya faɗa a fili. Kenan duka su biyun suke fitsarin kwance ko kuwa yau suka fara? Don shi tunda Khadeeja ta tare a gidan nan sau ɗaya ya taɓa ji an ce Shukra ta yi fitsari. Ya kalli Afaf wadda ita tana can ta takure a ƙarshen gadon tana baccinta, ya danna wayarsa ya kalli lokaci ya ga ƙarfe biyun dare.

    Ba zai iya tashin yaran nan ba don haka ya lallaɓa ya sauka daga kan gadon ya fice ya shiga ɗakin Khadeeja ya samo zanin gado ya zo ya rufe su saboda kar sanyi ya dinga kaɗa su ga danshi. Bayan ya gama rufe su ya zo ficewa daga ɗakin ɗoyin da yake ta ji ya sake dukan hancinsa; wannan ɗoyin ai sai ya kumburawa mutum ciki.

    Kamar daga banɗaki ɗoyin yake fitowa don haka ya koma ya buɗe ƙofar banɗakin ya shiga, ya karasa ya leka toilet din ya tarar babu komai a ciki duk da haka dai ya danna flushing ya juya zai fita. A daidai bakin kofa daga jikin bango ya ci karo da fo ɗin Shukra wanda ɗazu Afaf ta cire wandon Shukra mai ɗauke da kashi ta jefa a ciki. Pant ɗin yana nan da kashin a yanda ta ajiye har ya fara bushewa amma duk ya ɗumame bandaki da ɗoyi.

    Ya ɗan ja baya kamar a firgice, to wa Afaf ta ajiyewa wannan kashin? Yanzu ya zai yi da shi ga shi duk ya ɗumame gidan da wari. Ya ɗaga hannuwansa ya zuba a aljihu, danshin da ya ji ya tuna masa cewa wandon a jiƙe yake da fitsrin Shukra ce ko Nasreen shi ma bai sani ba. Ya yi tsaki ya fito daga banɗakin ya wuce ɗakinsa yana tunanin yanda zai yi da kashin, ga shi a jikin pant yake balle ya sa a toilet ya yi flushing.

    Sai da ya yi wanka ya canza kaya sannan ya fito daga ɗakin, yana fitowa ya ji warin kashin nan har parlor ɗin saboda ya bar kofar a buɗe. A fusace ya wuce kitchen ya ɗauko ƙatuwar baƙar leda ya zo ya ɗauki fo ɗin ya ƙulle a ledar, ya sake ɗauko wata ledar ya ƙara ƙullewa sannan ya ɗauki mukulli ya buɗe ƙofa ya fice ya jefa a shara; gari yana wayewa zai sami yaro ya fitar masa da sharar.

    Ya san dai Shukra ta iya hawa toilet yanzu, duk da idan ta so rigima sai tace sai ta hau fo amma shi dai ya zubar don ba zai iya wankin kashi ba kuma ba zai iya bari Afaf ta yi ba ta zo ta yi musu jagwalgwalo da kashi. Yana dawowa cikin parlor ɗin ya kalli agogon bango ya ga ƙarfe uku har ta wuce, abinda ya yi masa saura bai fi awa ɗaya da rabi ba a yi assalatu.

    Sai a lokacin ya tuna ba shi ma da abincin sahur, ga shi kuma ko a lokacin ma yunwa yake ji balle yace zai yi ɗore. Kai tsaye ya wuce kitchen ya ɗora indomie sannan ya tafasa ruwan shayi; nan da nan ya juye indomie ɗin a plate ya ɗumama stew ya zuba sannan ya haɗa shayi, ya kwaso ya dawo dining table ya fara ci.

    Tun kafin ya haɗiye lomar farko ya fara jiyo hayaniyar Shukra a ɗakinsu, yana zuba loma ta biyu ta buɗo ƙofar ɗakin ta fito tana kuka tana ‘Antiiii..’ Ya ajiye cokalin yace ‘Menene Shukra?’ ‘Shayi zan sha Abba’ Har cikin zuciyarsa takaicinta ya kama shi, to amma ya zai yi da ita? Haka ya kirawo ta ya zaunar da ita a kan kujera, tun kafin ya gama gyara mata zamanta zarni ya cika masa hanci; sannan ma ya tuna ta yi fitsarin kwance.

    Ya gyara mata zama yace ‘Bari na gama sahur sai na haɗa miki shayin.’ Ya ɗauki cokali ya zuba loma a bakinsa yayin da ita kuma ta fara mutssike ido tana kuka. ‘Menene kuma?’ ya tambayeta ‘Yunwa nake ji, shaaayiii.’ Ya duba agogon wayarsa, saura bai fi minti goma sha biyar ba a yi assalatu ga shi ba ya jin zai kai azumin nan idan bai yi sahur ba, ya kalle ta yanda take ta kuka kamar wadad aka ciza.

    Bai taba jin haushin Shukra kamar yau ba, amma babu yanda zai yi. Haka ya juye mata rabin shayin da ya haɗa zai sha ya saka mata madara da milo ya miƙa mata sannan ya cigaba da cin abincin. Yana yi yana kallon lokaci saboda kar a kirawo assalatu. Haka ya ci abincin nan ya yi sauri ya kwankwaɗe shayinsa rabin kofi sannan ya ɗora da ruwan sanyi duk a lokaci guda.

    Yana ajiye kofin aka fara kiran assalatu, ya kwantar da kansa a jikin kujerar yana mayar da numfashi. Shukra da take kan kujera tana gyangyaɗi bayan ta shanye shayinta ta taɓo shi tana cewa ‘Abba kashi zan yi.’ A ɗan zabure ya dube ta yace ‘Kashi Shukra?’ Cikin halin ko in kula tana murje idonta tace ‘Um.’ Ta fara ƙoƙarin sauka daga kujerar da take zaune.

    Ya jijjiga kai cike da takaici; su wai yara ba a hutawa da hidimarsu ne? Tunda ya dawo daga asibiti ake abu ɗaya ga shi duk yana neman fita daga hayyacinsa amma babu alamar sauƙi. So yake ma ya sami natsuwa ya turawa Khadeeja message ta whatsapp ya ga ko tana online amma ba su ba shi time ba, a halin yanzu ma kansa ciwo yake ga bacci duk kansa ya cushe bai ma san ta ina zai fara ba.

    Haka ya bi bayanta har banɗaki, Allah ya taimake shi ba ta ma nemi fo ba ya taimaka mata ta hau toilet ta yi kashinta. Yana zaune a gefen gadonsu ya jiyo ta daga banɗakin tana cewa ‘Abba na gama. Gaban shi ya faɗi da ya tuna wai shi take sa rai ya yi mata tsarki; ya juya ya kalli Afaf wadda take baccinta hankali kwance.

    Ya san idan ya tashe ta za ta yi mata tsarkin to amma fa ita ma bata kwanta da wuri ba. Ya jijjiga kai ya mike bayan da ta sake maimaita masa ta gama a karo na uku. Haka ya tashi ya shiga banɗakin ya wanke mata kashin ya wanko hannunsa ya fito ya canza mata kaya ya mayar da ita ya kwantar da ita a kusa da Habib saboda katifar kan gadon ta jiƙe; zuwa lokacin masallatai duk sun riga sun tayar da sallah.

    Yana fitowa daga ɗakin yayi alwala ya ta-da sallah a ɗakinsa, yana zaune a kan dadduma yana azkar Nasreen ta turo ƙofa ta shigo ɗakin, ta ƙaraso ta faɗa jikinsa tana cewa ‘Abba na tashi, ba ka dawo mana da Anti Khadeeja ba?’ ‘Eh, sai an jima.’ Ya faɗa yana ture ta. ‘Ki je ki ce Ant….’ Sai kuma ya tuna Antin ba ta nan don haka ya gyara zance yana ƙoƙarin miƙewa ‘Mu je na wanke miki jiki ki canza kaya sai ki yi sallah.”

    ‘Abba ni yunwa nake ji.’ Ya ɓata rai yace ‘Sai an canza kaya kuma kin yi sallah.’ Haka ya yi ta fama da yaran nan, ga shi ita Afaf ma fushi take da shi saboda bai tashe ta sahur ba tunda Anti tana tashinta tana yin azuminta. Sai wajen ƙarfe takwas na safe sannan ya tashi ya koma ya roƙo Baban Ummi ta shigo ta karɓi yaran don yana son ya tafi asibiti wajen Khadeeja. Yana shiga ɗakinsa ya zauna a gefen gado ya danna mata kira.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Biyar

    Edita@rumasau-kallamu

  • Abubuwan Da Ke Haddasa Rashin Zuwan Al’ada (AMENORRHEA)

    Abubuwan Da Ke Haddasa Rashin Zuwan Al’ada (AMENORRHEA)

    Idan al’ada tana daɗewa ba ta zo ba sai bayan watanni 3 zuwa 6, wannan shi likitoci suke kira “amenorrhea”. A gaskiya wannan yanayin bai kamata a ce mace tana fama da shi ba. Idan kuma ya auku, to, yana nufin cewa mace tana da matsala kenan.

    Amenorrhea ya kasu gida biyu kamar haka:

    1. Primary amenorrhea: Wannan yana nufin daɗewa na farko ko kuma daɗewa na asali wanda al’ada take yi ba ta zo ma mace ba. Abinda yasa ake kiransa daɗewa na farko ko na asali shi ne yana faruwa ne ga mace budurwa wacce ba ta taɓa yin al’ada ba a rayuwarta, sai ya kasance ta kai munzalin da ya kamata a ce ta fara al’adar, to, amma sai ba ta zo mata ba.

    Mafi yawanci budurwa tana fara al’ada ne tsakanin shekaru 9 zuwa 13. Don haka idan budurwa ta kai shekaru 16 zuwa 18 ba ta fara al’ada ba, to, wannan shi ne primary amenorrhea.

    2. Secondary amenorrhea: Shi kuma wannan yana nufin daɗewar da al’ada take yi ba ta zo ba har na tsawon watanni 3 zuwa 6 ga babbar mace, watau ba budurwa ba.

    Da primary amenorrhea da secondary amenorrhea suna faruwa ne saboda dalilai masu yawa, waɗanda suka haɗa da:

    1. Yanayin da Allah ya halicci tsarin jiki kamar ɗaukar ciki, shayarwa, nisan shekaru (menopause) da sauransu. Idan mace tana cikin ɗaya daga cikin waɗannan yanayin, to, za ta fuskanci ɗaukewar al’ada.

    2. Shaye-shayen magunguna kamar na family planning ko kuma domin warkar da wata cuta da take damun mace.

    3. Lahani wanda ya sami tsarin jikin mace na haihuwa (reproductive system defects) kamar jakar da take ɗauke da ƙwaya-ƙwayan haihuwa (ovary) ko mahaifa (uterus) idan suka sami matsala.

    4. Rashin daidaiton zubar sinadarai a cikin jiki (hormonal imbalance).

    5. Yin ayyuka na wahala.

    6. Damuwa (stress).

    7. Kasancewar mace ta zamo mai tsananin ƙiba ko tsananin sirantaka.

    Hanyar kaɗai da za a iya magance amenorrhea ita ce idan aka tuntuɓi likita ya yi bincike mai zurfi domin gano wasu daga cikin dalilan da suke haifar da shi, daga nan sai a bayar da maganin da ya dace.
    Karanta Yadda Tsiron Mahaifa Yake

    Edita@rumasau-kallamu

  • Amfanin Haƙuri

    Amfanin Haƙuri

    Haƙuri: Shi ne danne zuciya a kan wani abu mara kyau, wanda ya baƙantawa mutum zuciya.

    Haƙuri yana da matuƙar amfani ga mutane, kamar yadda ya zo a cikin littafin Sheikh Abdulrahim bin Ahmad Alkadhi mai suna “Daƙa’ikul khabar” shafi na 17 babi na goma sha biyu yace, labari ya gangaro cewa wanda aka jarabce shi da wata masifa, sai ya yaga tufafin sa ko ya bugi ƙirjin sa (to hukuncin wanda ya aikata haka) kamar (wanda) ya riƙi makami ne zai yi yaƙi da Allah (Subhanahu wata’ala).

    Sannan kuma an ruwaito daga Annabi Muhammad (Sallallahu alaihi wasallam) yace wanda ya ɓalle ƙofa ko ya yaga tufafin sa ya yi da wata masifa ta same shi ko ya bugu wajan zaman sa ko ya sare bishiya ko ya yanke gashin kan sa (saboda tsanani masifar da ta same shi), to za a gina masa gida na wuta a kan kowane gashi (wanda ya cire), sa’annan kuma Allah ba zai karɓi aikin sa na farilla ba ko na nafila matuƙar yana kan wannan hali.

    Har ila yau, Allah zai ƙuntata ƙabarinsa, kuma zai tsananta yi masa hisabi, sannan kuma dukkanin mala’ikun da suke sama da ƙasa za su dunga tsine masa, haka kuma za a rubutawa laifuffuka guda dubu a gare shi, sannan zai tashi a cikin ƙabarin sa tsirara.

    Haka kuma, wanda ya karya gefan jikin sa, saboda wata masifa, to Allah zai karya addinin sa, idan kuma ya bugi ko ya mari kumatun sa ko ya azabtar da fuskar sa, to Allah (Subhanahu wata’ala) ba zai kalle shi ba da rahmar sa ba ranar alƙiyama.

    Bugu da ƙari, kuma ya zo a cikin shafi na 18, babi na goma sha huɗu a cikin wannan littafin yace Sayyadina Aliyu bin Abu-ɗalib (karramallahu wajhahu) yace “haƙuri ana yin sa ne ta hanyoyin guda uku; na farko yin haƙuri a kan yi wa Allah biyayya, na biyu yin haƙuri a kan saɓawa Allah, na uku haƙuri a kan wata masifa wacce ta samu mutum.

    Saboda haka, duk wanda ya yi haƙuri a kan yi wa Allah biyayya, to Allah zai ba shi daraja guda ɗari, sa’annan kuma ko wace daraja yawanta ta kai tsakanin sama da ƙasa.

    Wanda kuma ya yi haƙuri a kan saɓawa Allah, to Allah zai ba shi daraja guda ɗari shida ranar lahira, haka kuma kowace dajara yawan ta ta kai faɗin sama da ƙasa, wanda kuma ya yi haƙuri a kan wata masifa wacce ta same shi, to Allah zai ba shi lada ba tare yi masa hisabi ba (ranar lahira).

    Karanta Tarihin Farfesa Abdallah Uba Adamu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Biyar

    Mijin Marigayiya Babi Na Biyar

    Ko da gari ya waye Khadeeja ba ta ma san lokacin da Ummi ta zo ba don tun daga bakin gate ya tare ta yace ta koma kada ta sake zuwa sai bayan Sallah. Sai wajen sha ɗaya sannan ta fito ta ɗan gayggyara gidan, wanke-wanke ne ma ya ɓata mata lokaci don yana da yawa sosai. Haka ta wanke su gaba ɗaya a famfon waje sai da shigo kifewa sannan Afaf ta taya ta.

    Tana gamawa ta shige ɗakinta ta kwanta; ba ta taɓa jin gajiya irin wannan ba a rayuwarta, ga shi duk wata gaɓa da take jikinta ciwo take yi. Tun 3pm ta shiga kitchen ta fara ƙoƙarin haɗa kayan shan ruwa; dankali da ƙwai za ta soya sai jollof sphagetti sannan ga peppersoup ɗin nama. Da akwai ragowar zoɓo na jiya don haka ba za ta sake haɗa wani ba.

    Yaran suna zaune a parlor ta zo ta wuce ta shiga kitchen, tana wucewa Afaf ta bi bayanta. Ta so ta koro Afaf ɗin daga kitchen amma dai ta haƙura ta bar ta, suna yin aikin. Ba su daɗe da farawa ba Habib ya shigo kitchen ɗin, ya kalli dankalin da aka ajiye a tsakiyar kitchen ɗin yace ‘Anti wannan ferayewa za a yi?’

    Tace ‘Eh, so nake na ɗora kifin nan sai na zauna na feraye shi.’ ‘Kawo wuƙa na feraye Anti.’ Ya faɗa yana buɗe cabinet, ya zaro roba ya tara ya ɗebu ruwa. Tace ‘Ka bar shi Habib zan feraye. Ya sa hannu ya ɗauki wuƙa a kan sink yana cewa ‘Na iya feraye dankali fa Anti, idan na feraye miki sai ki yanka.’

    Bai saurari amsarta ba ya tsuguna ya fara feraye dankalin. Afaf ta ajiye kayan miyan da ta gama wankewa a kusa da Khadeejan tace ‘Anti na wanke kayan miyan.’ ‘To ki yanka mana albasar nan, rabi slicing za ki yi rabi kuma ki yanka ƙanana sai a saka a soup da fried egg.’ Ta ɗauki albasar ta wanke ta zuba a chopping board ta fara yankawa.

    Ba su ji lokacin da Mustapha ya ƙaraso bakin ƙofar kitchen ɗin ba; a dai-dai lokacin nan wuƙar da Afaf take yanka albasa ta goce ta yanke mata hannu. Ta dire albasar ta make murya tana cewa ‘Waiyo Anti na yake.’ Da sauri ta saki abinda yake hannunta ta nufi wajen Afaf ɗin tana murmushi cike da kulawa tana cewa ‘Sorry, garin yaya Afaf. Ki…’Da sauri ya ƙarasa ya kama hannun Afaf ɗin yana cewa ‘Garin Yaya kika yanke, me ya sa kika dauki wuka?’

    Ya juya ya dubi Khadijan yana cewa ‘Na gaya miki sai kin san aikin da za ki dinga sa yaran nan amma ke gani kike kamar kawai bana son su taya ki aiki ne. Yaushe Afaf za ta iya wani yanka albasa.’ Afaf ta zare hannunta daga nashi hannun ta juya ta wanke a sink, ta dube shi tace ‘Ya ma daina jinin Abba bari na je na daure.’

    Yana juyawa ya dubi Habib wanda yake ta ferayar dankali ya daka masa tsawa ‘Ka ajiye wuƙar nan ka tashi, namiji da kai kana wani feraye dankali. Tashi ka ba ni waje.’ Ya juya kan Khadeeja wadda ta riga ta cigaba da aikinta kamar ba da ita yake magana ba, yace ‘Na gaya miki ki daina sa yaran nan aikin da ya fi ƙarfinsu, bana so. Shi Habib ma da yake namiji me ya haɗa shi da wani harkar girki? Bana so.’

    Bai ga alamar za ta ba shi amsa ba don haka ya juya shi ma ya fice suka barta ita kaɗai a kitchen ɗin. Ta rasa me ma za ta yi, ta goge fuskarta ta cigaba da aikinta. Haka ta lallaɓa ta gama komai, zuwa magriba ta zubawa kowa aka sha ruwa. Ta gaji iya gajiya don haka ba ta ma da kuzarin da zata iya wani musu da shi, ta dai riga ta gama yanke wa kanta hukunci da zarar an buɗe gari za ta tafi gidansu ba za ta dawo ba sai ta haihu ko kuma ya ɗauki mai aiki.

    A haka aka cigaba da azumi, kullum cikin wannan yanayin Khadeeja take haɗawa da hidimar gidan da ta yaran ta yi ta fama. Kullum sai ta yi wa Shukra da Nasreen wanka, tsarkin kashi tsarkin fitsari duk ita take musu. Duk wata fitinarsu ita ce me kulawa. Ga shi tana fama da Shukra wadda sai yanzu ne da suka kwana biyu ta fara hana ta kashin wando.

    Yanzu idan dai ba wasa take yi ba ba ta kashin wandon ta iya zuwa ta gayawa Anti za ta yi kashi. Amma idan tana wasa haka za ta tsuguna a wajen wasan sai ta gama kashinta sai dai a ji wari. Haka dai take ta fama.

    Juma’a ce yau ɗin, gaba ɗaya a jigace take jin ta saboda azumi na sha ɗaya kenan za a kai kuma kullum ita kaɗai take hidimar gidan da ta yara. Gashi kuma ta ƙi ta ajiye azumin saboda ko ba ta yi azumin ba ma ba iya cin abincin kirki take ba. Haka dai ta tashi jikinta duk babu ƙwari, ta ɗan yi iya abinda za ta iya ta koma ta kwanta.Tun wajen 2pm ta taso ta fara aikin abincin shan ruwa don tana so ta gama da wuri, tunda zuwa yanzu yaran ma sun hakura sun daina yunkurin tayata.

    Sai dai ita ɗin ma ta rage aiyukan da yawa don duk abinda ta kasa rabuwa take da shi. Dankali da ƙwai kawai ta soya ta dafa shinkafa ta ɗumama ragowar stew ta juye a flask, ta kawo ruwan shayi ta zuba a flask. Saura wajen rabin awa a sha ruwa ta gama ta kawo komai ta jera, ta wuce ɗaki ta kwanta bayan ta gayawa Afaf ta kula kada kannenta su yi ɓarna.

    Ba ta yi minti goma da kwanciya ba Nasreen ta shigo ɗakin da gudu tana taɓa ta tana cewa ‘Anti Shukra ta yi kashi, Abba ya ce ki zo ki wanke mata.’ Ta tashi zaune tace ‘A toilet ɗinku ta yi kashin?’ ‘A wandonta ta yi Anti.’ ‘Je ki ina zuwa.’ Ta ja tsaki ta koma ta kwanta bayan Nasreen ta fice daga ɗakin. Jiri take ji sannan a wani ce ta zo ta wanke kashi, kashin da tace a daina yi mata a wando.

    Ta yi zaton ma a toilet ta yi kashin ta je ta yi mata tsarki. Kafin ta gama yanke hukuncin da za ta ɗauka Abbansu ya shigo, bayan ta amsa sallamarsa yace ‘Ki zo ki wankewa Shukra ta yi kashi.’ Ta dafe kanta ta tashi tana cewa ‘Ba lallai na iya ba ne don wallahi jiri nake ji gashi yau tun safe marata take ciwo.’

    ‘To na ce ki ajiye azumin kin ƙi, ki bar shi haka ki huta. Ki taso ki gyara mata alwala zan je na yi an kusa kiran sallah.’ Ta miƙe a hankali ta biyo bayansa suka fito daga ɗakin. Tana shigowa parlor ɗin Shukra ta sunkuyar da kai, ta harare ta tace ‘Kin sani ai mara kunya, nace ki daina yin kashi a wando amma kin ƙi ko? Yau gidansu ƙyanƙyaso za ki kwana a can ake kashi wando.’

    ‘Don Allah ki yi mata a hankali, komai lokaci ne ai za ta daina ne a yi mata haƙuri.’ Ya faɗa yana shirin komawa ɗakin ya yiwo alwala. Ta tsuguna za ta ɗauke ta ta ji kanta ya biyo ta kamar zai faɗo, ta dafe goshi ta koma ta tsaye tace ‘Kai! Ba zan iya ba fa.’ Ya juyo ya tsaya ‘Menene?’

    ‘Ba zan iya tsugunawa ba fa, jiri kwasa ta yake.’ ta ƙarasa kan kujera ta zauna ta dafe goshi. Ta dubi Afaf tace ‘Ba ni ruwa na sha Afaf, ga kiran Sallah nan an fara. ’Nan da nan ta cika Kofi da ruwa ta miƙa mata, ta sha kaɗan ta jingine kanta tana riƙe da ruwan. Kukan Yusra ne ya katse su tana cewa ‘Anti na daina ba zan kuma ba, mantawa na yi daman.’

    Ta yunkura za ta miƙe Afaf ta yi sauri ta dafe ta. Abbansu ya dubi Khadija yace ‘Don Allah ki lallaɓa ki wanke mata kashin nan, Wannan wane irin abu ne? Yanzu wa kike so ya wanke mata kashin?’ Afaf ta aika Nasreen ta ɗauko fo a toilet ta cire wandon da yake cike da kashi ta jefe a fo ɗin sannan ta ɗauke Shukran ta nufi banɗaki. Ta wanke mata sannan ta dawo ta gyara wajen, zuwa lokacin Abbansu ya fito daga alwala.

    Ya zauna ya sha ruwa sannan ya miƙe zai tafi masallaci. A daidai lokacin ita ma Khadeeja ta ɗago kanta tace ‘A dawo lafiya.’ Yana jin ta ya yi banza da ita saboda yanda yake jin haushinta, kuma tabbas sai ya kora mata bayani in an sha ruwa. Daga yau ma ba za ta sake yin azumin ba tunda dama mai ciki tana da damar ajiyewa. Ta miƙe tana gatsina fuska, kawai sai gani ya yi ta sulale za ta faɗi.

    Ya zabura zai tare ta ya yi fatali da casserole ɗin dankali, a lokaci guda Habib ya saki jug ɗin zobon da ya fito da shi daga kitchen ya tarwatse a wajen ya ƙarasa kanta. Duka su biyun kafin su ƙaraso ta zube. Abbansu ya ɗago kanta yana jijjigawa ‘Khadeeja, Khadeeja, Inna lillahi wa Inna ilaihi rajiun, Khadeeja.’ Ko motsawa ba ta yi.

    Ya sunkuce ta ya kwantar da ita a kan three seater, ya ƙara gudun fanka sannan ya kunna AC. Ya cire mata ɗankwalin da yake kanta ya fara yi mata fifita. Yaran gaba ɗaya suka jeru a kanta suka yi tsuru-tsuru; Afaf ta leƙa fuskarta ta kafaɗar Abbansu tace ‘Abban ita ma mutuwa za ta yi ta bar mu ko?’

    ‘Ke bana son rashin hankali, ba mutuwa za ta yi ba.’ A take yaran suka saka masa kuka mai ban tausayi. Afaf ta rungume Nasreen da Shukra suka haɗa kai suna kuka. Habib ya taɓa shi yace ‘Abba ka kai ta asibiti kada ta mutu ta bar mu.’ ‘Kai rufe mana baki.’ Gaba ɗaya shi ma ya ruɗe, jikinsa har rawa yake yi. Ya janyo jug ɗin ruwan sanyi ya jiƙa hannunsa ya shafa mata a fuska. Ta ja numfashi ta buɗe idonta, sai kuma ta mayar ta rufe.’Khadeeja.’

    Ya kirawo sunanta da ƙarfi yana jijjiga ta. Da gudu su Afaf suka ƙarasa kanta suna kira ‘Anti, Anti.’ ‘Khadeeja.’ Ya kara kiran sunanta a firgice. Ta buɗe ido ta sake rufewa. Ya miƙe tsaye ya ɗan tura yaran yana cewa ‘Ku zauna na ɗauko mukullin mota, asibiti zan kai ta yanzu, babu abinda zai same ta in sha Allahu.’

    Ba tare da ɓata lokaci ba ya ɗauko mukulli ya fito, ya je ya buɗe kofar motar ya dawo ya ɗauke ta bayan ya yafa mata mayafi ya wuce yaran suna biye da shi ya kwantar da ita a bayan motar. Bayan ya rufe ƙofar motar ya juyo ya kalli yaran yana tunani; to yanzu ya zai yi da su? Wa zai bar wa su? Ya san shi kansa ma sai ya amsa tambayoyi a checkpoints ga shi ma’aikatan asibitin ma kamar tsoron mutane suke balle ya kwashi yara su tafi.

    Ya shafa kai sannan ya sake kallonsu cike da damuwa; da a ce gari a buɗe yake da sai ya wuce da su ya ajiyesu gidan Hajiya to amma ya san ba zai yiwu don zai yi ta ɓata lokaci a checkpoint. A take dabara ta faɗo masa. ‘Ku tsaya a nan ina zuwa.’ Ya ba su umarni sannan ya fice daga gidan ya turo gate ɗin.

    Yana fitowa ya ƙarasa gidan su Ummi, ya yi sa’a yana tsayawa maigidan yana dawowa daga masallaci. Bayan sun gaisa ya sanar da shi so yake Ummi ta zo ta zauna masa da yara ya je ya kai Khadeeja asibiti. Ya janjanta masa sannan ya shige gidan ya turo masa Ummin. Haka ya sako ta a gaba ya dawo gidan ya bar mata yaran ya ja motar ya nufi Aminu Kano Teaching Hospital da ke Kano.

    Yana zuwa asibitin aka nuna masa gynae emergency inda nan ne ake karɓar masu ciki waɗanda suke buƙatar taimako na gaggawa, nan da nan suka karɓe ta aka fara duba ta; duk da dai su kansu ma’aikatan za ka gane cewa suna cikin yanayi na tsoro saboda Covid19. A nan wajen aka nuna masa benchi ya zauna yayin da ita kuma aka tura ta a kan gadon marasa lafiya aka shige da itaɗdakin bincike.

    Tana kwance a kan gadon yayin da take amsa tambayoyin ma’aikaciyar jinya sai wata ma’aikaciyar wadda ta ji suna kira matron ta shigo, ma’aiakaciyar ta juya tana kallon matron tana cewa ‘Matron wannan fa sai an yi mata scaning, cikin nan na jikinta kamar ficewa zai yi duk da dai tace ba ta fara bleeding ba amma dai tana jin alamunsa.’

    Matron ɗin ta ƙaraso ta tsaya a kanta, tace ‘Ah! Wannan ai Khadeeja ce, wa ya kawo ta?’Jin an ambaci sunanta ya sa ta buɗe idonta a hankali, ta yi murmushi a gajiye lokacin da suka haɗa ido ta gane wadda ta ambaci sunan nata. Cikin sanyin murya tace ‘Anti Iyami.’ ‘Na’am, Khadeeja. Wa ya kawo ki?’ ‘Mustapha ne.’

    Ta juya ta kalli abokiyar aikin nata tace ‘’Yata ce ai, ita ce wadda muka yi biki kwanaki fa yarinyar Habiba wadda nace miki childhood friend ɗina ce.’ Da fara’a tace ‘Aaah! Allah sarki, to abun ya zo kenan haihuwa yaƙin mata.’ ‘Ai kuwa. Bari na kirawo Dr. Jamil ya zo ya duba min ita sai mu je na kai ta scanning ɗin mu ga ko za a iya sallamarta a daren nan.’

    Har ta juya za ta fice Khadeeja ta riƙo hannunta, ta juyo tana cewa ‘Akwai wani abu ne Khadeeja?’ Ta yi murmushin yaƙe ta goge ƙwallar da ta gangaro daga gefen idonta tace ‘Kada ki sallame ni Anti Iyami, ki yi wa Mommy waya ta zo ta ɗauke ni gida zan tafi.’ Ta ɗan ranƙwafo tana shafa kanta tana duban fuskarta tace ‘Ok, kada ki damu, ki samu ki huta tukunna likita ya duba ki. In sha Allahu yanzu zan kirawo ta ko ba ta zo ba da safe idan na tashi daga aiki sai na tafi da ke gidan Mommy ɗin. Kada ki damu.’

    Ta juya ta fice yayin da Khadijan ta mayar da idonta ta rufe. Tare da likitan suka dawo, bayan ya duba Khadeeja aka je aka yiwo scanning tare da Mustaphan aka dawo. Bayan likita ya duba scanning ɗin yace cikin jikinta ya lalace fita zai yi, don haka za a yi mata wankin ciki sannan akwai allurai da ruwa da za a saka mata.

    Da kansa ya je ya siyo komai ya kawo sannan suka koma wajen Khadeeja tare da matron; a nan Khadeejan take sanar da shi cewa martron kawar Mommy ce. Ya sake gaisheta cike da girmamawa, bayan ta amsa ta dubi Khadeejan tace ‘Likita ya ce cikin jikinki ya lalace don haka za a yi miki wankin ciki, ga magunguna kuma ya rubuta miki sannan ga drip idan an gama wankin cikin zan saka miki kin ga yau a nan zamu kwana da ni da ke.’

    Ta yi murmushin yake, ta dubi Mustapha tace ‘Ka tafi, ka bar yara a gida. Anti Iyami za ta kirawo ka  idan akwai wani abu tunda ka ga tare zamu kwana ma, zuwa da safe za mu yi waya in sha Allah. Matron ta fice ta ba su waje. Bayan ta fice ya matsa kan Khadeejan yana shafa fuskarta yace ‘Sannu, kin ba ni tsoro fa.’

    Ta yi murmushi.Ya cigaba ‘Kafin safiyar ta yi sai ki samu ki yi min message ɗin duk abinda kike so na taho miki da shi, idan kuma Allah ya sa da safen za su sallame ki ma shikenan sai kawai na zo mu tafi. Na yi maganar abinci ma Anti Iyami tace na bari za ta kawo miki, but in ana son wani abu kiyi min magana sai na saka miki kuɗi a account ɗinki ko transfer ne sai ki yi musu.’

    Ya sa hannu a aljihunsa ya zaro wayarta ya miƙa mata yana cewa ‘Ga wayarki, ba zan kirawo ki ba don kada na dame ki ko na tashe daga bacci, but please da kin farka ki kirawo ni.’ Ta karɓa tana murmushi tana cewa ‘Ok, ka gaishe min da su Yaya Afaf.’ Ya fice ya bar ta a kwance. Yana fitowa ya sami Anti Iyami da abokan aikinta a station ɗinsu, ya yi mata sallama bayan ta ƙarbi lambar wayarsa sannan ya wuce.

    Tun a daren Anti Iyami ta kirawo Mommy ta sanar da ita halin da ake ciki, sai dai ba ta gaya mata cewa Khadeejan tace gida zata taho ba. Ta dai sanar da ita cewa tana hannunta idan akwai wani abu za su ji zuwa wayewar gari. Tana tsaye aka yi wa Khadeeja wankin ciki sannan aka ba ta ɗaki, ta saka mata drip da alluranta sannan ta haɗa mata shayi mai kauri.

    Ta sakata a gaba bayan ta shanye sannan ta zuba mata shayi da kwai ta cinye sannan ta ajiye mata saucer da kankana da lemon ɓawo tace ta shanye kafin a jima. Ta sha tambayoyi a wajen Anti Iyami wadda take ƙoƙarin gane dalilin da yasa Khadeejan take son tafiya gida; sai dai ba ta sami komai ba don da a tunaninta ko Mustaphan yana abusing ɗinta ne. Ita kuma ta sanar da ita kawai ba ta da lafiya ne sannan kuma ga aikin gida da raino wanda ya yi mata yawa shi yasa take son ta je gida ta huta.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Huɗu

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ɗabi’ar Tsotson Ɗan Yatsa Take (FINGER SUCKING)

    Yadda Ɗabi’ar Tsotson Ɗan Yatsa Take (FINGER SUCKING)

    Tsotson ɗan-yatsa, musamman babban ɗan-yatsansa (thumb), ɗabi’a ce wacce Jarirai suke yi da ƙananan yara ‘yan wata 6 zuwa shekara 5. Wannan ɗabi’a tana faruwa ga Jarirai tun suna cikin mahaifa, idan aka yi awon Ultrasound akan iya ganin jariri yana tsotson babban ɗan yatsansa.

    Yara da Jarirai sukan yi tsotsan ɗan yatsa ne domin su jiyar da kansu daɗi, ko barci mai daɗi. Wannan ba matsala ba ne. Suna ɗaukarsa kamar suna shan nono ne, don haka sai su sami nutsuwa idan suna yi.

    Amma idan yaro ya wuce shekara 5 yanayin ɗabi’ar tsotson ɗan-yatsa, to, za ta iya haddasa masa matsalolin daidaituwar haƙora (orthodontics issues), kamar:

    • gantso (dental misalignment),
    • ko rashin daidaiton tsawon haƙora (open bite teeth),
    • ko matsalar girman ƙashin muƙa-muƙi (jaw growth issues),
    • ko matsalar magana yadda zai sha wahala wajan furta wasu kalmomin irinsu “S” “the,
    • ko matsalar tsaftar (hygiene problem)

    Tsotsan yatsa yana iya kawo yaɗuwar ƙwayoyin cuta daga hannu zuwa baki, sannan zai iya haddasa cuttutuka kamar ciwon ciki, gudawa, ko maƙogwaro, da sauransu. Iyaye za su iya ƙarfafawa ‘ya’yansu gwuiwar daina tsotson ɗan-yatsa ta hanyar:

    1. Yin musu bayanin rashin amfanin tsotson ɗan-yatsa.

    2. Samar musu da kayan wasa waɗanda za su ɗauke musu hankali daga tsotson ɗan-yatsa.

    3. Sanya musu safar hannu ko abubuwa masu ɗanɗanon ɗaci (bitter) amma ba masu cutarwa ba, kamar ganyen shuwaka, ganyan maina a hannu, saboda ɗacin ya hana su tsotson ɗan-yatsan.

    Kodayake wannan ba dole ba ne ya yi tasirin hana wani yaron tsotson ɗan-yatsa, saboda a lokacin yaye wasu matan sukan shafa abu mai ɗaci a nipples ɗinsu, amma hakan ba ya hana wani yaron shan nonon.

    Karanta Yadda Tsiron Mahaifa Yake (UTERINE FIBROIDS)

    Edita@rumasau-kallamu

  • Malamai, Malanta Da Hanyoyin Sada Zumunta A Yau (1)

    Malamai, Malanta Da Hanyoyin Sada Zumunta A Yau (1)

    Malam Imam Ahmad da sauran malaman sunan sun rawaito daga Abi Darda` (RA) ya ce: Manzon Allah SAW ya ce: “Lallai Malamai magada Annabawa ne, Su Annabawa ba su bar dinari ko dirhami ba, sai dai sun bar ilimi. Wanda ya yi riƙo da shi lallai ya yi riƙo da rabo babba”

    A cikin wannan rubutun duk inda aka faɗi malami ko malamai ana nufin malamin addinin musulunci wanda aka yarda da iliminsa da kuma tsoron Allahan sa. Irin waɗannan malaman su ne magada Annabawa, saboda suna yaɗa shiriya ga mutane (Wanda aiki ne annabawa). Ko kuma don su (malamai) suna ɗauke da wani abu (ilimi) wanda yake daga wurin Allah wanda aka samu ta hanyar Annabawa. Duk ɓangare biyun sun cancanci girmamawa.

    Malanta wata hanya ce da ta ƙunshi kyautata niyya, tsoron Allah, gwagwarmaya, haƙuri, jajircewa, ladabi da girmama wanda ake neman ilimi wurinsa, dan neman sanin abinda ya shafi addini, wanda ya ke ɗaukan lokaci mai tsawo. Duk mai neman ilimi yana ba da lokacinsa ne gaba ɗaya, ya lizimci malami, ya jajirce, tare da yi wa malami ladabi, da haƙuri ga duk abinda zai iya bijirowa ta ɓangaren malamin ko ta ɓangaren karatun ko yau da gobe.

    Duk wanda ya bi wannan hanyar, bayan wani lokaci ana sa ran ya sami wani abu na ilimi, har ma ya amsa sunan malami. Sanin kowa ne shi ilimi ba a daina nemansa kuma ba a iya ƙure samunsa. Sai dai mutum ya yi iya yinsa kawai. Sannan ba kawai don mutum ya sami ilimi shi ke nan ba, sai an cigaba da bincike, karatu da nazarce nazarce.

    A ƙarni na Sha-shida (16) a Arewacin ƙasar nan, Jami`ar Gobarau da kuma `yandoto ta Katsina sun zamo wurare da suka tara masana a kowani fanni na ilimi wanda manyan malamai daga duk faɗin nahiyar Afrika da ma wasu wuraren suke zuwa dan neman ilimi da ilimantarwa.

    Bayan jihadin Babban Malami, Shehu Usmanu Ɗan Fodiyo, cikin jama`ar Shehun malamin, manyan malamai irin su ƙaninsa, Abdullahi Ibn Muhammad Ibn Fodiyo (Abdullahin Gwandu), Malam Mustapha (Ɗan Tafa), Waziri Ɗan Laima da kuma irinsu ɗan Shehu Usman bin Fodiyo wato Muhammad Bello da ƙanwarsa Nana Asma`u da ɗanta Abdulkadir Ɗan Tafa da sauran manyan malamai sun yi ta ba da gudunmawa wurin karantar da mutane, rubuce rubucen littatafi da ƙasidu na ilimin addini, lugga da sauransu.

    Duk lokacin da aka sami tarin malamai a wuri, ko a lokaci ɗaya, sau da yawa akan sami wata mas`ala ta addini wadda za a iya samun saɓani a tsakanin malamai. Wannan yana faruwa ne sakamakon yawan bincike a kan mas`aloli na addidni daban daban da malamai su ke yi. Sabani ba wani abu ba ne da zai sa a ta-da jijiyar wuya ko a ɗau makami, tun da su masu ilimi ne, toh a ilmance ake komai ta hanyar rubuce rubucen ƙasidu, littattafai da wasiku da fitar da fatawa.

    MISALAI GUDA UKU KAƊAI DAGA MAGABATA.

    Misali na farko shi ne: Lokacin da Turawan mulkin mallaka suka shigo yankin Arewa, Sarakunan mu na musulunci sun ƙi miƙa wuya, kamar yadda turawan suka nema. Da yawa sun zaɓi su yaƙi waɗannan turawan.

    Sarkin Muslumi Attahiru I da sanyin safiyar ranar 15 Maris 1903 bayan an gwabza tsakanin jama`arsa da turawa na kimanin sa`o`i biyu, sai ya fahimci yaƙi da turawan nan babu nasara, saboda a ƙalla an kashe mutane kusan 100 cikin mutanen sa, a ɓangaren turawa ko mutum guda ba a kashe ba, saboda bindigogi na zamani da suke amfani da su a wancan lokacin.

    Ganin haka, ya yanke shawarar yin hijira zuwa gabas, bayan ya yi shawara da wasu daga cikin muƙarrabansa. A ranar 27 Yuli, 1903 aka yi yaƙin ƙarshe a wani gari da ake kira Burmi ranar Juma`a Sarkin Musulmi Attahiru I da kusan mutane 600 suka yi shahada a cikin masallacin juma`a. Wannan jajircewa da Sarkin musulmi da yayi, ɗaya daga cikin sojojin taurawan Ingila William Wallace ya tabbatar da haka.

    Ba tarihin Sarkin Musulmi Attahiru I zan bayar ba, amma ana cikin wannan taƙaddama bayan fitar Sarkin musumi daga birnin Sakkwato ranar 21 Maris, 1903 aka zaɓi Muhammad Ibn Ali Ibn Bello (Attahiru II) a matsayin sarkin Musulmi. A wannan lokacin Wazirin Sokoto Muhammadu Buhari ya nemi fatawa a wurin Alkalin Gwandu Ahmad Bin Sa`id kan maslaha ga musulmi; A miƙa wuya wa turawa, ko a ci gaba da yaƙarsu ko a yi hijira? Wanda wasu suna ganin ba bu wata maslaha da ta wuce a miƙa wuya wa turawa kawai.

    Wannan fatawa ta a miƙa wuya ta samu karɓuwa sosai musamman dalilin takardar da Wazirin Sokoto Muhammadu Buhari ya yi “Risalatil Wazir Ila Ahlil Ilmi Wat Tadabbur” ta yadda suka yi amfani da ilimin usul wurin bayanin hukuncin abinda ya kamata shugabannin musulmi su yi na miƙa wuya da yarda da turawan mulkin mallaka. Akwai waɗanda suka saɓa musu a ra`ayi suma da hujjojinsu, amma cikin rubuce rubuce na ilimi kowa ya fito da hujjarsa, ba hayaniya ko zage –zage da cin mutunci.

    Misali na biyu: Shi ne Lokacin da aka sami taƙaddama kan saka karatun Qur`ani a gidan rediyo a 1955 zuwa 1960 wanda Sheikh Ibrahim Nyass ya ba da fatawar ya halatta a sa karatun Qur`ani a gidan rediyo, shi kuma Sarkin Zazzau Malam Jafaru Ɗan Isyaku ya ba da fatawa sɓanin haka.

    Dukkansu (Sheikh Ibrahim Nyass da Sarkin Zazzau Malam Jafaru Dan Isyaku) kowa ya yi amfani da ilimi mai zurfi na Usulul Fiqh da hujjoji masu ƙarfi wurin bayanin hukuncin wannan mas`ala. Sheikh Ibrahim Nyass ya ba da fatawarsa ne sakamakon tambaya da wasu daga cikin malaman Kano suka yi masa. Sarkin Zazzau Malam Jafaru Ɗan Isyaku ya ba da nasa fatawar ne sakamakon tambayar da Sarkin Kano Malam Muhammadu Sanusi I ya tura masa duk da cewa shi ma Sarkin Kano Malam Muhammadu Sasusi I babban malami ne.

    Abin sha`awa a nan shi ne Shiekh Ibrahim Nyass har wani littafi ya yi wanda aka buga shi a shekaran 1956 a ƙasar Masar mai suna “Alhujja albaligha fi kawn Idha`at alQur`an fir radiyo Sa`igha”. Wannan mas`alar ita ma haka aka ƙarƙareta ta hanyar ilimi ba hayaniya da harigido.

    Misali na uku, a ƙarni na 19, an sami taƙaddama a kan Sadalu da Qabalu a sallah, wannan taƙaddama ta samo asali ne saboda bayyana da yaɗuwar tajdidin ɗarikar Tijjaniya da Sheikh Ibrahim Nyass ya kawo wanda kafin zuwan wannan tajdidi, ɗarikar Ƙadiriyya ita ce aka fi sani kuma ta fi daɗewa a ƙasar Hausa tun bayan jihadi.

    Malaman ɗarikar Kadiriyya sun tafi a kan sadalu cikin sallah. Sheikh Ibrahim Nyass da wasu malamai a Kano suka zo suka warware wancan fahimta ta sadalu da hujjoji. Wannan ya sa `yan Kadiriyya suke ganin `yan Tijjaniya sun zo da wani sabon abu har aka riƙa kiran `yan Tijjaniya masu bin wannan fatawar da “`Yan Ƙabalu”

    Shehunan malamai irin su Malam Muhammadu Salga (r. 1938), Malam Tijjani Usman Zagon Barebari (r.1970), Malam Shehu Maihula (r1988) da sauransu sun yi rubuce rubuce dan tabbatar da ingancin yin ƙabalu a sallah. A ɗayan ɓangaren na Qadiriyya wanda Malam Nasiru Kabara ya ke jagoranta sun yi na su rubuce rubuce kan ingancin yin sadalu a sallah.

    A nan ma wani abin sha`awa, shi ne duk rubuce rubuce na ilimi aka rinƙa yi, har yau waɗannan rubuce-rubuce suna nan. An sami irin wannan taƙaddama ta faru a sokoto har Malam Abubakar Atiku Gwandu (r. 1913) ya rubuta wani littafi mai Irshad al-ikhwan ila bayan hukm as-salat bis-sadlu wa al-kablu.

    A kwai misalai masu yawa kan taƙaddama ko saɓani da ake samu tsakanin malamai tun tuni, amma abin zai birge ka idan ka kalli hanyar da ake bi wurin bayyana ra`ayi da hujjoji da fito da komai fili, hanya ce ta rubuce rubuce na ilimi, ba soki burutsu da hauragiya da shirme ba. Kuma malamai su suke kayansu ba kowani kare da doki ba. Hargowa da hayaniya da shiga fagen ilimi daga ko wani kare da doki ya samu asali ne dalilin yaɗuwar hanyoyin sada zumunta.

    Wanda shi ne za mu tattauna a rubutu na gaba.

    Rabiu Musa Adam

    Whatsapp: 08039290267

    September 12, 2025

    Karanta Ayyukan Ta’addancin Matasa A Kano: Aure, Yawan Haihuwa Da Tarbiyya A Wata Mahanga

    Edita@rumasau-kallamu

  • Mijin Marigayiya Babi Na Huɗu

    Mijin Marigayiya Babi Na Huɗu

    Da farko Khadeeja ta yi tunanin idan ta sami ciki Mustapha zai yi ɗoki kuma ya ba ta kulawa ta musamman kamar ko wacce amarya, sai dai ga mamakinta hakan ba ya samuwa. Wani lokacin ma sai ta ga kamar bai san ma tana da ciki ba ko kuma ba da son ransa ta sami cikin ba; halin ko in kula ɗin da yake nuna mata ya yi yawa.

    Tunda aka saka lockdown sai ya zamana kullum suna gida ita da shi da yara, ta so sosai ta je gida ta wuni kafin a kulle garin amma ba ta sami dama ba. Duk da haka kullum sai sun yi waya da Mommy da Yaya Mama; don tun satin da za a fara lockdown su Nabila suka zo mata wuni da suka je gida suka gaya wa Mommy ciki ne da ita. Don haka kullum da safe sai ta kirawota ta duba ta.

    Hayaniyar da su Afaf suke yi a gidan ba kaɗan ba ce don haka idan gari ya waye ko gyangyaɗi ba ta samu ta yi; ko ta fara baccin ma haka za a yi wata hayaniyar a tashe ta. Ba ta gane yanayin da jikinta yake ciki, ita dai kawai ta san tana shan wahala. Kullum jikinta babu ƙwari ga shi ba ta son cin abinci, ga shi kullum cikin jin bacci take. Ga hidimar yara, wadda duk ranar da ta nuna ba za ta iya ba haka Mustapha zai yi ta ƙunci yana kin kula ta.

    Haka take dagewa ta yi duk wani abu da ya kamata. Kullum wuni suke kallon TV saboda ana samun wuta sosai, idan dare ya yi kuma Abbansu ya tada inji su cigaba da kallo. Ita dai ba ta isa ta canza channel ba don da ta canza za a fara kuka wanda ba ta son ji sanna kuma a take ubansu zai fito ya yi magana. Ta gaji da zaman haka barkatai don haka ta daure take saka yaran a gaba su yi karatun kur’ani.

    Da safe a jagwale take tashi don haka ta san ba za ta iya da safe ba. Amma kullum bayan sallar azahar idan sun ci abincin rana sai ta kashe TV ɗin kowa ya ɗauki kur’ani ta biya masa. Nasreen ce kawai ba ta son zama don haka sai Khadeeja ta ƙyale ta saboda a halin yanzu ba za ta iya ba. Amma har Shukra ake biyawa karatun.

    Duk wani motsinsu idonsa a kai, da zarar ya ji wata hayaniya ko ya ji su shiru zai leƙo ya duba. Kullum yana kwance yana faman latsa waya. Yau ma haka suka tashi tun asuba suke ta guje-guje, TV kuma dama tana kunne don da zarar wani ya kashe ta za a yi ƙorafi. Shinkafa da wake ta dafa da manja da yaji; bayan sun gama cin abinci kowa ya yi Sallah ta saka su a gaba kowa da kur’aninsa. Sai da suka yi tilawa sannan ta ƙarawa kowa aya biyar amma banda Nasreen.

    Ba za ta iya surutu ba saboda yanayin jikinta da kuma yanda yawu yake yawan taruwa a bakinta, sannan kuma idan ta ɗaga murya tana mata faɗa Abbansu ba ya so. Don haka sai ta ƙyaleta, suna zaune gaba ɗayansu sun kewaye Khadeeja suna karatu, har da Shukra; amma Nasreen tana zaune a kan kujera ta zuba kayan wasa a gaba tana yi wa ‘yar tsanarta kitso.

    Shiru ya ji sai muryoyinsu kaɗan-kaɗan suna karatu don haka ya taso ya fito parlor ɗin. Ya kare musu kallo sannan ya sami waje ya kwanta a kan 3-seater. Ya dubi Khadijan yace ‘Ita Nasreen ba a biya mata karatun?’ ‘Tace sai ta gama yi wa ‘yar tsanarta kitso.’ ta ba shi amsa ba tare da ta dube shi ba. Nasreen tace ‘Na ma iya karatun Abba, kitson nan nake so na gama tukunna.’

    Ya yi dariya ya cigaba da danna wayarsa. Bayan sun gama karatun ta koma ɗaki ta kwanta su kuma suka cigaba da kallonsu na TV.

    A kwance take a gefen gadon da alawar tomtom a bakinta saboda yawu, ya zauna a kan kujera. Ta juyo ta kalle shi ta koma ta cigaba da kwanciyarta don ba ta son magana. Jimawa kaɗan ya kirawo sunanta, ta amsa sannan ta juyo. Ya kalle ta yace ‘Wai me yasa bakwa karatun ne da Nasreen?’ Tace ‘Bata so ne, ni kuma ba daɗi nake ji ba shi yasa ba zan iya surutu da ita ba kawai na kyale ta.’

    ‘Ya kamata idan ma wani abu kika saka a ranki game da Nasreen ki cire, duk abinda za ki yi wa yaran nan ki yi musu gaba ɗaya kuma ki yi musu adalci. Ina kula komai za ki yi sai ki ƙyale Nasreen, idan banda haka ya za a yi a ce Shukra ma da ba ta shiga islamiyya ba kina biya mata karatun amma ita Nasreen kin yi banza da ita.’

    Tun da ya fara zancen ta miƙe ta zauna a kan gadon tana kallonsa, maganganun da take so ta faɗa masa suna da yawa sai dai tana buɗe bakinta yawu ya cika bakin. Ta taune ‘yar guntuwar tomtom ɗin ta haɗiye da ƙyar, ta taɓe baki ta kawar da kai kawai tace ‘Ka yi hakuri za a gyara.’ ‘Ya kamata dai ki dinga yi musu adalci don dukansu ‘yayana ne.’ ya faɗa.

    Ta zame ta kwanta zuciyarta har turiri take saboda takaici; shi yake hanata takurawa Nasreen, shi yake nuna ba ya son a dinga yi musu faɗa amma kuma yanzu yana mata maganar ba a karatu da ita. To ya za ta yi da ita? Ita adalci ne wannan yake mata da zai ce ta dinga yi wa ‘yayansa adalci? Ta share ƙwallar da ta gangaro a idonta tayi ƙwafa. Jimawa kaɗan ya tashi ya fice daga dakin.

    Wannan wunin da kowa yake yi a gida ba ƙaramin takurawa Khadeeja yake yi ba; tana cikin laulayi sannan ga hidimar gida da ta yara. Wuni suke cin abinci don haka gidan kullum kaca-kaca ga wanke-wanke ba ya yankewa. Wasu lokutan tana samu ta ɗan gyara amma wasu lokutan haka take ƙyalewa saboda ba za ta iya ba.

    Yau kwana biyu kenan dan almajiri da ta ɗauka yake zuwa ya yi mata wanke-wanke da sharar tsakar gida bai zo ba; ba ta sani ba ko suma lockdown ɗin ya shafe su don da dai suna fitowa tunda makarantarsu nan cikin unguwa take. Gidan gaba ɗaya yayi kaca-kaca don kitchen har warin lalatacce abinci yake yi.

    Suna gama cin abincin safe Abbansu ya miƙe ya shige ɗaki. Nan da nan ta saka yaran a gaba suka taya ta suka fitar da wanke-wanken suka kai fanfon waje, ta turasu waje ta gyara cikin gidan tsaf. Tana yi tana hutawa tana tofar da yawu, zuwa ƙarfe goma na safe ta gama.

    Ta fito tsakar gidan ta tara yaran a waje ɗaya, ta dube su tace ‘Afaf mu je fanfo ni da ke mu wanke kwanukan can, kai kuma Yaya Habib ɗauki tsintsiya ka share compound ɗin nan, ka fara daga kan baranda. Nasreen da ke da Shukra ku tsince toys ɗinku ku zuba a kwando, duk wadda ba ta tsince ba ba zan ba ta sweet ba.’

    Nan da nan kowa ya fara aiki. Ta saka kujera a bakin famfo tana wanke kwanukan Afaf tana mata ɗauraya. Sai da suka cika ƙaramin kwando da kwanukan ta kirawo Habib wanda ya kusa gama sharar tace ‘Ya Habib zo ka ɗauki wannan kwandon ka kai kitchen ka kwashe kwanukan a kan sink sai ka dawo da kwandon mu cigaba da zubawa.’

    Ya ɗauka a nufi cikin gidan; a kan baranda suka ci karo da Abbansu yana fitowa. Ya ɗan ja baya don ya ba wa Abban hanya ‘Kai ina za ka da kwanuka haka.’ ‘Anti ce ta wanke zan kai mata cikin gida.’ Yana ɗaga kansa ya hango Afaf a tsakiyar kwanuka suna ta wanke-wanke ita da Khadeejan. A fusace ya ƙarasa wajen, cikin tsawa yace ‘Ke Afaf me kike a nan? kalli yanda kike jiƙa jikinki sai kin gama ki yi ta mura.’ Ya dubi Khadeeja yace ‘Ina yaron naki?’

    Ta tofar da yawun bakinta a gefe sannan tace ‘Kwana biyu bai zo ba, ni ma ban san dalili ba.’ Ya dubi Afaf wadda ta cigaba da aikinta ba tare da ta kula da shi ba, ya daka mata tsawa yace ‘Ki fita daga cikin ruwan nan nace, me kika iya? Sai sanyi ya kama ki kina ta faman jiƙa jiki. Fice ki je ki canza kaya kuma kada ki sake fitowa nan.’Ta dube shi tace ‘Kwanukan ne da yawa, ni ɗin kuma ba daɗi nake ji ba idan muka gama gaba ɗaya za ta canza kayan ai.’

    Habib ya ƙaraso ya ajiye kwandon yana cewa ‘Anti ga shi.’ Ya juya ya cigaba da shararsa. Abbansu ya sake dakawa Afaf tsawa don haka ta fice daga wajen wanke-wanken ta shige gida. Har ya buɗe baki zai cigaba da magana ya hango Habib yana kwashe shara ‘Kai Habib wa ya saka sharar nan?’ Yace ‘Anti ce Abba, ai na ma gama kwashewa zan yi.’

    ‘Ajiye tsintsiyar nan ka shige cikin gida ka ba ni waje.’ ya faɗa a fusace. Ya jefar da tsintsiyar ya shige gidan. Ya juya kan Khadeejan wadda take cigaba da wanke-wankenta yace ‘Wai me kika mayar da yaran nan ne? Habib ne zai iya share wannan tsakar gidan ga ƙura ga komai. Ita ma Afaf ɗin wannan uban ruwan ai sai ta yi mura. Ke kika ce a bar mai aikinki ta tafi gida, da kin bari ai da yanzu tana nan; sannan kuma ki dinga ba su aikin da ya fi ƙarfinsu?

    Ba na son irin wannan; ba na son ki dinga yi wa yaran nan kallon wasu manya, ki ɗauke su kamar ke kika haife su shi ne za ki iya yi musu adalci. Idan an ji wani almajirin yana bara sai a kirawo shi ya ƙarasa wannan aikin ko kuma tunda kun kusan gamawa ki ƙarasa zuwa gobe a sami wani almajirin.’ Ko kallonsa ba ta yi ba ta cigaba da wanke-wankenta, ya ja tsaki ya juya ya nufi cikin gidan.

    Ta share hawayenta ta cigaba da wanke-wankenta. Ba za ta iya dogon surutu ba sannan kuma ba ta son tana biye masa suna faɗa a gaban yara, ita yanzu duk wani abu da zai sa a yi magana ma ba ta so; shi yasa ta gwammace ta yi masa shiru. Sai da ta gama wanke-wanken nan tsaf sannan ta kwashe sharar, ta ɗebi kwanukan ta shigar cikin gida.

    Suna zaune a parlor suna kallon TV. Tana kitchen ɗin tana kife kwanukan Afaf ta shigo ta same ta, ta ɗauki kwanukan ta fara kifewa. Ta dube ta tace ‘Afaf je ki zauna ai na kusa gamawa.’ Tace ‘Bari na taya ki Anti, ai nan babu ruwa.’ Ba don ta so ba ta ƙyale ta sai da suka kife kwanukan gaba ɗaya ta mayar da komai inda yake sannan ta wuce ɗaki su kuma suka cigaba da kallonsu. Can wajen 1pm bayan sun yi sallar azahar ta fito daga ɗaki ta shiga kitchen; tuwon alkama da miyar ɗanyar kuɓewa ta dafa jiya da daddare amma duk sai suka ƙi ci.

    Da yake akwai biscuits da cake sai kowa ya ci ya sha lemo, ita da abbansu ne kawai suka ci tuwon ga shi ta dafa shi da yawa. Da safe kuma da kwaɗayi ta tashi don haka wainar fulawa ta soya kowa ya ci. Wannan ragowar tuwon shi ta ɗauko daga fridge ta ɗumama shi, ta ɗumama miyar wadda ta sha kaza da nama. Ta zuba wa kowa abincinsa sannan ta kirawosu kowa ya ɗauki nasa suka zauna a table.

    Kallon tuwon kawai Habib yake yi yana juya shi amma ya ƙi ya fara ci, tana kallonsa ta yi banza da shi ta cigaba da kai lomarta tana ba wa Shukra don ita tuwon ya yi mata daɗi. Jimawa kaɗan ya dube ta yace ‘Anti tuwon jiya ne fa?’ ‘Eh, shi ne, ko ci ko bari.’ ta faɗa a gajarce ta ci gaba da cin abincinta.

    Daidai nan Abbansu ya fito ya zauna a table ɗin, ta tura masa flask da plate. Ya buɗe flask ɗin ya kalli fuskokin yaran sannan ya kalle ta yace ‘Wannan ai tuwon jiya ne, ba a yi abincin ranar ba ne?’ ‘Shi ne abincin ranar ai, ɗumamawa aka yi tunda babu abinda ya yi.’ Nasreen wadda ita ma take ta juya nata tuwon tace ‘Abba wallahi tuwon ba daɗi, ni bana son baƙin tuwo gaskiya.’

    Shi ɗin yana son tuwon alkama don shi ne ma ya sa aka yi tuwon da daddare, don haka ya zuba malmala guda ya fara ci. Ya sake duban fuskokin yaran, bayan ya haɗiye lomar da take bakinsa yace ‘Yanzu ba wani abu da za a iya dafawa yaran nan, Afaf ce kawai take cin tuwon nan.’ Ba tare da ta kalle shi ba tace ‘Babu.’

    Ta cigaba da cin tuwonta kamar ba ta san da su ba a wajen. Jimawa kaɗan Nasreen tace ‘Abba ni a haɗa min cornflakes.’ Ya dubi Khadeeja yace ‘Akwai cornflakes ko?’ Cikin halin ki in kula tace ‘Akwai.’ ‘Da Allah a haɗa mata ta samu ta ci kafin a yi abincin dare.’ Tace ‘To.’ Ta ci gaba da cin tuwonta tana ba wa Shukra a baki, yayin da ita kuma Nasreen ta tashi ta koma gaban TV.

    Jimawa kaɗan Habib ma ya mike, ya ɗauki kwanonsa da na Nasreen yana cewa ‘Abba ni ma na sha cornflakes ɗin kawai. ’Ya wuce ya kai kwanukan kitchen ya dawo shi ma ya zauna a gaban TV. Bai daɗe da tashi ba kuma ita ma Khadeejan ta gama cin nata tuwon, ta ɗauke kwanonta ta kai kitchen. Ta fito daga kitchen ɗin ta wuce ɗaki ba tare da ta kalle su ba. Tana shiga ta saka pillow ta kwanta a tsakiyar gadonta, da yake ta gaji sannan kuma ta koshi tana rufe ido bacci ya kwashe ta.

    Ba ta sani ba ko ta daɗe da kwanciya ko ba ta daɗe ba, kamar a mafarki ta ji Mustapha yana ɗan buga ƙafarta yana cewa ‘Khadeeja, Khadeeja, barci ma kike yi? Kin bar yara da yunwa fa ki zo ki haɗa musu cornflakes ko ki dafa musu indomie.’ Ta ɗan janye kafarta tana ƙoƙarin tashi; kafin aurensu fa ba ya kiran sunanta sai dai yace ‘yan mata, mekyau ko kuma yace babe.

    Ta yi zaton idan sun yi aure next level za su shiga a ƙara mata matsayi amma za ta iya cewa tunda ta shigo gidan nan sau ɗaya ya kirawota da babe a daren da suka tare. Yanzu kam ya ci dubu sai ceto don gatsal yake kiranta Khadeeja. Ta gyara zama tace ‘Me kake cewa?’

    ‘Ba ki ba wa yara abinci ba kin zo kin kama bacci.’ Tana jijjiga kai tace ‘Kowa fa na ba shi abinci ba ka gani ba ne?’ ‘Habib da Nasreen nake magana fa.’ ‘Oh, ba sun ce cornflakes za su sha ba, ai akwai a kitchen ɗin.’ ta faɗa tana ƙoƙarin kwanciya. ‘To ai sai ki zo ki haɗa musu ko?’ Ta gyara kwanciyarta a cewa ‘Wallahi babe na gaji, idan ban yi baccin nan ba ko abincin dare ba lallai na iya dafawa ba.

    Su je su haɗa cornflakes ɗin mana ko su ci tuwon da kowa ya ci.’ ‘Ya ina miki magana kina kwanciya Khadeeja, haka za ki bar min yara da yunwa.’ ya faɗa a fusace. Ta gyara kwanciyarta ta yi banza da shi. ‘Ina miki magana kina ji na fa Khadeeja bana son wulaƙanci.’ Ta tashi zaune, lokacin ya riga ya miƙe tsaye. Ta gyara zama tace ‘To me zan ce maka?’ ‘Ba za ki zo ki haɗa musu cornflakes ɗin ba kenan?’

    ‘Haɗa cornflakes ɗin ba wani aiki ba ne shi yasa nace su haɗa kawai, wallahi kaina ciwo yake.’ Ta ture abinda ta rufa da shi ta sauko daga kan gadon ta wuce banɗaki saboda yanda bakinta ya cika da yawu, ta mako kofar banɗakin ta tsaya a gaban sink; wallahi babu wani abinci da za ta haɗa sai dai ya yi duk abinda zai yi. Tana ji Nasreen ta leƙo tace ‘Abba yunwa nake ji.’

    Ya ja tsaki ya kama hannun Nasreen suka fice daga ɗakin bayan ya maka mata kofar a fusace. Haka ya je ya haɗawa yaran cornflakes ɗin suka zauna suka ci. Tun da ya haɗa musu cornflakes ɗin nan kuma sai ya shiga share Khadeeja, gaba ɗaya ya ƙi kula ta ko zama inda take. Ta kula da hakan don haka ita ma sai ta ja jikinta, domin ba ta cikin yanayin ma da zata iya saurarensa.

    Ko da dare ya yi ma har ta kwanta a ɗakinta sai kuma ta ga rashin dacewar hakan, tunda dai bai kore ta ba kuma ita ba fushi take yi da shi ba shi kaɗai yake fushinsa. Don haka bayan ta kwantar da yara sai ta shirya ta wuce ɗakinsa ta kwanta. Can wajen sha biyun dare motsin shigowarsa ya tashe ta, yana tsaye a gaban wardrobe yana saka kayan bacci. Ta sauko daga kan gadon ta wuce banɗaki don ta yi fitsari ta kuskure baki.

    Tana fitowa ta wuce ta kwanta, ta kalle shi yana zaune a gefen gadon yana dannan waya; so take ta ce masa “good night Babe” kamar yanda ta saba amma bakinta ya ƙi furtawa saboda yanda take cike da haushinsa. Don haka sai kawai ta juya masa baya ta kwanta. Kamar wanda yake jira ta kwanta sai ya gyara zama a kan gadon yace ‘Tashi mu yi magana Khadeeja.’

    Ta juyo ta kalle shi sannan ta tashi zaune ta jingine da jikin gadon; tana baƙin cikin yanda yake kiranta Khadeeja gatsal sai kace shi ya yanka mata ragon suna. Bayan ta zauna ya ƙara tsuke fuska sannan yace ‘Bana son yanda kike yi min taurin kai da neman kawo min raini a gaban yara, idan ma wani abu ne a ranki gara ki fito ki gaya min.’ Da mamaki take kallonsa don gaba ɗaya ma ta manta me ya kawo wannan maganar; ta yi zaton ma zai tambaye ta dalilin da yasa ba ta ci abincin dare ba ne domin taliya ta dafa kuma ta kasa ci don haka ruwa kawai ta sha ta kwanta.

    Ta yi murmushin yake tace ‘To, sai dai ban san lokacin da na yi maka taurin kan ba.’ ‘Dazu nace ki haɗawa Habib da Nasreen cornflakes kin ƙi, nan kika shige banɗaki kika bar ni a tsaye ina miki magana.’ Ta kalle shi suka haɗa ido ta kura masa ido har sai da shi ya kawar da kansa, ta buɗe bakinta wanda ya fara tara yawu tace ‘To in sha Allah zan kiyaye, amma ni ma don Allah ka dinga sauƙaƙamin rayuwa a gidan nan. Idan ba ka yi min saboda ƙauna ba to ka yi min saboda yanayin da nake ciki tunda ni ma ba lafiya ce ta ishe ni ba duk abinda ka ga ina yi daurewa nake yi.’

    Ya ɗan fara saukowa yace ‘Duk don na nema miki sauƙin ne ai nace a kawo mai aiki, kuma da ta dawo za ta cigaba da taya ki. Ita ma mahaifiyarsu haka take kula da su ko da kuwa tana da ciki don wannan ba wani abu ba ne a wajen macen da ta san me take yi. Bana son ki dinga yi musu abubuwan da za su ji maraicin uwarsu, ki riƙe su kamar ke kika haife su. Shi ne abinda zai samar da zaman lafiya tsakanin mu.’

    Ta gyaɗa kai tana kallonsa cike da tsananin mamaki tace ‘To.’ Ta sauka daga kan gadon ta shiga banɗaki ta tofar da yawun bakinta ta ɗaurayo bakinta ta fito ta kwanta bayan ta kashe fitila. Tana kwanciya hawaye ya fara bin idonta; wannan wace irin rayuwa ce? Wai dama haka ake aure ko kuwa ita ce ba ta dace ba? Shikenan shi da ‘yayansa ne kawai mutane? Ƙiri-ƙiri sai a ƙirƙiri laifi a ɗora mata kuma a saka ta ba da haƙuri.

    Da ya bar ta da yaran tabbas ta yi niyyar ta riƙe su kamar ita ta haife su, domin har addu’a take yi kada Allah ya ba ta ikon cutar da su. Sai dai zuwa yanzu gaba ɗaya sun fice daga ranta, duk wata ƙauna da ta tana da don ta nuna musu ba ta jin za ta iya tunda ga dukkan alamu ma ba zai bar ta ba. Shi ba so yake ta nuna musu ƙauna ba so yake kawai ta bauta musu, ba ta jin za ta iya hakan kuwa.

    Karanta Mijin Marigayiya Babi Na Uku

    Edita@rumasau-kallamu

  • Yadda Ake Addu’ar Razana A Cikin Barci

    Yadda Ake Addu’ar Razana A Cikin Barci

    Addu’ar wanda ya razana a cikin barci, da wanda ya kasa barci

    أَعُوْذُ بِكَلِمَاتِ اللهِ التّامَّاتِ مِنْ غَضَبِهِ وَعِقَابِهِ ، وَشَرِّ عِبَادِهِ ، وَمِنْ هَمَزَاتِ الشَّيَاطِينِ وَأَنْ يَحْضُرُون

    A’uzu bikalimaatil lahit tammati min gadabihi wa’iƙabihi, wa sharri ibadihi,wa min hamazaatish shayaɗeen wa’ayyahdurun

    Ina neman tsari da Kalmomin Allah cikakku daga fushinsa, da uƙubarsa, da sharrin bayinsa da kuma zungure-zunguren shaiɗanu, da su halarto ni (a cikin al’amurana).

    Karanta Yadda Ake Addu’ar Cire Tufafi

    Edita @rumasau-kallamu

  • Yadda Tsiron Mahaifa Yake (UTERINE FIBROIDS)

    Yadda Tsiron Mahaifa Yake (UTERINE FIBROIDS)

    Wannan wani tsiro ne dakan fito a jikin mahaifar mace inda jariri ke zama ya rayu lokacin goyon ciki. Tsiron na iya kasancewa a kowanne sashi na cikin mahaifa.

    ME KE KAWO SHI?

    Babu takamaiman abinda aka san yana jawo hia domin ɓangaren da yaso ya fito kurum ake gani ya fara tsirowa yana girma a karan kansa, sai dai hakan bai faruwa sai jikin matan da jikinsu ke fitar da sinadarin Estrogen da Progesterone da yawa. Sannan yana kama matan da ke cikin lokacin hayayyafa wato bearing Age daga shekara 15 zuwa 49.

    ALAMOMIN FIBROIDS

    Alamomin sun ƙunshi;

    1- Ganin fitar jinin haila da yawa.

    2- Nauyin bayan gida wajen tsuguno ake yi da kyar.

    3- Yawan fitsari

    4- Ciwon baya ko ciwon ƙafafu

    5- Zafin fitsari a riƙa yin shi yana fita a wahalce.

    6- Ciwon ƙugu ko kwankwaso

    7- Aga jinin haila ya ci gaba da zuwa fiye da sati

    8- Ciwon mara a kai a kai tare da cewa an san ba lokacin zuwan jinin al’ada ba ne,

    9- Jinkirin haihuwa

    10- Yawan ɓari

    11- Jin zafi yayin saduwa.

    SHAWARA

    Haƙiƙa duba da duk waɗancan alamomin ya kamata a fahimci lallai akwai level ɗin da in ya kai matsalolin da macen za ta ke fuskata ba za ta iya jurewa ba. Don haka akan duba a asibiti a ga a wanne ɓangare ya fito da yanayinsa.

    Lallai duk macen da ke fuskantar da yawa daga alamun da na lissafa kar tai wasa da lafiya ta je a duba ta. Idan an taɓa duba ki an tabbatar kina da shi to zama haka bai dace ba domin da yawa ba ya barin ciki ya zauna jikin mace ko da an samu ya shiga, ga yawan ciwon ciki, sannan fitar jinin al’ada da yawa ka iya sawa ki rasa jini ki haɗu da anaemia wato ƙarancin jini.

    MAGANIN MATSALAR

    Akwai magani da ake bayarwa domin jiki ya rage fitar da sinadarin da ke sa girmansa wato estrogen da progesterone inda zai motse toh fa sai dai maganin ba ya ga yasa fibroids ɗin ya motse yakan haifarwa mace da complications na bushewar gaba domin sinadarin da jikin ya dena samarwa na da mahimmanci, yana kuma haddasa dena ganin jinin al’ada sam, yana kuma iya haddasa zagwanyewar ɓargon jiki ya zamto ta riƙa Jin ƙafafunta kamar ba nata ba kuma abu kaɗan na iya sa ta karye (osteoporosis).

    SURGERY

    Sannan in aiki ya kama ai shi ma ya bambanta akwai wanda in gefe fibroids ɗin yake ake iya yanka saman marar mace kaɗan a yi amfani da device a soki jikin fibroids ɗin domin sa shi ya motse, ko ta hanyar datse jijiyoyin jinin da ke zuwa ma fibroids ɗin, ko ta hanyar yin aiki cikin mahaifar a cire fibroids ɗin.

    Amma sahihiyar hanyar rabuwa da shi dungurungun shi ne ta hanyar cire mahaifar mace baki ɗaya to amma wannan in mace na da son haihuwa ta tara ‘ya’ya ko in ma ba ta taɓa haihuwa ba kin ga ba zaɓi ba ne. Sai dai a bi sauran hanyoyin.

    Sannan fibroids a karan kansa yake fitowa musamman in jikin mace na samar da sinadarin estrogen da progesterone sosai don haka being ne ba cancer ba ne amma kuma daga baya ka iya haifar da Mummunan illa wacce ka iya taimakawa cervix cancer samun damar kama mace.

    Karanta Sunayen Wasu Kayan Abinci Da Itatuwa Da Turanci

    Edita@rumasau-kallamu